fashe da kuka kwana biyu ne bana nan ammh ya'yana ma sai makota ne suka kula da su inaga in ba na tare da su gabad'aya Allah kad'ai yasan wani Hali zasu shiga shiyasa zan Daure zan kuma Jajirce saboda goben su
Washegari da muka Dawo gida ma Tun Safe sa'adatu ta shigo ita ta shirya yaran tayi musu kari dayake ita bata taba Haihuwa ba,bayan sun tafi makaranta tazo ta gyaran gidan,ta koma gida chan anjuma kuma tadawo tayi ma yara girki nasan ko bata fada ba aranta tana so ta tambayeni bani da Dangi ne..?
Ai rashin gatan yayi yawa sai dai bata ce min ba nima ban ce mata ba.
Kwana na Hudu da dawowa asibiti na ji sauki Nace sa'adatu ta daina zuwa tana min wahala na samu lafiya,Ranar har gidan Habiba sai da na shiga na kara yimata godiya sai dai duk wanda yaganni yasan na rame duk na kara Lalacewa.
Sati daya da faruwar abun Badariya tazo Dubani tana bani Hakurin bata sani ba sai abakin Halisa taji har asibiti na kwanta,ta yinin mu sai yammah da Halisa tazo dubani suka tafi tare,Ita ce ma suna mgana da Hafsah ta wayar Goggo ta fad'amata nayi ciwo har asibiti na kwanta ashe su Hafsah suna kano Yaya Asiya ce ta Haihu,suna kano shekaranjiya akayi suna Hafsa ke fad'ama Goggo tana ta Fadan ba wanda ya fadamata ballatana sauran yan'uwana kuma suna ta kiran wayata a kashe basu san ta Lalace ba..
Ranar laraba da Safe sai ga su A gidana Daga kanon suke Yaya Isan goggo yaje ya Dauko su a motarsa,Goggo ce sai Anty Nasara da Yaya mariya sai Hafsatu sai matar Isa Amina,sun zo sun ganni suna ta tafad'a gani na duk na fad'a na rame Goggo ta kalleni tana fadin"In wayarki ta lalace baki aron wata wayar makota ki kiramu Fa'iza"?
Kaina na kasa nace"Goggo ban da lambar kowa a kaina kuma layin yana gida"
Anty Nasara tace"to wa ya zauna dake..?
Kaina na kasa tace"Matar makocin mu haruna mai kai su Amir makaranta"
Su Goggo suka saka salati suka Dire,Yaya mariya tace"Daman wa kuke tunanin zai zauna da ita..?
Mama ko Binta..?azzalumai bakomai a zuciyar su sai mugunta ayi dai mu gani"
Goggo ta juya tana kallonta Lokaci daya tana fadin"Mariya..mariya ana rabaki da kiwon awaki kina fadin kyalla ta Haihu daga Saudatun har Binta ai ba sa'anki ko.?
Yaya mariya ta tura baki kafin tace"Ai gaskiya na fada goggo wlh wani Hisabin sai a lahira kalli yadda Fa"iza ta koma kamar wata yar aiki kalli gidanta kalli kujerun ta duk sun Fita Hayyacin su kuma wai wannan mai kudi take aure Allah dai ya waddan kudin miji in dai na irin mijin Fa'iza ne bashi da amfani ko ni da mijina karamin ma'aikaci ne wlh d'akina yafi na Fa'iza kyau sau dubu Saba'in wlh"
Anty Nasara na gefe ta kad'a baki tace"Ai ba gidan ne ya fita Hayyacinsa ba..ita kanta Fa'izan ku dubeta ku gani yadda duk ta fita kammaninta"
Fadin haka yasa duk suka sakamin ido suna karemin kallo Goggo tace"Duk kubar mganar nan mganar kayan daki zamu sauya mata in sha Allahu ai mune yan'uwanta Dolenta na kanmu Ishaq ba wajibinsa ba ne yayi ma Fa'iza komai ba"
Yaya mariya ta kad'a baki tace"ammh ai yana da shi..kuma bai gagaresa ba in da mutumci a wahalan da Fa"iza tayi da shi da danginsa ta chanchanci komai a wajensa"
Goggo tayi saurin tare mganar da kallona tana fadin"Fa'iza wannan ramar tayi yawa me ke damun ki ne..?
