ne a zubo maka ne..?
Kai ya girgizamin kafin yace"Bari mu yi sallah naji an fara kira ma"
Ina shirin mgana Yaya Ishaq ya fito Daga bangaransa, da Sauri bayan sa Zainab ne da kanwarta,Wacce ke jan Hannun yarinyar da suka zo da ita baiwar Allah tana ta kuka.
Ganin su hankali tashe yasa Jamal ya mike cikin wani yanayi yana fadin"Me ke faruwa ne..?
Zainab ne cikin rawar murya tace"Farhan..Ba mu ga farhan ba"
Sai abun ya bani mamaki suna nufin basu ga Farhan goye a bayana ba..?
Kafin na iya mgana Zuzu ta mari yarinyar nan Lokaci d'aya tana Hankadeta cikin fada tace"Ina Farhan.?wa kika bama shi..?
Yarinyar sai ta kasa mgana sai kuka Ya Ishaq ya fara fadin"To ku ina kuka shige ku bar ta dashi..?
Zainab ta fara fadin"Muna ciki ni da zuzu muna mgana mu ka bar Farhan hannun Shema'u"
Ganin abun nasu ya koma kan yarinyar har Ya Ishaq ya fara fada ita kuma sai ta kasa mgana ta Dago tana kallona kafin nayi mgana da Sauri Anum tace"Jaririn Anty..?ga shi nan Umma ta goyasa"
Sai kallo ya koma kaina ni kuma sai na juya bayana suka ga Farhan goye a bayana,yana barcinsa cikin kwanciyar Hankali ina jin su suka Sauke ajiyar rai a tare Zainab tace"Thank god.."
Cikin yanayin mganata nace"Na shiga ne na iske yana ta kuka na karbesa ashe cibiyarsa ke ciwo shiyasa yake Rigima"
Kamar kiftawan ido nagansu a gabana,suna rige rigen kwancen goyen bayana ba Ya Ishaq ba,sannan ba Zainab ba kanwarta ba,zuzu ce ta kalleni tana fadin"So kike ya karye kafarsa..?ba'a fara goyasa ba"
Ni dai ban damu ba da Sauri na Sauko shi Tare suka karbesa ita da Zainab din Mamaki ya rufeni Lokacin da Ya Ishaq ya faramin fad'a meyasa ban yi mgana ba ina ji ana neman Farhan.
Na kallesa cikin yanayina Kafin nace"kayi hakuri na zata ka gansa a bayana"
Cikin Fusata yace"In da na gansa zaki ji muna neman sa..?
Kuma kada ki kara goyasa tunda bai saba ba,Ba irin yaran ki ba ne da kika Saba goyasu ba"
Kamar wata wawiya haka na bisa da kallon Zainab ta kara fadin"Honey kafarsa bata samu matsala ba ko..?
Tafada tana nuna masa suka Taru suna kallon kafarsa yaron suna Tattabasa kamar na shafamai mugun abu,Cibiyar Ta bude tana kallo Zuzu ta leka tana fadin"What is this..?
Wannan kayan fa..?
Tafad'a a wulakance,karbansa tayi Tun anan ta cire mai kayan da na sakamai,Ita da kanwarta suka koma ciki Shi kuma ya bisu,kamar wani bita zai zai,ni dai da kallo na bisu Jamal ne, ya koma zauna yana fadin Allah ya kyauta.
Yaran kuma duk sun yi wani iri,ganin abunda ya faru ni Dariya ma suka bani wai kafarsa zata samu matsala Saboda goye,Allah sarki rayuwa da goye na illa da tuni mu kan mu mun samu illah Tunda a baya kafin zamani ya zo da sauye sauye goyen aka sani ba wani gayu da feleke feleke irin na yan zamani masu nasaba da boko ya gama ratsasu ammh irin mu yan gargajiya ai goyen muka sani.
Daganan dakina na koma Dauke da Ahmad araina nace in na goya nawa ai ba mai cewa zan karya masa kafa,Amir da Musty tare da Babansu da Uncle suka tafi masallaci ni kuma muka yi namu ni da Anum.
