marwan kakan zuhairu ya yi musu addu’a
ta fatan samun nasara sannan suka yi sallama suka kama
hanyar birnin Bahazum.
Da isar su Birni suka wuce fadar sarki shaiban, suka
tarar da an shirya wasu manya jarumai cikin shirin yaqi, su
kimanin mutum arba’in da za su yi musu rakiya cikin tafiyar da
za su yi, zuhairu ya sauka daga kan dokinsa ya tafi gaban sarki
ya kai gaisuwa sarki ya amsa masa sannan ya ce da shi “Allah
ya baka nasara na gama shiri dan yin tafiya bisa ga alqawarin
da na xauka, na neman Gimbiya Hasima duk inda take a faxin
duniya”.
Sarki shiaban ya ce da shi “Na shirya wasu jarumai da
za su yi maka rakiya adadin mutum arba’in daga cikinsu akwai
mutum goma qwararu a fagen iya harbi da kibiya sannan akwai
61
BAKAR GUGUWA
wasu mutum goma da suka qware wajen faxa da mashi, sai
kuma mutum goma masu iya jifa da majaujawa, sai mutum
goma na qarshe sune qwararu a fagen iya faxa da takobi
waxannan sune adadin mutum arba’in Allah ya baku nasara
cikin tafiyar da za ku yi”.
Zuhairu ya yi godiya sanann sarki shaiban ya sa aka yi
musu addu’a ta fatan samun nasara ya kuma umarci baradan da
za su yiwa zuhairu rakiya su kasance ma su yi masa biyayya a
matsayin shugabansu har su je su dawo, daga nan suka yi
sallama da sarki aka yi musu rakiya zuwa bayan gari suka
kama hanya suka ci gaba da tafiya. Buniyatu tana gaba don yi
musu jagora zuwa bigiren da suke zaune tare da yayanta
matsafi Bahalu, don xauko rubutaccen saqon wanda zai shiryar
da su hanyar da za ta kaisu lardin Ashtar inda fadar da matsafi
Bahalu ya tafi da Gimbiya Hasima take.
Kwanci tashi suna tafiya cikin wannan daji tun daga
ranar da suka baro gida, har suka shafe kwanaki ashirin daga
cikin kwanaki arba’in da za su yi kafin su isa bigiren da
Buniyatu suke zaune a cikinsa, sukan yi tafiya daga bayan
ketowar alfijir har zuwa faxuwar rana sallah da cin abinci ne
kawai yake tsayar da su sai dare ya yi su yada zango don su
kwana kafin gari ya waye su ci gaba da tafiya. A rana ta ashirin
da xaya daga cikin ranakun tafiyarsu da la’asar sakaliya suna
tsakiyar tafiya sai suka hangi wasu rundunar mahaya cikin
shirin yaqi suna xauke da tutoci irin na mabiya addinin bautar
rana, su zuhairu suka yi nufin su ratse musu su ci gaba da
tafiya, don kada baradan su tsayar da su su vata musu lokaci
cikin tafiyar da suke yi, amma sai waxannan ayarin baradan
suka hangesu suka kan su suka tsayar da su, xaya daga cikin
62
BAKAR GUGUWA
baradan wanda kuma shi ne babbansu ya dubi zuhairu yace da
su.
“Kai waxannan matafiya daga ina kuke kuma ku
jama’ar wane birnine da inda kuka nufa? Sannan nina labarin
dukiya da guzuri da kuke tare da shi. Ku yi gaggawar miqoshi
garemu don a yanzu kun zama ribatattu a garemu ababen tafiya
da ku ya zuwa birninmu don kaiwa sarkinmu ku zama bayi,
kamar yadda mukan yi ga duk jama’ar da muka haxu da su
wannan daji cikin tafiyar da muke yi” Zuhairu yace da shi.
