Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
sha domin rage kokwanton da yake cikin zuciyarta kwanciyarta keda wuya sai barci ya saceta bata sani ba Tana farkawa saita tashi taje ta watsa ruwa ta wanke fuskarta ta Kafin ta fito daga wankan tuni kuyangi sun ajiye mata abinci da abin sha kala daban daban akan wani teburi dake tsakiyar turakar tata Ba tareda bata lokaciba ta zauna ta kai hannunta da nufin cin abincin Har hannunta yakai bakin kwanon abincin kawai saita tuna da maganar tsohon data gani jiya Ta tambayi kanta tace shin menene yake shirin faruwa dani? Kuma me yasa wannan mutumin ya tafi ba tareda ya amsa mini tambayoyi na ba? Ya zama dole na kara bincike akan wannan bakon jarumi daya bani labari akansa Kuma nasan hanyar da zan bullo masa domin nima na samu na biya bukatar dana dade ina burin cikawa nasan lokaci ya kusa da zan jefi tsuntsu biyu da dutse daya Tana gama fadin haka saita juya taje ta shafi wani madubin tsafi Wanda yake makale ajikin bangon turakar tata Yin hakan keda wuya take sai hoton jarumi rukyan ya bayyana Lokacin da yake fafata kazamin yaki da wannan dodon acikin daki na biyu Koda tayi arba da kyakkyawar surar jikinsa da kuma jarumtakar da yake da ita Sai taji take zuciyarta ta buga da karfi ta tambayi zuciyarta tace dama aduniya akwai namiji mai irin wannan kyau da jarumtaka kamar mahaifina? Indai kuwa har yana da wannan karfin damtse dolene Sai mahaifina yayi da gaske sannan zai sami nasara akansa Ni kuma idan har inaso bukatata ta biya ya zama dole na hada nabi ta kowacce hanya mu fita neman karagar ajali da mahaifina Sannan na gudu gurin jarumi salyar na yaudare shi da soyayyata Kuma mu nemo saiful laiham tare Inyaso ni kuma daga baya sai inci amanarsa na sace wannan takobin Daga baya naje na hau KARAGAR AJALI Shikenan daga wannan lokaci na zama sarauniya ta farko wacce zata mallaki duniya Koda hakan kuwa zai janyo sanadin raba alakar dake tsakanina da mahaifina Koda gama fadin haka saita tuntsure da dariya sannan ta shafi madubin tsafin hoton komai ya dauke ******* ********* ******* Acan cikin dakin halwar tsafin sarki gulbas kuwa tun a ranar dasu jarumi rukyan suka fara karbar horon sadauki farhan Shima a wannan ranar ya fara bisa wakilcin wani takadirin aljani mai suna luzzab Yanzu haka yana matakin farko acikin wata nahiya daban ba wacce ya saba gani ba a rayuwarsa domin duk yawon da yayi bai taba tsintar kansa acikin daji Makamancin wanda yake ciki ayanzu Shidai wannan dajin babu komai acikinsa face wata sahara Mai zafin gaske wacce babu wata halitta mai numfashi asamanta hatta tsirrai babu Saboda zafin da saharar take dashi har turiri ne yake tasowa ta kasanta Tun farkon shigowarsa cikin dajin makogaronsa ya bushe Yaji ya kamu da tsananin kishirwa kuma babu inda zai je ya sami ruwa acikin wannan saharar Haka dai ya daure yaci gaba da tafiya abinsa ba tareda sanin inda ya dosa ba Sai da yayi tafiya mai nisa akan saharar alokacin ya fara galabaita sosai Kawai sai ya hango wata korama daga can nesa kadan daga inda yake Koda ya