Daganan ta tafi bangaran Baban nasu,Ta damu sai taje sai nace ta tafi,Su Amir kuma sai da suka yi Isha'i suka dawo suma ban kara ganin su ba Bangaran suka shige Jamal kadai ne afalo na zubo mai abinci yaci muna dan Taba Hira sama sama bai jima ba yayi min sallama ya tafi.
Daki na koma nayi wanka nayi ma Ahmad,na shiryasa nan da nan sai barci yau bai yi rigima ba sosai su Anum sai goma saura suka Dawo Daki suna bani labarin sun ci nama da Ice Cream,Amir dai bana jin bakinsa sai bakin Anum da baya gajiya da mgana.
Washegari ba makarantar Boko sai Tahfeez tun safe nayi musu shiri suka wuce,Shinkafar jiya data rage na Dumama ma yara sukaci suka tafi,Sai Sauran Taliyan data rage na Dafa musu da miyar suka tafi da shi ni kaina Sauran Shinkafar naci bamu da dankali ba kwai ba komai na Kayan breakfast ballatana nayi musu sai na kama kaina,ina gama abunda zan yi na koma daki bayan na tattara kayan yara da suka zubar afalo.
Dakin su na shiga nayi musu kaye kayen kayan da suka watsar sannan na koma nayi wanka na yi ma Ahmad daman na Dama mai kunninsa na dura masa yasha sai ya cigaba da Wasan sa,Ganin ban da wani abu da zan yi sai na dauko Qur'ani na fara karantawa ina cikin karatun ne naji Muryan Yaya Ishaq na kiran sunana sai da na kai karshen Ayan sannan na Tsaya Daga bakin kofa ya tsaya Ahmad na ganinsa ya fara tafiya wajensa yana Washe mai baki ya Dauke sa ya daga sama yana fadin"Ahmad ka zama kato yanzu"
Shi ko sai bangala Dariya yake yi.
Hijabin jikina na gyara sannan na kallesa ina fadin"Ina kwana.."
Ya amsa ba tare da ya kalleni ba ya cigaba da fadin"Ba abun karyawa ne..?
Kai tsaye nace"Babu komai na cefane shinkafar jiya ce da nadafa ta rage muka dumama muka ci ni da yara"
Shuru yayi bai kara mgana ba daganan ya fice Dauke da Ahmad ashe kasuwa ya tafi yayo mana Cefane duk da bamai yawa ba ne zai iya isa har bayan sun tafi muma yayi mana Saura.
Na rana kadai yace nayi Inaga a waje ya siya musu wanda zasu karya da shi,couscouss nayi musu da rana mai Hanta da kayan lambu,basu fito ba nima ban bisu ba sai bayan La'asar na shiga muka gaisa sama sama Farhan na Hannun kanwar ta kamkamesa sai ban zura kaina wajen karbansa ba,na fito na koma Daki Ahmad kamar ya sani yaki ko sauka yaje wajen zainab din data ke kiransa ya lafe ajikina.
Tunda suka zo suna bangaransa komai sai dai na shigar musu da shi ban damu ba domin nasan lada zan samu ciyar da su din da nake yi sannan Gidana suka zo akwai hakkin abinci su a wuyana.
Kwanansu uku da zuwa Ya Ishaq yace na shirya zamu je gidan Mama na gaida iyayan zainab,Da daddare mukaje dukkanmu har da yara da ita Zainab din sai da naga mahaifiyarta da mahaifinta naga inda suka Dauko Kyan Fuska Mahaifiyarsu Hajiya Halima mun gaisa cikin Sakin Fuska Mahaifin su Dr.Lawal ya amsa min a Wani karkace ya kalli yarsa yana fadin"My dota wannan ce abokiyar zaman taki..?
Ta dagamai kai tana fadin"Yes Daddy"
Ya kalleni ina Duke gabansa Ahmad na Hannuna kafin yace"Sannu"
Nayi shuru domin ban jisa ba Itace tace"Daddy ta na da problem din Hearing sai ka daga murya"
Ido ya ware kafin yace"is that serous.."?
Kai ta gyada mai sai naga ya daga glass din sa sama yana kare min kallo araina sai naji girmamsa ya zube ai shi Babba ne kuma namiji irin kallon kurillah dayake bina da shi bai Dace ba.
