Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
na koma D'aki duk da cikina na jin yunwa ammh na kasa cin komai a fatar bakina nake jin abinci bazai iya shiga ba sai kawai na sha Ruwa na koma ma kishingid'a ina kallon su Amir nata wasa Ahmad yayi barci,ina zaune a wajen har akayi sallar Isha'i sai na mike nace su bar wasa su sake yo alwala suzo muyi sallah Bayan mun idar Anum nata rigiman zataje wajen Daada dakyar na lallasheta da yayi barci,kafin su kwanta sai da suka kara cin abinci sannan nayi musu shirin barci sai da sukayi addu'a na tayasu suka Tofa sannan na baro Dakin nasu na koma nawa Ko barayin Shashen Ya Ishaq ban kallah ba Tunda suka shiga Ciki ban kara jin motsin su ba. Ni kuma na kasa barci da ya fara Fizgata sai na farka gajiya nayi da juyi na shiga tiolet nayo alwala nazo ina ta nafila sai wajen uku na Dare na kwanta shiyasa na makara sallar asuba rana ta farko da Ya Ishaq bai fito ya tara su Amir sun tafi masallaci ba Amir sai fadi yake yau Daada bai je masallaci ba ne Umma..? Sai nace musu yaje yaga suna barci ya kyalesu har nayi musu shirin hadda nayi abun karyawa Haruna ya Dauke su ya kaisu basu fito ba yaran dakyar na janye su suka tafi batare da sun ce zasu je gaida Daadan nasu ba. Suna tafiya nayi ma Ahmad wanka na shiryasa nima nayi wanka sai nasha Tea kad'an naji cikina ya Toshe Breakfast din Amarya da ango a kicthen na bar musu komai na shige D'akina araina nace me yasa zan damu..?Ai ya jingine auran mu alfarma yake min da nake zaune ma agidansa yana ci da ni.' *Littafin KANA NAKA book 2,paid book ne biya kudin karatun ki akan Naira N500 Regular posting sau d'aya a rana.* *Ko kuma tsarin VIP 1000 Posting sau biyu a rana akan wannan acct din 0552179550 Jamila Umar Gt bank,sai a turo shaidar biya ta wannan lambar 09069067488 Wannan karon babu tsarin kati,kowani tsari zaka yi ka turo ta POS,Mutanen mu na Niger kuma zaku tuntubi Kausar Aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223* *Janafty* *KANA NAKA..!* *Wattpad:JamilaUmar315* *Mallakar:Janafty* *Arewa book:Jamilaumarjanafty* MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT Y'A SKWATO__SAKINA HASSAN 08066726866 INA MATA Y'AN KWALISA MASU SON GYARAN JIKI MACCE DA TASAN KANTA KULLUM CIKIN GYARA TAKE INA MATA MASU FAMA DA RAMA KU KINSA KAYA BASU KAMA JIKIN KI 😫 INA MATAR DA ADDA JIKI BAKI DA HIP BAKIDA BAYA IN KINYI DRESS BAYANKI A SHAFE INA WADDA KE FAMA DA ZUBEWA NONO KU KE BAKI JIN DADIN GANIN SU KAMAR SILIFAS KINYI TA GYARAN BRST HAR KIN GAJI HJY TA GYARAN BRST WAHALA GARESHI DUK WADDA TACE MIKI GA MAGANIN BRST DA SHA ZAIYI TO KARYA TAFADA MIKI GYARAN BRST YANA SON JUREWA DA DAGEWA IN KIN FARA BA'A TSAYAWA INSHA ALLAH SAI KIGA SUN ZAMA NORMAL MUNA DA INGANTATA ZUMA BRST DA MUNKA SARRAFA DA KAYAN ORGANIC HERBAL SU MACA DASU AGUAJE WADDA INDAI KIN RIKE TA INSHA ALLAH ZAKI GA SUN CIKO SUNYI KOSHI RUBA 2 KU 3 SUN ISA YAZAMA MIKI YADDA KK SO 4K MUNA DA GARIN HIP DA BRST YAKE GYARA DA GYARAN JIKI DA KARIN NIIMA YAKE YI 4K MUNA DA INGANTATA ZUMA TA HIP ITA MA MUN SARRAFA TA DA KNGAN TATUN KAYAN ORGANIC HERBAL DA KE