ka da naƙudar haihuwarka da shayar da kai. Asiya dai ta fini muhimmanci a wajenka ko? Shike nan kaje kayi duk abinda kake ganin dai-dai ne agareka. Amma ka sani ko mutuwa nayi kurwata bazata barka zaman aure da yarinyar can ba. Dan na riga na maka mata kamar yanda na faɗa maka. Garama ka shirya tun kafin takaimu da bakanta a cikin gidan nan. Amma bari shi Alhajin dake ɗaure maka ƙugu ya dawo gidan ina dai-dai dashi wlhy”.
Kasa iya furta komai Yazeed yayi, sai wani irin haɗiyar zuciya yake acan ƙasan ransa dan mutum ne mai zuciyar tsiya dama. Haka suka cigaba da masa masifa bai iya sake cemusu komai ba har sai da ALLAH ya taimakesa Daddy yay kiran wayarsa sannan ya tashi ya fita domin amsawa. Daga haka bai koma wajen su ba ya gudu sashensa dan ya shirya gashi har yana neman makara....
________
A ɓangaren Manaal bata sanarma Ammie komai ba. Sai ma ƴan uwanta ne da suka zagayeta suna yaba irin ƙyawun da gyaran yay mata. Daga haka Ammie ta korata dan ta shirya kada su makara. Saboda tasanta da nauyin shiri. Aiko bata kammala shirin ba sai da Ammie tai mata tsiya-tsiya. Faɗan Ammien yasa ta fito ɗauko da ɗan box ɗin da take ajiye kayan ƴan kunne da makamantansu ciki a hannu tana neman agogon da zata saka da zobe. Su Amal ne dake musu dariya suka amsa suna duba mata. Dai-dai fitowar Ammie tana faɗin, “K muje ai ba dole sai kinsa wani agogo can ba bana son shiririta”.
Jin hakan ya sata miƙewa dan tasan kaɗan daga aikin Ammien ta maketa ma saboda bata ƙaunar jira, da sauri Shahidah da takamo hannunta ta ɗaura mata wanda ta zaro kalar silba kawai ta shiga ɗaura mata batare da su duka sun maida hankali akansa ba. Daga haka suka fice hannunta riƙe da ƴar bag ɗinta sai gwangwanin maltina data ɗauka saboda yunwan da take ji kasancewar bawani break ɗin kirki tayi ba ta fita gyaran jikin, yanzu kuma Ammie tace bazata zauna cin abinci ba aiba itace ta hanata ci ɗazun ba sai dai ta bari idan sunje gidan bikin taci. Itako tasan bazata taɓa iyawa ba cin abinci a gidan biki koda na wanda ta sani ne balle wannan, duk da kamar gidane can ɗin ma saboda alaƙar dake tsakanin mai gidan da uban amaryar mai matuƙar ƙarfi ce, ta wani gefen ma za'a iya cewa akwai zuminci. Koda yake su sai dai suyi kara saboda Ammie kawai amatsayinsu na ƴaƴanta...........✍️
✨ZAFAFAN DAI ✨
1 ƘALBIM (Mamu gee)
2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo)
3 DUNIYAR MU (Huguma)
4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull)
Book 1:-500
Book 2:-1000
Book 3:-1500
Book 4:-2000
0022419171
Access bank
Maryam Sani Gumi
Shaida:- 09033181070
Kati MTN:- 09032345899
Ƴan NIGER 🇮🇷
1000CF
89825722
Nousaiba Lawali Maradi
Shaida:-09033181070
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_💞AJIYA A DUHU....💞_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
*_My TikTok account 👇_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram👇🏻_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_Arewabooks_*
Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30
_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_
🅿️➖0️⃣9️⃣
______________
Lady's collection and more
Zumar kiba
Zumar breast
Zumar hips
Zumar infection
Zumar sliming
Zumar sabon budurci
Back to virgin
Abayas
Atamfa
Less
Hijabs
Supplements
Kitchen items and more Muna maraba da masu siyan Daya ko
08169307477
Address bayan gidan drugs katsina State. Kayanmu nada inganci da zasu birge mai saye fiye da yanda yake zato. Maza ku garzayo kada ayi babu ku.
