ya hana, inaso kasan Baba sarki sun kasance sanadi ne kawai na faruwar hakan kasan komai da sanadin faruwar sa Kadaina ganin laifinsu suma bada son ransu hakan ta faru ba ka yafe musu ka kuma nemi yafiyar su hakan zai sanyaya ranka,"
"Zanyi hakan Ummi amma ba yanzu ba yanzu ina da bukatar kasancewa da ƴata ina kuma bukatar ta samu lafiya kamar yadda kika bukata zan barta tayi rayuwar aurenta amma bana naso mutanen duniya su san da ita kamar yadda ban bukatar Masarautar Kano su san da ita bawai dan ban yadda da ita mastayin ƴata bane inaso nayi bincike akan abubuwan da suke faruwa a Masarautar Kano daga rashin Othman da mukayi har zuwa na ita Zulaihat din tabbas akwai lauje cikin nadi akwai wanda ke shirya faruwar hakan don yana so ya cimma wani buri nashi ta hanyar mana ƙare dangi.
Yanzu ina da labarin cewa an rasa yarima mai jiran gado sannan kafin hakan Baba sarki yayi kokarin korar Fareed daga Masarautar bayan kananan abubuwa da suke faruwa,"
"Tabbas maganan ka gaskiya ne Kahter akwai abinda ke faruwa musamman ta bangaren shi ABDALLAH akwai wanda ke amfani da hankalinsa sai de ban san taya hakan ke faruwa ba amma akwai matsala gagarumi,"
Dogon ajiyan zuciya Malik Sultan yaja kafun ya fara magana cikin nustuwa
"Haka ne abinda kuka fada gaskiya ne amma yanzu abinda ya kamata mu maida hankali wajen samarwa Mehnoor lafiya sannan Musa staro mai karfi akan ta duk da bamu sanar da duniya asalin wacece ita ba, sai de mutanen dake family nan sun san da haka kuma kunsan a wassu lokutan shi munafikinka taburman ka ne,"
Cike da yadda sukayi na'am da abinda Malik Sultan yace.
END Of PAGE 29
Comment and share Please
THE TWO LIGHTS (RIKICIN GIDAN SARAUTA)
Story and written by
Queen Mahirah
Adapted Expert Writer
Ina godiya sosai 😁 OUM AFFAN da irin kaunar ❤️ da kike nunawa littafina wannan page din sadaukarwa ce agareki🤣😊
FREE BOOK
BOOK 1
PAGE 30
IRAQ
Wani katafaren Mansion ne mai dauke da kayan alatu da more rayuwa, tun daga waje kasan ba karamin kudi mamallakinta ya kashe mata ba, ita kanta gate din abun kallo ne daga ɓangaren dama akwai wani ƙaramin sign board da aka manna ajikin gini wanda yasha ado da kwalliya na musamman zaka ranste da glass akayi don yadda yake ɗaukan eyes 👀 ita kanta yadda akayi rubutun abun kallo ne tamkar da ruwan gold haka yake ɗaukan ido gashi anyi shi in a stylish form an rubuta ENGINEER. OTHMAN IBN ABDALLAH MANSION.
Daga ciki kuwa wassu fusatattun Body guard ne masu sanye da baƙin suit idonsu garkame da baƙin eye glass ba alamun ko fara'a a fuskansu.
Wata dalleliyar Car na hango mai ɗaukan ido da hankalin Me kallonta ta shigo cikin Estate din, Bata tsaya ako ina ba sai bakin tamkamemen Mansion din wanda aka rubuta Engineer. Othman Ibn Abdallah ,
cikin kankanin lokaci aka wangale musu gate din suka shiga cikin Mansion din Mashaallah shine abin na Fadi tabbas anyi barin Ƙudi ko ta ina anyi masa kawanya da kayan more rayuwa ba abunda ke tashi sai sanyi da kanshi hadaddun Flowers ga wani designer interlocks da aka zuba a harabar Mansion din.
