amsa da ameen
Innani ne ta tashi ta kamoni kamar wata yar yaye ta kaini dining area ta zuba mun abinci tace bissimillah ,
MASARAUTAR SUHATAJ MUHD { KANO STATE, NIGERIA}
Haba Faddi ya isa mana haka kukan dan Allah daga cewa akai ki Egypht kidan huta shikenan sai kihau kuka,"
cikin sheshshekar kuka tace zaka fadi haka mana tunda ba kaunata kakeyi ba,
kun salwantar mun da dana shine yanzu nima kake son kashe ni ko ba haka kukayi wa Zulaihat ba wai akaita Egypht kafin komai ya lafa yanzu ina take,
nifa na fahinci sona ne da kadena yi nida 'ya'ya na intafi in bar Mobina a wannan azzalumar matar naka mai fuska biyu ko taji dadin cinye mun ita da maitar ta dama ma ai yar tawa saura nea duk tabi ta zuke mata jini ta mai da ta wani abu daban wato intafi ta karasata nima ta karni ahanya,"
cikin kunan rai da gajiya da zancen nata yace " ya isa Faddi ya isa nagaji da yadda kike aibata mun mata,
haka kawai mai ta miki daga abun alkairi shikenan sai ki hau sababi akanta ya isa,"
fashewa tayi da kuka tace " ni kake wa stawa haka Mahbub akan matar ka,
haka alkawarin ya yake zaka fara nuna mun halinku na maza akan matarka ni ko,"
cikin wani yanayi ya kama hannunta yace " is okay Faddi am so sorry is all my fault pls komai ya wauce,"
wafce hannunta tayi tace " ya wace fa kace sai kace agarin gaba gaba duk kayan bakin cikin daka dura mun,
katuna ko tarewa bamuyi ba kamun kishiya wai kai mai biyayya sarkin hakuri ni kuma ka cuce ni ka hadani da ala kakai ka hadani da shegiya mai kissar stiya wallhi ka cuce ni da ko cleaner bana sharing,
sai gashi anwayi gari wai namiji muke sharing da wata banza marar asali,"
murmushi ya sake wanda ya bayyanar da zallan kyau da imani hadi da nustuwa da haiba da Allah ya masa,
ko yanayin dariayn zai nuna maka bakaramin hakuri yake dashi ba,
janyota yayi ya mata kyakkyawan runguma wanda ta gagara kwacewa karshe lamo tayi tana sauke ajiyan zuciya har bacci mai nauyi ya dauke ta ,
ganinta ajikinshi ba karamin farin ciki yake ji ba Allah ya jarrabesa da sonta, wanda ake kira da mastanancin so duk da rigimarta da abunda take masa bai sa yadena jin sonta ba,
yasan duk abinda ya faru shi yaja bai ga laifinta ba ko kadan shi mutum ne mai biyayaya ga iyayenshi da hakuri sam bai taba son GIMBIYA SAUDT ba kawai biyayya yayi ya aureta,
alokacin da dan uwan shi yaki auranta, sai de bai yi nadama ba don mace ce mai biyayya da iya kwantar wa miji hankali da tarairaya,
shine ma abinda yasa ya bata wani mastayi a zuciyarsa ,
sai de sam basu da hadi ita da Gimbiya Fadila , mastayin Fadila daban yake azuciyarsa,
ya godewa Allah da Faddi bata nuna kishinta a fili sai in sun kebe ita da shi a daki take masa bala'i iya son ranta,
cewa take SAUDAT bata kai tayi kishi da ita ba, wanda haka yake azahiri Saudat bata ko kamo hannunta a kyau ba na fuska dana sura,
da kuma iya gyara kanta, ga ta iya sace zuciyar miji da sa shi ciki wani yanayi.
bata yadda ko hanyaa ya hadata da Saudat inko sun hadu Saudat zata kauce, bata waasa da ita bare har reni ko fada ya shiga stakaninsu,
shiyasa itama Saudat take shakkanta da kokarin toshe duk wani hanya da zai hada su tashin hankali, tunda tasan tafi karfinta ako a komai.
kwantar da ita yayi jin ana buga kofa yasan Mobina na ne, izini ya bata akan ta shi bata wani bata lokaci ba ta shi go Masha'Allah starki da yabo ya tabbata ga ubangijin da yayi wannan kyakyakwan halittan,
wata kyak'kyawar diya ce da baza tafi shekara 19 ba aduniya farace tas mai zubin larabawa tana da madaidai cin stayi da jiki wanda yake a murje dashi mai laushi da daukan ido,
fuskanta da dan stayi hadi da fadi kadan, yana dauke da manyan idanunta masu daukan ido da sheki wanda suke dauke da brown eyeballs ga zararan eyelashes,
hancinata zarattt dashi dai dai face nata, sai madaidaicin lips dinta wanda yake pink colour mai sheki.