“Ba ma tare da wata dukiya ko guzuri da zamu baku
bisa ga buqatarku, cewa dai mu mun kasance matafiya ne cikin
wata buqata da take tare da mu,kuma bamu fito dan yin faxa da
kowa ba sai don tunkarar abinda muka sa a gaba saboda haka
muna neman afuwa a gareku, ku bamu hanya mu wuce ya
zuwa inda muka nufa” Wanda ya fara magana ya dubi zuhairu
yace da shi “Kai dattijo ma’abocin rauni da gazawa ka sani
cewa ba za ku kuvuta daga hannunmu ba har sai kun zama
ribatattu a garemu, don na ga alama kun kasance daga cikin
mabiya addinin musulunci ba masu bauta ga rana ba, za mu tafi
da ku ya zuwa birninmu don mu bautar da ku kamar yadda
muke bautar da duk wanda bai zamo daga jinsinmu ba kuma
baya bauta ga rana abar bautawa ta gaskiya, to kuwa sunansa
bawa a garemu kuma ya halatta mu bautar da shi ko mu
halakashi mu shayar da jininsa ga rana abar bautawarmu bisa
ga tsarin addininmu”
Zuhairu ya fusata da jin maganar wannan mutum ya ce
da shi, “Kaicon rayuwarka da abinda kake ambatawa cikin
zantukanka masu munin ambato, Allah wadai da miyagun
kalamanka na zalunci da ke bayyana tsantsar shirka da vata
63
BAKAR GUGUWA
mabayyani na bauta ga rana abar halitta, kuna shayar da jini
gareta ka sani cewar halaka ta tabbata gareka da rundunar
baradan da kake jagoranta sababin abinda kake aikatawa na
zalunci a doron qasa, don shafe ruhinka daga bayan qasa shi ne
mafi alkairi ga sauran jama’ar musulmi”.
Barden nan ya bushe da dariya saboda jin abinda
zuhairu yace sannan ya dubeshi yace da shi “Kai dattijo
ma’abocin rauni da gazawa saurara ga ambaton waxannan
kalamai naka da kake ambatawa, ka bari matasa masu ragowar
jini a jiki da jarumta su yi magana, ba kai dattijo ma’abocin
rauni dan haka ko ku miqa wuya garemu ko mu tursasaku ga
aikata abinda muka umarceku ta hanyar qarfi da tsananin
yawanmu”.
Zuhairu ya zare takobinsa ya fita gaban rundunar
baradan yace da su “Ba zamu zama masu tsoro ko karaya da
ganin yawan rundunarku da ku ke alfahari da ita ba, don Allah
da muka yi imani da shi muke bauta masa zai iya bamu nasara
akan ku koda kun fi yawan adadin qasa, don haka idan da mai
qarar kwana ya fara fitowa gareni ya ga yadda zan aika da
ruhinsa barzahu, idan kuma kun qi fitowa ni na gabata cikinku
na hau ku da sara da kisa irin na qare dangi, har sai na tarwatsa
rundunarku na sanyaku nadamar halittarku a bayan qasa da
abinda kuke aikatawa”.
Jarumi nan ya sake bushewa da dariya lokaci guda
kuma sai ya turvune fuska, irin na mugunta da zalunci ya dubi
zuhairu yace da shi “Ban zamo daga cikin mutane masu imani
da zan ji tausayin tsufanka ba na qyaleka ba, tunda har kana jin
ka isa jarumi bari ni na halakaka da kaina, don ya zama izina
ga sauran jama’ar da ke tare da kai” Ya zare takobinsa ya taho
64
BAKAR GUGUWA
ga zuhairu sai kuma ya sake shawara ya maida takobinsa yana
mai faxin cewa “Ai halaka ka da takobi ma nuna rashin
jarumta ne, da gazawa don kuwa iskar gudun dokina kaxai ta
isa waftoka daga kan dokinka ka faxo qasa ka halaka”.