cike da takama wannan dalleliyar Car din ta cigaba da tafiya bisa wani shinfidadden kwaltan dake shimfide inda ya sada su da wani gate din na daban inda wassu murdaddun sojoji ke kula da shiga da futa ba tare da bata lokaci ba suka wangale gate din Kasancewa sun san waye aciki, Car din ta cigaba da Rasta shinfidadden kwaltan har ta isa parking lot wato inda aka tanadar don parking cikin jerin wassu hadaddun cars wanda yasa na fara tunanin 🤔 ko Company mota nazo ina cikin wannan tunanin ne karan bude cap din motan ya dawo dani normal sense Dina,
Cike da mamaki na sake baki🤤 ganin wanda ya fito daga cikin wannan lafiyayyiyar Car din.
Sanye yake da School uniform fari ne tas tamkar balarabe mai tsananin kyau da ɗaukan hankali Fuskansa ɗauke da fara'a wanda ya kusan zautar dani 🤯 sabida wani annurin kyau daya bayyana a face dinsa Kasancewarsa mutum mai dogon hanci madaidaici wato dai dai face dinsa na yara ga small cute lips din sa wanda yake pink colour ga dara daran lulu eyes 👀 dinsa da well shaped eye brow dinsa gashin kansa zaka ranste na mata ne kasancewar sa baki wuluk mai tsantsi.
Murmushi ya sake yaron cikin muryansa me zaƙi da dadin sauraro "thanks Masroor " ya faɗi haka yayin da yake mika mishi hanu alaman ya bashi school bag dinshi,
Cike da girmamawa wanda aka ƙira da Masroor ya dan duka dai dai tsayin yaron da bazai wuce ten years ba ya bashi school bag din, karba yayi ya fara tafiya cike da nustuwa yana dumfaran wani Duplex wanda yasha white paint gefen hagu da dama kuwa flowers ne wanda suke from different varieties,
ya cigaba da tafiya yana dumfaran tafkeken ginin mai hawa biyu wato Duplex daya daga cikin soldiers din dake tsaye agun ne yayi saurin mara masa baya ya bude masa well designd kofan dayake tamkar glass sai de koda wasa baka kallon wanda yake ciki sai de shi ya ganka.
Tabbas Allah ba azzalumin bawansa bane duba da irin arzikin da aka kashe awannan farlon sai ka ranste ba'a duniya kake ba zamu iya cewa aljannar duniya ce wannan farlon komai na cikinsa unique ne white and black dashi akayi anfani wajen ƙawata farlon da kayan ado kana shigowa sanyin ac da kamshin air freshener ne zai fara maka welcome .
Da shigansa house maid din dake faman jera abinci a dining area ne ta fara welcoming nashi tana sanye da wani kaya wanda ko ba'a fada ba kasan uniform ne Black and white sai half sunna dake kanta wanda yake fari tas dashi da fara'a a fuskanta take tarbansa hakan kaɗai ya isa ka fahimci akwai shakuwa mai ƙarfi a stakaninsu,
"'Ahlan wa sahlan you are highly welcome Mr SAWBAN, Good afternoon,"
Cike da fara'a wanda da alama halittansa ne yace da ita "Afternoon Nanny Maya,"
"Where is my Mom?,"
Da index finger dinta tayi pointing wani kofa dake saman beni "she is inside her room,"
"Okay 😊 but I hope she is fine?,"
"Yes Mr Sawban she is fine,"
Kanshi kawai ya gyada kafun cike da zumudi yayi hanyar stairs wato matakala ya hau directly dakin da yake facing yayi knocking ko jira baiyi an mishi iso ba ya shiga dakin Kasancewa abude yake sannan ita kanta kofan da Tom print take aiki.
Cikin hadadden farlon ya Rasta da gudunsa ya wuce daya daga cikin kofofin dake farlon ya bude ya shiga cikin narkeken dakin da yasha ado na alfarma wata mata na hango zaune ko ince kishingide bisa royal king size bed ta lumshe idonta tana sanye da white abaya mara nauyi da ado kanata sanye cikin white turban tayi kyau matuka hannunta da chasbahanta tana ja da alama dhikr take yi kana kallonta kasan balarabiya ce mai ji da kyau da zallan ISA da Takama kana kallonta kasan Hutu ya Rasta ko ina ajikinta ga wani haske da Annauri dake fitowa daga fuskanta.