hangi wannan koramar sai farin ciki ya kamashi Ba shiri ya nufi wannan koramar don ya sha ruwan dake cikinta Sannan ya cika battarsa da ruwan don yayi guzuri dashi ya kara gaba Cikin sauri ya karasa bakin koramar da isarsa sai ya sunkuya yakai hannunsa Da nufin ya kwarfo ruwan ciki yasha har hannunsa yakai saman ruwan Kwatsam sai gani yayi wata bakar kunama tayi fitar burgu daga kasan koramar tasa hannunta guda Ta zabga masa naushi dashi take yayi sama kamar an ya luluka acikin iska Tun kafin ya dawo kasa tuni kunamar tayi wani gunji ta fita da gudu zuwa inda yake ta tsayar da karinta tana jiran dawowarsa ta tsire shi Koda ya leko da kansa yaga mugun tanajin da kunamar tayi masa sai ya kara wani tsallen a saman iska ya juya jikinsa ya dira acan nesa da inda kunamar take Yana bisa digadigansa ya kurawa kunamar ido Nanfa aka tsaya ana kallon kallo tsakaninsa da kunamar Shi dai ya rasa wanne zabin zaibi tsakanin ya tari kunamar suyi yaki Ko kuma su yaje wannan korama ya sha ruwan ruwan dake ciki Tunda awannan lokaci babu abinda yake damunsa face tsananin kishirwa Sai dai kuma gashi koda zaije bakin koramar dolene sai ya fafata da wannan kunamar tunda ba wata hanya da zaibi face ya ratsa ta gabanta Nanfa ya rasa zabin daya kamata yabi. Yana cikin wannan tunanin ne kawai yaga kunamar ta sake tahowa inda yake gadan gadan cikin mugun nufi tana gudun kasar gurin tana amsawa saboda tsananin girmanta Arayuwar sarki gulbas tunda yazo duniya bai taba ganin kunama mai girma da muni kamar wannan kunamar ba Domin kana ganinta kasan ba halittune wanda ka saba gani ba Dole an samar da itane cikin ilimin bokanci domin biyan wata bukatar SHIN SARKI GULBAS, BOKA SURKAIS DA JARUMI RUKYAN SUNA KUBUTA DAGA CIKIN TARKUNAN MUTUWAR DA SUKA FADA KUWA ? TAYA GIMBIYA SUHAILA ZATA IYA RISKAR JARUMI RUKYAN HAR TA YAUDARESHI TACI AMANARSA? SHIN ACIKINSU WANENE YAKE DA SA'AR DA ZAI MALLAKI KARAGAR AJALI? DON JIN AMSOAHIN WADANNAN TAMBAYOYI SAI MU HADU A KASHI NA GABA DAGA NAKU HABIBULLAH KBR WHATSAPP NO 09081494322 LIKE AND COMMENTS ARE OUR************KARAGAR AJALI ********-----*2 PART A LBR ***********HABIBULLAH KBR Whatsapp no 09133502477 Lokacin da sarki gulbas da wannan kunamar suka tsaya sukayi cirko cirko suna kallon juna Sai kawai sarki gulbas yayi kukan kura yayi fitar burgu ya afkawa mata Suka kachame da bakin artabu mai matukar muni shi da ita Ya zamana cewa kowannensu yana kaiwa abokin gwaminsa mugayen hare hare Saidai kunamar ta ninka sarki gulbas sau biyar a karfin damtse da kuma kuzari Aduk sanda ta kawo masa sara da karin dake jikinta da zarar ya kauce Saidai kaga bakin ruwa mai yauki yana feshi daga jikin karin nata Nanfa guri ya yamutse kura ta tashi ta turnuke a sararin samaniya Inbadon yana da tsawon rai ba da kuma matukar zafin nama da tuni kunamar tayi kacha kacha dashi Itadai wannan kunamar ta dage sosai wajen ganin ta hallaka shi Shi kuwa burinsa kawai yaga ya tsira yaje ya sha ruwan wannan koramar don gusar da kishirwar data addabeshi Amma babban tashin hankalin shine har tsawon