Kafin ya gama magana zuhairu ya fusata ya xaga
takobinsa ya kai masa sara, jarumin ya yi sauri ya sanya wata
garkuwa ta baqin qarfe ya kare saran, kaifin takobin zuhairu ya
keta garkuwa gida biyu ta tarwatse, jarumin ya yi baya tagataga kamar za su faxi daga shi da dokinsa da qyar dokin ya
tirje ya tsaya saboda qarfin saran da zuhairu ya kai masa irin na
sadaukantaka, jarumin nan ya dubi zuhairu cikin tsananin
mamaki kafin ya qare mamakinsa zuhairu ya sake kai masa
wani saran cikin qarfin zuciya da zafin nama jarumin ya yi
sauri ya zare takobinsa ya kare saran, a wannan karon ma sai
da ya sake yin baya kamar zai faxo daga kan dokinsa saboda
qarfin saran.
Zuhairu bai saurara masa ba ya ci gaba da kai masa sara
a fusace, barden nan ya yi qoqarin ya kare amma tuni ya
makara kaifin takobin zuhairu ya sari tirken dokin wuyansa,
kansa ya fita daga gangar jikinsa, ya yi tsalle sama ya tafi ya
faxi a gaban sauran baradan da ke tare da wannan jarumin.
Da ganin haka sai ragowar baradan dake tare da wannan
jarumin suka harzuqa suka taso kan zuhairu cikin qaraji da
gunjin fusatuwa, suka far masa da sara da suka kamar za su
halakashi, zuhairu ya shiga karewa da maida martani yana
saransu da halakasu, suma ragowar jarumai da suke tare da shi
tare da Buniyatu suka zare makamansu suka farwa baradan nan
da sara, nan take waje ya yamutse qura ta turnuqe ta tokare
65
BAKAR GUGUWA
sararin samaniya, qarar haxuwar takubba ta cika wajen
kururuwar mazaje da haniniyar dawakai ta yawaita.
Kafin wani lokaci su zuhairu sun ragargaza rundunar
baradan nan da suka taso kansu suka tarwatsa su,maxaukaka
daga cikinsu suka zama maqasqanta, manyan jarumai da ke ji
da kansu suka zama raunana, da yawansu suka halaka sai ‘yan
qalilan daga cikinsu ne suka arce don su tsira daga halaka, a
sanda ake tsakiyar gabza yaqi. Bayan zuhairu sun tarwatsa
rundunar baradan nan suka yi godiuya ga Allah a bisa nasarar
da suka samu cikin iko da kiyayyewarsa kuma babu wanda ya
halaka daga cikinsu, daga nan suka kaxa linzamin dawakansu
suka ci gaba da tafiya ya zuwa inda suka nufa.
**
Al’amarin matsafi Bahalu kuwa bayan da ya fice daga
xakin da ya ajiye Gimbiya Hasima ya tafi izuwa nasa xakin
cikin murna da farin cikin samun nasarar xauko Gimbiya
Hasima tare da mallakar wannan fada ta mahaifinsa da ya gada,
hankalinsa ya kwanta don a yanzu babu abinda ya ke jira illa
bayyanar haxewar wannan taurari na alqaluman sihiri da za su
tabbatar da kasancewar Gimbiya Hasima matarsa ya samu
damar kusantar ta, ya yi sani da cewa mahaifin Gimbiya
Hasima zai tura wanda za su shiga duniya nemanta, saboda irin
qaunar da yake yiwa ‘yar tasa, amma ya san babu wanda zai
iya shigowa lardin Ashtar bare ya samu nasara shiga fadarsa,
ko ya karvi Gimbiya Hasima daga hannunsa, saboda ma’abota
tsaro da kariya dake tare da fadar.
