kallo na bisa kafin na mike na fara serving dinsa, ina gamawa na mika masa abincin, komawa nayi na zauna muka ci gaba da hira ni da Commandore Fareed, sallamar Innani ne ya kaste mana hiran, cike da jin dadi ta karasa inda muke tana washe hakora kamar gonar auduga, "Mashaallah Abu yayi kyau, abinci kuke ci ashe ƴan samari,"
Fareed ne ya ce "ehh Innani Barka da dare,"
Kara washe hakora tayi ta ce "yauwa Barka, ɗan albarka, ya mai jiki?,"
"Jiki da sauki sosai, Alhamdulillah,"
"Tohh Allah ƙara sauki,"
"Amen summa Ameen"
Toh gwanar laste laste ke baza ki ci abincin bane, kizo kuci tare mana ai yafi dad'i, kuma zai ƙara muku haɗin kai,"
Ba tare da ta ce komai ba ta taso tazo dining area ta zauna tayi serving kanta ta fara ci cike da Miskilanci,
Wani murmushin jin daɗi Innani tayi taja wani dogon numfashi ta ce "Allah albarka ci rayuwar ku ya kuma ƙara hada kanku,"
Cike da zumudi Commodore Fareed ya ce "Ameen Innani, kin ga na samu ƙanne dama nawa daya ne, in zan tafi sai in kaisu gurin Ammi na ta haɗa su da Mobina sai su zama su uku, kinga mu uku suma su uku,"
wani ɗan guntun ƙwalla Innani ta goge cike da tausaya ta ce "kai yah Fareedu bawan Allah Allah de ya nuna mun wannan rana, da zan miƙa amanar dana dauka ga masu shi,"
Cike da fara'a da ƙwarewa wajen aikinsa ya ce "Ameen summa ameen, ƴar tsohuwa dama ita alƙawari kaya ne mai nauyi musamman inka rike shi a cikin ka,"
"Hmmm wassu lokutan aikewa aciki yafi ka fidda shi sarari, kasan mahassada sun yi yawa, wai kana ta kai su kuma suna ta kai,"
"So sai ma kuwa Innani ai ni zan fada Miki hakan, kinsan fa Yan zu an dena kiwon dabba sai mutum,"
Cike da jimami Innani tace "ohh duniya ina zaki kaimu, Allah de ya kare mana ku,"
"Ameen summa ameen,"
"A'a shi mara lafiyan fah, Nuriyya zo ki kai mishi abinci,"
a dan razane na dago kaina na ganta kafin na,nayi kicin kicin da fuskana na ce 😚 nifa Innani ni wallahi gaskiya ki tura Barira ta kai mishi abincin,
"Eyyeh wai samu ya fi iyawa hawa dokin maciji, in ce ki kai ki kice na aiki Barira, yar tselen uwa ke zaki kai,"
ƙukan shagwaba na fashe dashi na fara shure shure da kafa a kasa, ni ni wallahi abinci nake ci, to ke ki kai da kanki mana tunda ke kin fishi damuwa da yunwar cikin shi,
"Ehyehh kin san Allah zan zazzage Miki bakin rashin mutunci Nuriyya in baki tashi kin kai mishi ba,"
Bil hakki da gaskiya na fashe da kuka ni wallahi bazan jeba nikam, naje ya kashe ni jiya ma da kika aike ni ina sanda ya gwalmadar mun da ƙashin ƙunkumi na,
Sake baki galala Innani tayi tana kallonsa kafin ta fara tafka salati kai kace an aiko mata da saƙon mutuwa,
"Ohhh ni Khadijatu matar Sheik, Yan zu a baƙon ma sanda kika Ni na bakinku na tsiwa,"
Dan kifta ido nayi na mamaki na zaci zata fara surfa bala'i an Jimin ciwo kawai naji ta karya kwana,
"Yan zu ɗiyar nan sanda kika nuna halin naki na tiyara ,"
Zumburo baƙi nayi na ce 😚 nifa ban gane mai kike nufi ba , daga cewa ya gwalmadar mun da ƙashin ƙunkumi, sai ki fara zuba kamar ƙorama, baƙi ma ji abinda ya faru ba har kin yanke hukunci.
