Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kafe na sandare na dena mosti gaba daya , cikin tashin hankali Innani ta fashe da kuka, ta ce dan kwal ubanki kibar wannan danne danne da wayan kije ki kira mun Sheik yana dakinsa yanzu ya tafi," cikin tasahin hankali Islam ta tafi kiran Jaddi, Fudhal ko dakyar ya kama Fahreen ya mai dashi cikin falon don so yayi ya rikice gaba daya sai fisge fisge yakeyi, nikuwaa Fareed ne ya sunkuce ni ya shiga falo dani, ko sakan biyu bamu kai ba saiga Islam da Jaddi sun shigo falon hannunsa dauke da wani gora wanda yake dauke da ruwan zam zam da addu'a aciki, yana shigowa ya rasa gun wa zai fara zuwa, mika roban yayi a Islam yace taje ta shafa masa sannan ta kama mishi kai ba musu ta karba don tasan mai yake nufi, babu abinda basu iya ba dan yana koya musu abubuwa sosai, karba tayi ta wuce inda Fahreen yake Fudhal ya rungumeshi sosai ajikinsa, tana zuwa ta zauna agefensa ta bude goran tashfa masa a fuska yunkurowa yayi kamar mai yin dambe, amma Fudhal ya rike sa batare da storo ba ta kama kansa ta shiga tofa masa addu'a wani irin gumi ne ke stattafowa daga jikinsa yunkurin kokuwa yake tayi da ita wani wawan stawa ta daka masa " zaki staya ne ko saina ci ubanki muna fuka " da ido 👀 Fudhal yake ta binta ganin yadda halittanta ya canja lokaci daya, in baiyi karya ba har wani huci yaga tanayi hayaki na fitowa daga bakinta da hancinta wani abu ya hadiya, abun mamaki gani yayi Fahreen ya dena shure shuren ya nustu, kuma bugu da kari yaji ta ambaci mace kuma de yasan su duka maza ne sai ita ce mace to mai haka yake nufi ? wikil wikil 👀 ya fara yi da idonsa, cikin kan kanin lokaci ya sake wani dogon ajiyan zuciya, yayi shiruu dago da rinanun idonta tayi tace " gyara masa kwanciyar sa," ba musu yayi abinda tace, abangaren Jaddi kuwa ya karaso inda nake Innani sai kuka takeyi niko na kafe na bushe kamar gawa, karasawa yayi ya zauna agefena shide Fareed yana ganin ikon Rabbi, ahanakali ya fara tofa mun addu'a wani irin mika nayi can nafara fisge fisge sai kuma na nustu, mikar dani yayi ya zaunar, kafaun yace bayan skekara 20 yau Allah ya kaddara haduwan mu, dago kan ka ka kalleni sannan ka kayi gaggawar war ware abinda ka kulla ka cire ajiyan da kayi ajikinta tun kafun mu kwashi yan kallo da kai," kauda kaina nayi gefe ina dan harare harare, murmushi Chief yayi yace Islam kawo min goran ba musu ta kawo masa, karaf idona{ ko ince idonsa tunda ayanzu bani bace zan iya cewa aljanin jikina ke magana}, ya fadi akan goran, aikuwa ya mike mai kyau ya gyara zaman sa ya kalli Chief yace " kafadi mai kake so zanyi, amma banda wannan ruwan," yayi magana cikin wani murya mai razanar wa , wanda yasa kowa nacikin falon mai da hankalinsa kaina don abun mamaki ne ace karamar yarinya tana irin wannan maganan cikin muryan gardawa, murmushi Chiefa ya kara sakewa yace " bazan kuma mai maita kaina ba nasan kaji mai nace tun farko" "kade fadi wani abun daban amma banda wannan don gaskiya bazan iya ba an riga anbiyaa ni kudi akan aikin nan, ni bazan iya saba alkawari ba," " bude murfin goran Chief yayi ya wasta masa ruwan wani irin razananen kara ya