Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 10
marwan kakan zuhairu ya yi musu addu’a ta fatan samun nasara sannan suka yi sallama suka kama hanyar birnin Bahazum. Da isar su Birni suka wuce fadar sarki shaiban, suka tarar da an shirya wasu manya jarumai cikin shirin yaqi, su kimanin mutum arba’in da za su yi musu rakiya cikin tafiyar da za su yi, zuhairu ya sauka daga kan dokinsa ya tafi gaban sarki ya kai gaisuwa sarki ya amsa masa sannan ya ce da shi “Allah ya baka nasara na gama shiri dan yin tafiya bisa ga alqawarin da na xauka, na neman Gimbiya Hasima duk inda take a faxin duniya”. Sarki shiaban ya ce da shi “Na shirya wasu jarumai da za su yi maka rakiya adadin mutum arba’in daga cikinsu akwai mutum goma qwararu a fagen iya harbi da kibiya sannan akwai 61 BAKAR GUGUWA wasu mutum goma da suka qware wajen faxa da mashi, sai kuma mutum goma masu iya jifa da majaujawa, sai mutum goma na qarshe sune qwararu a fagen iya faxa da takobi waxannan sune adadin mutum arba’in Allah ya baku nasara cikin tafiyar da za ku yi”. Zuhairu ya yi godiya sanann sarki shaiban ya sa aka yi musu addu’a ta fatan samun nasara ya kuma umarci baradan da za su yiwa zuhairu rakiya su kasance ma su yi masa biyayya a matsayin shugabansu har su je su dawo, daga nan suka yi sallama da sarki aka yi musu rakiya zuwa bayan gari suka kama hanya suka ci gaba da tafiya. Buniyatu tana gaba don yi musu jagora zuwa bigiren da suke zaune tare da yayanta matsafi Bahalu, don xauko rubutaccen saqon wanda zai shiryar da su hanyar da za ta kaisu lardin Ashtar inda fadar da matsafi Bahalu ya tafi da Gimbiya Hasima take. Kwanci tashi suna tafiya cikin wannan daji tun daga ranar da suka baro gida, har suka shafe kwanaki ashirin daga cikin kwanaki arba’in da za su yi kafin su isa bigiren da Buniyatu suke zaune a cikinsa, sukan yi tafiya daga bayan ketowar alfijir har zuwa faxuwar rana sallah da cin abinci ne kawai yake tsayar da su sai dare ya yi su yada zango don su kwana kafin gari ya waye su ci gaba da tafiya. A rana ta ashirin da xaya daga cikin ranakun tafiyarsu da la’asar sakaliya suna tsakiyar tafiya sai suka hangi wasu rundunar mahaya cikin shirin yaqi suna xauke da tutoci irin na mabiya addinin bautar rana, su zuhairu suka yi nufin su ratse musu su ci gaba da tafiya, don kada baradan su tsayar da su su vata musu lokaci cikin tafiyar da suke yi, amma sai waxannan ayarin baradan suka hangesu suka kan su suka tsayar da su, xaya daga cikin 62 BAKAR GUGUWA baradan wanda kuma shi ne babbansu ya dubi zuhairu yace da su. “Kai waxannan matafiya daga ina kuke kuma ku jama’ar wane birnine da inda kuka nufa? Sannan nina labarin dukiya da guzuri da kuke tare da shi. Ku yi gaggawar miqoshi garemu don a yanzu kun zama ribatattu a garemu ababen tafiya da ku ya zuwa birninmu don kaiwa sarkinmu ku zama bayi, kamar yadda mukan yi ga duk jama’ar da muka haxu da su wannan daji cikin tafiyar da muke yi” Zuhairu yace da shi. “Ba ma tare da wata dukiya ko guzuri da zamu baku bisa ga buqatarku, cewa dai mu mun kasance matafiya ne cikin wata buqata da take tare da mu,kuma bamu fito dan yin faxa da kowa ba sai don tunkarar abinda muka sa a gaba saboda haka muna neman afuwa a gareku, ku bamu hanya mu wuce ya zuwa inda muka nufa” Wanda ya fara magana ya dubi zuhairu yace da shi “Kai dattijo ma’abocin rauni da gazawa ka sani cewa ba za ku kuvuta daga hannunmu ba har sai kun zama