"Da ban san halin ki bane da sai na tsaya bin sassala, ai dama tun farko kin nuna bakya son kai abincin dama nasan za'a rina,"
Lallale Innani ya mareni kuma ke ki hanaani ƙuka,
"Ai ni Nourda bai karya ƙunkumin ki Bama ban ji dadi ba,"
Bude baki na nayi galala na yan mintina cike da kututun baƙin ciki na rike kirji na ko ince na dafa ƙirjina, na ce lalle kan Innani zaki fadi haka wai somi ta uwar wawa, lallae ai dama naga take taken ki akan wannan jibgegen basamuden, sai de ban san abin naki ya kai har haka ba amma ba komai, ai dan kinga Hamma Faruq baya nan ne shiyasa kike aikata wajen wani gardi harda maste ni a gini,
Na karasa zan cen ina maste ƙwalla, amma ba komai zan bar miki gidan, kai ƙasar ma gaba daya zan bari, sai shi ya maye miki gurbina dama naga kin fi son shi.
Na karasa maganan yayin da na mike nayi hanyan ɗakin mu.
Galala Innani tayi ta sake ɓaki ta na bina da kallo ta ma rasa mai zata ce, in akwai abinda ta tsana a rayuwar ta bai wuce taga bacin rai na ba ko ince zan bar ƙasar nan hankalinta to ranta inyayi dubu zai tashi.
Fareed ganin tuhumar bana ƙare bane yasa ya ce" ki ɓari Innani inna gama zan tafi masa dashi , shima kina ganinsa ba ƙanwan lasa bane, yana da tsokala, kuma sai wanda yasan halinsa zai gane hakan ,"
Cike da sanyin jiki Innayi ta ce "shikenan to ka kai mishi," ta karisa maganan yayin da hankalinta ke kan hanyar ɗakin mu.
KANO STATE, NIGERIA
MASARAUTAR SUHATAJ MUHD HABIBULLAH
TURAKAR GIMBIYA SAUDAT (KILISA)
Kamar kullum tana Hakim ce a sashin ta bayi na ta faman mata hidima, sai de yau shigar nata na daban ne kasancewar an yi rasuwa tana sanye da fararen kaya hannunta dauke da casbaha.
Sanarwa akayi na karasowar Sarauniya Sareena, cike da taƙama ta shigo ta samu guri ta zauna, bayin na ganin haka suka sallama kansu bayan gaisuwar da suka mata,
Cike da zallan isa ta fara magana kamar haka "bayan kin kashe shi mai ne ne kuma dalilin zamanvmakoki da kike yi anan,"
Cike da izza ta dago kai ta ƙarewa ƴar Tata kallo ta ce "ban gane mai kike nufi ba,"
Murmushi ta sake kafin tace "zaki fadi haka mana Ummi, ina so kisan wawa daban mai wayo daban,"
Murmushi Kilishi ta sake 😏 na gefen ɓaki, "yaro yaro ne wai baisan wuta ba sai ya taka, har yanzu da sauranki Sareena, na haife ki amma naga alama ban haifi halinki ba, yarinta na ɗawainiya dake, ko ince kin ɗauko halin ɗan uwan ki da ake cuta a kullum,"
Kicin kicin Sarauniya Sareena tayi da fuska tace "Ni fa ba zuwa nayi nan don ƙi mai dani yarinya ba, zuwa nayi ki fada mun mai ye dalilin da yasa kike amfani da Mubeen?
Kuma mai Mobina ta miki da kike so ki lalata rayuwar ta?"
Jijjiga Kai kawai tayi kafin ta tsuke fuska ta ce "ina so kisan ni ce mahaifiyar ki, baki da dalilin da zaki zo ki tsaya kina mun wannan tambayoyin marassa ƙan gado,"
"Hummm Ummu kenan, abin da nake so kusani anan shine duk abinda zakiyi ki tabbatar kin tauna rami dai tsayin ki kuma wallahi ki bi ahankali don duk abinda kuka shuka sai kin girbe shi tsabb,"
Cike da bacin rai tace "ya ishe ƙi haka Sareena Ni uwar ki ce ba Sa'ar wasan ki ba, ƙinyi ƙankantar da zaki zo ƙina gaya mun magana sin ranki, Ni zaƙi gani ƙice ina amfani da Mubeen mai yake da shi shudin banza ƙaramin alhaƙi, in Kuma na lalata rayuwar Mobina mai zan tsira dashi, yarinyar daki ishirin bata cika ba, ce Miki akayi ina da lokacin ɓatawa ne akan kananan ƙwari irin wa'yannan,"
Cike da rashin yadda take ƙare mata ƙallo, don in akwai abinda bata yadda dashi a duniya ba to mahaifiyar ta ne.