sake, ya kara wasta masa, ganin zai illata sa ne yasa shi fara ja baya yana jijjiga kai yace "naji kayi hakuri zanyi koma mai kake so" murmushi Chief yayi ya shafa farar gemunsa yace " kamar yadda na fada ma afari zan kara mai mai ta kaina, kacire mata ajiyan da kayi ajikinta," cikin azaba yace" zan cire amma ba duka ne nawa ba abinda nasa mata stanan shi ne kawai" Chief yace bangane mai kake nufi ba" cikin azaba yace " labarin dogon labari ne kuma a sarkake yake abun ya samo asali ne tun kafin su fito duniya akayi abubuwa akansu wanda ba mutum daya bane, war ware abun zai yi wiya ayanzu har sai ta koma cikin masarautar su kafun komai zai ware, amma kaga wannan yaron yayi magana yana nuna Fahreen dake kwance, itace maganin jinyarsa ita din garkuwa ce agaresa saukin sa yana cikin taraiyar su, kasancewarsu a guri daya zai samar mashi da kwancaiyar hankali," shiruu chief yayi yana nazarin magan ganun sa jijjiga kai kawai yayi yace " naji amma inaso kasan ba wai na dauki wannan zancen naka bane sabida sauki yana wajen Allah, sannan duk abinda ya faru da wani to tabbas da sanin Allah ba wani wanda ya isa ya cutar da wani ba tare da Allah ya yadda ba, da kuka raba su kuka kuma koresu daga cikin ahalinsu da tunanin kun salwantar da rayuwarsu, shin hakan yayiwu ne gashi sun cigaba da rayuwa, wannan ba ikon Allah bane ko haka ya isa ya sa ku risina ku tabbatar da cewa in Allah ya kaddara faruwar abu ba wanda ya isa ya dakatar, kun nesantasu da juna na stawon shekara 20 gashi cikin kankanin lokaci basirar ku ta shafe kunyi abinda kuka hada su batare da kunsan kunyi hakan ba, inaso kusani ba yadda kuka iya da wayannan yaran sai de ku gansu ku barsu su din hadin Allah ne kuma halittar sa ne, kamar yadda kuke gudu to hakan ne zai faru hasken da kuke storon zai haaska duhun da kuka mamaye masarautar dashi yana nan kuma yana tahowa da sannu kamai zai ware, inaso kaduba yaran nan gaba daya katabbatar ka cire ajiyan da aka aiko ka kayi musu" cikin muryarsa marar dadi yace " kayadda dani banyi ajiya ajikin ko wa acikin su ba, bani na musu ajiya ba suma nasu masatalan daban ne wata daban ne tasa aka musu ba ni ba ba wacce tasa ni wannan aikin bane nasu daban ne, kuma ta fimu karfi sosai ita mastafiya ce ita da kanta take aiki da wani kungiya a kasar Eagypht ni kuma daga kasar India nake ni dan can ne," jijjiga kai Chief yayi yana mamakin wannan lamarin yace " shikenan kayi aikin ka kawai ka barni dasu sauran," wani irin mika nayi na koma na kwanta wufff bacci mai nauyi yayi awun gaba dani, dogon numfasahi Chief ya sauke yace Fareed taimaka kadan mika mun ita daki tasamu tayi bacci, gyada kansa yayi ya mike cos he is totally speechless, daukana yayi kamaar wata baby Innani da tayi jugum ta masa jagora ya kaini daki ya kwantar dani, karewa fuska na kallo yayi na yan sakanni yana kokarin fahinmtar wani abu game da fuskan, gani yake tamkar yasan wani mai irin wannan fuskan to amma a ina dogon numfashi yaja ya fito daga dakin, "sannu dan albarka na gode ko zaku iya tallafawa dan uwan naku ku kaishi ya kwanta shima don ya huta kafun anjima zan zo sai muyi magana ," gyada masa kai kawai