Sai nayi shuru na kasa mgana nasan in nace Hawan jini gareni na bude Sabon Shafi sai nayi kamar ban ji ba Sai da goggo ta kara mgana Sannan na ce mata Zazzabin cizon Sauro ne.
Goggo nata fad'an ko bana kunna mganin Sauro ne ni dai nayi shuru ban ce komai ba.
Hafsatu tayi girki Yaya mariya kuma ta ragemin wankin su Amir,daman sun taru Aminan isa kuma ta gyara Falon da Dakunan.
Bayan sun ci abinci sun yi sallar azahar na saka Hafsatu ta shiga da su gidan Sa'adatu suka yi mata godiya daganan nace suce ta kai su gidan Habiba itama suka mata godiya sukace bakomai ai yiwa kai ne.
Muna tare da su har La'asar akace Dan'uwa mai dadi naji Dadi sosai Yaya mariya ta nuna min Yaya asiya da D'anta a waya hoton da suka Dauka Ranar suna tasha kyau abunta sunan yaron Muhammad Auwal.
Sai bayan La'asar suka yi shirin Tafiya,Yaya Isa daman ya shiga cikin gari ne sai ga shi ya Dawo Hafsatu ta sakamai abinci da yake tana fashin Sallah tana falo Aminan Isa da Anty Nasara na Dakina suna sallah ni kuma ina Dakin su Amir ina sallah da ni da Yaya mariya Ahmad na goye a bayan Goggo Tun da ya fara rigima ta karbesa ta goyasa.
Ni dai na idar da sallah ina zaune ina azkar Sai naji mgana sama sama afalo Yaya mariya ta tashi ta fita,ba jimawa sai ga Hafsatu ta leko tace Goggo na kira na,Ina fitowa nagan su Tsaye sun yi cirko cirko gabana ya fad'i na zata ma wani abu ne,Goggo ta kalleni da Kwalin mganina a hannunta kafin tace"Ashe Fa'iza hawan jini gareki kikace mana wai zazzabin cizon sauro ne..?
Sai na kasa mgana na Dukar da kaina Yaya mariya ta yi kyafci kafin tace"ai bazata fad'a miki ba Goggo..Na rasa me Ishaq ya bama Fa'iza ya shanyeta bata kaunar Laifinsa daga shi har Danginsa"
Goggo ta kalleni ta kara kallo na kafin ta saka salati tana fadin"Na shige su ni Indo..Yanzu da ba domin Nasara taga mganin nan kuma tasan ko na menene ba da haka zata bar mu a matsayin Maleria ke damunta haba wannan ramar na Fa'iza ya yi wa ashe ashe Hawan jini gareta da kananun shekarunta"
Yaya Isa na gefe yayi karamin Tsaki kafin yace"Ba Dole ta kamu da Hawan jini ba Goggo..An aura mata wanda baisan Darajanta ba..Ina jin Labarin zaman Hakurin da yarinyar nan ke yi ku kuma su goggo kun kasa D'aukan mataki akan haka ai aure ba Bauta ba ne ibadan ubangiji ne ba na abokin Hallita ba..Ya maida matarsa kamar wata yar aiki ko baiwa yana chan Abuja ya tare sai yaga Dama yake zuwa Fisabillahi wannan adalci ne..?
Goggo tayi saurin tare shi da Fadin"Mijinta ne ya fi mu iko da ita..Sannan zaman aure ai zaman hakuri ne,Kuma ibada take yi Isa kada kace bamu Dauki mataki ba in ba so kake mu kashe mata aure ba"
Yaya mariya tayi karaf tace"Wlh Goggo da auran Fa'iza dai gwara zawarci"
Goggo ta aika mata da Dakuwa tana Fadin"Ya'yan nata fa ke zaki rike mata su in ta fice ta barsu da kananun shekaru..?
Yaya mariya ta tura baki kafin tace"Su zauna gidan Uban su mana Goggo"
Goggo tayi dariyan takaici kafin tace"Kayya mariya ai rikon ya'yan wani ba kowa zai iya ba sai wanda Allah ya bama wannan..Sannan kuma ya'ya sai uwar su mariya..Yanzu dai Allah ya kyauta..Tunda abun ya zama haka Mariya in ba Damuwa ki kara kwana ko zuwa gobe jibi in megidan naki zai bari lokacin ta kara watsakewa kinga Hafsatu suna da makaranta"
Yaya mariya tace"Bakomai da na kirasa bazai ce komai ba su Abba kuma suna gidan kakkaninsu daman."