_______________
.........Tunda suka fito ya zuba mata ido daga inda yake tsaye jikin mota. Itakam sam bata lura da shi ba tana ta ƙoƙarin gyara kayan data zubo a handbag ɗinta dataƙi rufuwa. Sai da suka iso gab da shi ta tsinkayi muryarsa yana gaida Ammie. Yayinda Amrah ta taɓota itama tana gaida Ammien. Ɗagowa tai ta dubi Amrah ɗin, suka sakarma juna murmushi, harta maida kanta sai kuma ta ɗan ɗago dan sai yanzu hankalinta ya kai garesa sosai. A take ta shanye murmushin saman fuskarta ziciyarta na takurewa waje ɗaya a ƙirjinta. Tabbas da tasan tafiyar nan tare zata kasance musu ALLAH duk yanda zatai da sai tayi ta zame kanta a masu yinta. Amma yanzu babu yanda ta iya dole ta dake. Ganin su Ammie sun shige itama ta fara ƙoƙarin shiga kusa da su amma sai Amrah tai saurin rufe murfin tana faɗin, “Kije wajen Yaya mana gashi can ya buɗe miki”.
Tsaye tai kawai tama gagara cewa komai, koda ta saci kallon Ammie sai taga ta ɗan harareta, dole ta shiga kusa da shi ɗin tana faman sauke ajiyar zuciya. Ɗan karkatowa yay inda take kaɗan kamar zai ɗauka abu a ƙasan ƙafafunsu. Cikin raɗa ya furta, “You look so good dear”. Kasa cemasa komai tayi, sai ma takurewa data ɗanyi jikin kujerar, yayinda shi kuma ya ɗaga yana gyara zamansa tamkar bashi yay maganar ba dan fuskarsa sam babu wani walwalan kirki.
Sun fara tafiya shiru motar babu mai magana. Sai da suna gab da barin titin anguwar gaba ɗaya kamar ance ta kalla hannunta idanunta suka sauka akan agogon da Didi Shahidah ta ɗaura mata. Ba ƙaramin bugawa ƙirjinta yay ba har kana iya ganin yanda maƙoshinta ke kaiwa da komawa a wuyanta. Ta ƙurama agogon ido wani abu mai shegen nauyi na sake saukar mata a dukkan illahirin jikinta. Bata masan wani ƙarfi yazo mata ba tasa ɗayan hannunta ta fincike agogon, kamar zatai wurgi da shi waje sai kuma ta daure ta ɓalle bag ɗinta ta jefashi ciki batare data zuge zip ɗin ba ta maida kanta ta nannaɗe cikin ƙafafunta data ɗage gaba ɗaya zuwa saman kujerar. A take wasu hawaye masu zafin gaske da raɗaɗi suka fara zirara mata. Yanda tayi ɗin sai sukai tunanin ko barci take, musamman Ammie da tasan bawani barcin kirki ta samu ba a safiyar yau dama daren. Shima Yazeed daya ɗauka barcin tayi sai kawai ya farama Ammie hira. A haka har suka iso Zaria kasancewar tafiyar ba wata mai yawa bace ba. Da yake Yazeed yasan hanya basu wani sha wahala ba nan ma suka iso. Sun sami anguwar kanta da mutane sosai balle ƙofar gidan daya kasance masha ALLAH dan har Ammie na faɗin, “Anya Yazeed zamu iya keta mutanen nan zuwa cikin gidan kuwa?”.
Amsa ya bata da faɗin, “Ammie zaku iya shiyyasa ma nai parking tanan ganin yafi ƙarancin mutane. Zan bidaku ta baya ne akwai wata ƙofa dana sani Uncle na amfani da ita nasan zata kasance buɗe yau kodan baƙinsa”.
Cikin gamsuwa Ammie ta ce, “To Alhamdullah hakan ma yayi”.