sukayi suka dan bibbigi Fahreen ya tashi suka tallafa mishi suka kaishi dakinsa suka kwantar dashi kafun kowa ya zauna ya fara karanta wasikar jaki, kamar haka ,wacece wanan yarinyan ? sannan wani masarauta yake magana akai ? mai ne ne alakanta da Fahreen ? kuma wani ajiya yake magana akai ? wa kuma yayi ajiyan kuma ta yaya ? DOMIN SAMUN WANNAN AMSA SAI KU CIGABA DA BIYONI DON WASAN YANZU AKA FARA YANZU LABARIN ZAI SOMA QUEEN MAHIRAH Follow this link to join my WhatsApp group and shower 🚿 me with comment and react 😁😍🤩😘 https://chat.whatsapp.com/DEb6DCrj50r88WN25D5xu9 ??THE TWO LIGHT ✨{RIKICIN GIDAN SARAUTA??}?? Story and written by Queen Mahirah ADAPTED EXPERT WRITER 📖🖊️ BOOK 1 ?Monday, ?February ?26, ?2024 02:30:18 PM GUDU SAURI SAURI,???? KU MASTO KUJI NI DA KUNNEN ?? BASIRA, ??NA KUSA DENA POSTING FREE PAGES GROUPS , GAME BUKATAN SON CIGABA DA GANIN POSTING YAYI GAGGAWAN SHIGA GROUP LINK NA SAMA ANAN ZAKA SAMU POST AKAI AKAI, KO YAMUN MAGANA TA WANNAN NUMBER 09168962485. 2️⃣4️⃣ NIGERIA { RUGAR HARDO BELLO} Suna zaune jigum jigum ba wanda yake cewa kala, hasalima kowa da abinda yake tunani da sakawa a ranshi har aka kira sallan azahar ba wanda ya mosta acikinsu, zuwan Chief ne ya mikar dasu alwala sukayi bayan tada Fahreen da sukayi shima yayi alwalan ya musu jagora har zuwa tankamemen masallacin dake kofar gidan, hadadde mai tashin kamshi da sanyi A/c zaka ranste a villa mosque kake stabar yadda gurin ya staru da kayan alatu da more rayuwa, daga Fudhal har Fareed duka sake baki sukayi suna mamakin wassu abubuwa game da wannan Rugar daya ke kamar aljannan duniya, bayan sun idar da sallah ne suka kama hanyan komawa gida inda suka samu an ajiye musu abincin rana, suna shiga suka samu guri suka zauna, kamar kullum MG Fahreen ya samu guri ya zauna ya kishingida a jikin laulausan kujeran falon ba abinda yakeyi sai salatin annabi da ya zame masa ruwan sha da kuma ci, don tunda ya fara wannan jinyan ya dena komai sai bautawa ubangijinsa dama ba gwanin surutu bane sai ya lumshe idonshi yayi ta istigfari da hailala ko salatin annabi, tohh yauma hka yayi ya lumshe idonsa, Chief yace "bissimillah kuci abinci sai muyi maganan daya kamata" ," Fudhal da kamar dama jira yakeyi yace " no need for mu fara cin abinci kawai let go straight to the point, cos baza ma mu iya cin abincin ba muna da tambayoyi da dama da zasu hana mu jin dadin abincin infact bamu da ma appertite," murmushi Chief yayi yace " shikenan, yanxu mai kuke so ku sani " Fudhal ya dan muskuta ya gyara zaman sa yace " yauwa firstly muna son sanin mai yake damun Fahreen?? sannan bamu gane mai kake magana akaai ba game da ajiya dake jikinmu,?? sannan wannan yarinyan wacece ita,?? kuma mai yasa garinnan ya zama haka,?? a iya sanina ruga ai karamin guri ne wanda fulani ke rayuwa kuma babu gini sai bukka da tarin shanukai, but anan da ban ban ci ko mai yasa hakan," gyada kai Chief yayi murmushi yace " malam Yarima iirin tambayoyi haka da wanne zan fara" Fareed yace " Jaddi ba sai ka takura kan ka ba kawai ka fada mana abinda ya kamata mu sani, kabar wannan marar hakurin dama hka yake yana da gajen hakuri," yana magana