tana sanye da wani fitted gown na atamfa dinkin ya mugun fidda asalin surarta wanda zakayi mamaki in ance ma shekarunta 19 ne aduniya yanayin jikinta zaka ranste ta kai 23 ko fiyeda yadda ta ko ina yake dammm acike kamar su fashe ko su stole ido,
stabar yadda sauka cika kayan, kanta ko ba dan kwali hakan ya bawa yalwaceccen gashinta daman zubowa har kugunta baki sidik dashi mai stansti da dauka ido sai tashin kanshi yakeyi.
ahankali take tafiya komai na jikinta na mosti har ta iso cikin tamfastetsen dakin, ta karasa inda yake sukayi pecking kumatun juna kafun ta waiga taga inda Gimbiya Fadila ke kwance cikin wani yanayi na sarewa da zallan damuwa wanda ya bayyanar da hawaye dakea kwance cikin farin idonta tace
" Abbu yaushe Ammi zata samu lafiya,"
tayi maganan cikin melodious voice dinta kaga kullumm sai tayi kuka fa har bp dinta ya hau,"
ganin yanayin nata ne yasa shi rungumota yace " shhhhh Ibnatiii banda kuka Ammi will be alright insha'allah tana bukatar hutu ne kinji yanzu mu je gurin Fulani tabaki Fura kisha ko tace ma tunjiya baki je gunta ba,"
gyada kai tayi ya kama hannunta sukayi hanyar waje da ita tamkamemen faloin suka futo bayi ne suka zube suna kwasan gaisuwa hannu kawai ya daga musu ya umar ci daya daga cikinsu data kawo alkebban Sarauniya Mobina da kallabinata,
ba bata loakci ta dauko aka shiryata ita ko sai turo baki takeyi tana tubune face,
"Abbu akwai zafi fahhh kuma da nauyi,"
murmushi ya sake ya lakaci hancinta yace " silly girl to ahaka zaki futa, karki manta ke princess ce ,"
"but Abbu is too heavy i can endure it infact ana zafi and skin nawa bayaso yanzu sai fito ya da kurajen da that are so painfull ," tana magana ne cikin zallan shagwaba
murmushi yayi yace okayyy in mun je can sai ki cire in kuma kin masta Akhie Fudhal yana nan kin san halinsa sarai,"
narai narai tayi da eyes tace " naji tohhh muje tayi gaba ta barshi abaya,"
murmushi yayi yayi taku dabai fi 2 ba ya cimmata abinka da dogo, hannunata ya kama suka cigaba da tafiya har suka fito haraban masarauatar duk inda suka gibta sai an gaishe su har suka isa sashin Fulani da tun da suka yo hanyan sashin nata aka sanar da zuwansu.
suna shiga suka hangota zaune bisa royal chair dake falon tana sanye da bakar abaya daya fidda hasken fatarta kaman da sukeyi da Princes Mobina ne ya bayyana karara hannunata dauke da carbi daya kuma da tahzeeb kasancewar la'asar tayi har ma anyi salla hakan yasa takeyin azkar,
sallaman sune yasa ta ajiye tahzeeb din ta dago fararen dara daran eyeballs dinta wanda ke cike da kwarjini da nustuwa da kyan haiba zuba musu tana sakin murmushi daya fidda zallan kyanta inda fararen hakwaranta wanda ke jere reras suka bayyana cikin muryanta wanda ko ba'a fada maka ba kasan balarabiya ce tace
" waalaikumus salam, ahlan wa sahlan ya hafidatii sagira taali ilah hun,"
Princes Mobina kamar dama jira take tayi mata magana da gudu taje ta rungumeta tace " i miss you so much Jaddatii,"
Fulani breaking hug din nasu tayi tace " humm dube ta mana kina nan amma kinki zuwa ki duba ni kuma kike cewa wani you miss me so much, tohh naabi missing din da gudu,"
kyalkyalewa Princes Mobina tayi da dariya ganin yadda Fulani ke hade face shi kanshi yadda tayi maganan ma abin dariya ne,
ta yishi cikin salo najan hankali wanda ke tare da ita musamman mai kananun shekaru irin na Mobina cos she may easly find it funny kamar de yanda ya faru abin ya bata dariya,
"Jaddatii da gaske nayi missing dinki kinsan Ammi bata da lafiya shiyasa ban samu daman zuwa ba gashi muna shirin fara final exams namu 2 weeks zamuyi mu gama,"
" masha'Allah kice kin zama graduate a degree holder ,"
"ehhh Jaddatii kinga yanzu Akhie Fareed bazai na stokala na ba,
wai fahh cewa yakeyi kafun nagama school za'a rufe kamfanin pen & book, kuma gashi at the end am gonna be a degree holder with just 19 years old, bakaman shi ba da sai da ya kai 23 years ya gama universty,"
murmushi Fulanai ta sake tace " Masha'Allah, kinga yanzu kin kusa kwace girman daga hannunshi tunda kin gama school sai batun aure shiko gashi har 29 years ba budurwa bare asa ran yayi aure,"