wannan lokacin da suka diba suna Wannan fafatawa shi ya kasa samun nasara ko kadan akanta Saboda yadda take kawo mai mugayen hare hare yana kaucewa Saida suka shafe dakiku masu yawa suna fafatawa ba tareda daya ya sami nasara akan daya ba Kuma duk. Sanda sarki gulbas ya sami nasarar sara ko kuma ya soki jikin kunamar da tsinin takobinsa mai makon takobin ta huda jikin saidai kaga tartsatsin wuta ya tashi kamar haduwar karfe da karfe Saidai kaga kunamar tayi jijjiga kamar ma kara mata kuzari yake kara mata Ma'ana dai bata da wata makasa ajikinta Abinda bai sani ba shine ba zata taba mutuwa ba face yasha ruwan wannan koramar domin shine kadai makashinta Koda aka shafe wasu sa'o'i uku ana wannan hali sai ya zamana gaba daya sarki gulbas ya fita daga hayyacinsa Saboda tsananin kishirwar dake addabarsa ya zamana hatta yawun bakinsa ma ya bushe Don haka babu sauran kuzari ajikinsa da kyar ma yake iya kare hare haren da take kawo masa Nanfa ya fara tunanin hanyar daya kamata yabi don tsira daga sharrin wannan sihirtacciyar kunamar Don ya tabbata muddun aka cigaba da wannan fadan acikin wannan hali sai ya zamana cewa Kare harin nata ma ba zai iya ba daga nan shikenan ta sami nasara akansa kuma za'a rufe tarihin gwagwarmayar da yayi abaya Muddin bai mallaki karagar ajali ba Don haka dole ya samarwa kansa mafita kota halin kaka ya samu ya sha wannan ruwan Kafin lokaci ya kure masa Koda gama wannan tunanin sai yaja da baya kamar taku goma Sannan ya kara falfalowa da gudu kamar zai yi gaba da gaba da ita Koda yazo daidai inda take sai ya zame ya kwanta ya wuce ta karkashinta Sannan ya mike ya nufi koramar da gudun gaske Wohoho nanfa aka kasa tsere atsakaninsu Ya dage iya karfinsa yana gudun ceton ransa itama kuwa ta biyoshi da dukkan karfinta tana domin ceton tata rayuwar Duk wannan gudu da sukeyi tazararsu bata wuce taku goma ba Don haka sai dada kawo masa sara take da karin nata Kafin ya shiga cikin koramar da zarar ta kawo masa harbi saidai kaga Ya zame masa ko kuma yayi tsalle ya kaucewa karin nata Cikin kankanin lokaci ya isa bakin koramar yana zuwa Ya daka tsalle ya afka cikinta yayi nutso akasanta ya bude bakinsa ya fara kwankwadar ruwan Aikuwa ruwan yana shiga cikin bakinsa take kunamar ta kama da wuta Ta kone kurmus koda sarki gulbas ya gama shan ruwan koramar Sai yayi ninkaya a saman koramar da nufin ya fito daga cikin ta Kwatsam sai yaji kasan koramar ta dare wata iska mai karfi ta fito daga ciki ta jashi can kasanta sannan komai ya koma daidai kamar yadda yake abaya Koda iskar ta zukeshi zuwa kasan koramar sai ya tsinci kansa acikin wani tafkeken gida Wanda akayi masa gini irin na tsofaffin gidajen tarihi na birnin farisa Saboda yadda ginin gidan yakeda matukar tsawo da dogayen dirkoki Saidai kuma ko ina acikinsa cike yake da yanar gizo gizo ta yadda baka isa ka matsa gaba ba face ka share wannan yanar da hannayenka Shi dai wannan daki babu alamun akwai wata halitta mai rai acikinsa saboda yadda gidan yayi tsit Ajikin bangon gidan kuwa an cikashi da zanikan halittu