Mikewa tayi cike da gadara ta ce"bude na fada miki, in kina vin kasa ki ƙiyayi ta shiri,"
Tana gama fadan haka ta baza alkebban ta tayi gaba,
Wani irin ƙuna zuciyar Kilishi keyi tabbas daban dan Sabreena ƴar ta ɓace da ba tan tama yau zata baƙunci lahira, wani abu da ta tuna ne yasa ta sake wani murmushi na gefen ɓaki, ta ce "yaro yaro ne ni dake shege ka fasa, zaki gane ni ba sa'ar ki bane, ki gamaa baki shirin, kina gani zan mulki wannan masarautar babu yadda kika iya dani,"😏
Zaune take cikin wani ɗaki mai shegen duhu tana sanye da wassu kaya jajaye, ba abun da kake iya hange ajikinta hatta fuskar ta a rufe take, hannunta dauke da candle dashi take amfani wajen haska gurin, sanda na kara baza ido kafin na hango wassu samudawa zaune gaban ta yayin da take Hakim ce bisa wani kujera wanda tasha ado da ƙwaran gwal, haka wuyan ta na sanye da wani tafkeken sarka da ƙananan ƙwaran gwal, dana ƙarewa ɗakin kallo ba komai aciki sai wani table mai dauke da wani kwarya akai, da mamakina cikin shi dauke da jini a cike, sai wani ƙaton ƙwaran Gwal ciki an kunna wuta, daga gefe kuwa wasu manyan gumaka ne jibge, komai na ɗakin ja ne.
Cikin wani murya mai wuyar fassaruwa take magana "na baku daga yau zuwa gobe ku tabbatar kun gabatar da aikin dana sa ku,"
Cike da girmamawa da rawar jiki na tsoron abin da zai fito daga ɓakinsa yace" a mana afuwa INNA UWASU INNA UWA MABA DA MAMA adann ƙara mana lokaci, zamu gabatar da wani shiri yanzu yarinyar akwai tsaro mai karfi akan ta muna da buƙatar a fito da ita sai mu ƙaaddamar da aikin mu,"
Cikin razananniyar Muryar ta mai sa maza rawar ɗari ta ce " na ƙara muku ƙwana ɗaya ku tabbatar kun ƙammala cikin ƙwana uku, nake so a rufe babin wannan yarinyar."
Cike da girmamawa suka zuba sujjada a gabanta sua ce "Ran mu fansa ce gareki INNA UWASU, INNA UWA MABA DA MAMA, INNA UWASU BABU IRIN KI A DUNIYA..,"
IRAQ
HOSPITAL
Ƙawance take bisa lafiyayyiyar gadon asibiti, tana sanye cikin kaya na marassa lafiya, fuskan ta yayi fayau dashi kana ganin ta kasan taji jiki.
kallo na ƙarewa dakin zaka ranste dakin wani hamshaqin mai ƙudi ne a Nigeria, komai na dakin a tsafta ce yake, gashi komai fari tas ga sanyin ac dake tashi da wani ƙamshin haɗadden turare ko ince room freshener, daga wani ɓangare na ɗakin kuwa tamkar farlo koma ince farlo ne, yana ɗauke ɗa haɗaddun Couch da madaidai cin Chinese carpet sai Centre table dake stakiya , daga jikin gini kuwa wani ɗanƙareren plasma Tv ne.
Dawowa nayi inda gadon mara lafiyan yake anan naci karo da halittar data ɓan mamaki 😳 wai wata saɓon gani 👀 mai zan gani haka!!