Su Amir kuwa da suka gaishesa ya amsa yana fadin"Bakaken ya'yan Ishaq kuna lafiya..?
Naji abunda yace sai naji ban ji dadi ba saboda su yara ne abu kad'an za'a fada su dauka wani abu ne Jikansa ya amsa yana ta mai wasa Anum nata son ya bata ta Dauka yace"No..No..baza ki iya ba kada ki kada shi..Kinga farin yaron da babu a gidan ko..?
Duka har su Mama suna falon Ammh ba wanda ya damu da mganarsa sai ma Dariya da Mama tayi tana fadin"Wlh kuwa Alhaji uwar ai sai dai in ta Haihu su dauko bakin Fatarta"
Hajiya Halima ce duk bataji dadin Mganganun ba sai ta juya tana yi ma Zainab mgana,ni dai ina zaune kamar wata yar aikin cikin su na kosa mu koma gida,aiko sai wajen goma muka koma gida,Da safe ina yi ma su Amir shirin makaranta Amir ya kalleni yana fadin"Umma menene baki..?
Gabana ya fadi na kallesa na kasa mgana ya kara cewa"Umma baki ba abu ba ne mai kyau..?
Da Sauri nace"Da baki da fari duk abu ne mai kyau Amir kaji ko..?
Ban kara basa damar mganar ba saboda bansan me zan ce mai a gaba ba,Bana so ya'yana su fuskanci abunda na Fuskanta tsawon shekaru
Ashe basu tsira ba Dole dai sai an goranta ma ya'yana kwanansu shida Zainab din tagayamin washegari zasu koma saboda ayyukansu sun zo sun gaishemu tunda naki zuwa nace mata zan zo in sha Allahu.
Zainab ba ruwanta macece Faram Faram ko ta na da wani abu aranta bata taba nuna min ba Kanwarta ne mai D'agawa da isa harta su Amir basa Rabanta,Har Anum da take da Son Jama'a basa zuwa kusa da ita ta cika Fad'a da isa da fadin rai.
Ni ban isa na hana su Amir shiga bangaran Mahaifin su ba,Suna son Daukan Kaninsu ni kums ban isa na Hanasu ba ai dan'uwansu ne ni bansan abunda ya faru ba da yammah bayan sun dawo daga makaranta Kayan su kadai suka cire ko abinci basu tsaya ba suka tafi chan wajen Farhan har da Amir da bai cika shiga ba in dai ba Tare da Babansu ba.
Ina kitchen ina Zuba musu abimci Amir ya shigo har da hawaye a gefen Idanuwansa na kallesa ina Fadin"Babana wa ya tabamin kai..?
Bai min mgana ba ya fita nima na Dauki abinci zuwa Falo na ijiye Saman Cafet din dake Falon na isa ga Amir daya zauna yayi Tagumi.
Na cire hannun Tagumi ina Fadin"Uhm..gayamin wa ya tabamin kai..?ko Anum ce ta tsokane ka..?
Cikin ido ya kalleni yace"Umma kin ce baki abu ne mai kyau..Ammh yar'uwan Anty tace min ni baki ne kada na Shafa ma Farhan baki na"
A rarrabe ya fadi mganar kuka yaci karfinsa Amir na da zuciya shiyasa bai cika Hayaniya ba.
Jawosa jikina nayi na Rumgume ina Fadin"Ya isa..Shiii..Ya isa"
Na dagosa na Share mai Hawaye ina Fadin"Kada ka damu da mganarta Da fari da baki duka Hallitan Ubangiji ne sannan Duka d'aya suke a wajensa.."
Zai kara mgana na girgiza kai ina Fadin"Ya isa zauna ka ci abinci"
Bai yi musu ba ya zauna sai dai sai ajiyar zuciya yake saukewa Raina sai naji ya baci taya zasu rika Gurbatamin Tunanin yarana Amir dan Shekaru tara da wani abu suna neman sakamai Tunanin banza.