masu firgitarwa Wadanda kallon su kadai ya isa ya kawarwa da mutum kwanciyar hankali da nutsuwa har iya tsawon rayuwarsa Koda sarki gulbas yayi arba da wadannan kalar zanika Saiya girgiza kansa yace lallai wannan karaga taci sunanta KARAGAR AJALI Kuma duk wanda baiyi yawon duniyaba bazai san wahalar dake cikinta da kuma dadinta ba Tabbas duk yadda akayi akwai halittu masu matukar hatsari acikin wannan daki kafin na shiga na gaba na tarar da abinda yake cikinsa Koda gama ayyana haka sai ya dora hannunsa guda akan kufen takobinsa Kuma ya kara gyara damararsa yaci gaba da kutsa kansa acikin gidan Har ya wuce ta cikin dakuna guda goma bai hadu da wani abin cutarwa ba Sai a daki na sha dayan ne ya fara jin wani sauti yana giftawa ta cikin kunnensa Kamar sautin giftawar iska, nanfa ya fara waige waige da dube dube Ko zaiga abinda yake giftawa amma sai yaga babu komai Amma duk da haka yana jin sautin acikin sautin har wata dariya ake kyakyatawa Shi kansa wannan ihun ya isa abin firgitarwa da razana mai sauraro Yana cikin wannan hali ne kwatsam sai yaga kasa ta tsage wasu irin fatalwoyi suka dinga tasowa daga cikin kasar Adadin wadannan fatalwun kuwa ya zarce guda dari biyar da doriya Kowanne daga yana ruke da wasu gajerun adduna guda biyu Bakinsu kuwa cike yake da zakwa zakwan hakora masu kaco kaco birjik abakinsa masu tsini ba kyan gani Idanunsu kuwa sun rine sunyi jawur kamar an gasa dan buda a wuta Kai da kagansu kasan fatalwu ne masu shan jinin dan adam Koda gama fitowar wadannan halittu duk sai sukayiwa sarki gulbas kawanya suka soma kewaye shi Ta gaba da baya suna zagaya shi taredayin wani gurnani mai firgitarwa Daga can kuma sai suka afko masa da dukkan karfinsu Suna masu karaji da kururuwa take shima ya zare takobinsa daga cikin kufenta ya afka musu da dukkan karfinsa Suna haduwa suka kachame da azababben yaki a tsakaninsu Ya zama shi kadaine a tsakiyar wadannan fatalwu suna masu kawo masa sara da suka Tako wanne bangare domin suyi gunduwa gunduwa dashi Nanfa guri ya yamutse in banda karar karafkiyar karafa babu abinda kunne keji Inda acewa mutum zai tsaya kallo alokacin da suke wannan bakin artabu sai yayi zaton sarki gulbas ba mutum bane Saboda yadda yake da matukar bakin zafin nama kamar Shaidani dukda yawan wadannan fatalwu sai gashi yana kare duk harin da suke kawo masa kuma alokaci guda ba tareda Wani ya sami nasarar lakutar koda gefen rigarsa ba Saidai babbar matsalar daya fuskanta guda daya ce Takobinsa ko kadan bata lakutar jikinsu da zarar ya kai musu sara ko suka sai dai kaga takobin ta ratsasu ta wuce ba tareda ta illata su ba Ma'ana dai kamar ya sari haske ko kuna inci iska Gaba ki daya dakin ya cika da sautin karafkiyar karafa Ya zamana duk inda ka waiga babu abinda zaka gani face dakarun fululu kuma duk yawansu mutum daya suka tararwa Ana cikin wannan fafatawa ne wani daga cikinsu ya shammaceshi ya daga addarsa ya kafta masa sara agadon baya Take gadon baya nasa ya dare jini yayi tsartuwa daga gurin raunin Take sarki gulbas ya kwallara ihu saboda zafi da