Engineer Othman Ibn Abdallah (ABI), ya na zaune bisa chair dake gaban gadon, yana rike da hannunta daya, da nasa hannun, kallo daya zaka masa ka hango zallan damuwa dake shinfiɗe a face ɗinsa.
Sanda na ƙare masa kallo na hango manyan tan da yayi, sai de duk da haka bai hana zallan kyansa baiyana ba, har ilah yau yana nan yan da yake a giant balarabe, mai farin fuska da kyau wanda ke ɗauke da zallan nustuwa da Chrisma wato ƙwarjini, game da murɗadɗen jiki ko ba abinda ya sauya, yana sanye cikin Black suit wanda ya cire coat din ya bar white long sleeve ɗin.
Daga ɓangaren dama kuwa Fatima ne zaune cikin shiga na alfarma, daga nata ɓangaren itama ta manyan ta sosai, sai de gyara da kula da fata da jikin ta ke samu ya hana girman bayyana, don inka ganta zaka ranste bata fi shekara 25 ba, kasancewar ta mutum mai yiTƙaramin jiki, wani ƙyakyawan yaro ne mai kama da Abi ke ƙwance luff ajikinta, wannan ba kowa bane sai SAWBAN, wanda ya kasance ɗan auta ƙaramin ɗan Fatima mai shekara goma a duniya.
Suna cikin wannan zaman kurame da kowa ke saka abubuwa a ransa ne aka yi sallama, cikin wata siririyar murya ko ince murya mai ɗauke da zallan nustuwa, imani haɗi da zallan Izza.
Ba tare da sun ɗago kan su ba kasancewar sun san waye ne suka amsa sallamar.
Mashaallah lah ƙuwata Illah billah, wannan shine abinda na ce a lokacin da nayi tozali da wannan kyakkyawan halittan, wani farin giant ne mai kama da larabawan Fulani, yana sanye cikin kaƙin sojoji wanda yayi bala'in karbansa wato ya amshi fatar sa ko ince fatar sa ta amshi kayan, kasancewar sa mutum mai haska kaya ba kaya ta haska sa ba, fari ne tas sai de ba irin farin nan mai kashe ido ba, i can say yana da soft and creamy white skin, kamar yadda na faɗi a farko giant ne wato ya na da tsayi da murɗadɗen jiki hadi da faɗi, fuskanshi nada fadi kaɗan da tsayi, fuskan na ɗauke da golden eyes nashi masu sheki da daukan hankalin mai kallon su, bugu da ƙari yasa maza rawar disco musamman marassa gaskiya, golden eyes nashi na ɗauke da long moist eyelashes, wanda suka ƙarawa idon wani ƙyau na musamman, sai well shaped eyebrows nashi Wanda tamkar shi ya seta abin shi, idan ka gangaro zuwa hancin shi kuwa kamar shi ya tsaida abinsa, yayin da inka gangaro lips dinsa ko they are so cute, zaka ranste red lipstick yake shafawa kasancewar su ja, fuskanshi na zagaye da kwanceccen lafiyayyiyar man's pride dinsa wanda aka narkawa Naira, baki sidik dashi ƙawance luff, yayin da kanshi yake a cike da gashi da yayi nasaran saukowa har wuyansa, baki ne sidik mai tsansti, idan ka ƙare mishi kallo zaka rasa a wani fasali zaka ajiye shi, baza ka kirashi da balarabe ba, haka ka zalika baza kace dashi bafulatani ba, sai de yanayin sa yafi kama da bahaushe wato dan Nigeria, duk da kyau da yake dashi bai hana asalin sa bayyana ƙarara ba.
Wannan ba kowa bane sai LITTLE IMAM(FARUQ) Wanda ayanzu duniya ta shaide sa da MAJOR GENERAL UMAR FARUQ IBN OTHMAN ZUNNURAIN.