A kowace rana yakan ziyarci xakin Gimbiya Hasima
don ya ganta ya ji sanyi a ransa saboda qaunar da yake yi mata,
sai dai ba shi da ikon kusantarta ko ya tavata, saboda
66
BAKAR GUGUWA
alqaluman sihiri da ya yi imani da su basu bashi damar aikata
haka ba, har sai ranar da wannan taurarin na aikin sihiri suka
haxe da juna suka zama xaya, saboda haka a kowane dare ya
kan zauna a daidai qofar da taurarin suke ya zira ido yana
dubansu da sauraron ya ga sun haxe da juna har zuwa wayewar
gari, sai rana ta fito ya tashi ya koma xakinsa, haka yake yi a
cikin kowanne dare tun daga ranar da ya kawo Gimbiya
Hasima wannan fadar.
Bayan wasu kwanaki matsafi Bahalu ya yi tunanin ya yi
bincike don ganin halin da ‘yar uwarsa Buniyatu take ciki, ya
tashi ya tafi ga tarkacen kayan bokancinsa na aikin sihiri, ya
zauna a gaban wani kasko na lu’u-lu’u a cikinsa akwai farin
rairayi, ya sa hannu ya yi zane akan farin rairaiyin sannan ya
rufe idanunsa yana karanta wasu xalasimai na aikin sihiri,
bayan wani lokaci bayanai suka bayyana gareshi a saman farin
rairayin sai ga siffar qanwarsa Buniyatu tare da zuhairu da
sauran baradan dake tare da su sun bayyana tafe akan
dawakansu kan hanyarsu ta zuwa bijiren da suka zauna tare da
mahaifinsu kafin ya rasu.
Matsafi Bahalu ya yi mamaki da ganin wannan al’amari
ya sake share rairayi ya yi wani zanen a kansa, bayanai suka
sake bayyana a gareshi cikin alqaluman sihirinsa ya ga cewa za
su je wannan kogon dutsen ne don xauko wani rubutaccen
saqo na sirri da za su samu damar sanin inda wanan fada
take,hankalinsa ya yi matuqar tashi nan take ya tashi cikin
sauri ya shiga shiri, dan tafiya wannan kogon dutsen ya rigasu
zuwa ya xauke wannan rubutaccen saqo da za su je xaukowa a
cikinsa.
67
BAKAR GUGUWA
Bayan ya gama shirin ya fice daga fadar ya kama hanya,
ya yi tafiya har ta tsawon kwanaki shida cikin alqaluman
sihirin rage nisan tafiya, sannan ya isa inda wannan kogon
dutsen yake da zuwansa ya shiga cikin kogon dutsen ya soma
duba da binciken inda wannan rubutaccen saqon yake, amma
ya rasa inda aka ajiyeshi babu abinda matsafi Bahalu bai duba
ba ko ya bincika cikinsa a cikin kogon dutsen amma ya rasa, ya
yi bincike cikin alqaluman sihirinsa bayanai suka tabbatar
masa da cewa babu shakka rubutaccen saqon yana cikin
wannan kogon dutsen amma ya yi duk binciken da zai yi ya
kasa gano inda rubutaccen saqon yake.
Da matsafi Bahalu ya gaji da nema sai ya haqura ya fita
daga dutsen sannan ya yi aikin sihiri akan kogon dutsen yadda
Buniyatu ba za ta iya samun damar shiga cikinsa ba, bayan ya
kammala ya yi dariyarsa daya saba yi irin ta mugunta da
zallunci sannan ya vace ya bar wajen.
**
Su zuhairu suka ci gaba da tafiya har suka shafe sauran
kwana goma sha tara da suka rage musu, kafin su iso inda
wannan kogon dutsen yake a ranar da suka iso wajen da sanyin
safiya suka tunkari inda kogon dutsen yake.
Da isarsu wajen kafin su kai ga shiga cikin kogon
dutsen sai suka ji wata irin tsawa mai tsananin qarfi da ban
firgici ta gauraye wajen tamkar faxuwar aradu, qasa ta soma
girgiza tana raurawa tamkar za ta tsage, zuhairu da sauran
jarumai da suke tare da shi su afka ciki su nutse, can daga nesa
sai suka hangi iska mai tsananin qarfi tare da tsawa da rugugi
mai matuqar ban firgici kamar sau uku gaba xaya dajin ya yi
68
BAKAR GUGUWA
baqiqirin sararin samaniya ya yi duhu mafi tsanani daga yankin
duhun dare.