turbune face Princes Mobina taayi tace " aure kuma Jaddatiii shekarun nawa 19 nefa ko kin manta,"
"ko kadaan ban mantaa nasani ammaa in ba auren kika yiba tohh mai zakiyi tunda kin gama degree,"
"sai nayi masters daga nan nayi phd kingaa kafun nan nakara girma,"
"tohhh fahh kina ganin hka mai yuwu wa ne da alkawarin aure ahh akanki ko kin manta ne,"
hade giran sama da kasa tayi tace " ban manta ba kawai ni bana son shi ne yanzu,"
murmushin manya Fulani tayi tace " dama ana dena so ne,"
" tohhh ni de na dena son Mubeen,"
"hmmm fada mun ko ya miki laifi ne sai a masa magana ya gyara,"
" kohh ya gyara ma ni bana son shi dama ma tun can ba sonshi nake ba, kawai dan yana kulawa da ni ne yasa nake son yadda yake nuna kamar da gaske yake sona ,"
"ikon Allah nikam ban gane ba cire ni a duhu,"
"hmm wallahi nikam na fita rakiyarsa mayaudari ne kuma fahh har neman mata yana yi kuma wallahi shi pregnenting zuwaira kuma ba ita kadai ba bayin masarautan nan da yawa ya musau hka,
shine aka daura laifin a Akhie Fareed, in baki yadda bama zan iya proving miki, cos ina da prove,"
ba Fulani ba har Suhataj shiruuu sukayi sauna sauraran Mobina da zancen bakinta daya sasu a wani yana yii
" Fulani tace lemme see it, ina prove din,"
ba tare da wani shakka ba ta daauko phone dinta dake hannunta tayi wani yan danne dannen ta ta mika wa Fulani,
cikin zallan mamaki daya bayyana karara a face nata ta mikawa Suhataj wayan don abun yafi karfin kwaanyar ta, daaga nasa ban garen shima ya girgiza sosai da saurara sannan kuma da ganin abun da ke faruwa,
ba abinda Fulani keayi sai salati kawai ta fashea da kuka " ashe tun da zaluntar yaron nan kukeyi ashe da gaskiyarsa a banza kuka masa hukunci har bulala 80 nin ba kuka masa ashea hakkinsa kuka dauka,
shiyasa kullum nake ce wa Baba sarki yayi bin cike mai zurfi kafun ya yanke hukunci amma samm baya ji ba so daya ba ba so biyu ba wannan na uku kenan fahhh ,"
shiruuuu Suhataj yayi yana sauararon mahaifiyar tasa tabbas abunda ta fada haka ne Allah ya rufa asiri basu yi exacuting nashi ba don rikicin da Fulanin tayi na cewa sai de su bar masarautar tare dashi don baza ta lamunci haka baahh.
mikewa yayi da niyan mata sallama zai tafi tace " ina kuma zaka je ai aikin gama ya riga da ya gama, kazo kai da uban naka ku warware wannan auren da kuka hada ban isa jikata kwalli daya ta auri mazina ci ba wallahi ,
kuma wallahi ku tabbatar kun wanke mun sunan jikana adena masa kallon mazina ci , ku kuma hukunta mai laifi,
in tattara kayana na koma gidan ubana ."
cikin girmamawa ya sadda kanshi yace " kiyi hakuri Ummi insha'Allahu zaayi abin da kika ce yanzu ma zanje na same shine muyi magana,"
" kai de kasani kai da shi din kuyi ko inbar muku masarautar taku kuma wallahi dauke diyata da jikata zanyi in tafi dasu don bazan yadda magauta su hallaka mun su ba da raina."
" ki huta lafiya Ummi ,"
ya fadi haka yayin da ya sadda kan sa kasa kafun ya fara tafiya cikin isa da takamaa ya fita daga tamkamemen sashen wanda yake gurn shakatawa ne,
juyo wa tayi ta fuskan ci Mobinaa tace " ke kuma ya akayi kika samu wannan video diyar alkairi,"
" hmm ranan ne fahh na gagara bacci da dare kuma Ummi na plat din Abie don ranan girkinta ne shine na fito nace zanzo nan na kwana dake,
har na kamo hanya sai na fasa nace nari naje gun Akhie Mubeen ya rako ni sabida lokacin bayi na sashin su,
shine naje plat dinsa na shiga farlon naga ba kowa nayi ta sallama shiruuu baa amsa ba haar zan tafi sai naaji kamar karan mutane shine naje na duba ko shine,
na daga labulen sai na hango shi a staye a garden dinsa ban ga kowa ba alokacin shiyasa na fara sanda don na storatar dashi sabida mun saba irin wasan dashi,
shine na fara sanda amma ina karasawa sai naga alaman mutun sai de bka kallon komai ajikin mutumin, dana kara sa ido sai naga ashe mace ne da abaya ajikinta fuskanta da nikab hatta hannunta da hand socks baka iya kallon komai ajikinta,
shine naji suna wannan maganan ganin yafi karfin
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 16 Chapter of 25