zugin da yaji Cikin karaji yayi kukan kura atsakiyarsu irin wanda ke firgita mazan fama a filin daga Saboda karajin da yayi saida sukaja da baya suna kallonsa Take ya yagi rigarsa ya daure raunin da sukayi masa Suka sake dawowa suka ci gaba da bakin artabu babban abinda ya baiwa sarki gulbas mamaki game da wadannan fatalwoyi shine Yadda takobinsa Take iya haduwa da makaman hannunsu amma kuma bata iya ratsa jikinsu Wani lokacin ma makaman hannun nasu har subucewa suke su fadi kasa amma kuma sai yaga sunyi zumbur sun sunkuya sun dauki makamin An cigaba da yakin Nanfa ya tabbatarwa da kansa dole akwai wani sirrin dangane da wadannan makamai Ba tareda bata lokaci ba ya canja salon fada ya zamana Babu abinda yake yi face yunkurin yaga ya buge makamansu daga hannayen nasu Saboda ko kadan ya daina mai da hankalinsa akan sukar jikinsu Gaba daya ya tattara karfinsane wajen kaiwa makaman nasu duka Ai kuwa cikin sa'a daya daga cikinsu ya kawo masa sara da addarsa Take sarki gulbas ya kauce yasa kafarsa ya daki kotar addar Take addar ta kwace daga hannun nasa tayi sama Cikin zafin nama sarki gulbas ya daka tsalle yabi takobin sama ya cafketa Tun kafin ya diro kasan ya kaiwa mai addar sara da ita Nan Take kansa ya tsinke daga jikin gangar jikin ya fadi kasa Koda fatalwun suka ga haka suka kara yunkurowa da karfinsu Suka kara kachamewa da wani sabon yakin wanda yafi na farko A wannan lokaci sai ya zamana cewa yaki yasha banban Sarki gulbas inbanda muguwar barna babu abinda yake yi musu Duk inda ya ratsa acikinsu saidai kaga yana zaftare kawunan su Da hannayensu yana gididdiba su kamar ana sassabe agona Nanfa guri ya rinchabe ya hautsine inbanda ihun Wadannan fatalwu babu abinda kunne keji Su kuwa kara danno kai suke ba tareda suna tsoron mutuwar ba awannan lokaci sunga bala'in da basu taba gani ba 🙂🤣domin tun suna turo kansu sai daya zamana sun fara ja da baya saboda ganin mutuwa muraran da sukayi da idanunsa Kafin a kara daukar wani lokaci mai tsawo tuni sarki gulbas ya gama karar dasu duk sun dagargaje sun baje akan kasa tamkar ba'a taba tashinsu ba Don haka sai sarki gulbas ya sunkuya ya dauki takobinsa ya maidai ita acikin kufenta yaci gaba da kutsawa ta cikin dakunan wannan gida WANNAN SHINE ABINDAYA FARU GA SARKI GULBAS BAYAN YA KUBUTA DAGA TARKO NA FARKO DA KUMA NA BIYU ********* ************* **** Al'amarin boka surkais kuwa lokacin da suka kasa tseren gudu da wannan wutar sihirin Saida suka shafe sa'o'i masu yawa suna gudu ba tareda ya tsaya da gudunba Kuma yana gudun yana nazarin yadda zai koma da baya domin bude kofar shiga Cikin wannan gida don tsallake matakin farko da kuma ragowar matakan Yana cikin gudun ne kawai yajiyo kugin wutar daga bayansa Cikin sauri ya waiwaya bisa mamaki sai yaga wata murtukekiyar bulalar haske tana dukan wutar tana korata baya Koda ganin wannan al'amari sai boka surkais ya cika da tsananin mamaki yace aransa Duk yadda akayi wannan wuta bata shiri da haske Domin yanzu rana ta fadi idan har inaso na gano kofar shiga wannan gidan wutar dolene nayi