Popularly known as 🐅 TIGER. Yana daya daga cikin manyan jami'an tsaron da Duniya ta shaide su , kasancewar sa Jami'i na ƙasa da ƙasa, wanda yasan aikin sa, duk da kasancewar sa mai ƙananun shekaru bai hana zallan Izza da ƙwarjinin sa baiyana ba ako ina, musamman a filin daga wato filin da zai yi fito na fito da maƙiyansa, ya kasance mutum mai tarin masoya haɗi da maƙiya, kasance warsa mutum ne da bai yadda da rashin gaskiya ba, wanda sanadin hakan ya samu cigaba da dama a ɓangare daban daban na rayuwa, a yau yake da shekara 30 da wasu watanni ya tsallaka gada da dama wadda mutane dayawa basu tsallake ba , ciki har da wayan da basu kai sa shekaru ba, idan na cigaba da baku labarin irin nasarorin da MG FARUQ ya samu tabbas zamu wuni mu hanste anan, saboda haka back to normal labari...😁
Cike da zallan isa, mazantaka da zallan Izza yake tafiya har ya iso bakin gadon mara lafiyan wanda ZULAIHAT je ƙwance luff, Abi ne ya dago tunanin idonsa ya zuba su a fuskan MG FARUQ ya ce "what did the Doctor said?,"
Digon numfashi yana kafin ya ja kujerar ya zauna ya ce " No need to worry, she is alright, Bp ta ne ya hau sai kuma zuciyar ta da tsinke but munyi magana da Dr Fauziyya ta ce mu tabbatar bata kara shiga irin wannan yanayin ba, we should make sure an mata abinda take so, so that zata rage tunani, that will help her heartbeat to settle down,"
Dogon numfashi yaja ba tare da ya ce komai ba suka ji ta fara tari tana buƙata ruwan sha, cike da rawar jiki Fatima (Ummi ) ta mika wa Abi bottle water, cikin sauri ya bude yayin da MG FARUQ ya tallafe ta ajikinsa shiko Abi ya bata ruwan, cike da ishi bukatar ruwan take sha, sanda ta kishi Dan kanta kafin ta ƙauda kai ya cire mata bottle din daga bakinta, shi kuma Mg Faruq ya gyara mata kwanciyar ta wato ya ƙishin giɗar da ita ajikin filo, cikin wani yana yi ta fashe da ƙuka mai cin rai wanda kana gani ƙasan daga ƙasan zuciyar ta ke fitowa.
Ummi ne ta ƙira Mg Faruq "Faruq zo ka ɗauki SAWBAN kuje waje,"
Ba musu a zo ya ɗauki SAWBAN da yayi wulwul da ido yana don yin kuka ganin halin da Momyn sa take ciki, be yi wata wata ba ya sa hannu ya dauke shi kamar yaro ɗan shekara uku,
ta cigaba da kuka cikin wani yanayi, jiki ba ƙarfi Abinda hau rarrashinta yana cewa "Sabr yah Ukhtie,"
Cikin sheshshekar kuka ta ce "ya zan yi hakuri Akhie a dake Ni a zamanin ƙuka , sun auren dole kuma su koreni daga gida batare da tunanin wani hali Ni Ko abin na haifa zasu shiga ba, kaduba kaga Akhie shi hankalin sa a kwance har da yin wani auren biya barni da igiyansa a kaina,"
Cike da rashin fahimta ya ce " I don't understand waye yayi auren ?,"
"Ni ma ban sani ba Akhie, yayi auren sa harda ƴarsa zama tayi aure Ita ma,"
Dan shiru yayi din sai Yan zu ya gane mai take nufi kafin ya ce "wa ya ce Miki zai aurar da ƴarsa?,"
"Ba Sawban ba ne yake fada mun and am very sure shine cos har sunan sa ya fada mun wai Shahzad ne zai aure ta,"
Dan shiruu yayi alaman tunani kai tsaye bazai ƙaryata zancen ba don shima yaji magana makaman cin wannan,