Barada da suke tare da su zuhairu suka yi matuqar
razana da ganin wannan yanayi da kuma al’amarin da yake
faruwa mai matuqar firgitarwa shi kuwa zuhairu ko a jikinsa
don ya saba da ganin irin wannan yanayi a duk sanda matsafi
Bahalu zai bayyana, kuma ya san wanna ba komai ba ne face
aikin tsafi da sihiri irin na ma’abota shirka da tacewa wa iyazu
billahi ya ce a zuciyarsa yana duban wannan baqar guguwa da
ta tunkaro inda suke cikin jarumta da qarfin zuciya har ta
qaraso ta tsaya a gaban su ta sauka. Da tsayawar iska sai ga
matsafi Bahalu ya bayyana ta cikin baqar guguwar a wannan
karon ya sha babban da yadda suka saba ganinsa ya bayyana, a
yanzu yana sanye ne da suturu irin na alfarma da manya
sarakuna da suke ji da kansu a duniya suke sanyawa, hannunsa
na hagu yana riqe da kurtunsa na sihiri a dama kuma yana riqe
da sandarsa ta tsafi, ya dubi su zuhairu ya yi magana da murya
irin ta nuna qasqanci a garesu yace da su.
“Ban yi zato ga samun nasara cikin abinda ku ke nufin
aikatawa ba don kuwa a yanzu lamarina ya ta’azzara akan wani
abin halitta ya samu nasara a kaina komai qarfin tasirin tsafi da
sihirinsa, na san za ka fito neman Gimbiya Hasima da nufin
zuwa fadata ku karvota daga hannuna, sai dai ina mai sanar da
ku cewa abinda ba za ku tava samun nasara a kansa ba ne ku
riski inda fadata take, bare ku karvi Gimbiya Hasima daga
hannuna, kuma halaka ta tabbata ga duk wanda ya shiga lardin
Ashtar da nufin zuwa fadata saboda ma’abota tsaro da masu
bada kariya dake tare da ni, babu wata jarumta ko aikin sihiri
da zai yi tasiri a kaina, kuma babu wani masani na ilimin
69
BAKAR GUGUWA
bokanci da zai iya sanar da ku yadda za ku samu nasara zuwa
fadata.
Ya dubi ‘yar uwarsa Buniyatu yace da ita “Ke kuma kin
yi zavi ga abinda zai kai ki ga halaka, kasancewarki tare da
wannan jarumin da kike son taimaka masa idan har ba ki rabu
da shi ba, don kuwa ba za ku tava samun nasara ba, kuma
hallaka ta kusanta ta gabata gare ki matuqar kina tare da shi
cikin wannan tafiya da ku ke yi, ki zama mai neman afuwar a
gareni tare da yin rantsuwa da alqaluman sihiri masu girma
akan za ki rabu da wannan jarumi ki dawo gareni, kuma na
miki alqawari zan maida miki alqaluman sihirin da na qwace
daga gareki na tafi da ke fadar mahaifinmu da na mallaka a
yanzu, mu zauna tare da ke cikin salama da aminci kamar
yadda mahaifinu ya so mu kasance kafin ya rasu” Buniyatu ta
amsa da cewar.