hakuri zuwa gobe da safe idan rana ta bude yana gama fadin haka saiya sami guri ya zauna ya kishingida da wani Dutse dake bayansa aikuwa yin hakan keda wuya sai barci ya dauke shi ba tare daya sani ba Bai farka ba sai washe gari da rana lokacin da hasken rana ta kwalle hasken yazo ya bugi idanuwansa Firgigit boka surkais ya farka daga barcin daya sha Yana mikewa ya bude jakarsa ya fiddo abinci yayi loma uku sannan ya gyara damararsa ya cigaba da gudu amma a wannan karan wutar yake tunkara Saida yayi gudu kamar wanda yayi abaya Sannan ya isa inda wutar take Yana zuwa ya sami guri ya tsaya cak yayi cirko cirko yana mai kallonta A sannan ne ya lura wutar tana da wasu dogayen harshuna guda biyu Wadanda suka kalli sama atsaye kamar bishiyu atsakiyarsu kuma wata katuwar kofa ce mai maganadisu ajikinta wanda kan iya janyo duk wani karfe dake kusa da ita Amma ita kanta kofar tayi jawur saboda hucin hutar Atsakiyar kofar kuwa wata hudace ta zura makulli acikinta Amma fa kafin ya riski wannan kofar dole sai ya ratsa ta cikin wutar Nanfa ya tsaya yana tunanin yadda zaifi ya riski wannan kofar Daga can sai dabara ta fado masa Take ya falfala da gudun gaske ya tunkari wutar duk da yanajin hucin wutar yana ratsa jikinsa kamar zai zagwanyar da jikinsa Koda yazo daidai bakin wutar sai ya daka tsalle ya dunkule jikinsa aguri guda Yayi fitar burgu zuwa cikin wutar kamar an harba kibiya daga cikin baka Yana zuwa daidai inda kofar take saiya zura wannan makulli a gurinsa Ai kuwa yin hakan keda wuya sai kofar ta bude kanta Ya fada ciki sannan kofar ta maida kanta ta rufe koda shigarsa cikin wannan gida sai ganinsa yayi acikin wani kogon dutse Wanda babu komai acikinsa face duwatsu da wasu koguna wanda kowanne kogo daga cikinsu shima ya kasance babba kuma mai fadi da tsawo da kuma tsananin duhu Ta yadda baya iya ganin abinda ke cikin kogunan a saman dakin kuwa wata jijiyar bishiya ce Wacce a samanta anyi rubutu cikin babban baki kamar haka BARKA DA ZUWA KOGON UWAR MACIZAI YAKAI BAKON WANNAN KOGO KA SANI ACIKINSA AKWAI MACIZAI MASU MATUKAR YAWA DA KUMA TSANANIN DAFI WANDA IDAN HAR DAYA DAGA CIKINSU YA SARI JIKINKA IDAN HAR BAKA CI WANNAN JIJIYAR BA CIKIN DAKIKU GOMA KACHAL JIKINKA ZAI KAMA ZAGWANYEWA KAMAR NARKAKKIYAR DALMA KUMA DUKKANSU BA ZASU TABA MUTUWA BA FACE KA GANO MAHAIFIYARSU KA KASHETA DON HAKA SAI KAYI AIKI DA LURA Koda gama karanta wannan rubutu sai rubutun komai ya dauke Lokacin da boka surkais ya gama ganin wannan sanarwa Sai kawai ya sami guri ya tsaya cak yana jiran ganin daga wanne bangare ne macizan zasu fara fitowa Jim kadan sai ya fara jiyo wani sautin kukan macizai yana fitowa daga cikin wadannan kogunan tako ina Kafin cikar wasu dakiku tuni kogon ya cika da wasu irin macizai wadanda kawunansu suka kasance jajaye jelarsu kuwa bakake ne sidik tako'ina babu banbancin komai babu wanda yafi wani daga cikinsu , Kai komai ruwan idon mutum bai isa ya iya tantance waccece ta haife su ba Koda gama fitowar wadannan macizai duk sai suka fara wani kuka mara dadin ji Kuma dukkansu