FIDDA MIKI HIP 6K MUNA DA ZUMA KIBA WADDA ZAKIYI FRESH DA BULBUL ITAMA RUBA 2 KU 3 ZATA YIMIKI YADDA KK SO 2K MUNA DA GARIN GYARAN BRST DA KARIN NIIMA SHIMA GUDA 2 KU 3 ZAKI SHA 2K GASKIYA DA AMANA ITACE NASARAR.MU MUNA AIKA KAYA KU INA CIKIN YARDA DA AMINCI MMN MUJAHID __SAKINA HASSAN MUNA SOKOTO DA KEBBI 08066726866        *🅿️09* Saboda barcin da ban samu jiya sosai da Daddare ba, ina zuwa shimfid'ar da Ahmad da ya yi barci nima sai na bingire barcin ya fara figata sama sama naji kamar ana kiran sunana a saman kaina Dishi dishi na bude ido na kafin naji ana tab'a kafata guda daya da sauri na mike zaune har wuyan rigana yana dan ja ya yage kada'n,Ido hudu muka yi da Yaya Ishaq da ke tsaye a kaina yana sanye da Riga da wando sauka'kku na zaman gida. Mitsike ido nayi kafin na fara kokarin saukowa daga kan gadon Lokaci d'aya ina Fadin"Ina..ina kwanaa.." Amsawa yayi da lafiya lau kafin yace"Ina abun karyawan mu fa..? Ina kokarin gyara daurin D'ankwalina nace"Yana kitchen" Juyawa yayi zai fita lokaci Daya yana Fadin"To fa'iza sai na fad'a miki abunda ya kamata ki yi..? Da kika gama sai ki shigo mana da shi ciki ko..? Daga haka ya fice nima sai na maramai baya shi ya koma Shashen sa ni kuma na fada kitchen na samu Babban Faranti na hada komai na nufi bangaransa yau ma ba kowa afalon sai dai duk sun yi kaca kaca da kwanukan da suka yi amfani da shi jiya Bayan nasauke na Hannuna ni na Duka ina tattara na jiya na kwashe na kai kitchen na Dawo Daukan jug da kananun kofina shi kuma Ya Ishaq ya fito daga cikin bedroom din sa yana ganina yace"Yauwa Fa'iza wai me kika yi mana na karyawa ne yau..? Kaina na kasa na lissafa mai Baki ya tabe kafin yace"Zeey kuma tace Fatan dankali take so da Safen nan" Kallonsa nayi kai tsaye Lokaci d'aya ina Fadin"Akwai dankali sai ayi mata" Da Sauri yace"Yauwa Hanzarta Fa'iza in dai yau bataci abunda take so ba Rigima zata dinga yi min" Ko kala ban kara cewa ba na fice Ina zuwa Kitchen sai da na yi wanke wanke sannan na fere dankalin na Dora mata ko araina ban ji Haushin su ba,Sai nake ganin ma ai taimako na yayi yana min alfarma ya bani wajen kwana sannan yana ci da ni duk da ya Jingine aure tsakanina da shi.. Kafin na gama ya leko kitchen din nan yafi sau uku ban gama ba yana ta fadin baya son Rigiman zeey,ina gamawa na juye mata a kula na kwasa na kai mata ina shigowa ya karb'a na Hannuna Lokaci daya yana fadin"Fa'iza tayani dauko sauran yau mulki take ji bazata iya fitowa ba tace kinsan mun sha gajiyan Hanya..Dayake tafi sabawa da Tafiyar Jirgi ita" Ni dai ban tankasa ba,Dayake ma ba Duka mganarsa naji ba yana gaba ni kuma ina bayansa da Farantin kayan karyawansu har zuwa cikin bedroom dinsa nan saman cafet din na Sauke komai ita Amaryan tana nad'e cikin Blanket dakin na bi da kallo komai ga shi nan a kasa hatta kayan da suka cire Kayan zeey din ta bakinsa duk gasu nan a zube a kasa kila wajen daukan wani abu ne ta zazzago kayan kasa ni dai kaina na kasa bazan iya juran ganin Ishaq ya sunkunya yana mata mgana a kunne ba. Mikewa nayi zan fice da Sauri cikin dan Daga Sauti yace"Ki tsaya ku