Goggo ta kalleni tana fadin"Ga mariya nan zata zauna ta kara taimaka miki zuwa jibi ni kuma zan tafi da Ahmad tunda kin yayesa in kika ji Sauki kika warke sai na Dawo miki dashi"
Ban iya ma Goggo musu ba na tafi na Had'o kayan Ahmad na bata,Nasan tayi hakane saboda ta ragemin wahala sannan duk da ina jin Tsoron me zai biyo baya,ammh bazan iya ce ma Goggo A'a ba saboda ita kamar makwafin Tamadina ne a wajena duk da tana raye.
Ya Isa nata fad'a Goggo bata Biye masa ba Ta lallasheni tare da kara Jadaddamin nayi hakuri watarana sai Labari Goggo ta bani dubi biyar Ya Isa dubu uku kafin su tafi,Suka barni da Yaya mariya ta tasani tana ta min Fad'a wai na zauna na zama sakarya miji da Danginsa suna yadda suka ga Dama dani ni dai ban ce mata komai ba sanin Halinta.
Da yammah ko da su Amir suka Dawo basu ga Ahmad ba,na fad'a musu Goggo tazo ta tafi da shi suka fara Tsallen suma Yaya mariya ta tafi da su ta kyabe baki kafin tace"Wannan uban naku mai bakin hali ai bazai bari ku rabemu ba duk dai abun su bai isa ya sauya ma Tuwo suna ba"
Ban tab'a kawo ma raina Ya ishaq zai iya Dawowa ba sai ga shi washegari da yammah ya Diro dirowan bazata yayi mana Muna falo ni da yaya mariya,ita wayarta take latswa ni kuma ina kwance kan kujera mai zaman mutun uku duk da naji Sauki ammh jikina ba karfi su Amir na makaranta basu dawo ba.
Ko sallama ma bai yi ba sai da ya shigo Falon kuma da Yaya mariya ya fara cin karo suka yi ma juna kallo daya suka Dauke kai ni kuma jikina na rawa na tashi zaune ina gyara Wuyan rigana cikin rawan jiki da na zuciya nace"San..nnu..da zuwa.."
Wani irin kallon da ya bini da shi yasa Hantar Cikina ta kad'a na fara maimaita innalillahi acikin raina ko amsani bai yi ba kamar Hadari haka ya shige shashensa ya Banko kofa.
Na dago na kalli Yaya mariya sai tayi kamar bata ganni ba ta mike ta shige Dakina tayi kamar tana waya ni kuma jikina na rawa na shiga Kitchen bamu da ruwan gora na Daukomai purewater na saka a Filet da kofi gabana na fadi na nufi bangaransa Gabadaya ilahirin jikina ba inda baya raawa ina fatan kada Abunda nake tsoron Faruwarsa ya faru da na shiga Uku.
*ASSALAMU ALAIKUM*
*KAYA SUN SAKE SAUKA*.
*INGANTATTUN SAIWOWI DA SASSAKE NE DA AKE DAHUWAR GIMBIYAR KAZA DA SU*.
*ABIN BIRGEWA BA SAU DAYA AKE AMFANI DA SHI BA*.
*KINA DA KANNEN DA ZA'A AURAR KO KUWA KE DA KANKI ZAKI YI GYARA?*
*INA SAKE YIN ALBISHIR DIN GARIN DAKA MAI KYAU DAN CHADI, SHA DA MADARA KO NONO DA KUMA TSUMIN GAMGAM*.
*GADALIN MATA AKWAI*.
*INA DA TABBACIN INGANCINSU*.
*SANNAN WACCE TAKE SON A DAFA MATA KAZAR, ZA'A DAFA*.
*TUARAREN WUTA NA ASALIN CHADI AKWIA SU AVAILABLE, SAI KIN GWADA ZAKI BADA LABARINSU*
*TUNTU'BI SURAYYA HALIN YAU DOMIN KARIN BAYANI*
*08032773332*.
*NATION WIDE DELIVERY*.
*SERIOUS BUYERS ONLY PLEASE*
🙏.