“Ai babu juya baya ga abinda na tabbata a kansa, na
taimakawa abin begena da kasancewa tare da shi har abada
kuma yadda mahaifinmu ya bar duniya abadan ba zai sake
dawowa cikinta ba, haka na rigaya na rabu da kai har abada ba
zan sake komawa gareka ba, kuma ka sani a yanzu na karvi
addinin musulunci tare da yin imani da Allah mahaliccin kowa
da komai, don haka ba zan sake komawa ga alqaluman sihiri
da bautar gumaka da tsafi ba, wanda a yanzu na yi sani da
cewa aikata hakan shirka ce da vata mabayyani,Allah ya
kiyashemu da sake afkawa a cikinsa” Matsafi Bahalu yace da
ita“Ke dai kina cikin fagamniya da vata saboda kasancewar
zuciyarki akan begen wannan jarumi, kin zavi kasancewa da
shi cikin halin wahala da qunci wanda qarshensa halaka. Fiye
da kasancewa dani xan uwanki cikin salama da tasirin aikatawa
70
BAKAR GUGUWA
abinda ki ke so na alqaluman sihiri, to kuwa za ki kasance abar
yiwa kaico da danasani mara misaltuwa cikin wannan hali
kuma ba za ku tava samun nasara akaina ba, cikin qudirinku
idan ma kina da wani sirri da ki ke son xauka a cikin wannan
kogon dutsen kamar yadda bayanai suka tabbatar mini to kuwa
ba za ki samu nasarar shiga cikinsa ba, bare ki xauka don na
xaure kogon dutsen da xalasimai na aikin sihiri da ba za ki iya
shiga ba, tunda ba kya tare da alqaluman sihiri a yanzu”.
Zuhairu ya zare takobinsa cikin fushi yana mai maida
masa raddi da cewa “Mu mun yi sani da cewa samun nasara ko
rashinta daga Allah ne, kuma a gareshi muke neman taimako
don haka muka yi imani da cewa zai bamu nasara a kanka, ko
don ya tabbatar da qarfin iko da buwayarsa akan duk wani
aikin sihiri da ya sa ke inkarin samun nasara a kanka, kuma
bari na fara tabbatar maka da cewa kai ba komai bane a cikin
rayuwar duniya, na hallaka ruhina da salwantar da rayuwarka,
wata qila san da zamu isa fadarka mu xauko Gimbiya Hasima
kai ka daxe da tafiya barzahu.
Ya saki linzamin dokinsa a sukwane ya iso gare shi, ya
kai masa sara a fusace da dukkanin qarfinsa, matsafi Bahalu ya
vace saran ya wuce shi kuma ya bayyana a baya, zuhairu ya
sake juyowa gareshi ya kai masa wani saran, Bahalu ya sake
vacewa bai sake bayyana ba sai da ya yi nisa da inda zuhairu
yake sannan suka hangeshi ya bayyana akan wani qaramin
dutse dake gabansa yadu bi zuhairu yace da shi.
“Ai yanzu girman matsayina ya fi gaban na yi arangama
da kai dan fafatawa,ka sani a yanzu ni ne shugaba na duk wani
ma’abocin aikin bokanci da sihiri da ke wannan yanki a duniya
don haka yin mubazara da kai nuna qasqancine a gareni, kuma
71
BAKAR GUGUWA
idan na halaka ka da kaina zai zama nuna gajiyawa cikin aikin
sihirina don haka zan bar ka ka halaka ne cikin wannan tafiya
da ku ke yi daga kai har sauran jarumai da ku ke tare da su”
Yana gama maganar sai baqar guguwar nan ta sake turnuqewa
ta gauraye wajen, iska mai qarfi ta taso ta yi sama da guguwar
ta nufi vangaren yamma inda baqar guguwa ta vullo tunda
farko, suka riqa duban wannan baqar guguwar har ta vacewa
ganinsu sannan sai suka ga wajen ya washe duhun da ya
lulluve sararin samaniya ya yaye ya washe duhun da ya lulluve
sararin samaniya ya yaye, komai ya koma yadda yake alamar
matsafi Bahalu ya tafi kenan.
Bayan tafiyar matsafi Bahalu sai Buniyatu ta sauka daga
kan dokinta, ta nufi qofar shiga kogon dutsen da zuwa qofar
sai suka ga wata irin iska mai tsananin qarfi ta fizgeta ta yi
sama da ita ta makata da jikin wani qaramin dutse dake kusa da
wajen, Buniyatu ta yi qara a firgice sannan ta zube a qasa
sumammiya sulken jikinta ya kama da wuta za ta qone ta
halaka.
