Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
8 / 9
biyu Mummy tayi murmushi tace ai gwamma da aka maka kafar taje can nima na huta da zaman kishi da ita Daddy yace kai mummyn Hakeem badai kishiba To nikuma ba inda za aje min da mata inasonta Meenat dai yau duk surutunta bakin ya mutu Hakeem yace amina Dan Allah karkisake biye ma su laila kizo kibamu kunya Kinga dai gidan mutunci ne ko Meenat tadaga kai sama tace to daddy Hakeem yawa mummy da daddy saidafe yawuce part dinshi Daddy da mummy suka cigaba dawa meenat nasiha harshima daddyn yaje byakwanta Hakeem nashiga part dinsu yaga husnah kwance tayi bacci cikin wasu fitunannun sleeping dress Ya karasa kusa da ita yakwantar da kashi a kirjinta husnah dai bacci yayi nisa Yaga dai bazata tashiba Dan tunda tasamu cikin intafara bacci kaman ta mutu Yashiga yayi wanka kafin yafito yayi shirin kwanciyar sa Ya kwanta tare da manno husnah ajikinshi Dan harsunsaba baya iya bacci saiyajita jikinshi haka itama idan tabude ido taga yana kusada ita tofa tana jikinshi Yana nashafa mata kanta yaso yatasheta sai kuma yafasa Dan yaga taji dadin baccin ta ****** anty kubra zaune itada umma suna lissafin kudin dazai kawo na sayayyar kayan lefe itafa anty kubra komai takeyi daurewa kawai saboda kwata kwata bata jin dadi sosai Taki nunawa ne saboda karaga kaman saboda maganar auren yasata damuwa Suna gama wa ta tashi tadauki hijabinta tace umma barin shiga nan makwafta yarinyar salma ba lafiya manal Umma tace ayya koshiyasa bana ganinta kwana biyu anty kubra tace wallahi Umma tace kigaishemin Da ita Anty kubra tana fita gidan doctor salma tashiga taci sa akuwa tana gida Doctor salma tace kai yau kubra kece komafarki nakeyi anty kubra tayi murmushi tace nice wallahi doctor Tace mushiga daga falo Nan suka shiga bayan sungaisa Takewa doctor salma bayanin yadda takeji kusan sati uku da suka wuce Doctor salma tayi mata tambayoyi ta amsa Tace kitashi kishiga kiyi fitsari zanmiki P T test Anty kubra batayi musuba Tayi doctor tayi gwaje gwajensu taga yasa mata positive aikuwa da murna tasanar da anty kubra anty kubra tsaban farin ciki saiga hawaye sharshar yana bin kuma tunta Doctor salma tace haba kubra ai murna yalamata kiyi ba kukaba Kubra tace hakane Allah nagode maka amma Dan Allah karkifa dawa megidanki Kinsan idan megidanki yasani zaifadawa shamsu kuma banason mijina yasan da wannan cikin Doctor salma ta gwalo ido tace kekuwa kubra meyayi zafi haka abinda kukadade kuna nema Allah yabaki kice kar a fadawa mijinki Kubra tace ina da dalili mai karfi ne yasa nafadi haka kuma zanfada miki yanzu Nan anty kubra tabata labarin komai Tace kinga idan wallahi nasan zaice yafasa auran Kuma idan yafasa auran bazan yafewa kaina ba zanga kaman nice sila Kuma gashi gidan mutunci zai yi auran idan yace yafasa ai zasu daukeshi karamin mutum Doctor salma baki tasake kawai tana sauraron karfin hali irin na kubra Gaskiya ko ita kubra ta matukar burgeta Tana hali mai kyau Wanda kowani miji zaiyi alfahari da ita Murmushi salma tayi tareda jinjina mata tace Allah dai yabiyaki kubra wannan jahadi da kikeda niyyar yi Kuma insha Allah keda kanki zakifadawa mijinki alokacin daya dace Nan sukayi sallama kubra ta koma gida ******* Biki ya rage saura sati kowani bangare sunata shiri kamar masu aurar da budurwa ko saurayi komai da ake bukata ya shamsu kubra yakeba itakuma tazage tsakaninta da Allah tanayin komai Ba Wanda ya lura da cewan tana da shigan ciki ajikinta saboda komai da jikinta takeyi abunta Kayan lefe kuwa masu kyau da tsada guda dozin wato shabiyu itama kubra yasake mata komai kuma yabata makudan kudi taki karba yanuna rashin jindadinshi Saita karba tamishi godiya Kamar kullum sunzo kwanciya tace honey yanzu Dan Allah abinda kakeyi ka kyauta Ya