*Janafty*
*KANA NAKA..!*
*Wattpad:JamilaUmar315*
*Mallakar:Janafty*
*Arewabook:Jamilaumarjanafty*
MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT 08066726866
Ni MMN MUJAHID Ina da kayn gyara kala kala na kasa da sama Ina Saida supplement da kayan mata kala kala cikin sauki Mai kama da kyauta
Hjy ta ki ajiye kunya kifitu kiyi bayani matsala ki abaki ABINDA yaddace Dake
Ina matan da ke FAMA da bushewa gaba
Ina maccen da take a bushe kamas ba niima miji sai yasa yawun sa ku BASILIN 😳
Ina matar da kishiya ta tayi mata zarra ga miji ke rasa Ina matsala take
Ina wadda mijinta kamar kurma baya nuna ya gamsu Dake Dan ku ayi ku abari duk dai suke dashi
Shin ke ku y'ar kuwa ga mijin ki baya Yi da sanbatu in kinji ana Fadi sai kece karya ce
Nazo muku da hadin Zuma wadda duk zata magance way'anga matsalolin cikin ikon Allah wanna Zuma ta samu yabo ga duban mutane Sha yanzu magani yanzu ce Banda haufi akanta wanna Zuma tana ta yadda sha'awa Kai tsaye ruba babba 2500 karama 700👌👌
MMN MUJAHID KAYAN MATA AND SUPPLEMENT MUNA SAKWATO DA KEBBI INA AIKAWA KU INA 08066726866
IN BAKI SHIRYA BA KIBARI HAR KI TASHI SAYE 😀
*🅿️12*
Ina shiga Bangaransa na iske sa tsaye a tsakiyar falon yana ta safa da marwa saboda bala'i hatta jakar da ya dawo da ita bai iya sauketa ba kamar yana jira na ina shigowa da sallamata yayi saurin zaburowa Sauran, sallaman tawa ma iya makoshina ta makale jikina ya Dauki karkarwa kamar wacce taga mutuwarta.
Hannunsa manuniya yasa ya na nuna ni cikin Matukar fushi yace"Me na gaya miki..?
Nace me na gaya miki Fa'iza akan wannan mara mutumcin yayar nan taki..?
Yafad'a Lokaci d'aya yana dagamin murya sai na tsaya na kasa gaba ballatana baya jikina na wani gif gif kamar wacce wani abu ke ja kafafuwana suka fara barazanar kayar dani sai nabi Raunin su suka rinjaye ni na koma na Durkushe saman kafafuwa na lokaci daya ina sauke sauke farantin Hannuna ina so nayi mgana na kasa tsoro nake ji kada Yaya mariya ta jimu tunda Jikin Shashen sa na jikin Dakina ne bazan so a ce yau mijina ya Tozartamin yar'uwa ba.
Ina wannan tunanin sai ji nayi ya sakar min gigitaciyar Tsawa Lokaci d'aya yana kara fadin"Nace me na fada miki Fa'iza..?
Hawaye suka gocemin na Tsoron abunda zai biyo baya,na yi baya da jikina ina karkarwa na had'a Hannayena cikin yanayin mgana ta da rawan baki nace"Don..Allah..Kayi hakuri ka yi shuru..Na kasa fad'a mata ne bazan iya ba..wlh bazan iya ba.."
Sai hawaye sharr suka gocemin wasu na korar wasu,Tsayawa ya yi yana min wani irin kallo na raini da kaskanci kafin yace"Au bazaki iya fada mata ba ko..?To ni bari naje na fada mata tunda gida na ne ba gidan wani ba"
Ya karishe fada a fusace yana sauke jakar da ya shigo da ita nan tsakar Dakin nasan zai aikata tunda ya furta Da sauri na mike na isa garesa na Durkusa ina kuka ina fadin"Don Allah..don Allah..!
Mgana ta ta kasa fitowa saboda kukan da yaci karfina Ganin yayi banza dani ya nufi hanyar ficewa yasa na kwashi gudu na isa ga kafarsa na kama na rike gam ina kuka kamar raina zai fita ina fadin"Kada ka tozartamin yar'uwa..Ka bari zata tafi..Zata tafi.."
Sai ya tsaya yana kallona kafin yace"Yaushe zata tafin..?
Cikin kuka nace"Gobe..Gobe zata tafi na rantse da Allah.."
Ko sake kallo na bai yi ba ya Fizge kafarsa sai da nayi baya na fad'i ya Fice da Sauri,ina ganin haka na mike sai da kaina ya sara jiri ya kwasheni ammh ban damu ba na marasa baya ba inda jikina baya rawa har da zuciyata ma gudu take yi da sauri a lokacin.