Sun firfito yayinda a kallo ɗaya Ammie ta fahimci Manaal tayi kuka duk da gilashin dake a idonta. Sai dai ta fassara kukan nata da zaman gaba da aka sakata yi ne dole. Dan haka ta watsar da ita tama haɗe fuska. A wannan yanayin suka shiga gidan ta inda Yazeed ɗin ya faɗa. Aiko sai suka samu sauƙi jama'a anan sai falon Uncle ɗin ne ma da mutane dan akwai takalma kusan ƙafa bakwai a wajen masu ƙyau. Wucewarsu sukai zuwa cikin gida dan itama Ammien ba wannan ne zuwanta na farko ba. Hakama Amrah. Maanal ce dai bata taɓa zuwa ba dama sai yau ɗin. Amma ta ɗan san yaran gidan saboda suna zuwa can gidan nasu lokaci-lokaci...
★-----------
Babu jimawa da shigewar su Maanal tawagar ango da abokansa suka iso ƙofar gidan. Cikin tsari da nutsuwa tarin motocinsu suka layantu dai-dai inda Yaya Yazeed yay parking motarsa. Firfitowa duk suka shiga yi, kowa ka kalla shar da shi cikin dakakken yadi mai shegen ƙyau da tsada, wasu kuma shaddoji. Sai shima ango dake sanye da shadda fara ƙal tanata maiƙo da ɗaukar idanu. Sun gama firfitowa sai motar dake kusa data Yazeed ce kawai wanda ke ciki baida alamar fitowar, sai da angon ya juya yana ɗan kalle-kalle da faɗin, “Wai Uncle fa?”.
Duk motar suka kalla. Kafin wani a cikin abokan yace, “Bai kai ga fitowa ba kamar ma suna magana ne da Uncle Nass”.
“Oh ai fa an haɗu. Ni dai suyi su fito kar a fara neman waliyyai aga duk basa kusa. Bara ma na taɓa su Uncle Fawzan suma”.
Dariya abokan nasa suka sanya masa da shaƙiyanci. Yayinda yay gefe yana dariya. Wanda dai ya ambata da Uncles basu fito a motar ba sai kusan bayan mintuna talatin, suma ɗin dai ba tsoffi bane, matasane da shekarunsu ya haura talatin kaɗan, ɗaya ma zai iya girman ɗayan. Wanda bai kai shekarun ba dake sanye cikin yadi milk ne ya fito ta sashen da motar Yazeed take. Ɗan jingina yay da motar yana amsa waya kansa a sunkuye ta yanda ko fuskarsa ba'a wani gani da ƙyau. Yaci fin mintuna biyu a haka kafin ya katse wayar yana mai kai wa duƙe ya ɗauki abinda idonsa ya sauka a kai tun fitowarsa dake yashe a ƙasa. Agogo ne silver na mata mai ƙyau sosai, juyawa yay ya kalla motar daya jingina batare da yayima agogon wani kallon tsaf ba. Har ya kai hannu zai aza agogon saman motar da tunanin maybe masu motar ne suka yadda sai kuma ya fasa. Tunanin ajiyewa yay a hannunsa dan maybe su haɗu da masu motar sai ya basu, kada ya ajiye kuma wani ya ɗauka dan a ɗan kallon fisha da yay ma agogon ya fahimci mai daraja ne da za'a iya sayensa da kuɗi masu yawa. Motar da suka fito ya buɗe ya jefa agogon sit ɗin mai zaman banza daya zauna dan ɗayan ne yayo driving ɗin. Daga haka ya juya abinsa kawai....
______________★
Duk da yawan taron jama'a bai hana ai musu tarba ta musamman ba da girmamawa da mutuntawa. Dan can ƙuryar ɗakin amaryar gidan aka kaisu tare da musu sauka ta musamman da abinci da kayan ciye-ciye irin na biki. Sai nan nan Hajiya Majdiya keyi da Ammie dan tuntuni take son su jone su zama ƙawaye Ammien ce dai bata maida hankali ba. Ita kuma ba komai yasa hakan ba sai sanin uwargidanta jone suke da Hajiya Yaya 5&6, ko bikin nan ma dan na yarinyar matar tsakkiya ce shiyyasa Hajiya Yayan bata zo ba saboda suna matuƙar adawa da juna. Ita kuma aminiyar Hajiya Basariyya ce dan ita tun sassafe ma tana nan Zaria ɗin da duka yaranta kuma kwana zasuyi dan har Abuja inda za'akai amarya zasuje ma.