ribatattu a garemu, don na ga alama kun kasance daga cikin mabiya addinin musulunci ba masu bauta ga rana ba, za mu tafi da ku ya zuwa birninmu don mu bautar da ku kamar yadda muke bautar da duk wanda bai zamo daga jinsinmu ba kuma baya bauta ga rana abar bautawa ta gaskiya, to kuwa sunansa bawa a garemu kuma ya halatta mu bautar da shi ko mu halakashi mu shayar da jininsa ga rana abar bautawarmu bisa ga tsarin addininmu” Zuhairu ya fusata da jin maganar wannan mutum ya ce da shi, “Kaicon rayuwarka da abinda kake ambatawa cikin zantukanka masu munin ambato, Allah wadai da miyagun kalamanka na zalunci da ke bayyana tsantsar shirka da vata 63 BAKAR GUGUWA mabayyani na bauta ga rana abar halitta, kuna shayar da jini gareta ka sani cewar halaka ta tabbata gareka da rundunar baradan da kake jagoranta sababin abinda kake aikatawa na zalunci a doron qasa, don shafe ruhinka daga bayan qasa shi ne mafi alkairi ga sauran jama’ar musulmi”. Barden nan ya bushe da dariya saboda jin abinda zuhairu yace sannan ya dubeshi yace da shi “Kai dattijo ma’abocin rauni da gazawa saurara ga ambaton waxannan kalamai naka da kake ambatawa, ka bari matasa masu ragowar jini a jiki da jarumta su yi magana, ba kai dattijo ma’abocin rauni dan haka ko ku miqa wuya garemu ko mu tursasaku ga aikata abinda muka umarceku ta hanyar qarfi da tsananin yawanmu”. Zuhairu ya zare takobinsa ya fita gaban rundunar baradan yace da su “Ba zamu zama masu tsoro ko karaya da ganin yawan rundunarku da ku ke alfahari da ita ba, don Allah da muka yi imani da shi muke bauta masa zai iya bamu nasara akan ku koda kun fi yawan adadin qasa, don haka idan da mai qarar kwana ya fara fitowa gareni ya ga yadda zan aika da ruhinsa barzahu, idan kuma kun qi fitowa ni na gabata cikinku na hau ku da sara da kisa irin na qare dangi, har sai na tarwatsa rundunarku na sanyaku nadamar halittarku a bayan qasa da abinda kuke aikatawa”. Jarumi nan ya sake bushewa da dariya lokaci guda kuma sai ya turvune fuska, irin na mugunta da zalunci ya dubi zuhairu yace da shi “Ban zamo daga cikin mutane masu imani da zan ji tausayin tsufanka ba na qyaleka ba, tunda har kana jin ka isa jarumi bari ni na halakaka da kaina, don ya zama izina ga sauran jama’ar da ke tare da kai” Ya zare takobinsa ya taho 64 BAKAR GUGUWA ga zuhairu sai kuma ya sake shawara ya maida takobinsa yana mai faxin cewa “Ai halaka ka da takobi ma nuna rashin jarumta ne, da gazawa don kuwa iskar gudun dokina kaxai ta isa waftoka daga kan dokinka ka faxo qasa ka halaka”. Kafin ya gama magana zuhairu ya fusata ya xaga takobinsa ya kai masa sara, jarumin ya yi sauri ya sanya wata garkuwa ta baqin qarfe ya kare saran, kaifin takobin zuhairu ya keta garkuwa gida biyu ta tarwatse, jarumin ya yi baya tagataga kamar za su faxi daga shi da dokinsa da qyar dokin ya tirje ya tsaya saboda qarfin saran da zuhairu ya kai masa irin na sadaukantaka, jarumin nan ya dubi zuhairu cikin tsananin mamaki kafin ya qare mamakinsa zuhairu ya sake kai masa wani saran cikin qarfin zuciya da zafin nama jarumin ya yi sauri ya zare takobinsa ya kare saran, a wannan karon ma sai da ya sake yin baya kamar zai faxo daga kan dokinsa saboda qarfin saran. Zuhairu bai saurara masa ba ya ci gaba da kai masa sara a fusace, barden nan ya yi qoqarin ya kare amma tuni ya makara kaifin takobin zuhairu ya sari tirken dokin wuyansa, kansa ya fita daga gangar jikinsa, ya yi tsalle sama