Cike da murnan ganinta ya shiga da gudu "Oyo momcy,"
Ware large eyes dinta tayi ta zuba masa su na yan wassu sakanni kafin ta sake wani kayaceccen smile daya sa na kusa zaucewa mikewa tayi daga kishingiden da take ta ware masa hannunta ya fado ƙirjinta cikin melodious voice dinta ta fara magana wanda kana ji kasan ta haɗa da jinin sarauta
"Ooyo yo my dear I miss you so much 😍 my boy ,"
"Nima nayi missing dinkin Momcy how was your body?
I hope you are fine ?"
cike da ƙauna ta fara shafa yalwacecen sumar kanshi " am fine little pumpkin I have recovered,
How was your day at school ?"
"It was superb but inna tuna baki da lafiya sai naji wani iri "
Folding face dinshi tayi ta lakaci hancin shi "uhmm You don't have to worry that much am fine I already recovered,"
"Okayy but kinci abinci ,"
Murmushi tayi kafun ta gyara masa zamansa mai kyau ajikinta
"You don't have to worry about me,
Ahaaa that remind me how was the Mathematics Class Mai aka muku yau?,"
Tabe baki yayi "The class is so boring Mom Maths teacher din mu yayi tafiya wai zaije wajen aure a can Egypt there Crown Prince will marry ,"
Wani rass taji a ranta dajin abinda ya fada haka kawai ta tsinci kanta cikin wani yanayi na waswasi wanda ita kanta bata san na maiye ba duk da bayau ta saba shiga wani yanayi ba in an ambaci kasar Egypt hakan na tuna mata da wasu abubuwa da suka faru a baya wanda yanzu bata fatan tuna su kasancewar ta fara sabon rayuwa mai cike da kwanciyar hankali kafin wannan ƙaddara ta sako kai wanda ya dawo mata da komai sabo har ya haifar mata da Bp dinta ya hau sosai.
"Momy kinyi shiru baki ce komai ba ,"
Firgita tayi ta dawo normal since dinta "ohhh sorry pumpkin muje ka cire uniform dinka ko kayi wanka ko in maka ,"
Murmushi ya sake cike da jin kunya " Ni Mom zan yi da kaina ai na iya ,"
"Okayy as you wish your majesty,"
Murmushi ya sake cikin jin dadin sunan data kirasa dashi wanda ta saba kiransa dasu ko ince ire-iren sunan.
Tare suka fito daga dakin nata Suka nufi dakin dake kusa da nata shiga sukayi ko ba'a fada ma ba kasan wannan dakin mamallakinta yaro ne kasancewar komai na yara ne a dakin Sannan anyi amfani da white and blue colour wajen ƙawata Dakin, dressing room suka wuce directly ta taimaka masa ya cire uniform dinsa sannan ya shiga bathroom cikin mintinan da baifi uku ba sai gashi ya fito daga bathroom din yana sanye da bathroom towel , Dan ware ido tayi da ganinshi don batayi tsammanin ganinshi yanzu ba,
"Ohh my God of mercy Sawban don't tell me cewa har kayi wanka,"
Gyada Kai yayi yace ehh Momy na fita sosai ko
Sake baki tayi tana kallon shi "as how Sawban ?