Ƙorafin da take tayi yasa Ammie bama su Maanal umarnin cin abincin. Amrah ce ta zuba ma Ammie sannan ta zuba musu. Maanal na cewa ta ƙoshi Hajiya Majdiya tace, “Haba ɗiyata kada kimin haka mana, idan kuma baƙya sonshi na canjo miki wani ko na dafo miki yanzun nan”.
Da sauri ta ɗauki spoon ta saka cikin abincin, hakan ya saka Amra kwashewa da dariya. Sunci abincin Ammie da Hajiya Majdiya na hira sai ga wata budurwar yarinya ta shigo ɗakin. Zasu iya zama sa'anni dasu Maanal, tayi ƙyau cikin lass da nake ƙyautata zaton ankonsu kenan dan ƴammata da yawa na dashi a wajen bikin. Tafawa suka ɗan yi da Amrah alamar sun san juna sosai sai kuma ta ɗan zunguri Maanal cike da tsokana ta furta, “Kurman Ammie”. Hararta Maanal ta ɗan yi duk da ba wani sabo sukai ba gaskiya, dan ko gidan sukaje iyakar Maanal ɗin da su gaisuwa ne. Cikin dariyar da suke ta gaida Ammie, yayinda Amrah ke faɗin, “Amma fa sunan nan ya dace da ita sosai, Najwa kin iya saka suna ALLAH”.
Dariya Ammie da Hajiya Majdiya suka sake yi. Nan dai suka cigaba da tsokanar Maanal ita da Amrahn. Bayan sun tsagaita ta dubi Maman nata tana faɗin, “Ummy Uncle Rafeeq fa ya iso”.
“Oh Masha ALLAH har ya ƙaraso, da'alama gudun nashi na tsiya yayi kenan. Yana ina?”.
“Na kaisa ƙaramin falonki wai yunwa yake ji, sai yaci abinci zai fita wajen ɗaurin aure”.
Ƴar dariya tai da faɗin, “Acici kenan mala'ikun tauna. Ga key dama na haɗa masa abincin ai. Idan kin ɗauka ki rufe min kitchen ɗin, sai ya gama sai nazo mu gaisa”.
Amsa tai tana miƙewa, sai kuma ta kalli su Amrah, “Ku taso muje kunzo kun ƙunshe a nan. Amrah karfa ki bari Maanal ta koya miki halinta”.
Da sauri Amra ta ce, “Da naga takaina. Maanal fa ko maijego bazata faɗa mata zaman ɗaki ba, magana kuwa yakan iya sati batayi da kowa ba”.
Hararar su Maanal tayi batare data motsa ba ko yin magana. Ganin haka suka fahimci bazanje ba. Dan haka Najma tai saurin kai ƙararta wajen Ammie. “Ammie kinga wai bazata ba”.
Kallon Maanal Ammie tayi dole ta miƙe badan taso ba suka fita. Kitchen ɗin ta shiga ta ɗauka basket ɗin da aka shirya kayan abincin sanan suka bi wani ƙofa, roƙonsu take akan suje kai amarya Abuja dan ALLAH. Yayinda Amrah ke bata amsa da basuzo da wasu kaya ba. Dai-dai zasu shiga take cewa baga nata kayan ba tasan zasu musu ai, kokuma idan zasu wuce Abujan su tsaya kd ɗin su ɗauki kayan. Shigarsu tasa babu wanda ya bata amsa. Falone ƙarami amma yayi ƙyau sosai cikin tsari.
“I'm sorry Uncle na barka kana jira”. Ta faɗa dai-dai tana ƙarasawa gaban mutumin dake zaune ya ɗan juya ma ƙofa baya ta yanda basa ganin fuskarsa da ƙyau. Juyowa yay ya kallo ta inda suke cikin sigar harara, sai idanunsa cikin na Maanal.