ne yayin da yake aunawa Fudahal harara don yaji haushin tambayoyin nashi, murmushi Chief ya saake yace " da farko de inaso ku gode wa Allah don yayi muku baiwa mai tarin yawa wanda baku san dashi ba, sannan game da rashin lafiyan dan uwanku wannan daga Allah ne, amma a komai akwai sanadin faruwarsa, tohh zan iya cewa sanadin faruwar rashin lafiyansa ba komai bane sai sharrin makiya da kuma magauta hadi da miyagu, wanda ke kokarin salwantar da rayuwarshi su mai da ta marar amfani ta hanyar mai da shi majnoon, amma kunsan Allah ba azzalimin bawan sa bane, yana kaunar bawansa fiye da yadda uwa ke kaunar danta, sannan bawai rashin son sa da yakeyi bane yasa ya bar wassu miyagu daga cikin bayinsa na cutar dashi, kamar yadda kuka sani Allah ya kaddara abin da zai faru da mutum tun kafin zuwanshi duniya, sai de abu 2 na iya canja kaddaran mutum na 1 shine karfin addu'a, na 2 kuma shine sihiri, wayanan na canja kaddaran mutum bawai dan Allah ya gaza ba a'a sai de dan ya barka da halinka yaga yanda zaka kaya, yakan baka sa'a na wassu lokuta kafun komai ya kubuce maka, tohh anan abinda nake so ku gane bakomai bane illa game da sha'anin rayuwar dan uwanku, wanda tun tashin shi rayuwarsa yake adagule badan komai ba sai dan sharrin miyagu, wanda sukayi kokarin canja masa kaddaransa sabida son zuciyarsu batare da sanin halitta na daban suka mai dashi ba, akarshe wassu daga cikinsu sunyi kokarin sabauta shi batare da sanin cewa hakan da sukayi sun kara hadashi da kaddaranshi ne ba, abun da zamu fahimta anan shine su sunyi nasu yanxu kuma lokacin na Allah ne, abinda nakeso ku gane anan shine arayuwa kowa da nashi kaddaran da fadi tashi, ako wani family suna da nasu salon rikicin sai de RIKICIN GIDAN SARAUTA ya ban banta dana ko ina , anan akwai mutanen da ba Allah azuciyarsu wanda basu dauki sabonn Allah ako mai ba muddin zaasu samu biyan bukatansu, sun manta cewa duka wayanan abubuwan aaduniyan zamu barsu kamar yadda muka samo su, sun dauki shirka sana'ar yinsu sunyi amfani dashi wajen raba kan wannan ahalin don samun cikan burinsu, sai de Allah baya bacci akaikai ce ya hada ku tahanyar da ku kanku baku sani ba, ya hada kawu nan ku ya kuma dauke idon makiyanku da kanku yasa sunyi tunanin burinsu yacika na son ganin bayan yan uwanku, tohhh Alhamdulillah komai yayi farko zaiyi karshe anjima za'a kawo muku ruwan magani wanda zaku na amfani dashi kaba gayan ku, na karya sihiri ne da kuma kariya sanan zan baku addu'ar da zaku nayi wanda zai sa makiyanku manta wa da kashin ku, zaku zamo shafaffu a allon stafinsu ma'ana zaku zama invisible ga makiyanku, fatan shine Allah karbi ibadun mu," cikin sanyin jiki suka amsa masa da ameen, murmushi yayi ganin yadda jikinsu ya mutu gaba daya ga wani yanayi daya bayyana a face nasu, ya dubi Captain Fudhal yace " Yarima ko nace Captain Fudhal, shi rayuwa ahankali ake binta musamman inka na so kaci moriyarta da zancen cikinta, sanin wassu abubuwa lokaci guda bayana nufin warwarewar mastalan data yi shekara 20 da ginuwa ba, sannan awassu lokutan yana da kyau mu fawwala Allah komai awananan duniyar da kake ciki yanxu musamman ma kasaar mu