ya tafi ya faxi a gaban sauran baradan da ke tare da wannan jarumin. Da ganin haka sai ragowar baradan dake tare da wannan jarumin suka harzuqa suka taso kan zuhairu cikin qaraji da gunjin fusatuwa, suka far masa da sara da suka kamar za su halakashi, zuhairu ya shiga karewa da maida martani yana saransu da halakasu, suma ragowar jarumai da suke tare da shi tare da Buniyatu suka zare makamansu suka farwa baradan nan da sara, nan take waje ya yamutse qura ta turnuqe ta tokare 65 BAKAR GUGUWA sararin samaniya, qarar haxuwar takubba ta cika wajen kururuwar mazaje da haniniyar dawakai ta yawaita. Kafin wani lokaci su zuhairu sun ragargaza rundunar baradan nan da suka taso kansu suka tarwatsa su,maxaukaka daga cikinsu suka zama maqasqanta, manyan jarumai da ke ji da kansu suka zama raunana, da yawansu suka halaka sai ‘yan qalilan daga cikinsu ne suka arce don su tsira daga halaka, a sanda ake tsakiyar gabza yaqi. Bayan zuhairu sun tarwatsa rundunar baradan nan suka yi godiuya ga Allah a bisa nasarar da suka samu cikin iko da kiyayyewarsa kuma babu wanda ya halaka daga cikinsu, daga nan suka kaxa linzamin dawakansu suka ci gaba da tafiya ya zuwa inda suka nufa. ** Al’amarin matsafi Bahalu kuwa bayan da ya fice daga xakin da ya ajiye Gimbiya Hasima ya tafi izuwa nasa xakin cikin murna da farin cikin samun nasarar xauko Gimbiya Hasima tare da mallakar wannan fada ta mahaifinsa da ya gada, hankalinsa ya kwanta don a yanzu babu abinda ya ke jira illa bayyanar haxewar wannan taurari na alqaluman sihiri da za su tabbatar da kasancewar Gimbiya Hasima matarsa ya samu damar kusantar ta, ya yi sani da cewa mahaifin Gimbiya Hasima zai tura wanda za su shiga duniya nemanta, saboda irin qaunar da yake yiwa ‘yar tasa, amma ya san babu wanda zai iya shigowa lardin Ashtar bare ya samu nasara shiga fadarsa, ko ya karvi Gimbiya Hasima daga hannunsa, saboda ma’abota tsaro da kariya dake tare da fadar. A kowace rana yakan ziyarci xakin Gimbiya Hasima don ya ganta ya ji sanyi a ransa saboda qaunar da yake yi mata, sai dai ba shi da ikon kusantarta ko ya tavata, saboda 66 BAKAR GUGUWA alqaluman sihiri da ya yi imani da su basu bashi damar aikata haka ba, har sai ranar da wannan taurarin na aikin sihiri suka haxe da juna suka zama xaya, saboda haka a kowane dare ya kan zauna a daidai qofar da taurarin suke ya zira ido yana dubansu da sauraron ya ga sun haxe da juna har zuwa wayewar gari, sai rana ta fito ya tashi ya koma xakinsa, haka yake yi a cikin kowanne dare tun daga ranar da ya kawo Gimbiya Hasima wannan fadar. Bayan wasu kwanaki matsafi Bahalu ya yi tunanin ya yi bincike don ganin halin da ‘yar uwarsa Buniyatu take ciki, ya tashi ya tafi ga tarkacen kayan bokancinsa na aikin sihiri, ya zauna a gaban wani kasko na lu’u-lu’u a cikinsa akwai farin rairayi, ya sa hannu ya yi zane akan farin rairaiyin sannan ya rufe idanunsa yana karanta wasu xalasimai na aikin sihiri, bayan wani lokaci bayanai suka bayyana gareshi a saman farin rairayin sai ga siffar qanwarsa Buniyatu tare da zuhairu da sauran baradan dake tare da su sun bayyana tafe akan dawakansu kan hanyarsu ta zuwa bijiren da suka zauna tare da mahaifinsu kafin ya rasu. Matsafi Bahalu ya yi mamaki da ganin wannan al’amari ya sake share rairayi ya yi wani zanen a kansa, bayanai suka sake bayyana a gareshi cikin alqaluman sihirinsa ya ga cewa za su je wannan kogon dutsen ne don xauko wani rubutaccen saqo na sirri da za su samu damar sanin inda wanan fada take,hankalinsa ya yi matuqar tashi nan take ya tashi cikin sauri ya shiga shiri, dan tafiya wannan kogon dutsen ya rigasu zuwa ya xauke wannan rubutaccen saqo da za su je xaukowa a cikinsa. 