gaba Daya fa baka fi 3 min a bathroom din Nan ba and wai ka gama wanka wannan jika jika kayi ba wanka ba ,"
dan zumburo baki 😙 yayi gaba "Mom nayi wanka mai kyau fa da bath foam ma nayi amfani ba soap ba har sponge sanda nayi wanka dashi yau ,"
galala tayi tana kallonsa "yah Allah sawban don't tell me baka amfani da sponge dama in zakayi wanka ,"
Willi Willi ya fara yi da ido 👀kamar barawon ƙaya
"That shows magana ta gaskiya ne kenan ,"
dan sadda kanshi yayi kasa ya fara zagaya gurin da yake tsaye da kafansa ko ince babban ya tsantsa,
Ajiye kayan data dauko mishi tayi bisa hadaddiyar gadon dake dakin wanda aka lailaye da bedsheet blue color jikinsa da zananen avengers inda yake ta karasa tasa hannunta a kunci sa ta tallafo
"These shows baka wanka da sponge sawban so kake ka zama dirty boy "
da sauri ya girgiza mata Kai alaman a'a murmushi ta sake ta Kano hannunshi akan chair dake gaban dressing mirror dinshi ta ajiye shi tagoge mishi jikinsa tsaff ta shirya sa cikin kayansa marar nauyi sky blue armless t-shirt da white 3 quarter.
Cikin kankanin lokaci ta gama shirya sa suka fito farlo already an jera masu abinci a dining area can suka wuce suka samu gurin zama after serving nashi da tayi ta shiga bashi abincin a baki.
"Momy mai yasa mu baza muje Egypt ba tunda muma yan can ne "
Wani rasa taji a ranta wanda yasa take ta ajiye spoon din hannunta ta dago ta ganshi
"Mai yasa za muje Egypt?""
"Muje auren ɗan Sarkin Egypt Ameer Mahbeer naji ance za'a yi taro sosai wai an dade ba'a yi aure ba kuma wai ƴar Ameer Muhd Kahter Ibn Abdallahh zai aura,"
Fas fass!!! Kake ji ƙaran breakable cup din dake hannunta ya fadi wani ras zuciyanta ya bayar cikin kankanin lokaci ta canja
Matar da yanzu shigowan ta ne tayi kanta da sauri "subahanallhi Zulaihat mai ya faru "
kokarin tashi take amma ta kasa tsabar yadda heart dinta ke bugu so fast kamar zai fito waje dakyar ta mike wanda ko sakan batayi ba ta fadi rigijibbb akasa
Ware ido tayi ta karasa da gudu cikin rudu take ambatan sunan Allah ganin ko numfashi mai kyau batayi ne yasa ta kwala kara "Sawban kira Akhie dinka da gudu yana farlo ,"
KANO STATE (NIGERIA)
MASARAUTAR SUHATAJ MUHD HABIBULLAH
Court room (kotu dakin Shari'a)
"Bayan bin cike mai tsayi da akayi an kama Yarima Mubeen da laifin keta hakkin bayi ba daya ba biyu ba har goma sha biyar, sannan an kama shi da laifin cin amana da kuma bata sunan Yarima Fareed bugu da ƙari ya zubar da kima da darajar Masarautar nan mai tarin albarka.
Da duka wannan laifin yasa wannan kotu mai tarin albarka dake ƙarƙashin Masarautar Suhataj Muhd Habibullah ta yanke masa hukuncin dai dai da laifinsa kamar haka;
Na farko kotu ta yanke masa hukuncin daurin rai rai Kasancewar bai wahalar da Shari'a ba yasa ta masa sassauci batara ba kuma horo mai tsanani.
Na biyu kotu ta yanke hukuncin warware alkawarin auren dake tsakaninsa da Sarauniya Mobeena Kasancewa yaci amana sannan bada zuciya daya yake sonta ba.
Na uku zai wanke Yarima Fareed daga zargin da ake masa na lalata rayuwar bayin Masarautar nan.
Wannan shine abinda kotu ta yanke,"
Cike da girmamawa Sarkin Shela ya fuskanci Suhataj da kuma Baba sarki yadan sadda kansa Alaman girmamawa cike da isa Baba sarki ya masa alama daya mike sannan yayi gyaran murya wanda yasa kowa hankalinsa ya dawo inda yake don sauraron abinda zai fada
"Har yanzu kana da damar sanar damu dawa kake aiki a Masarautar nan?
waya saka ?