suka nufo inda boka surkais yake suna masu kewayeshi Daga can sai dukkansu sukayi tsalle alokaci guda suka fado kansa da nufin duk suyi masa rubudugu su dura masa dafin dake bakunansu WANNAN SHINE ABINDA YA FARU GA BOKA SURKAIS BAYAN YA SAMI NASARAR RATSAWA TA CIKIN KATANGAR WUTA ******* ********* ********** Al'amarin jarumi rukyan kuwa lokacin da yaki yayi tsanani tsakaninsa da wannan maridi Saiya fuskanci cewa tabbas karfin damtsensa bazai kwaceshi ba daga hannunsa Don haka sai ya canja salon fada ya zamana yana ta faman zullewa maridin yaki yarda ya rutsa shi a guri daya Wani lokacin ma sai kaga har tashi sama yake yana gudu ajikin katangar dakin tamkar yana gudu akan doron kasa Kuma yana gudun yana cigaba da kaiwa maridin dodon hari Nan fa hankalin dodon ya birkice ganin yadda karamar halittar daya raina tana kokarin bata masa lokaci Don haka saiya dinga kaiwa rukyan duka ba kakkautawa Cikin kankanin lokaci suka birkita dakin ya fara kokarin ruftowa kansu gaba daya saboda karfin dukan da dodon yake yiwa dirkar ginin Koda jarumi rukyan yaga abinda ke shirin faruwa ga dakin ya shammaci dodon Lokaci guda ya tsaya da guje gujen da yakeyi sannan yayi tsalle ya kama hawa jikin dodon cikin sauri kamar yana hawa kan bishiya Nanfa dodon ya fara buge buge don ya kado daga jikin sa Amma saboda zafin namansa kafin hannun yazo inda yake Tuni yayi tsalle ya sauka daga gurin ya koma wani gun daban Koda ya isa kan wuyan dodon sai yasa takobi ya datse shi Take jini yayi feshi kamar an bude idaniyar ruwa kan dodon kuma ya fadi kasa ya gangara can gefe guda Cikin zafin nama rukyan ya dira daga jikin gangar jikin nasa Alokacin ne gangar jikin ta sulale ta fadi kasa rikica jini na zuba daga jikinsa Sai a sannan ne ya lura da cewa rana ta fadi kuma dare har ya fara Don haka dolene ya kwana a wannan daki kafin gari ya waye yaci gaba da tafiya KARAGAR AJALI 2 ********PART B LBR ***********---------HABIBULLAH KBR Lokacin da jarumi rukyan ya sami guri ya kwanta bayan ya sami nasarar kashe wannan maridin dodon Sai kawai ya tsinci kansa cikin tunani kala daban daban game da abubuwan da suka faru da shi a baya Da kuma irin gwagwarmayar daya sha a rayuwarsa tun yana yaro karami Da irin kyawawan 'yan matan da suka kamu da soyayyarsa abaya yaki amincewa dasu Yace bazai taba yin aure ba sai ya sami daukakar datafi ta kowa a wannan zamanin Sai nadama tazo masa yace lallai dan adam akwai shi da buri Da ace ya amince dasu da yanzu ya sami macen da zata zama abokiyar rayuwarsa Kuma wacce zata kula masa da dan da zasu haifa koda bayan ransa Amma yanzu Gashi ya shigo tafarkin da bashi da tabbacin fita daga cikinsa Tsananin sa'ace kawai zata fitar dashi Daga wannan gida Har yakai ga cika babban burin da yake tanadi akansa Yana cikin wannan tunanine yaji cikinsa ya fara murdawa alamar yunwa tana addabarsa ba tare daya sani ba Cikin sauri ya kwance jakar guzurinsa ya fito da wani busashshen gasashshen nama daga ciki ya fara ci Sai dayaci ya cika cikinsa sannan ya daure bakin jakar ya maida ita jikin kugunsa