67 BAKAR GUGUWA Bayan ya gama shirin ya fice daga fadar ya kama hanya, ya yi tafiya har ta tsawon kwanaki shida cikin alqaluman sihirin rage nisan tafiya, sannan ya isa inda wannan kogon dutsen yake da zuwansa ya shiga cikin kogon dutsen ya soma duba da binciken inda wannan rubutaccen saqon yake, amma ya rasa inda aka ajiyeshi babu abinda matsafi Bahalu bai duba ba ko ya bincika cikinsa a cikin kogon dutsen amma ya rasa, ya yi bincike cikin alqaluman sihirinsa bayanai suka tabbatar masa da cewa babu shakka rubutaccen saqon yana cikin wannan kogon dutsen amma ya yi duk binciken da zai yi ya kasa gano inda rubutaccen saqon yake. Da matsafi Bahalu ya gaji da nema sai ya haqura ya fita daga dutsen sannan ya yi aikin sihiri akan kogon dutsen yadda Buniyatu ba za ta iya samun damar shiga cikinsa ba, bayan ya kammala ya yi dariyarsa daya saba yi irin ta mugunta da zallunci sannan ya vace ya bar wajen. ** Su zuhairu suka ci gaba da tafiya har suka shafe sauran kwana goma sha tara da suka rage musu, kafin su iso inda wannan kogon dutsen yake a ranar da suka iso wajen da sanyin safiya suka tunkari inda kogon dutsen yake. Da isarsu wajen kafin su kai ga shiga cikin kogon dutsen sai suka ji wata irin tsawa mai tsananin qarfi da ban firgici ta gauraye wajen tamkar faxuwar aradu, qasa ta soma girgiza tana raurawa tamkar za ta tsage, zuhairu da sauran jarumai da suke tare da shi su afka ciki su nutse, can daga nesa sai suka hangi iska mai tsananin qarfi tare da tsawa da rugugi mai matuqar ban firgici kamar sau uku gaba xaya dajin ya yi 68 BAKAR GUGUWA baqiqirin sararin samaniya ya yi duhu mafi tsanani daga yankin duhun dare. Barada da suke tare da su zuhairu suka yi matuqar razana da ganin wannan yanayi da kuma al’amarin da yake faruwa mai matuqar firgitarwa shi kuwa zuhairu ko a jikinsa don ya saba da ganin irin wannan yanayi a duk sanda matsafi Bahalu zai bayyana, kuma ya san wanna ba komai ba ne face aikin tsafi da sihiri irin na ma’abota shirka da tacewa wa iyazu billahi ya ce a zuciyarsa yana duban wannan baqar guguwa da ta tunkaro inda suke cikin jarumta da qarfin zuciya har ta qaraso ta tsaya a gaban su ta sauka. Da tsayawar iska sai ga matsafi Bahalu ya bayyana ta cikin baqar guguwar a wannan karon ya sha babban da yadda suka saba ganinsa ya bayyana, a yanzu yana sanye ne da suturu irin na alfarma da manya sarakuna da suke ji da kansu a duniya suke sanyawa, hannunsa na hagu yana riqe da kurtunsa na sihiri a dama kuma yana riqe da sandarsa ta tsafi, ya dubi su zuhairu ya yi magana da murya irin ta nuna qasqanci a garesu yace da su. “Ban yi zato ga samun nasara cikin abinda ku ke nufin aikatawa ba don kuwa a yanzu lamarina ya ta’azzara akan wani abin halitta ya samu nasara a kaina komai qarfin tasirin tsafi da sihirinsa, na san za ka fito neman Gimbiya Hasima da nufin zuwa fadata ku karvota daga hannuna, sai dai ina mai sanar da ku cewa abinda ba za ku tava samun nasara a kansa ba ne ku riski inda fadata take, bare ku karvi Gimbiya Hasima daga hannuna, kuma halaka ta tabbata ga duk wanda ya shiga lardin Ashtar da nufin zuwa fadata saboda ma’abota tsaro da masu bada kariya dake tare da