Na maka alkawarin idan ka fada zansa a maka sassauci koma a yafe maka duka laifinka naga Alaman kai yaro ne har yanzu amfani kawai ake da yarintar ka, ka fadi koma waye ne za'a masa hukunci dai dai da abinda ya aikata "
Mubeen dake durkushe akan guiwansa da dogarai a gefen hagu da damansa hannunsa ko a daure tam ya sake wani murmushin gefen baki
"For all this years kun kasa gane wanda yake hada kanku ya gwara yake wargaza maku farin ciki, shine yanzu kake tsammanin inna fada ma zaka yadda kuma zaka iya yin maganinsa"
Cike da karsashi dogarin dake tsaye akansa ya daga dori nan sa zai zuba masa
"Kai hattara karamin mutum a gaban manya kake ka kiyaye harshen ka,"
Bai kai ga zuba masa ba Baba Sarki ya daga masa hannu wato ya dakatar dashi
"Ban gane mai kake nufi ba jikana ,"
"Baza ka taba ganewa ba abinda kawai nake so kasani shine maka shinka yana tare dakai yana kuma maka tono kuskure kadan zakayi ka fada cikin wannan ramin inaso kasan yadda da wassu mutanen ba karamin illah bane ka nustu kasan mai kake ciki koda kun kawad dani inaso kusan kun kashe maciji ne baku sare kai ba, dakai nakeyi mai martaba Suhataj kar kayi tunanin dan uwanka na jini ne ke maka wannan abun don dan uwanka zai iya cin naman ka amma bazai taba tauna ƙashinka ba,"
tass!!! Kake ji Gimbiya Zunnura ta wanke fuskan Mubeen da mari
"Kaci amana ta ka tauna mun asiri Ni ba wannan tarbiyan na maka ba Mubeen kaduba kaga mutanen nan su suka maida kai mutum suka baka mukami daga jikan Waziri kazama Yarima Mubeen sun ci dakai sun shayar dakai sun tufatar da kai, ba banbanci tsakaninka da ƴaƴan da suka haifa shine zaka saka musu da Wannan danyen aikin,"
Cukumoshi tayi cikin ƙunan rai tana kuka maiƙona zuciya "ka fada mun dawa kake aiki waya ke saka Wannan ɗanyen aikin ,"
bata kai ga kammala zancen bakinta ba jiri ya kwashe ta zata fadi cikin sauri Gimbiya Fadeela dake gefenta ta tare ta inda sauran bayi suka taimaka mata cikin kankanin lokaci kotu ta hargiste hankalin kowa ya koma kan Gimbiya Zunnura tuni aka samo mata Doctor aka mika ta Clinic dake kusa na cikin Masarautar wanda yake kafin Hospital din Masarautar nan aka shiga bata agajin gaggawa.
Daga fannin Mubeen kuwa aka maida shi cikin kurkuku aka kulle shi.
Ya bar zukatan mutane da dinbin tambayoyi
Shin dawa Mubeen yake aiki ?
Waye Mubeen mai ne ne Asalinsa?
Mai Mubeen yake nufi mai kuma yakeson fadawa Suhataj Muhd Habibullah?
Domin jin amsa wannan tambayoyin ku cigaba da bina a ƙafafen sada labarai kamar haka
Arewabooks
Wattpad
Telegram
My WhatsApp group
My WhatsApp Channel
Anan zaku samu Update akai akai ko ka tun tube Ni ta wannan lambar a WhatsApp 09168962485
Story and written by
Queen Mahirah
Adapted Expert Writer 🖊️❤️
Masu comment ina godiya sosai 😁
Comment and share Please 😔
🧚THE TWO LIGHTS ✨ (RIKICIN GIDAN SARAUTA🏰)🧚
The story contains the fact sympathy,ego, Royalty, hatred, hardship, disastrous love and twin flame journey...
Masu comment 😁ina godiya Allah barmu tare.🤗
Oum Affan ina godiya da irin ƙaunar da kike nunawa littafina.❤️
Story and written by
Queen Mahirah ❤️
The adapted Expert Writer 🖊️🐊
Ga masu bukatan the two lights (rikicin gidan sarauta), zaku iya samu ta hanyar following account nawa da channel Dina kamar haka 😁
Wattpad
queenmahirah14
Arewabooks
Queen mahirah
Ko ku tuntube Ni ta wannan lambar a WhatsApp 09168962485
Don na sambada ku cikin groups da Channel nawa.