gaisa da Honey mana Fa'iza" Dawowa nayi na durkusa nan gabda kofa sannan na Dago ina kallonta itama Lokacin ta D'ago ammh Rabin jikinta yana jikin Ya Ishaq ne da Sauri na maida kaina kasa ina Fadin"Ina kwana..?ya bakunta.? Cikin yanayin mganata Hannu ta Dagamin kafin ta juya tana ce mai"Honey ni dai zan rika daga mata hannu..kasan ban iya mgana cikin Ihu ba.." Mirmirshi yayi batare da yayi mgana ba sai ma karan Hancinta da yaja yana fadin"Kin gan ki ko..?ga Abunda kikace kina jin ci nan Fa"iza tayi miki ki taso mu karya kinsan nayi ma Daddy alkwarin zan kula dake sosai" Kasa kasa suke mganar ina jin tashin Dariyan su,ta kasan ido nake kallon su shi ya tallafota ta mike tsaye jikinta Daga ita sai wata rigar barci Fara iyakarta gwiwanta sannan shara shara ce ana ganin jikinta.. Ni dai kafafuwan su na gani a gabana da yasa nayi Saurin mikewa ina fadin"Sai..i..anjuma.." Ina jinta tana fadin"Honey ita tayi Dinner din jiya ka tabbata ba oder d'insa kayi ba" Ina ji yana gayamata da gaske ni nayi da karfi tace"Hy..Sai kuma ta koma tace"Sorry Fa'iza ko..? Ta fada tana kallonsa sai ya Daga mata kai kara kirana tayi da karfi sai na Dakata da Fitan na juyo ina amsa mata tana jikinsa har Lokacin ni kuma sai nayi kasa da kaina cikin mganarta da sanyin Muryanta tace"Kina jina..?.. Sai na Daga mata kai Da Sauri tace"U are good in cooking..I Mean..Honey plz Help me ka fadamata da Hausa zai bani Wahala" Ina jin Sautin Dariyansa Lokaci d'aya yana Fadin"Fa'iza Abunda Honey ke nufi shi ne Kin ,iya girki sosai" Baki ta washe tana gyada min kai sai nayi mata martanin Mirmishinta ban ce komai ba ta kalleni ta kara kallona ina gabansu ne shiyasa naji abunda take fadi"Honey ammh ba ka ce min matarka cousin sister d'inka ce Dad din ka ya aura maka ita ba..? Da kai yayi mata mgana cikin kara bayyana mamakinta tace"So meyasa bakwa kama da juna..? Infact She is  Blank and.." Sai ta kasa karisawa ta tsaya tana kallona ni kuma sai na kauce ma ganinsu idanuwana suna kallon Kwalliyar Cafet din dake D'akin. Kai Tsaye Ishaq yace"Kuma gata Mummuna ko..? Haka kike son fad'a ko..? Sai ta Rufe baki alamun taji mganar ta mata girma gira ya D'aga mata kafin yace"Yes ki fada kanki Tsaye ai ba karya kika yi ba Fa'iza bata da kyau..Yes Cousin Sister dina ce Ammh da daad din mu da nata baban D same Father suka hada uwa kowa da tasa..Shiyasa zaki ga muna da bambamci sosai da su" Ina jinta tana fadin"Ok" Daganan ni ko kara tsayawa jin su ban yi ba, na fice daidai yana ce mata"Shiyasa kika ga su Amir basa kama da ni..Ita suka debo gabadaya" Ammh nasan soon kin kusa Haifamin masu kama da ni Honey" Tashin Dariyan su naji ban ko Tsaya ba Sai da na koma Daki sai kuma naji san mganarta bata batamin rai ba,Komai yaje ya Dawo wanda baisan Darajata ba ne ya tayata suka tozartani Saboda na kauce ma Tunanin kayan su Amir da ya fara Taruwa na kwashe na kai baya na fara wanki ina yi ina tilawar Karatun Qur'ani acikin raina bana so kuma Tunani ko damuwa su shiga raina. Na gama wankin kenan ina Shanya sai ga shi ya leko cikin Shirin Fita sai Tashin kamshi yake yi da key