ni, babu wata jarumta ko aikin sihiri da zai yi tasiri a kaina, kuma babu wani masani na ilimin 69 BAKAR GUGUWA bokanci da zai iya sanar da ku yadda za ku samu nasara zuwa fadata. Ya dubi ‘yar uwarsa Buniyatu yace da ita “Ke kuma kin yi zavi ga abinda zai kai ki ga halaka, kasancewarki tare da wannan jarumin da kike son taimaka masa idan har ba ki rabu da shi ba, don kuwa ba za ku tava samun nasara ba, kuma hallaka ta kusanta ta gabata gare ki matuqar kina tare da shi cikin wannan tafiya da ku ke yi, ki zama mai neman afuwar a gareni tare da yin rantsuwa da alqaluman sihiri masu girma akan za ki rabu da wannan jarumi ki dawo gareni, kuma na miki alqawari zan maida miki alqaluman sihirin da na qwace daga gareki na tafi da ke fadar mahaifinmu da na mallaka a yanzu, mu zauna tare da ke cikin salama da aminci kamar yadda mahaifinu ya so mu kasance kafin ya rasu” Buniyatu ta amsa da cewar. “Ai babu juya baya ga abinda na tabbata a kansa, na taimakawa abin begena da kasancewa tare da shi har abada kuma yadda mahaifinmu ya bar duniya abadan ba zai sake dawowa cikinta ba, haka na rigaya na rabu da kai har abada ba zan sake komawa gareka ba, kuma ka sani a yanzu na karvi addinin musulunci tare da yin imani da Allah mahaliccin kowa da komai, don haka ba zan sake komawa ga alqaluman sihiri da bautar gumaka da tsafi ba, wanda a yanzu na yi sani da cewa aikata hakan shirka ce da vata mabayyani,Allah ya kiyashemu da sake afkawa a cikinsa” Matsafi Bahalu yace da ita“Ke dai kina cikin fagamniya da vata saboda kasancewar zuciyarki akan begen wannan jarumi, kin zavi kasancewa da shi cikin halin wahala da qunci wanda qarshensa halaka. Fiye da kasancewa dani xan uwanki cikin salama da tasirin aikatawa 70 BAKAR GUGUWA abinda ki ke so na alqaluman sihiri, to kuwa za ki kasance abar yiwa kaico da danasani mara misaltuwa cikin wannan hali kuma ba za ku tava samun nasara akaina ba, cikin qudirinku idan ma kina da wani sirri da ki ke son xauka a cikin wannan kogon dutsen kamar yadda bayanai suka tabbatar mini to kuwa ba za ki samu nasarar shiga cikinsa ba, bare ki xauka don na xaure kogon dutsen da xalasimai na aikin sihiri da ba za ki iya shiga ba, tunda ba kya tare da alqaluman sihiri a yanzu”. Zuhairu ya zare takobinsa cikin fushi yana mai maida masa raddi da cewa “Mu mun yi sani da cewa samun nasara ko rashinta daga Allah ne, kuma a gareshi muke neman taimako don haka muka yi imani da cewa zai bamu nasara a kanka, ko don ya tabbatar da qarfin iko da buwayarsa akan duk wani aikin sihiri da ya sa ke inkarin samun nasara a kanka, kuma bari na fara tabbatar maka da cewa kai ba komai bane a cikin rayuwar duniya, na hallaka ruhina da salwantar da rayuwarka, wata qila san da zamu isa fadarka mu xauko Gimbiya Hasima kai ka daxe da tafiya barzahu. Ya saki linzamin dokinsa a sukwane ya iso gare shi, ya kai masa sara a fusace da dukkanin qarfinsa, matsafi Bahalu ya vace saran ya wuce shi kuma ya bayyana a baya, zuhairu ya sake juyowa gareshi ya kai masa wani saran, Bahalu ya sake vacewa bai sake bayyana ba sai da ya yi nisa da inda zuhairu yake sannan suka hangeshi ya bayyana akan wani qaramin dutse dake gabansa yadu bi zuhairu yace da shi. “Ai yanzu girman matsayina ya fi gaban na yi arangama da kai dan fafatawa,ka sani a yanzu ni ne shugaba na duk wani ma’abocin aikin bokanci da sihiri da ke wannan yanki a duniya don haka yin mubazara da kai nuna qasqancine a