Ko kuyi searching group Dina a Facebook wato Novels by Queen Mahirah.
FREE BOOK
BOOK 1
🧚31🧚
RUGAR HARDO BELLO (KANO STATE, NIGERIA)
7:30
Zaune muke a dining kamar kullum munyi shirin tafiya school, cikin kwanciyar hankali muke cin abinci ko ince cikin nustuwa da sanyin jiki, kasancewar mun samu labarin cewa Momy ba lafiya, duk da Hamma Faruq ya tabbatar mana da cewa jikin nata da sauki sai de hakan baisa hankalin kunya kwanta ba.
"Iko sai lillahi Rabbi, kuna cin abinci kamar dole aka saku, makarantar ne baƙwa son zuwa?,
Ko abincin ne bai muku ba?"
Cewar Innani kenan da yanzu shigowan ta farlon ta taradda mu muna cin abinci shine ta hau sababi yadda ta saba.
"Ina muku magana kun zuba mun idanunku kamar na tsofin Mayu kuna kallo na"
Dogon numfashi naja na mike da niyan barin dining area don bani da ra'ayin biye mata yau.
"Ohh 😯 ni Khadijatu daga magana sai cibi ya zama ƙari, tun da baza kici abincin ba zoki kaiwa yayin baku abinci,"
Zumburo baki nayi gaba na hade gira nace yayu a ina kenan,?
Dama muna da wassu yayu ne bayan Hamma Faruq,?
Na mata tambayan ina tsare ta da lulu grey eyes Dina
"Ohh ni Khadijatu Nooriyya bana son bakin hali fah sai aka ce Miki bayan Sheik fetel ya haramta kuyi wassu yayu?
Bana son Wannan hade fuskan naki karku ƙore mana baki da bakin hali ki da ƙwayar idonkin kamar na mage,"
Cuno baki nayi gaba na kara bata face cike da zallan tabara na fara magana,
Ni Ni wallahi ba yayu na bane haka kawai, wassu masu murdadden halitta da hadadden fuska kice wani yayu na, sun wani cikawa mutane gida da ƙattin sojoji ba gyira ba dalili,
Ni wallahi bani da hadi dasu.
"Kyaji dashi ƴar tselen uwa, abinci ne de sai kin Kai musu ko zaki sheke, jiya Islam ce ta kai, toh yau ke zaki kai, kafun su saba su fara zuwa nan suna ci,"
Ware ido nayi in disbelief nace wai a ina ?
Kina nufin nan dakin ƙatti zasu na cin abinci, tab wallahi da sake, magana kike son ji ai ko zaki samu buhu buhu,
"Kede kika sani ki fito ki kai musu abinci, cin abinci anan kuwa ba abinda zai fasu, in kuma kece dani ba nine da ke ba sai ki hana mu gani ,"
Tayi magana yayin da ta bani baya wato tayi hanyar futa daga farlon, ta barni tsaye kamar statue cikinsa cike da takaici.
Cike da jin haushi na juya na fuskanci Islam nace kiji abinda matarnan take fada, kuma wallahi da gaske takeyi, Ni wallahi bana ƙaunar su ko kadan, musamman wannan mai Manyan idon,tuna shima yana sani jin wani tashin hankali i na musanman,
Cike da manyan ce Islam ta tari tissue ta goge lips dinta, dafa kafada a tayi cike da lallashi
" Cike down Noor don't bother yourself, kinsan halin tsohuwar nan sarai da kafiya, taurin kanku bazai sauya mata ra'ayi ba.
Kibarsu su zo na dan lokaci ne, su irin baƙin nan ba'a musu baƙin hali, ko baka son su kadanne zasu bar mana gidan, so kawai ayi sha'ani, amma in sun nuna ɗan yen kai then zamu nuna musu ba'a ja damu,"
Ta kammala maganan yayin da take buga kafadana with full of hope.