Cak kuwa ta tsaya kamar wadda aka buge mata ƙafafu da sanda, hakama numfashinta sai da yay rawa. Shima ɗin da wani kalar mamaki ya zuba mata idanunsa har yana ɗan warosu waje na kasa ɓoye mamaki. Sai yanda yay ɗin ya saka su Amrah kallon Maanal ɗin suma cike da tambayoyi.
Lips ɗinsa ne suka ɗan motsa a hankali ya faɗi abinda ita da su duk basu ji ba. Yayinda Najma ta furta, “Uncle ko ka sansu ne?”.
Maimakon amsa mata sai ya saki wani ƙayataccen murmushi kawai da kai hannu ya ɗan shafo sajensa siriri yana lumshe idanu da kauda kansa gefe. Itama Maanal janye nata idanun tayi a hankali daga garesa, sai kuma ta juya da nufin fita. Najma ce ta riƙota da sauri tana faɗin, “Kimma isa madam. Dawo ku gaisa. Ai mu wannan abin farin ciki ne agaremu Uncle Rafeeq da budurwa a yau”.
Da sauri Maanal ta harareta da faɗin, “Aka faɗa miki”.
“Basai an faɗa mana ba komai ya bayyana kansa ko Amrah?”. Tai maganar da kallon Amrah da jikinta duk yay sanyi. Murmushin yaƙe ta mata da faɗin, “Ai kam dai gara mu sani”. Maanal zatayi magana suka ja hannunta suka ƙarasa cikin falon dole badan taso ba. Zama sukayi ita da Amrah, yayinda Najma ta duƙa gabansa tana haɗa masa abincin. Shiko ya zuba ma Maanal ido ko ƙyaftawa baiyi. Ita kuma data ɗago taga ita ɗin yake kallo sai ta ɗan hararesa, shi kuma ya sakar mata murmushi. A haka Amrah ta gaishesa. Ya amsa mata cike da basarwa kafin ya maida dubansa ga Najma, cikin sigar tambaya yay mata nuni da Maanal. Juyawa tai ta kalleta itama da ƴar dariya a fuskarta ta ce, Ƙawayena ne kuma ƴan uwana.”
“Uhm yayi ƙyau” ya faɗa yana maido kallonsa kan Maanal dai. Hakan yasa cikin dauriya da sake tsuke fuska ta ce masa “Ina yini”.
Kansa tsaye ya amsa da, “Ya gajiyar tafiya? Da ƙin amsa min waya?”.
Jitai kamar ta ja abu ta wulwula masa bisa kai amma dai ta daure kodan su Najma, batare data kallesa ba ta ce, “Hummm”.
Shima Humm ɗin ya faɗa yana ɗaukar spoon ya fara cin abincinsa.
“Oh oh mukam an sakamu a duhu, Uncle Please ka mana bayani”.
“To uwar gulma anƙi ɗin. Ga ƙofa maza kama gabanki idan na gama zan nemoki. Auntyn ma kice ta hutar da kanta ma gaisa bayan an ɗaura auren”.