Ina cikin Tunanin naji yace"Umma su Anum suna wajen Anty"
Kai na gyada mai ina fadin"Bari naje na taho da su"
Kai Tsaye bangaran nashi na shiga Zainab din bata falo sai kanwar nata,Sai yarinyar dake kula da farhan Tana rike da shi ita kuma Zuzu tana danna wayarta Anum da Musty suna ta wasan su ya'yan Anty ne su.
Ina shigowa kai tsaye ita na Nufa ina Fadin"Me kika fad'ama Amir..?
Da yanayin mganata ta Dago tana kallon kafin tace"Ni..?
Lokaci daya tana nuna kanta tana wani tabe baki ban damu ba nace"Baki Tunanin shi yaro ne..?in bazaki bari ya Daukesa ba,sai ki hanasa ba wai ki gayamsa mganar da Hankalinsa bazai iya Dauka ba.."
Ta kuramin ido tana kallona ban damu ba na cigaba da fadin"Kada ki kara gayama yara na abunda zai Dame su bana so..Ke bakuwace ki gama bakuntarki ki tafi bana so ki shiga Tsarin Tarbiyan yara na"
Har na juya na juyo ina kallonta Lokaci da'ya ina Fadin"Sannan in baki sani ba ki sani da Bakin da Farin duka Hallitun Ubangiji ne sannan d'aya suke a wajensa Launin fata bazai taba zama wariya ga musulmin kwarai ba"
Daga haka na juya na kama Hannun Anum Da Musty muka fice ina kallo Har Zainab din ta fito daga cikin Dakin ta tsaya tana kallona ni kuma ko kallonta ma ban yi ba.
Haka kurum naji ni zan iya Daukan kowani cin zarafi ammh bazan aminta arika cin zarafin yarana ba a bata musu Tunanin su ba Shiyasa naja mata kunne tun da wuri.
Ni ban san ashe wannan mganar tajawo min bala'i ba sai da Daddare sai ga Mama da mahaifan Zainab din Har da Anty Binta sun zo gidan,Ya Ishaq da bai yini a gida ba shima ya Dawo Kirana kawai yazo yayi da kansa Fuskar nan tasa a hade kamar Hadari Allah ya taimake ni yaran sun kwanta da wuri da a gabansu za"a cimin zarafi.
Ima fitowa tun da naga mama da Anty Binta na sadakar wannan taron nawa ne sai kanwar Zainab da ke jikin Mahaifinsu tana ta sharban kuka Fuskar kowa ba fara'a na samu gefe na zauna ina gaida su Mama ko amsani batayi ba ta fara dakamin Tsawa tana fadin"Rike gaisuwarki mara Mutumci me wannan yarinyar tayi miki kika zageta kika ci mata Mutumci..?
Sai da ta fad'a na Dago ina kallon Zuzu din har tana wani matse kwalla da majina sai alokacin na Fahimci komai ban ji nayi nadama ba cikin yanayin mganata nace"ni ban zageta ko naci mata mutumci ba..nayi mata fad'a ne"
Anty Binta tayi zaraf tana fadin"Fada..?Sannu uwarta yarki ce da zaki tasata kina mata fada ishasshiya.?
Hajiya Halima ce tace"a bi a sannu Hajiya"
Mama tace"Hajiya ai bata da mutumci ne..Daman bata so auran Ishaq da Zainab ba,kuma tun tuni take neman daman cin mana mutumci bata samu ba sai yau"
Ni dai sai na kasa mgana Yaya Ishaq ya kalleni ya watsamin Harara yana Fadin"Daga kawai ta hana Amir Daukan Farhan Saboda bazai iya Daukansa ba sai ki bita har Daki ki zageta ki zagi iyayanta sannan har kina ikirarin cewa gidanki ne uban wa ya ce miki nan gidan ki ne..?
Ko da sunan ki na siya gidan ban sani ba..?
Kaina na kasa na kasa mgana ina jin wannan cin mutimcin Mama tayi kafyci tana fadin"Ahto tambaye ta dai"
Sai kawai na samu bakina da Fadin"Ku yi hakuri ba.."