Nigeria, babu gaskiya acikinta wannan na nufin koda ka tauno abinda yake abinne tofa sai de kabar hukunci a hannun Allah ubangijin talikai, shi yafi kowa iya hukunci, kuma ita gajen hakuri yana daya daga cikin abinda ke iya sauya kaddaran mutum anan Allah zai barka da halinka yaga iya gudun ruwanka, sannan inasao ku cire duk wani tan tama akanmu ku kuma fahin ce mu ku jami'ai ne, tohh inaso ku ganmu da idon basira ku kuma fahimce mu da kunnen basira, ku dauki yaran nan tamkar yan uwa a gareku na tabbata baza kuyi dana sani akan hakan ba, abinci da kuma gyara muku sashin ku zasu na yi sai wanki akwai mai yinshi in da injin wanki kuke so yayi muku zai yi inkuma da hanune duk wanda ya muku, ku dauka mu daku abu daya ne shine fatana yana gama fadan haka," ya mike ya da niyan tafiya Fareed ne yace " mun gode Jaddi insha'Allahu zaka same mu ayadda kake so kuma basai an wahalar dasu ba na kawo mana abinci, zama mu shiga muna ci tare dasu in ba damuwa," cikin fara'a Chief yace " ba komai ai duk abu daya ne," har bakin kofa Fareed ya raka shi ya dawo yana shigowa Fudhal ya jefa mishi wani harara yace "sannu uban yan shishhigi kana wani kokarin cusa mu jikinsu, dakai da su din duk daya kuke sai wani cusa yaran yake jikin mu kamar wani ...," bai gama zaancen ba sana din wani wawan stuka da Fareed yaja " mtschwwwww kaide har abada kan ka bazai taba dauka ba kan mutum kamar an dura dusa baya fahimtar komai, ba abinda ke shiga ya zauna kamar ba yanzu ya gama maka nasiha ba, ohhhh na ma gane kai storonka kar zance na ya tabbata na saaka wanke wanke, tohh wallahi ka ajiye ya zama jazaman kayi wanke wanke agidan nan tunda naga shine abinda kake gudun," yana gama fadin haka ya fuskanci Fahreen yace "Tweeny ina fatan ka saurari abinda mutumin nan ya fada," gyada mishi kai kawai yayi murmushi ya sake yace " inka kula kamar akwai lauje cikin nadi, in mun maida hankali zamu iya samun abunda muka dade muke nema in ka fusakanci zancen shi nacewa yann uwan mu da muka rasa , kasan ba mutum daya muka rasa ba mun rasa mutane na farko yayan Abba mun da aka rasa shi duk da cewa ance ya mutu amma ai babu wani kwakwaran shaida akan mutuwarsa, kuma fahhh kasan bamu san komai game dashi ba ko a photo bamu taba kallonsa ba, labarin ma albarkacin Fulani ne muka ji muka san sa , sai kuma Amni da twins dinta kaga shima ance tayi accident after all babu koda ashes dinsu ne da kuma car din, sai kuma Pops da Mubaraq kasan about 20 years bamu san inda suke ba and am very sure Mubaraq ne yayi hiding information dinsu, you know he is wizkid on computer ko charles barbage dayake father of computer bazai nuna mishi kanta ba, so the point here is akwai possibilities din da wannan old man din yasan wani abu very important things game da family din mu, and the biggest part is who are these ladies mai yasa suke kama da larabawa tunda su Fulani ne?," shiruu dakin ya dauka kowa da aabinda yake sakawa ta fannin Fahreen wannan yarinyar ne ta fado masa arai da incidence din da yayi occuying a staka ninsu, wani irin sarawa kanshi yayi ga wani bugu da heart din shi yayi acikin abinda bai fi 2 sec ba ya

Chapter 14 of 25