Sai dai me zuciyata ta tsaya waje d'aya lokacin da na fito na iske Yaya mariya Tsaye a tsakiyar falon daga dukkan alamu ta gama jin duka mganganun mu Saboda Ya Ishaq da karfi ya Dinga Tijaransa,Kasa karisawa nayi kawai sai na Tsaya ina raba ido jikina da zuciyata gabadaya yayi wani Dum kamar ya daina aiki na wani Lokaci.
Ya ishaq kuma yana ganin Yaya mariya bai yi wata wata ba ya gyara Tsayuwa yana fadin"Nasan yar'uwan ki bata gaya miki sako na ba ko..?
Yaya mariya ta kallesa cikin idon da bacin rai yasa s Launin su ya sauya kafin tace"Bata gayamin ba..Ammh Tunda kaga ai waka a bakin mai ita tafi dad'i"
Tafad'a Tana kokarin yaki da zafin zuciyar dake taso mata,Taji duka mganganun Ishaq ta dade tana jin Labarin Rashin mutumcinsa, bata taba katari da shi ba sai yau lalle ko zai sha mamakinta domin in ya yi mata kan kara wlh sai tayi masa na itace.
Cikin gadara yace"Na fad'a mata tun kwanaki da kada na kara ganin ki acikin gidana..Bazai yuyu ki rika shigomin gida bakya daraja ni ba..Kamar ni zaki rika gani kina D'auke kai kamar kin ga kashi..?ai ba gaba da ni kike ba ko Yayarku Asiya ba Sana'ata bace ballatana ke karamar alhaki kin raina uwata da yayata suna fada kina fada sannan ki rika shigomin gida kina raina min wayau bazai sabu ba..Kada na kara ganin kafarki acikin gidana Daga yau sai yau..In yar'uwanki zata yi zumunci dake in kun had'u awani waje ban hanaku zumunci ba ammh ba acikin gidana ba"
Ya karishe fad'a cikin nuna cin mutumci har yana nuna ta da Hannu,Yaya mariya tayi dariyan takaici kafin tace"Shikenan sakon naka..?
Ya daga mata kai Lokaci d'aya yana fadin"eh shikenan"
Yaya mariya ta gyara tsayuwa kafin tace"To ai ba saboda kai ko dangin ka nake zuwa wajen Fa'iza ba..Ku ai baku isa ba wlh Fa'iza yar'uwata ce baka isa ka raba jinin dake Tsakanina da ita ba gida kuma bazan fita ba sai dai kayi abunda zakayi"
Tafad'a cikin Jaddada mganarta cikin mamakinta yace"Haka kika fad'a..?
Ta daga kai kafin tace"Kwarai haka nace in kuma kana da yadda zakayi dani Bismillah.."
Kawai sai ta koma ta zauna kafa d'aya kan d'aya tana latsa wayarta cikin Fushi ya juyo yana kallona cikin Tsawa yace"Wlh ki Fad'ama yar'uwanki ta fice ta barmin gida tun kafin raina ya baci na hadata da jami'an tsaro.."
Na zaro ido cikin rawan murya ina fadin"Yan sanda.."!
Ko kulani bai yi ba ya shige bangaransa da Sauri ni kuma sai kawai na fashe da kuka da Sauri na karisa gaban Yaya mariya zan yi mgana kenan ta Dakatar dani da Sauri kafin tace"Kada ki ce Tak in na isa dake fa'iza in sha Allahu yau zan kawo karshen duk zalunci da yake miki acikin gidan nan"
Cikin kuka nace"Yaya mariya yan Sanda fa yace zai kira miki"
Tayi wani mirmishi kafin tace"in shi takamar shi iskanci na shanyesa na Dokesa ya Dade bai kira yan Sanda ba in yaso ya Dauko gabad'aya police din kasar nan gabadaya yau ko ni ko shi acikin gidan nan"
Tafad'a tana mai kara tabbatar min da mganarta nasan Halinta tana da kafiya da Taurin kai ban kara mgana ba ammh na tsorata sanin Halin Ya Ishaq na kasa zaune na kasa tsaye,Kawai sai gashi ya fito yana waya kalmar da naji ita ta Razani Cikin Fushi yake fadin"Yallabai gida na zasu zo akwai wata matsala ne..Ok sai sun kariso.."