Muryan Dr.Lawal ta katseni a Fusace yana fadin"Sorry for ur self..Akan ya'yana zan iya shari'a da koma waye..Daga tazo gidanki sai ki ci mata Mutumci..?ke ba domin Ishaq ba kin isa ki ga Zuzu a inda kike..?ai kalan zaren ba kalan yadin ba ne..Ba domin ina jin kunyar shi da iyayansa ba da sai kin gayama aya zakinta akan kukan da kika sa yata tayi kin san wacece ita..?ko ni bana sakata kuka Koda yaushe ina Tattalin Dariyan ya'yana ne ba Zuzu ba ko Zeey da kuka Hada miji kika kara yarda kallon Banza ma ya had'aku sai nayi maganinki sai na saka an batar dake da Dangin ki gabad'aya"
Yafad'a cikin Kaushin murya Hajiya Halima kunya ya kamata ta kasa mgana ta Dafe kai Zainab ce tace"Is ok Daddy. "
A fusace yace"No zeey kinsan ba na Had'a ku da komai a nan duniyan ko..?
Ko mommy ku ta sa ku kuka ina jin Dalili ballatana wata shara chan"
Hawaye suka wankemin Fuska ni ce shara..?ina jin Zainab din na fadin"I know Daddy..Forgive her bata sani ba ne zuzu plz ki bar kuka kada kanki ya fara ciwo..Gobe zamu koma Abuja is ok kin ji..?
Kai ta d'aga mata ta koma ta lafe jikin Baban nasu yana share mata hawaye yana fadin"Am sorry Angel..am sorry"
Mama tayi kayci kafin tace"Ai daka Dauki matakin da kayi niyya Alhaji da sai tafi gane matsayinta"
Hajiya Halima tace"Hajiya komai ya wuce insha Allahu"
Ni ko ina zaune jikina ya gama mutuwa hawaye suna zubomin na saka gefen Hijabina na share Yaya Ishaq yace"Ki dago ki bata Hakuri tunda ita kika yi ma laifi"
Na kasa Dagowa sai ya dakamin Tsawa haka na Dago fuskata Shabe Shabe da Hawaye cikin yanayin mganata nace"Ki..yi..hakuri.."
Juyawa yayi yana fadin"Ta baki hakuri am sorry Zuzu.."
Kai ta gyada ta na kara kwanciya jikin Baban nata,Mama ta kalleni tana fadin"Sai ki tafi ki bamu waje mara mutumci"
Na tashi da Sauri na shige Daki na,na fada kan gado ina sakin kuka na bansan Lokacin da suka tafi ba sannan ni kaina bansan adadin Lokacin da na Dauka ina kuka ba kaina ya fara ciwo,ko sallar daren da na Saba a daddafe nayi saboda Jiri naji yana Dibana da Safe dakyar na iya tashi na shirya yara suka tafi makaranta kuma ahakan nayi musu abun karyawa na bar musu a kitchen na koma Dakina nasha panadol na kwanta ina jin kamar zazzabi zai kamani.
Ban san tafiyar su ba Domin Wanda ya ijiyeni bai min sallama ba Ballatana Dangin da sukace zasu batar dani,ni da Dangina Saboda an saka yar gata kuka,fitowa kawai nayi naga gidan wayam,sannan na Fahimci Daga ni sai halina acikin gida Zuwa yammah jikina ya Rikice jiri da Ciwon kai nasan jinina ne ya hau Allah gafurin Rahimun a ranar sai ga Hafsaatu ta zo Allah ya aiko ta Domin ta taimakeni ta iskeni kwance ba Lafiya ita ta taimakamin tayi ma yara Girki ta kula da su.
Ina da Sauran mganina na Hawan jini shi na sha bayan naci abinci,Gari na wayewa kamar waraka daga Allah sai naji Sauki,Naji dadin zuwan Hafsatu Goggo ta aiko ta ta dubami tazomin da su Kuka,kubewa,tsaki,garin kunu da wake,har da kudi in ji Goggo na karba araina ina roko ma Goggo Gida a gidan Aljannah Saboda yadda ta rike zumunci bata yada shi ba.
Kwana Biyu Hafsatu tamin ta koma saboda makaranta sannan tana kunshi yanzu sosai take samun masu zuwa nayi mata murna saboda sana'a itace mace a wannan zamanin da muke ciki.