Turbune face nayi nace nifa wallahi reni ne da bana so, ba yadda za'a yi su mai dani baiwarsu naga su yan sarauta basu da mutunci wassu lokutan.
"Don't worry Sis, gidan mu suka zo neman magani so I don't think zasuyi gan gancin Mai damu bayinsa, inji sukayi hakan tabbas zasu taruwa kansu match da baza su iya kare kansu ba, trust me ni na fada muku haka ba'a ja damu,?"
Shike nan Allah basu ikon kama girmansu, don shine abinda zan iya fadi yanzu,
"Ameeen, so know hurry up ki kai musu abincin kinsan munyi latti, yanzu about seven fourty, let us not be let,"
Kai kawai na gyada mata na fice kamar bana so simi simi, ina fita na tarar da Innani sai surfa masifa takeyi wai ban fito da wuri ba na shanya ta, ko kula ta banyi ba don takaici na dauki abincin fuskata kamar anyi gobara tsabar bacin rai har yayi jaa, ita kanta ganin yanayi na yasa ta tsagaita da masifan nata.
Cike da gadara hadi da bacin rai nake tafiya har ji nake kamar iska Zaiyi sama dani don bacin rai, na isa bakin kofan nasu, knocking nayi da ɗayan hanuna da ba komai na kai akalla ten second Ina knocking ba wanda yace dani kala, hakan ne yasa na kara hasala ba bata lokaci na murda handle din kofan na shiga da sallama wanda nayi shi a ƙufule, shima har ilah yau ba wanda ya amsa, cikin takaici na isa tsakiyan falon nadire basket din, har na juya zan tafi nau'i kamar alamun mutum abaya na hakan yasa Ni gaggawar juya wa mai zan gani!!!
Mutum na gani zaune bisa daya daga cikin Sifa dake falon yana sanye da farar jallabiya, idonshi a lumshe da alama ba bacci yakeyi ba, ahankali soft pink lips dinshi ke mosti wanda ke nuna tasbihi yakeyi ga Ubangiji.
Kallo daya na masa na gane shine wanda mukayi karo dashi, wani dam dam!!!! zuciyata ta bayar batare da wani dalili ba, wani sabo al'amari ne ya sauko mun lokaci daya wanda na rasa dame zan fassara sa, ahankali na kumshe idonsa na kuma kara bude su tarai akansa na tuna masa Lulu grey eyes nawa wanda Ni kaina bansan dalilin yin hakan ba kasancewar Ni ba mutum bane mai yawan kallo, kamar yadda bana so a yawaita kallo na,
Ji yayi tamkar ana tsikaran naman jikinsa tsabar yadda idona ke yawo a jikinsa, tsuka yaja Wanda yasani dawowa normal sense Dina,
Cikin husky voice nashi ya fara magana cike da gadara kamar haka "Are You iut if your sense,"
Ya karkashe maganan yana kafeni da oily snake eyes dinsa masu firgitarwa,
Niko da karfin hali tsuke face dina nayi jin abinda ya fada, wanda tsabar takaici yasa na juya batare da nace mishi komai ba da niyan na falon gaba ɗaya, sai de bankai ga kara jefa kafata ba nashi yace
"If you dare turn your back on me I will scattered you into pieces,"
Tsabar taurin kai da kafiya irin nawa da kuma ƙarfin hali yasa na cigaba da tafiya majestically,
Mugun fisgan dana ji an mun ne yasa Ni ayyana cewa Mala'ikan mutuwa ne ya Kawo mun ziyara, sai de ban kai ga tantance hakan ba na jini a broad chest nashi, batare da tance tance ainihin abinda ke faruwa dani bane naji an hankada na fadi kasa nayi zaman yan bori wani razananniyar kara na sake wayyyoh!!!!!
End of page 31 follow me for more
Story and written by
Queen mahirah ❤️
Adapted Expert Writer 🖊️📖
Comment and share Please
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 20 Chapter of 25