Nasan zai aikata ba ni da Daraja a idanuwansa,ballatana Dangina su yi Daraja a wajensa zai iya aikata duk abunda yaga dama bai damu ba,kuma nasan bazai taba Saurarata ba sai kawai na zube gaban Yaya mariya na Hada Hannayena duka Biyu cikin kuka na fara fadin"Don Allah..Don Allah..Yaya mariya ki tafi bana so ya Tozartaki bana so aci mutuncin ki"
Yaya mariya ta dakamin Tsawa cikin fada tana fadin"Bazan fita ba ina nan inajiran duk abunda zai yi"
Shi kuma yace"Zaki gani sai kin raina kanki yau d'in nan"
Bana so wani abu ya faru shiyasa nake rokonta tatafi cikin wata murya tace min"Ni kike roko na bar miki gidan ki fa'iza saboda wannan azzalumin mijin naki..?
Lokacin da ta fadi haka baya falon ya koma bangaransa ganin bazata Fahimci ba yasa na tashi zan koma Shashen nasa sai gashi mun ci karo da juna,cikin sauri na rikesa ina Fadin"Don Allah kayi hakuri..Kada ka kira mata yan sanda"
Ba laifinta ba ne Goggo ne da suka zo Dubani jiya tace ta zauna na kara jin Sauki shine..Shine ma.."
Sai na kasa karisawa Cikin Tsawa yace"Shine me..?
Cikin In ina nace"Ta tafi da Ahmad tunda..Tunda na ya ye..s.."
Tas..! Kake jin karan marin da ya yarfamin sai d na yi gefe dafe da kuncina cikin Bacin rai ya nuna ni da Hannu yana fadin"Wacece ke da zaki yanke hukunci kan ya'yana ba tare da kin Sanar dani ba..?uban wa yace ki kai min yaro na wani waje? Ban miki kashedi kan hakan ba..?.
Nace ban miki kashedi kan haka ba Fa'iza..?shine kika aikata gaban kanki saboda kin raina ni ko..?
Yana mgana yana nunani da yatsa cikin bacin rai sai kawai na koma na durkushe ina kuka yaya mariya ta mike cikin Takaici da bakin ciki kafin tace"Ba dai Ubanmu kake zagi ba ko..?
Sannan daman ai dabba shi ke dukan matarsa wannan abun da kayi ya tabbatar min da cewa kai Dabba ne acikin mutane"
Ya Ishaq ransa ya baci ya taso mata itama ta taso da Sauri na shiga Tsakaninsu na rike Yaya mariya ina wani irin kuka kamar zan shide cikin Shakewar murya nace"Ki tafi..Ki tafi don Allah yaya mariya ki tafi.."
Yaya mariya ta kalleni kafin tace"Zan tafi..ammh ba ni kadai ba tare da ke Fa'iza yau zaki bar ma wannan azzalumin gidansa in kina da amfani in kuma baki da shi zai sani"
Sai na Rud'e na kasa mgana ta ja Hannuna keey kamar rakumi da alaqa zuwa Dakina ta fara Hadamin kayana tana yi tana fadin"Kin gama zaman aure in da ba'a san Darajan ki ba..da ikon Allah hakkin ki bazai barsa ba sai Allah ya saka miki"
Ni dai na kasa mgana sai uban kuka nake yi,Ta gama had'a min kaya cikin karamar akwatin Amir itama ta Hada nata kayan ta zura hijabi,Nima tace na Dauko Hijabi na saka ganin na kasa tashi yasa ta dauko min ta sakamin tajani,har zuwa Falo yana Tsaye hannayensa goye a bayansa yana Safa da marwa acikin Falon.
Yana ganin mu ya saki mirmishi kafin yace"Better..Ni bazan hanaki tafiya da yar'uwanki ba ni dai ban ce ta tafi ba in kuma tabiki wannan ra'ayinta ne sai dai ta sani in dai ta saka ta bar gidan nan to ta Rubuta ta barsa har abada"
Yaya mariya tace"To sai me..?ai daman ta bar sa har abada kenan wannan bakin gidan da bakomai cikinsa sai zalunci da mugunta da ikon Allah sai Hakkin Fa'iza ya Bibiyeka"
Ya ishaq yace"Sai dai hakkin kashe aure ya Bibiye ki dai..Sakarya wacce bata san inda ke mata ciwo ba..Na dai gama mganata ni dai in dai ta Fita to a bakin auranta sannan har Abada bazata Dawo ba"
Yaya mariya ta fincikeni tana fadin"Zaka gani yau kam zaman Fa'iza da kadaddaran auran ku ya kare"
Bai damu ba ya koma ya zauna ya Dora kafa d'aya kan d'aya ko ajikinsa,Yaya mariya ta rika jana har kofar Falo cikin Dashewar murya nace"Ban saka takalmi ba yaya mariya"
Cikin Fada tace"in mun je tasha na siya miki"
Na kara turjewa ina fadin"Yara na..Yaya mariya su Amir fa..?in na tafi wazai kula da su..?