*Littafin KANA NAKA book2and3,paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.*
*Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223*
*Janafty*
*KANA NAKA..!*
*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT 08066726866
Ni MMN MUJAHID Ina da kayn gyara kala kala na kasa da sama Ina Saida supplement da kayan mata kala kala cikin sauki Mai kama da kyauta
Hjy ta ki ajiye kunya kifitu kiyi bayani matsala ki abaki ABINDA yaddace Dake
Ina matan da ke FAMA da bushewa gaba
Ina maccen da take a bushe kamas ba niima miji sai yasa yawun sa ku BASILIN 😳
Ina matar da kishiya ta tayi mata zarra ga miji ke rasa Ina matsala take
Ina wadda mijinta kamar kurma baya nuna ya gamsu Dake Dan ku ayi ku abari duk dai suke dashi
Shin ke ku y'ar kuwa ga mijin ki baya Yi da sanbatu in kinji ana Fadi sai kece karya ce
Nazo muku da hadin Zuma wadda duk zata magance way'anga matsalolin cikin ikon Allah wanna Zuma ta samu yabo ga duban mutane Sha yanzu magani yanzu ce Banda haufi akanta wanna Zuma tana ta yadda sha'awa Kai tsaye ruba babba 2500 karama 700👌👌
MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT MUNA SAKWATO DA KEBBI INA AIKAWA KU INA 08066726866
IN BAKI SHIRYA BA KIBARI HAR KI TASHI SAYE 😀
*🅿️15*
Haka nan na cigaba da gungura rayuwata cikin dad'i da akasasin na cire damuwar komai a raina na riga nasan Yaya Ishaq ya zabi zainab daman a kaina sannan yanzu da abubuwa su kara kamari sai na Fahimci bayan ni ma ya zabi Sabon Iyalansa da Zainab ta fara tara mai fiye da ya'yansa sai na saka araina ni kadai suke da bayan ni ba su da kowa
Nasan zafin maraici nasan zafin rayuwa a gidan da ba gidan ku ba,bana fatan daya daga cikin ya'yana su fuskanci abunda na Fuskanta shiyasa duk kai da kawo na da Hakurina saboda su ne.
Ko da yaushe in na yi sallah ina D'aga hannuna sama nayi ma Allah kirari da sunanayensa matsarkaka sannan na yi masa magiya da naci domin ya sama min mafita kan rayuwar da nake ciki nasan bani na Tsara ma kaina ba Allah ya tsaramin kuma yaso ya ganni a haka to bazan yi masa butulci ba, sai dai zan rokesa ya sama min mafita. cikin irin kyakyawan mafitar da yake sama ma Salihai daga cikin bayinsa.
Sannan a koda yaushe addu'ata akan ya'yana shine Allah ya shiryamin su Allah ya jibanci lamarin su Allah ya sa su kaunaci junansu kada Allah ya Dora musu hassada da son kai Allah yasa su daukaka su haskaka acikin al'umma.
Na cire Ishaq da abunda ya shafeshi acikin raina,Domin ina da tabbacin an kawo gabar daga ni har shi mun Fahimci wani irin zama muke gudanarwa ko da yake ni ai na Dad'e da sanin irin yanayin zamantakewa ta dashi shine a wajensa yake kallon duk abubuwan da yake yi min ahakan ma kamar yana min alfarma ne.
Tunda suka koma ban kara jinsa ba,Nima ban damu ba tunda ko ina da wayar baya nema na sai na maida kaina wajen kula da ya'yana,Ba na ganin kowa sai jamal shima sai in ya shigo anguwar tamu ne,Badariya kuma Mama ke hanata zuwa tunda basu koma makaranta ba sai na Dad'e ban ganta ba.
Ko cefanen mu ya kare sai dai nayi ta Dubaru na, saboda yara in ni nayi hakurin yunwa su baza su iya ba,akwai Ranar da sai mu yini bamu ci ba Daga karshe Garin kunun Ahmad nake dama musu su sha su kwanta,saboda bani da inda zan fita in nema koma naje tona ma kaina asiri zan yi sannan daga karshe ace karya nake yi,ana ganina a katon gida sannan an san mijina babban ma'aikaci ne ba kowa ba ne zai san yanayin da yawan mata suke Fuskanta acikin katon gida ba,da yawan mu ai kurace lullube da fatar akuya.