“Oyooooo!! Korarmu ma ake, kinga Amrah taso mu ware to”. Tai maganar tana kama hannun Amrah suka nufi ƙofa. Miƙewa itama Maanal tayi dan bazata yarda a barsu su biyu ba, sai taga shima ya miƙe idanunsa a kanta kamar zai cinyenta da su.........✍️
✨ZAFAFAN DAI ✨
1 ƘALBIM (Mamu gee)
2 ƘIRJIN MAI HANKALI (Miss xoxo)
3 DUNIYAR MU (Huguma)
4 AJIYA A DUHU (Bilyn Abdull)
Book 1:-500
Book 2:-1000
Book 3:-1500
Book 4:-2000
0022419171
Access bank
Maryam Sani Gumi
Shaida:- 09033181070
Kati MTN:- 09032345899
Ƴan NIGER 🇮🇷
1000CF
89825722
Nousaiba Lawali Maradi
Shaida:-09033181070
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*
*_Typing📲_*
*_💞AJIYA A DUHU....💞_*
*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*
*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*
_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._
*_My TikTok account 👇_*
https://www.tiktok.com/@bilynabdull?_t=8mfvWuXADVF&_r=1
*_Instagram👇🏻_*
https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv
*_Arewabooks_*
Read My Book "AJIYA A DUHU" on ArewaBooks::https://www.arewabooks.com/book?id=675067e55c3130f457527f30
_Duk wanda bai fallowing ɗina ba ALLAH yasa kada yaga AJIYA A DUHU har a gama😂😂🏃🏃_
🅿️➖🔟
______________
Abubuwan da nake saidawa
Atamfofi
Laces
Shadda
Materials
Takalma
Jakunkuna
Mayafai
Trolley
Sarka da dan kunne
Oil perfumes
Numbers
08034469681
08135142610
Handles
Instagram @ummu_mahnoor_luxuries
TikTok username @ummu_mahnoor_luxuries
Facebook ummu_mahnoor_luxuries
____________
........Fuska ta ɓata sosai kafin ta kallesa babu wasa. “Kasan fa bana son irin haka ko?”.
Kansa ya ɗan rausayar gefe yana murmushi da raba idanunsa a kanta. Cikin raɗa-raɗa ya ce, “Sam ban sani ba sai dai yanzu da kika faɗa min”.
Harararsa ta sake yi zata raɓasa ta wuce yay saurin shan gabanta yana ƙara faɗaɗa murmushinsa. “ALLAH idan kika ce sai kin fita tare zamu fita ne, kuma duk inda kika shiga sai na biki a gidan nan kin dai sani”.
Ɗagowa tai da mamaki ta kallesa, “Ka bini fa?”.
“Yes gwada kuma ki gani, kin dai sai ni nafi mayen ƙarfe ai garama ki koma ki zauna kawai”.
Kanta kawai ta ɗan girgiza, a zuciyata tana faɗin (Kai guy ɗin nan bala'i ne). A fili kam sai kawai ta koma ta zauna a kujerar dake kusa da ƙofar dama anan ta tashi. Ajiyar zuciya ya sauke shima tare da komawa ya zauna a inda ya tashi. Sai da ya ɗiba abincin zai kai baki sannan ya ɗago ya kalleta. “Bismillah”. Kanta ta girgiza masa kawai batace komai ba. Shima sai bai damu ba ya cigaba da faɗin, “Ina su Aneesa?”.
“Gida”.
Ta faɗa a taƙaice.
Kansa ya jinjina kawai shima. Sai kuma falon yay ɗan shiru, a can ƙasan zuciyarsa wani irin farin cikine ke ɗawainiya da shi. Har dai ya kasa dannewa sai da ya furta, “Ashe ma ni a gida nake farauta amma naita wahalar da kaina. Ya kuke da su Najma?”.
Ɗagowa tayi na ɗan kallesa, ganin shima ita yake kallo sai ta maida kanta ga wayata kawai.
“Humm zama da miskilin mutum dai sai haƙuri, shike nan tunda bazaki sanar min ba. In tai wari naji. Ni bara na faɗa miki nawa alaƙan da su to. Mahaifiyarta Yaya tace uwa ɗaya uba ɗaya. Nine autan ɗakinsu, shiyyasa kikaji Najma na kirana Uncle”.
Har cikin rai sai da taji tashin hankalin alaƙar tasu. Amma sai ta dake a taƙaice ta ce, “Masha ALLAH”.
Murmushi yayi da ɗan girgiza kansa. Dai-dai nan Hajiya Majdiya tayi sallama. Amsawa yay yana mai maida dubansa ga ƙofar tare da bata izinin shigowa. Koda ta shigo idonta a kansu, fuskarta kuma ƙawace da murmushi. “Auta na kasa haƙuri ne ALLAH, yanzu Najma taje mana da wani daddaɗan labari”.
“Kai wannan yarinya da gulma take aunty”.