"hmmm Zulaihat I know how you are feeling right know, but I want you to know and understand Babu Wanda Ya Isa Ya hana abinda Allah ya ƙaddara faruwar sa, they abondone us Kuma sun mana iyaka da komai nasu, kin san ƙa'idar su in suka yi exiling naka to baka da wani ikon yin bincike ko Sanin abu game da Masarautar, so please come down, let it be , let the past fly away, try and brainwash them from your mind, I know is hard but try as possible as you can, mun girma mun ajiye iyali ga yaran mu sun girma ƙaramin cikin su shine mai shekara goma, pls kiyi hakuri Allah bai manta damu ba, ya rufa mana asiri ayanzu muna da duƙiyan da zamu iya ciyar da Mutanen dake Masarautar Suhataj Abdallah, gamu da yara da suka zamanto sanyin idaniyan mu, babu abinda muka rasa ku cigaba da addu'a ayanzu in muna da damuwa bai wuce na rashin Myreen ba, muyi addu'a Allah bayyana mana ita,"
Wani dogon numfashi taja don maganar tayi tasiri a zuciyar ta kafun tayi narai narai da ido ta ce "Please Akhie take me to Innani and Abba i miss them so very much,"
Tayi maganan yayin da ta ƙara narke face din ta, gyada Kai yayi ya ce "okay I will talk to Faruq zai shirya muku tafiyar,"
Dan turbune face Fatima tayi ta ce "Ni fah,"
Da wani ƙallon gefen ido na ƙasa ƙasa ya bita
dashi bai ce komai ba, ita Ko sai kara narke fuska takeyi, Zulaihat ko sai zuba murmushi takeyi don ba karamin burge ta suka yi ba, ganin in bata sa baki ba bazai barta ba yasa ta ce " shike nan sai mu tafi dasu ILHAMA da AJLAL naji sun ce gobe zasu dawo Sawban kuma jibi za'a basu hutu, shikenan sai muyi best Vocation ever, I guess we will have lot fun,"
Shiruu Ayi Bai ce komai ba, in akwai wanda ya tsana rayuwar bai wuce ace Fatima zata masta daga inda yake ba ma'ana tayi nia dashi.
Dogon numfashi yana ɗon bazai iya cewa Fatima ba zata je ba , sabida a yanzuyan son farin cikin Zulaihat ga ita ƙanta Fatima ta daɗe sosai bataje ganin gida ba,
,"hmmm okay,"
Cikin farin ciki Fatima ta bashi wani side hug batare da ta samu tayi hakan ba, sautin murmushin ZULAIHAT da ta jiyo ne ya sata ta sake shi da sauri, kawai ta rufe fuskanta, Zulaihat kuwa ta kwashe da wani dariya mai ƙyataar wa, ta fara tsokalan ta.
" Sannu Gimbiyar alkunya wai har yanzu baki dena ƙunya nan ba yau shekarar ku talatin da aure amma har yanzu baki dena ba yar fillo,"
END OF PAGE 37
Follow for more 😍😘
Story and written by
Queen Mahirah 👑
The wordsmith 🖊️📖
🧚THE TWO LIGHTS ✨ (RIKICIN GIDAN SARAUTA🏰)🧚
The story contains the fact Royalty, Ego, Separation, disastrous love, hatred, hardship, twin flame journey...
Story and written by
Queen Mahirah
The wordsmith
WHATSAPP CHANNEL
https://whatsapp.com/channel/0029VacL1MhFy723j9fdgJ20
WHATSAPP GROUP
https://chat.whatsapp.com/CztvtzKaDeqHqlqpuCyeNG
📱 Typing
FREE BOOK 📚
BOOK 1
🧚38🧚
RUGAR HARDO BELLO (KANO STATE, NIGERIA)
Cikin sanyin jiki Innani ta koma farlo ta samu guri ta mawa kanta mazauni, rafka uban tagumi tayi, yayin da take facing ɗakin su Mahnoor sai saƙa da warwara takeyi.
Cikin nustuwa Chief Imam yayi sallama wanda yayi nasaran dawo da Innani cikin normal sense ɗinta, a ƙasan maƙoshinta ta amsa sallamar tasa kasancewar bata cikin mood mai daɗi, Fareed ne ya amsa sallamar cikin fara'a da sakewar fuska, yayin da Islam ta isa har inda yake ta karbi abinda ya shigo da shi ta kuma mishi sannu da zuwa, sannan ta dauko mishi ruwan sha.
Fuskar sa ɗauke da fara'a wanda ya bawa Innani mamaki matuƙa har yasa ta fara tunanin koɗe an samu labarin Myreen ne, cikin Muryar sa mai cike da zallan dattaku da nustuwa ya ce" Barka da dare uwargidan Sheik?