gareni, kuma 71 BAKAR GUGUWA idan na halaka ka da kaina zai zama nuna gajiyawa cikin aikin sihirina don haka zan bar ka ka halaka ne cikin wannan tafiya da ku ke yi daga kai har sauran jarumai da ku ke tare da su” Yana gama maganar sai baqar guguwar nan ta sake turnuqewa ta gauraye wajen, iska mai qarfi ta taso ta yi sama da guguwar ta nufi vangaren yamma inda baqar guguwa ta vullo tunda farko, suka riqa duban wannan baqar guguwar har ta vacewa ganinsu sannan sai suka ga wajen ya washe duhun da ya lulluve sararin samaniya ya yaye ya washe duhun da ya lulluve sararin samaniya ya yaye, komai ya koma yadda yake alamar matsafi Bahalu ya tafi kenan. Bayan tafiyar matsafi Bahalu sai Buniyatu ta sauka daga kan dokinta, ta nufi qofar shiga kogon dutsen da zuwa qofar sai suka ga wata irin iska mai tsananin qarfi ta fizgeta ta yi sama da ita ta makata da jikin wani qaramin dutse dake kusa da wajen, Buniyatu ta yi qara a firgice sannan ta zube a qasa sumammiya sulken jikinta ya kama da wuta za ta qone ta halaka. Zuhairu da sauran jaruman da suke tare da shi suka diro daga kan dawakansu cikin sauri suka tafi gareta don kai mata xauki kada ta halaka, suka yi qoqarin kashe wutar da ta kama jikinta har ta mutu, kafin ta fara qonata, daga nan zuhairu ya ci gaba da shafa mata ruwa a goshinta yana yi mata addu’a har ta farfaxo daga suman da ta yi, bayan ta dawo hayyacinta ta tashi ta dubi zuhairu tace da shi. “Haqiqa ba zan iya samun nasarar shiga wannan kogon dutsen ba, saboda aikin sihiri da yayana matsafi Bahalu ya aikata, don haka sai dai wani daga cikinku ya shiga saboda ni bani da damar shiga cikinsa” Da jin haka sai ragowar baradan 72 BAKAR GUGUWA dake tare da su suka yi shiru, babu wanda ya yi magana bare a samu wanda zai ce zai shiga, saboda ganin abinda ya faru gareta, shi kuwa zuhairu cikin qarfin zuciya da jarumta sai ya amsa da cewa “Ni zan shiga kogon dutsen na xauko wannan saqo, sanar da ni inda saqon yake na je na xauko”. Buniyatu tace da shi “Saqon yana rubuce ne a jikin wata fatar vauna dake cikin akwatin baqin qarfe da ke ajiye a qarshen wannan kogon dutsen, idan ka shiga cikin kogon dutsen kada ka sake ka tava komai sai wanan aikwati, kada ka sake ka ji tsoro ko ka razana akan duk abinda za ka ga ya tunkaroka idan ka shiga kogon dutsen haka kuma kada ka yi magana ko ka yi waiwaye ka juyo baya har ka isa inda akwatin take, idan ka isa gareta sai ka xauko akwatin ka fito da ita, ni kuma zan buxe mu xauki wannan rubutaccen saqon dake cikinta”. Da zuhairu ya gama jin wannan bayani na Buniyatu sai ya tashi ya nufi qofar wannan kogon dutsen ba tare da wani tsoro ko fargaba ba, yana zuwa ya shiga cikinsa da shigarsa wuta ce ta fara tasowa kansa tana wani irin huci da ruri na azaba, zuhairu ya xaga hannun zai kare fuskarsa don kada wutar ta qonashi amma sai ya tuna da maganar Buniyatu cewa duk abinda ya gani kada ya ji tsoro ko ya razana don haka ya ci gaba da tafiya har wutar ta qaraso gareshi ya ji ta wuce ta jikinsa ba tare da ya ji zafinta ko kuma ta qonashi ba. Ya sake ganin wani qaton dutse ya taho daga sama zai faxo kansa ya halakashi, zuhairu bai razana ba, har dutsen ya kusa kansa amma sai ya ga ya vace babu shi ya sake jin kamar muryar kakansa marwan ya kira sunansa ta baya, zuhairu bai juya ba ya ci gaba da tafiya. 