Zuhairu da sauran jaruman da suke tare da shi suka diro
daga kan dawakansu cikin sauri suka tafi gareta don kai mata
xauki kada ta halaka, suka yi qoqarin kashe wutar da ta kama
jikinta har ta mutu, kafin ta fara qonata, daga nan zuhairu ya ci
gaba da shafa mata ruwa a goshinta yana yi mata addu’a har ta
farfaxo daga suman da ta yi, bayan ta dawo hayyacinta ta tashi
ta dubi zuhairu tace da shi.
“Haqiqa ba zan iya samun nasarar shiga wannan kogon
dutsen ba, saboda aikin sihiri da yayana matsafi Bahalu ya
aikata, don haka sai dai wani daga cikinku ya shiga saboda ni
bani da damar shiga cikinsa” Da jin haka sai ragowar baradan
72
BAKAR GUGUWA
dake tare da su suka yi shiru, babu wanda ya yi magana bare a
samu wanda zai ce zai shiga, saboda ganin abinda ya faru
gareta, shi kuwa zuhairu cikin qarfin zuciya da jarumta sai ya
amsa da cewa “Ni zan shiga kogon dutsen na xauko wannan
saqo, sanar da ni inda saqon yake na je na xauko”.
Buniyatu tace da shi “Saqon yana rubuce ne a jikin wata
fatar vauna dake cikin akwatin baqin qarfe da ke ajiye a
qarshen wannan kogon dutsen, idan ka shiga cikin kogon
dutsen kada ka sake ka tava komai sai wanan aikwati, kada ka
sake ka ji tsoro ko ka razana akan duk abinda za ka ga ya
tunkaroka idan ka shiga kogon dutsen haka kuma kada ka yi
magana ko ka yi waiwaye ka juyo baya har ka isa inda akwatin
take, idan ka isa gareta sai ka xauko akwatin ka fito da ita, ni
kuma zan buxe mu xauki wannan rubutaccen saqon dake
cikinta”.
Da zuhairu ya gama jin wannan bayani na Buniyatu sai
ya tashi ya nufi qofar wannan kogon dutsen ba tare da wani
tsoro ko fargaba ba, yana zuwa ya shiga cikinsa da shigarsa
wuta ce ta fara tasowa kansa tana wani irin huci da ruri na
azaba, zuhairu ya xaga hannun zai kare fuskarsa don kada
wutar ta qonashi amma sai ya tuna da maganar Buniyatu cewa
duk abinda ya gani kada ya ji tsoro ko ya razana don haka ya ci
gaba da tafiya har wutar ta qaraso gareshi ya ji ta wuce ta
jikinsa ba tare da ya ji zafinta ko kuma ta qonashi ba.
Ya sake ganin wani qaton dutse ya taho daga sama zai
faxo kansa ya halakashi, zuhairu bai razana ba, har dutsen ya
kusa kansa amma sai ya ga ya vace babu shi ya sake jin kamar
muryar kakansa marwan ya kira sunansa ta baya, zuhairu bai
juya ba ya ci gaba da tafiya.
73
BAKAR GUGUWA
Haka ya yi ta ganin abubuwa na ban tsoro da razanarwa
iri daban-daban, amma zuhairu bai razana ba har ya isa inda
wannan akwatin baqin qarfen take ya ganta da matuqar girma
yadda idan mutum ba sadauki bane ba zai iya xaukarta daga
inda take ba, ya matsa gareta ya sa hannu ya cicciveta da qyar
ya rabata da qasa ya xora a kansa saboda tsananin nauyi,
sannan ya juyo ya kama hanyar fitowa daga kogon dutsen.