Ta juyo tana min wani kallo kafin tace"Ko mutuwa zasu yi sai dai su mutu nan d'in ne gidan Ubansu ke kuma ai ba gidan naki uban ba ne wuce muje.."
Ta kara jana naki yarda na Bita na Turje ta juyo ta kara kallona afusace kafim tace"Fa'iza kada ki bari na saka miki Hannu"
Na kasa mgana sai kuka ya'yana nake Tunani in na tafi basu da wani Sauran gata bani da mafita sai zabin Dawowa na cigaba da zama acikin yanayin da nake saboda ya'yana.
Yaya mariya mamaki ya kara kamata lokacin da na kwace hannuna daga gareta na juya baya ina kuka nace"Ki yi hakuri..Kiyi hakuri..Ki tafi don Allah..BAzan iya tafiya na bar ya'ya na ba"
Kiyi hakuri"
Sai kawai na kwashi gudu zuwa Cikin D'akina ina kuka kamar raina zai fita kaina har wani bugawa yake yi Dif dif,Yaya mariya ta kasa motsi saboda abunda nayi Ya Ishaq kuma na zaune yana Dariya kasa kasa kafin ya mike yana kallon Yaya mariya cikin gadara yace"Fita ki bar min gida bakar munafuka..Kin dai ji kunya wlh kin kuma yi asara..Yar'uwan naki da kike Hakilo a kanta ta nuna miki baki da wata Daraja sama dani..Sai ki fice min Daga gida kada na kara ganin siraran kafafunki acikin gidana.."
Yafad'a yana nuna mata hannun alamun ta fice ta bar mai gida Takaici da bakinciki yasa Yaya mariya Zubar kwallah ta kalle shi ta kara kallonsa kafin tace"Naji kayi nasara a kaina zan tafi..kamar yadda ka bukata bazan kara zuwa gidan ka ba..Sannan mganar Fa'iza karyan ka ta sha karya ai jini yafi ruwa kauri sannan wata kusan tafi wata..Zan cigaba da zumumci da yar'uwata domin ba kai ka Had'amu ba..Mgana ta karshe shine akwai Allah kuma yana nan a madakata Duk abunda kake aikata ma Fa'iza na sharri da zalunci kai da Mahaifiyarka da yayarka,Da ikon Allah sai kunga sakkaya tun a duniya sai Allah ya jarabceka da iftila'in da sai ka rasa ina zaka saka kanka in sha Allahu sai Allah ya saukar da aya akan maza ire iren ka da basu darajan matan su sannan basa adalci ya yin zamantakewar su,Kuma kada ka manta akwai Hakkin zumunci shima sai Allah ya tambaye ka, sannan hakkin Fa'iza bazai barka kayi rayuwar da kake Buri ba Ishaq Kabir karofi."
Tana gama fad'in haka ta Sauke karamin akwatin na data Dauka,ta juya ta fice tana zubar da hawayen bakinciki da takaici duk da kalamanta sun Dakesa ammh bai damu ba ya Bita har get yana gayamata bakaken mganganu sannan ya Dawo Cikin gida ya Iskoni har dak'i yana gayamin duk mganar da ta fito bakinsa har yana fadim Tunda ya aureni bai Huta ba yake cikin Matsala ni ba matar kirki bace ni matar Tsiya ce.
Nayi kuka,kukan da ban taba yi ba,kukan yadda ya tozarta yar'uwata ni ban damu da kaina ba Daman ni bani da wata Daraja ammh Yaya mariya fa..?yar'uwata ce bata chanchanci cin zarafi da tozarci ba.
In da nagode ma Allah Yaran basu dawo daga makaranta ba,da
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 14 Chapter of 25