din mota a Hannunsa. Gayamin yayi zasu fita sai yammah zasu dawo nayi musu fatan Dawowa Lafiya har ya juya sai kuma ya Dawo yana Fadin"in kin gama wankin nan Fa'iza ki shiga Shashena ki gyara saboda kinsan zeey bata saba kowani aiki ba chan ma yan aiki gareta  suke mata komai Dakin duk ya Hargitse ki dan kintsa mana shi kafin mu Dawo" Batare da wata Damuwa ba na amsa mai ya juya yana fadin na kula da Ahmad ya lekasa yaga har Lokacin bai tashi ba.suna fita ba Dadewa na gama wankin na koma cikin gida Bangaransa na shiga kamar yadda yace na gyara Hatta da Rigar barci da pant da Bra din ta bata Dauke ba nan ta Watsar da su ni na Tattara komai na gyara na kwashe kwanukam da suka yi amfani dashi na kai kitchen nazo na share Dakin na yi goge goge na Fesa Turaren kamshi na Rufe masa Shashensa na koma Dakina nayi alwalan sallar azahar bayan na Idar Ahmad ya tashi da Rigima ni kuma ban wani ci abinci ba sai na Hada Tea na bashi Nono na ba ruwa sosai aciki. Naji dadin jin jikinsa da Dama yau ya fara Dawowa da kuzarinsa. Yunwa ce ta kusa min illah yasa na tashi na Dafa Farar shinkafa naci da manja da yajin da Yaya Asiya tazo min dashi muka kwanta barci sai La'asar na tashi bayan nayi sallah na Goya Ahmad na Fada kitchen. Jallop din Cousscouss nayi da Kifi Saboda acikin Cefanen da Jamal ya kawo har da kifi,Sai na Dibi Naman jiya da ya rage nayi musu Ferfesu da shi. Kafin mangariba na gama komai Lokacin Haruna ya Dauko su Amir Daga makaranta sai da suka cire kaya muka yi sallah sannan na zubo musu abinci suka ci Anum sai tambayan ina Daada yake shi da Sabuwar Umman su nace sun fita ammh yanzu zasu dawo wasa waasa sai wajen tara da wani abu suka Dawo Lokacin ma ina koya ma Amir Haruffa ne Anum kuma suna ta wasa da Musty suka shigo suna ganinsu suka tashi suka nufesu gabadayan su suna musu oyoyo ita ta Daga Musty shi kuma ya Daga Anum sai ya Rungume Amir.. Daga inda nake ban tashi ba nayi musu barka da dawowa shi ya amsa ita kuma Hannu ta Dagamin saboda bazata iya Daga murya ba ammh Tana da Fara"a sosai nima sai na Daga mata Hannu. Su da yaran shashen shi suka shiga sai na mike na Shiga kitchen na kwaso musu abincin su na bisu da shi sun baje afalo yaran suna ta wadaka da Ice_cream da su Sweet har da gashishiyar kaza,Zeey din tana zaune gefen Ya Ishaq har kafadunsu na dukan juna tana mgana a waya sai dai ba Hausa take yi ba,sannan ba Turanci ba kamar dai Fullanci. Na sauke farantin Hannuna na mike kenan ya kirani na Dawo na durkusa a gabansu ya tambayeni abunda na Dafa na gayamai ya juya yana kallonta da ido suka ma juna mgana naga ta tashi tana wani Rangaji Har Lokacin tana mgana cikin Shagwaba ta shige ciki shi kuma kamar wani Sauna ya Bita da kallo ni kaina na kalleta ballatana shi. Ahmad ya tambaya nace yana barci Sai cewa yayi"Meke damun yaron nan ne..?barcin sa ya fara yawa fa! Ni dai ban ce komai ba na tashi na fice bayan nace ma Amir suzo su kwanta da Wuri Saboda makaranta gobe. Falo na koma na Tattara musu littafan da jakunkunan su na kai musu Dakin su na gyara musu in da kowanne zai kwanta na fito musu da kayan barcin