Bayan zuhairu ya fito ya nufi inda su Buniyatu da
sauran jarumai da suke tare suke tsaye suna jiran fitowarsa ya
sauke akwatin a gabansu, Buniyatu ta yi matuqar farin ciki da
samun nasara xauko akwatin da ya yi, sannan ta sa hannun ta
buxe murfin akwatin, wani haske mai tsananin qarfi tamkar
walqiya ya tashi sama bayan da ta buxe, baradan dake tare da
su suka ji tsoro suka ja da baya,yayin fitar wannan hasken
bayan lafawar hasken Buniyatu ta sanya hannu a cikin akwatin
ta xauko wata baqar fatar vauna dake nannaxe da baqin zare
wadda ita kaxaice a cikin akwatin,sannan ta dubi zuhairu tace
da shi.
“Tunda har mun samu wannan rubutaccen saqon na
sirri,to kuwa mun samu damar samun nasara akan matsafi
Bahalu yanzu zamu tafi ga tsohuwa DIYANNUWA don ta
karanta mana wannan rubutaccen saqon, ta kuma sanar da mu
yadda zamu iya zuwa wannan fada ta Darul sabar da matsafi
Bahalu ya tafi da Gimbiya Hasima, don babu wanda zai iya
karanta wannan rubutaccen saqon a faxin duniyar nan sai ita”
Zuhairu ya dubeta cikin mamaki yace da ita “Wacece
kuma tsohuwa Diyanuwa da zamu tafi gareta don ta karanta
mana wannan saqo kuma menene alaqarta da wannan rubutu
da ke jikin wannan fata da babu wanda zai iya karantawa sai
74
BAKAR GUGUWA
ita?” Buniyatu ta ce da shi “Ita wannan tshowar Diyanuwa
kakata ce ta wajen uwa, kuma a hannunta na girma tun
tasowata, bayan mahaifiyata ta rasu, tana matuqar qaunata fiye
da yadda take son komai a duniya don babu abinda zan nema a
gareta ta gaza mallaka min matuqar tana da ikon bani shi, sai
dai kuma ba ta qaunar xan uwana Bahalu tare da mahaifinmu
kauwas a rayuwarta ta duniya, ta tsanesu da mafi munin tsana
saboda kasancewar halinsu iri xaya na tsananin mugunta da
zalunci, wannan ne dalilin da ya sa mahaifina ya karveni daga
hannunta ya dawo dani gareshi, a halin yanzu ta makance ba ta
gani kuma mahaifinmu ne sanadin makancewarta, sakamakon
jifanta da alqaluman sihirin sa da ya yi.
Babu wanda zai iya karanta wannan rubutaccen saqon
sai ita duk da cewa makaniya ce ba ta gani, kuma idanunta ba
za su warke daga wannan makantar ta aikin sihiri ba har sai an
xebo ruwan dake cikin rijiyar dake tsakiyar fadar Darul sabar
ta wanke idanunta da shi, idan muka isa gareta muka sanar da
ita buqatarmu babu shakka za ta taimaka mana ta kuma sanar
damu bayanan da bamu sani ba, game da ita wannan fada, ko
don mu xebo mata ruwan dake cikin wannan rijiya ta tsakiyar
fadar ta warke daga halin makantar ta aikin sihiri da ke tare da
ita” Zuhairu ya sake cika da mamaki ya dubeta ya ce da ita.
“To ita da take cikin halin makanta ta yaya za ta iya
karanta wannan rubutaccen saqon dake jikin wannan fatar?”
Buniyatu ta yi murmushi sannan ta ce da shi “Idan muka isa
gareta za ka gani har ma da wasu abubuwan ban mamaki da
al’ajabi daga gareta, don Allah ya yi mata baiwa gane duk
abinda ya kusanceta koda kuwa tsutsune ya wuce a sama ba
75
BAKAR GUGUWA
tare da ya yi kuka ba, idan ta ji hucin iskarsa za ta faxa maka
sunansa kuma babu kuskure ka ga shi ne ya wuce”
Zuhairu bai sake cewa komai ba ya ci gaba da mamakin
wannan