ya daure Koda gama cin wannan abinci sai take yaji barci ya kama idanunsa Nan da nan kuwa cikin kankanin lokaci ya buge da barci ba tare daya sani ba Kwanciya barcinsa keda wuya sai yayi wani mafarki Da Wata bakar inuwa mai canja siffofi tana biye dashi a kan hanyarsa ta dauko takobin saiful laiham duk inda yayi wannan inuwar tana makale dashi daga karshe kuma daga shi har inuwar sai su fada cikin wani mahaukacin tarkon mutuwa Haka dai a cikin wannan barci yayita mafarkai iri iri masu abubuwan al'ajabi acikinsa Har zuwa safiya lokacin da gari ya waye yayi haske rana ta gama takewa Yana farkawa daga barcin take ya mike tsaye saboda ganin yadda rana ta take cikin hanzari ya gyara damararsa ya daure Ya gyara jikinsa sosai domin tunkarar daki na gaba yana gama shiryawa sai ya nufi hanyar da zata kaishi daki na gaba kai tsaye ba tareda shakkar mai zai tarar acikinsa ba Bai jima yana tafiya ba ya iso bakin wata katuwar murtukekiyar kofa wacce aka kerata da zallan bakin karfe mai matukar kauri da fadi Wacce kaifi da tsini ba zasu taba tasiri ba jikinta ba tsawonta kuwa ya wuce tsawon doguwar bishiyar dabino Yana zuwa daf da wannan kofa take yaji sautin zare wasu mahaukatan sakatu Wanda sautin zarewarsu ya cika dakin da yake ciki tareda amsa kuwwa Sai da aka dau dakiku dari biyu da tamanin ana zare sakatun sannan kofar ta bude kanta Ya shige cikin dakin yana shiga cikin dakin sai kofar ta maida kanta ta rufe Sakatun suka sake maida kansu suka rufe bam ta yadda babu wanda ya isa ya iya zaresu saboda yanayin shirin da akayi musu Yana shiga cikin sai ya iske babu komai acikinsa face sassan jikin bil'adama da aljanu asakale ajikin garu jini yana tsiyaya daga jikinsu Wasu kuwa an daure su ne da hanjin cikinsu suna reto a saman dakin gaba daya dakin ya cika da jini hatta shafen dakin anyi shi ne da jini Komai rashin imanin mutum idan yaga yadda akayi wa wadannan fursunoni kacha kacha da jikinsu dolene ya tausaya musu Koda ganin wannan bakar kisan gilla da akayiwa wadannan fursunoni sai Yayi sauri ya kauda fuskarsa ga barin kallonsu ya cigaba da tafiya acikin dakin Dakika dari da ashirin kadai yayi acikin wannan daki kwatsam sai gani yayi wasu irin aljanu masu munin gaske kuma suna matukar kama da bil'adama ta bangaren fuskokinsu da kirar jikinsu saidai kuma suna da hakora zako zako masu matukar tsini Idanunsu kuwa 'yan mini mini ne kai kace basa gani da idanun Hannayensu kuma gaba dayansu na karfuna ne wadanda ajikinsu akwai farata masu kaifi da tsini Agadon bayansu kuma wasu Kananun fuka fukaine guda hudu Wani irin jini mai maiko aai dalale yake daga cikin bakin nasu Adadin wadannan aljanu kuwa sun wuce guda dubu da doriya Kai da ganin wadannan aljanu kasan suna daga cikin jinsin mayun aljanu wadanda basu da abinci sai zallan jini Duk wanda yayi arba da wadannan aljanu dolene y shiga taitayinsa saboda irin munin halittar da suke da ita Koda gama bayyanarsu duk sai suka kura masa idanu suka zuba masa arwa Nanfa yaji jikinsa na kakkarwa kamar kafafuwansa ba zasu iya

Chapter 3 of 21