su,nayi ta jiran su har goma ta wuce suna tare da su sai kawai na wuce Dakina naje na Duba Ahmad sai sharan barcinsa yake haka kawai na kasa barci batare da ya'yana sun kwanta ba,Ban samu natsuwa ba sai da naji Hayaniyar su afalo na fito falon Amir nayi ma fad'an meyasa basu zo sun kwanta da Wuri ba su san gobe suna da makaranta"? Anum ya kallah yana fadin"Umma Anum ce taki tasowa." ina kai kallona wajenta ta wani kwabe Fuska tana Fadin"Umma ni wajen Anty da Daada zan kwana" Sai yarinyar ta bani Dariya in ban yi wasa ba Anum ta Dauko iyayi wajen Ubanta to in ba Salo ba da shi ta Saba kwana ko yaushe ta san Anty ma..? Dariya nayi, da yasa yaran suka Tsaya suna kallona hannunta na kama da na Musty Amir na bayan mu zuwa Dakinsu Lokaci daya ina Fadin"Baki san ba kyau yaro ya kwana inda Babba yake kwana ba. ? Na fada ina zama gefen karamin gadon Anum cikin kallona tace"Umma to ba Ahmad na kwana a wajen ki ba..? Kai na girgiza ina Dariya Anum akwai kalkalin baki cikin Mgana ta nace"Shi bai girma ba ai bai kai ku girma ba..Da shima ya kai kamar Mutsy ko Anum dina zan daina kwana da shi zai Dawo Cikin yan'uwansa" Zata kara mgana na Dakatar da ita da Fadin"Shii..Sai gobe sai mu karisa Anum yanzu Dare yayi gobe akwai makaranta ku sauya kaya Mai jin Fitsari ya shiga yayi kafin ku kwanta" Suka amsa min da Toh ni na saka ma Anum da Musty kayan barcin su araina ina Tunanin in na yaye Ahmad ya kara girma zai dawo kwana wajen su Amir ita kuma Anum Lokacin ta kara girma ita macece sai na cireta cikin yan Maza na koma muna kwana tare. Sai da na tabbatar da sun kwanta Mun yi addu'an barci na taya muka Shafa jikinsu sannan na baro Dakin na koma nawa nima nayi shirin kwanciya yau da wuri barci ya kwasheni,Kila Saboda na gaji ne sosai sannan abun mamaki har barcin rana nayi ammh kuma na samu ishashen barci da Daddare. Da Safe ma kamar jiya ne har su Amir suka tafi makaranta basu fito ba Haruna mai adaidaita sai da yayi min mganar kudinsa yace ayi ma megidan Tuni Tunda yaga yana gari nace zan gayamai in sha Allahu yayi hakuri. Kamar jiya yau ma har kuryar Daki na kai musu abun karyawan su ita Zainab din tana Tiolet kamar yadda yace ban jira ta ba nayi fitowa ina gasgata mganarsa da yace bata aikin komai bata ma iya ba ganin yadda komai kuma ta kara Birkitasa kamar jiya ban gyara ba yau din basu fita da wuri ba sai yammah,Suna cikin Shashen sa sun kule,Ga shi nayi ta Dakon sa nayi masa mganar Haruna basu fito ba sanda kuma suka fito suna tare da ita Hannunuwan su sarke da juna shiyasa ban yi mai mganar ba yace min gobe zasu koma Saboda aikin su zai kaita gidan Anty Binta da gidan Anty Mahma sai kuma su zaga gari nayi musu adawo lafiya. Yace kada nayi abinci da su zasu ci a waje na amsa mai da toh sannan ya kara Umartana da in shiga bangaransa na gyara musu kamar jiya nan ma na amsa mai da toh. aiko basu dawo ba sai goma da Rabi na Dare ina Falo ina fama da guga Anum da Musty sun gaji da jiran Dada da Anty  sun yi barci Amir ne ke taimakamin in na goge daman kayan su ne, sai ya rika Dauka D'aya bayan d'aya yana kaima kowa cikin