73 BAKAR GUGUWA Haka ya yi ta ganin abubuwa na ban tsoro da razanarwa iri daban-daban, amma zuhairu bai razana ba har ya isa inda wannan akwatin baqin qarfen take ya ganta da matuqar girma yadda idan mutum ba sadauki bane ba zai iya xaukarta daga inda take ba, ya matsa gareta ya sa hannu ya cicciveta da qyar ya rabata da qasa ya xora a kansa saboda tsananin nauyi, sannan ya juyo ya kama hanyar fitowa daga kogon dutsen. Bayan zuhairu ya fito ya nufi inda su Buniyatu da sauran jarumai da suke tare suke tsaye suna jiran fitowarsa ya sauke akwatin a gabansu, Buniyatu ta yi matuqar farin ciki da samun nasara xauko akwatin da ya yi, sannan ta sa hannun ta buxe murfin akwatin, wani haske mai tsananin qarfi tamkar walqiya ya tashi sama bayan da ta buxe, baradan dake tare da su suka ji tsoro suka ja da baya,yayin fitar wannan hasken bayan lafawar hasken Buniyatu ta sanya hannu a cikin akwatin ta xauko wata baqar fatar vauna dake nannaxe da baqin zare wadda ita kaxaice a cikin akwatin,sannan ta dubi zuhairu tace da shi. “Tunda har mun samu wannan rubutaccen saqon na sirri,to kuwa mun samu damar samun nasara akan matsafi Bahalu yanzu zamu tafi ga tsohuwa DIYANNUWA don ta karanta mana wannan rubutaccen saqon, ta kuma sanar da mu yadda zamu iya zuwa wannan fada ta Darul sabar da matsafi Bahalu ya tafi da Gimbiya Hasima, don babu wanda zai iya karanta wannan rubutaccen saqon a faxin duniyar nan sai ita” Zuhairu ya dubeta cikin mamaki yace da ita “Wacece kuma tsohuwa Diyanuwa da zamu tafi gareta don ta karanta mana wannan saqo kuma menene alaqarta da wannan rubutu da ke jikin wannan fata da babu wanda zai iya karantawa sai 74 BAKAR GUGUWA ita?” Buniyatu ta ce da shi “Ita wannan tshowar Diyanuwa kakata ce ta wajen uwa, kuma a hannunta na girma tun tasowata, bayan mahaifiyata ta rasu, tana matuqar qaunata fiye da yadda take son komai a duniya don babu abinda zan nema a gareta ta gaza mallaka min matuqar tana da ikon bani shi, sai dai kuma ba ta qaunar xan uwana Bahalu tare da mahaifinmu kauwas a rayuwarta ta duniya, ta tsanesu da mafi munin tsana saboda kasancewar halinsu iri xaya na tsananin mugunta da zalunci, wannan ne dalilin da ya sa mahaifina ya karveni daga hannunta ya dawo dani gareshi, a halin yanzu ta makance ba ta gani kuma mahaifinmu ne sanadin makancewarta, sakamakon jifanta da alqaluman sihirin sa da ya yi. Babu wanda zai iya karanta wannan rubutaccen saqon sai ita duk da cewa makaniya ce ba ta gani, kuma idanunta ba za su warke daga wannan makantar ta aikin sihiri ba har sai an xebo ruwan dake cikin rijiyar dake tsakiyar fadar Darul sabar ta wanke idanunta da shi, idan muka isa gareta muka sanar da ita buqatarmu babu shakka za ta taimaka mana ta kuma sanar damu bayanan da bamu sani ba, game da ita wannan fada, ko don mu xebo mata ruwan dake cikin wannan rijiya ta tsakiyar fadar ta warke daga halin makantar ta aikin sihiri da ke tare da ita” Zuhairu ya sake cika da mamaki ya dubeta ya ce da ita. “To ita da take cikin halin makanta ta yaya za ta iya karanta wannan rubutaccen saqon dake jikin wannan fatar?” Buniyatu ta yi murmushi sannan ta ce da shi “Idan muka isa gareta za ka gani har ma da wasu abubuwan ban mamaki da al’ajabi daga gareta, don Allah ya yi mata baiwa gane duk abinda ya kusanceta koda kuwa tsutsune ya wuce a sama ba 75 BAKAR GUGUWA tare da ya yi kuka ba, idan ta ji hucin iskarsa za ta faxa maka sunansa kuma babu kuskure ka ga shi ne ya wuce” Zuhairu bai sake cewa komai ba ya ci gaba da mamakin wannan

Chapter 5 of 10