Ko sa'adatu da muke zumunci da ita sosai ban taba bud'e baki na fad'a mata matsalata ba sai dai yau da gobe bata bar komai ta fara Fahimtar gidan ne kawai da mijin ammh babu wani Sauran jin dadin da nake ciki da ni da ya'ya na har ta kai yara su ka daina zuwa da Abinci makaranta Saboda komai ya kare sai dai ruwa,Tsakin da Goggo ta aiko min dashi da garin Danwake duk ya kare a kitchen di'na ko kwaran Shinkafa bani da shi ban kuma san inda zan je na mema ba.
Mun yi sati cikin wannan yanayin Duka Dubaruna sun kare nima na kasa,Ranar wata laraba ko makaranta basu je ba,Basu ci abinci jiya da Daddare ba haka da Safe Anum da Musty suna kwance suna fama da ciwon ciki kuma nasan na yunwa ne Ahmad kuwa ya lafe ajikina sauran garin kunu ne na dama mai kadan ya sha shima ba domin ya ishesa ba,Amir kuma saboda ya na babba yasa bai nuna gazawarsa ba,Ammh shi kan shi yana jin yunwa ni kaina Dauriyan kawai nake yi ammh na fara Sarewa.
Muna zube afalo kamar kayan wanki kukan zucci nake yi na kasa na Sarari na Daga hannuwana sama nace"Ya Allah ga baiwar ka nan Fa'iza ka fini sanin Halin da nake ciki..Allah kayi gaggawan kawo min mafita d'aya daga cikin mafitar ka ya Allah"
Ban gama sauke Hannuwa na ba naji Sallama ina d'ago kaina naga Sa'adatu ashe Haruna ne yace ta shigo ta duba yau su Amir basu je makaranta ba Allah Sarki bawan Allah wajen wata biyar Yaya Ishaq bai biyasa kudinsa ba ammh bai taba gazawa daga kai su makaranta ba har mgana nayi mai ko zai bari ne yace min bakomai yiwa kai ne.
Ko ban fad'a mata ba ganin mu cikin wannan yanayin ya bata tsoro ta kalleni cikin Tausayawa tana fadin"Maman Amir Allah yasa dai lafiya na gan ku duk a kwance sannan Mallam yace yau su Amir basu je makaranta ba shiyasa yace na shigo na duba ko kuna lafiya?
Ina kokarin mikewa Ahmad ya lafeni na jingina da kujera ina fadin"Lafiya lau Sa'adatu yau din dai basu samu zuwa ba ne"
Shuru tayi kafin ta kalli su Anum lokaci d'aya tana fadin"Anum ko ba lafiya ne yau ban ji Surutun ki ba..?
Kawai sai yarinyar nan ta saka kuka cikin kukan take fadin"Yunwa muke ji tun jiya bamu ci abinci ba"
Musty ma sai ya fara kuka wai shima Yunwa Ahmad na jin su shima ya saka Rigima na saki baki kawai ina kallonsu na kasa mgana ta Dago tana kallo na kafin tace"Haba Maman Amir sai ki bar yara da yunwa in suka samu wata matsalar Dalilin haka fa..?
Sai na kasa mgana Hawaye suka cika kwarmin idona cikin wani yanayi nace"To ya zan yi Sa'adatu..?
Bani da wata mafita sai wacce ubangiji ya kawo min kawai"
Cikin mamaki tace"In shi babansu baya gari ba ga gidan iyayansa ba,bai kamata suna garin nan kuna zama cikin wannan halin ba ai yunwa bala'i ce musamman ma ga yaran nan"
Mirmishin takaici nayi mata ban kara mgana ba da Sauri ta mike ta fita ba jimawa sai ga shi ta Dawo da kuni da yawa abotiki da Soyayyan Dankalin Hausa ta Diremin tana
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 17 Chapter of 25