Cikin dariya Hajiya Majdiya ta ce, “Aini gulmar tata ta biyani. Kai idan hakan ta kasance zanyi matuƙar farin ciki Rafeeq. Kaga tuwona maina kenan, ALLAH ya tabbatar da alkairi dai”.
Ko kunya Babu ya amsa da, “Amin aunty. Sai kita tayani addu'a dan gimbiyar har yanzu taƙi bani babban fili koda na zuwa gidane a sanni. Kuma shekara ɗaya kenan muna tare”.
“Kai haba shekara ɗaya fa? Wai kodai dama itace kake faɗa mana ni da Aunty Babba kwanaki wadda kuka haɗu a jos?”.
“Tabbas itace aunty”.
“Ikon ALLAH, ni ashema abu a kusa dani yake haka. Karka wani damu kanka Maanal yarinyar kirki ce kamar yanda kake mutumin kirki. Na tabbatar itama zata soka”.
Ko kunya babu ya kalli Maanal yana wani ɗage gira da faɗin, “Wai haka?”.
Da sauri ta ɗauke kanta zuciyata na wani irin gudu da sauri-sauri. Yayinda take jin wani irin takaicinsa na yanda ya ɗaureta gaba ɗaya a wajen matar da take matuƙar ganin girma da kimarta. (Ya ilahi, RK kuwa nada hankali?) Ta ayyana a zuciyarta tana jin kamar ta saki kuka. Ita sai ma taji tausayin Hajiya Majdiya ɗin yanda taketa farin ciki kamar ma ance an aura masa Maanal ɗin.....
Bayan ficewarta ta kallesa da idanunta da suka kaɗa dan masifar dake cin ranta. Sai dai tana motsa baki zatayi magana ya mike yana dariya. “Koma mi kike son faɗa haɗiye abinki ni na tafi wajen ɗaurin aure, ALLAH yasa muma azo namu nan kusa”. Yay ficewarsa yana kashe min ido ɗaya ga dariyar rainin wayo yana yi. Yana fita baifi da mintuna biyu ba, kafin Maanal ta gama tattaro abinda ya dunƙule mata nunfashi Najma da Amra suka dawo. Rungumeta Najma tai tana farin ciki wai zata zama matar Uncle ɗinta. Surutanta take amma ita Maanal sam bata wani fahimtar komai....
_____________★
“Wai nikam lafiya duk kin zama wata sukuku ko duk gajiyar bikin ce haka Auta?”.
Didi Shahidah ce mai maganar tana zama kusa da Manaal dake kwance a doguwar kujera idanunta a lumshe. Tunda suka shigo gidan ta zube a wajen tana bitar abinda ya faru a Zaria. Ƙaramin murmushi ta sakar ma ƴar uwar tata. Sai kuma ta yunƙura ta tashi zaune sosai. “Babu komai Didi. Kawai na kwanta ne dai”.
Murmushi Didin tai mata, sai kuma ta kai hannu ta ɗan shafi fuskarta. “Auta gyaran jikin nan na amsarki sosai. Idan kika yosa duk sai ki canja kamar wata amarya dake”.
Da sauri Maanal ta ɓata fuska. Zatai magana aka buga ƙofar falon da ƙarfi har duk sai da suka razana. Hajiya Yaya ce sai yaranta biyu biye da ita. Cikin hargagi da masifa ta shiga ƙwala kiran ainahin sunan Ammie. Duk miƙewa sukayi, dan yanda take a birkice zakasan babu lafiya. Ita kanta Ammie da sauri ta fito ɗankwalinta a hannu.
“Ya salam Hajiya miya faru?”. Ammien ta faɗa tana ƙarasowa cikin falon da sassarfa.
“Oh tambayata ma kike miya faru? Wai Asiya nikam kodai ke kika haifar min Yazeed a gidan nan ne?”.
A hankali Ammie ta sauke ajiyar zuciya tana mai girgiza kanta. Sai kuma a nutsenta ta bata amsa da “Hajiya kiyi hakuri ban san akanmi kike magana ba.
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 5 Chapter of 17