Dirowan kayansa. Albarkacin Zainab har aka kawo ma su Amir Chips da su pizza,Sai kuma suka Tarar da su Anum din sun yi barci Ya Ishaq shi kadai ya shiga bangaransa ita ta tsaya tana waya naji dai Tana ta ambaton wani suna Daddy tana mgana cikin shagwaba irin na ya'yan gata..sai da ta gama sannan ta Dagamin Hannu sai nima na Daga mata Amir ta yafito da hannu yazo wajenta tana mai mgana ni ban ji me take fadamai ba. Ta mike tana kallo na inaga abun gugan da taga ina yi ya bata mamaki kusa dani ta kariso da takalminta mai Tsini ta Duka a gabana tana fadin"Sannu fa" Na amsa mata da mirmishi kallona tayi kafin tace"Hannun ki da bayan ki basa ciwo ne..?ba mai wanki da guga ne..? Sai ta karkato kanta tana Fadin"Kina jina..?. Sai ta ma bani Dariya cikin yanayina nace"Ina jin ki mana..ai ina jin mgana in kika yi a kusa dani" Kai ta jinjina kafin ta kara kallona ta ce"Sannu fa" Na kara amsa mata sai tace"kina kokari fa..na ji dadin girkin ki..In da a Abuja kike da kin samu kudi..Gidajen mu duk kukus suke d'auka sannan irin ku kuna samun aiki a manyan Restaurant wajen saida abinci kin gane..? Tafad'a tana kallona Saboda Hausan nata sai a hankali bai zauna ba sai na daga mata kai alamun ina jinta sai kawai taci gaba da fadin"Meyasa baki yi karatu ba Fa'iza..?na tambayi Honey yace kece baki so why.? Sai kawai na kalleta abunda na Lura da Zeey din macece faram faram bata da girman kai ko D'agawa sannan ita Kai Tsaye ce duk abunda ya shige mata Duhu sai ta yi mganarsa shiyasa ban damu da mganarta ba sai na yi mirmishi kafin nace mata"Ba ni ba ce ba na so..Karatun ne bai dace da Kaskantattun mata irina ba..Wad'anda basu da gata sannan masu nakasun ji irin ta Lalurata.." Kallona ta tsaya tanayi ina ganin bakinta na motsi ta kasa mgana ita kuma tana so tayi mgana ammh hausan bata san yadda zata min na gane ba,Muna cikin hakane sai ga Ya Ishaq ya leko ya kirata sai ta tashi ta tafi ammh sai da ta waigo ta kalleni nima na kalleta ina tunanin mamakin mganata take yo menene ban sanin mata ba. Daganan bamu kara haduwa ba sai da Safe da zasu tafi,misalin karfe goma na Safe yara tuni sun tsufa a makaranta,ganin har suna shirin tafiya yasa na yi mai mganar Haruna ina ga saboda a gabanta ne yasa bai yi Fada ba,ya cire dubu goma sha Hudun sa ya bani Saboda duk wata Dubu takwas ne,Sannan ni kuma ya bani Dubu uku na rike a hannuna wai bashi da kudi nidai na amsa ina godiya,Zainab ta bani Hannu mun yi musahaba tana ce min"Sai na ganki kun zo min hutu Abuja ke da yarana" Mirmishi kawai nayi mata ta Dauki Ahmad har Haraban gidan na Rakasu ko Saboda ganinta ne yasa ya bude get din da kansa Dubu biyar ta bama Ahmad sabbi tace ya raba shi da su Anum,Har motar su ta bar Haraban gidan tana Dagamin hannu nima ina Daga mata bayan sun fice sai na maida get din na kulle na koma cikin Gida ina Sauke Numfashi. Ban zata haka amaryan tasa zata karbeni ba sai ga shi na sameta a yanayin da ban zata ba. Da yammah da Haruna ya Dauko su Amir daga makaranta na basa kudinsa yana ta godiya Anum har zata min kukan banza don nace Daada da Anty sun koma Abuja sai da