Da fatan na same ku lafiya?,"
Wani dogon numfashi taja yayin da ta nemi duk wani damuwa ta rasa, ita kanta tasan tayi Sa'an miji, idan da akwai abinda ke kara sata farin ciki da son cigaba da rayuwa bai wuce Sheikh da Mahnoor ba, tasan soyayyar da ke tsakaninta da Nooriyya wannan hadi ne na ubangiji, Sheik kuwa ƙyawawan halayyar sa na daya daga cikin abinda yake ƙara mata son sa.
Authors Note
"Shin kun lura da wani abu anan kuwa🤔?
Shigowan Sheikh Innani bata ce dashi ƙala ba😞, haka bata karbi jakan hannun shi ba Wato abinda ya shigo dashi.
Amma abin mamakin anan shine, shi yana zuwa ya fara tambayar lafiyanta bayan mika mata gaisuwa da yayi.
Kuma fa karku manta cewa bata gaishe shi ba.😳
Akwai wanda zai iya fada mun mai yasa bai damu da rashin kula shi da bata yi ba?🤔
Nawa bangaren Ni Queen Mahirah nace abinda yasa Sheik bai damu da rashin karbansa da bata yi abu biyu ne✌️,
👆 Shine a lokacin da sa ya shigo ya kula da yana yinta wato ya fahimci cewa tana cikin wani hali na ƙunci, shiyasa ya mata uzuri.
mai yasa ya mata uzuri?
Shine mutum ne shi mai saurin fahimta bugu da ƙari ya karanci halayyar ta, sannan shi mutum ne mai saukar da kanshi musamman abangaren rayuwar sa da iyalinsa, wato zamanta kewar sa na aure.
✌️Ya mata uzuri sabida ba haka tasaba mishi ba, kasancewar ta mutum mai tsananin biyayya da basa kula, yana daya daga cikin abinda yasa ya mata uzuri a yau.
Darasin da zamu ɗauka anan shine, ita rayuwa musamman na aure ana da bukatar fahimtar juna, sannan ka kasan ce mai yiwa abokin zaman ka uzuri a wasu lokutan, ka kuma yawaita karantar yanayinsa a lokaci mabanbanta, ma'ana lokacin da mutum ke cikin farin ciki da akasin haƙa."
BACK TO LABARI 😁
Dogon numfashi taja kafin tace "Sannu da Zuwa Sheikh, lafiyan mu kalau, ya aiki da fama da jama'a,"
"Alhamdulillah,"
"Toh Allah kara rufa mana asiri ya Kade hau, ya raba ka da cin haram, da kuma sharrin maƙiya,"
Gyada Kai yayi cike dajin daɗin addu'ar da ta masa ya ce "Ameen summa ameen Mar'atussaliha, Allah ya yiwa rayuwar ki albarka,"
"Ameen summa ameen,"
"Ina Noorul hudah,"
in ji Sheik wanda ya tambayi Islam, cike da miskilanci ta ce "tana daki, bari na ƙirata,"
Gyada mata Kai kawai yayi, yayin da ita kuma ta Kama hanyar dakin da niyan ƙiran Mahnoor.
Innani ne ta tattara hankalinta zuwa ga Chief Imam ta ce" Mashaallah naga yau kana cikin farin ciki Allah de yasa alkairi ne ya samu?,"
Wani murmushin ya kuma sakewa kafin ya ce "yau munyi waya da Hamma,"
Washe baki Innani tayi ta ce "😁 to to mashaallah ince Zulaihatu na lafiya,?"
Bai kai ga bata amsa ba, sallamar Mahnoor ya kaste su, amsa sallamar suka yi yayin da Innani takafe ta da ido tana so tasan wani yanayi take ciki.
cike da nustuwa na karasa inda Chief Imam yake na tsugana har kasa na gaishe shi, cike da fara'a ya dafa kai na ya amsa gaisuwan nawa hadi da samun albarka.
"Mun yi waya da Abi ya ce mun nan da ƙwana uku Ummi da Momyn ku zasu zo dukansu,"
Cikin wani farin
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 23 Chapter of 25