nayi mata jan ido sannan ta shiga Taitayinta. Tunda suka tafi bai kirani ba,nima ban kira ba nadai san shuru lafiya ne in da ba Lafiya da naji Labari sai nima na kama kaina na cigaba da kula da kaina da ya'yana tafiyar su da Sati Daya Sai ga Goggon karofi tazo min kamar Daga sama nayi murnan ganinta har bansan yadda zan kwatanta ba. Tazo min da su kuka,Kubewa garin kunu garin Danwake,kayan miya da kuli kuli,Sai ta zo ma da su Amir gyada da mai gishiri da mai bawo,Sai alewan yara,Suna makaranta ko da ta iso da rana ne Lokacin nama zata ko Daga gidan Mama take sai tace min Daga Dutsemah take ta biya ta gaida ta Madina ta dade bataje ba naji Dadin jin Tamadina tana lafiya. Bakina yaki Rufuwa da Goggo tace min kwana zatayi sai gobe zata koma ni kawai tazo dubawa. Su Amir nata tsalle da suka Dawo suka ganta,suna son zuwa karofi ammh Ya Ishaq baya bari daga makaranta sai gida sai ko gidan Mama in ma sun je to yini ba kwana ba. Bamu samu kebewa ba sai Dare bayan yaran sun kwanta Goggo ta na gayamin taji duk abubuwan da suka faru basu yi mata Dadi ba Sai dai tayi ma Yaya mariya fada meyasa ta biye ma Binta ai ko banza ni yar'uwanta ce bai kamata ta taho ta kyaleni ba,Goggo tace kinsan mariya da bakar Zuciya,Sannan ta riga ta rantse ne yasa bata ce ta Dawo ba,ni nake fadama Goggo zuwan ya Ishaq da amaryansa na gayamata mun zauna Lafiya da ita har suka koma Goggo ta cigaba da min nasiha duk akan nayi hakuri ne watarana sai Labari. Sai Wajen d'aya saura na Dare muka kwanta da Safe kuma da Goggo Tayi shirin tafiya nace ta leka gidan Mama su gaisa tace min bazataje ba Dakyar na Lallasheta tace zata biya tayi mata Murna dagachan zata wuce a bakinta nake jin Hajiyar Dala ta kirata a waya tana mata fadan bata kyauta ba da bata zo ba Goggo tace nayi mata Tas daga Lokacin bata kara kiranta ba. Sha d'aya na Safe na raka Goggo Har bakin Hanya mun rabu tana ta kara jadaddamin nayi hakuri da rayuwa watarana komai zai wuce sannan na Dage da gayama Allah shine Sarkin Duka Duniya gabadaya. Mun rabu kamar na bita haka nakeji ammh ba Dama,har da kwallata sai da nayi,Bansan ya Goggo suka kare da Mama ba sai da washegari Badariya tazo take bani Labari Mama har da kuka ta kira Anty Binta da Ya Ishaq akan Goggo Tazo tayi mata cin mutumci Saboda ni.. Gabana ya fadi na zare ido ina kallon Badariya kafin nace"Sabo da ni kuma..? Badariya tace"Tabbas..Kinsan Halin Mama har Hajiyar Dala sai da ta kira ta fada mata..Ni dai nasan kila Goggo Fada tayi mata shikenan sai cibi ya zama kari Anty Binta nata fada haka ma shi kan shi Ya Ishaq din a waya sai Fada yake barin ma jin Mama nata kuka" Sai jikina ya fara rawa nasan komai kaina zai dawo aiko hakan ce ta faru Badariya ta tafi ba Dadewa daman Daga makaranta ta biyo sai ga Anty Binta da Mama har cikin gida wanda bazan iya tuna zuwan mama gidan nan na karshe ba. Zagi da gori da cin mutumci ba wanda basu yin ba ina da goyon Ahmad a baya na Mama ta saka Hannu ta tsinkeni da mari,na Dafe kuncina Hawaye suka Gocemin,Ahmad na barci ne ammh sai da ya tashi Hayaniyar Mama yasa ya tsorata ya

Chapter 11 of 25