shamsu dake aiki a lap top dinshi yajuyo yace meya faru honey Anty kubra ta ce yau kusan saura sati fa auranka amma Baku taba magana ba aizaka sa iyayenta suji badadi suzargi basonta kakeba kaman dole akama Ya shamsu ai basonta nakeba kubra inada mace kamanke mezan nema agun wata mace Kubra ta taso ta ringumeshi tabaya tace nasani mijina amma inason kaduba iyayenta Dan Allah Ya shamsu yasaukar da ajiyar zuciya yace yanzu yakikeson ayi Kubra tace gobe kaje Kaduna kufahimci juna Dan Allah kabata abinda take bukata na hidimar biki Ya shamsu yace naji Allah yakaimu shikenan hankalinki ya kwanta Kubra tadaga kai tace yauwa honey Yanzu kabar wannan aikin Dan Allah kazo mukwanta bacci nakeji gashi gobe zakayi tafiya ta kashe computer taja hanunta mijinta zuwa kadu gado ****** Washagari kubra takira Husnah tasanar da ita zuwan ya shamsu Tace tasanar da meenat Husnah tace toshike nan kifada mishi yataho minda furar umman nan Dan Allah anty kubra tace to mama food Husnah tace anty hardake ko kinacemin mama food ko Anty kubra tayi murmushi tace aidole wannan babyn dai yasaki ci wallahi Suna gama waya husnah ta kalli meenat tace yaufa mijinki yanahanya saiki tashi kifara shiri Meenat tace banason wasafa niwacece da zakice zaizo domina tadafa kirji Husnah ta ce ke amatarshi mana Meenat tayi murmushi tace hmm ninasan fa bawani sona ya shansu yakeba amma zanmishi biyayya insha Allah zaiyi alfahari dani Yauwa antyna meya yashamsu yafi so acikin abinci amma fa saikin tayani kisan har yanzu hanun baifada ba Tayi murmushi Husnah dai tausayin meenat yakamata ashema itama tasan ya shamsu bayasonta Tare sukaje kitchen sukayi aikin abinci Large shabiyu da rabi sukagama Kowacce tashiga wanka Meenat tasha gayu sosai da taimakon husnah Yashamsu karfe daya darabi Next page Your comment is needed fans Ina alfahari da Ku over wallahi πŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–Š [06/05, 11:22 AM] UMMU AFAN 🌹: πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ— BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM STORY & WRITTEN BY THE SPECIAL AUTHOR /WRITER UMMU AFAN πŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–Š 🌹FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION🌹 🌹F.C.T.W.A.🌹 🌹HOME OF QUALITY AND TRUSTED WRITERS OF THE NATION🌹 πŸŽ—I DEDICATE THIS PAGE TO YOU SISTER BALARABA Ina alfahari da comment dinki over kina kokari sosai wajen suburbudo comment Allah yabar zumunciπŸŽ—πŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉ πŸŽ—AKWAI LOKACI πŸŽ— πŸŽ— PAGE 158 to 150πŸŽ— Afalon su mummy aka sauki ya shamsu shi sosai suka gaisa da Da mummy Husnah dake da mummy tace yaya ina furana Ya shamsu yayi murmushi yace mummy kina fama da shawagwabar husnah umma dai huta sai mummy kuma Mummy tayi murmushi tace tayi abinta lokacinta ne ai tana debe min kewar yarinya mace Yashamsu yace aitagirma dayawa mummy tace mummy tace wadin ai husnah yarinya ce idan batayi shagwabar ta yanzu sai yaushe zatayi Husnah tayi murmushi tace to yaya kaji daiko Saika bani furana kawai Ya shamsu yace ai na manta da furar ki Husnah tayi murmushi tace caf ai kuwa da bazan bari kaga matarka ba nima sai ka koma kakawo min kafin kaganta Mummy tayi murmushi yanayin shakuwar ya shamsu da husnah yabata sha'awa Sosai duk da yagirme mata hakan bai hanashi Jan kanwarshi ajikiba Key din motar yabata yace tadauko a mota Da murna ta karba tayi hanyar waje Mummy tace yi a hankali 'yata kefa saikace bame cikiba bakya nauyin cikin ma kai yarinta me dadi Mummy tace to nibazan Barka kaci abinci Barin turo ma ita aminar Ya shamsu wayarsa yadauka yayi Dial number din kubra tana ganin kiranshi tadauka tayi sallama tace honey ka isa lafiya ya kanwata Ya shamsu yace zakifara ko nifa nakiraki ne naji nice voice dinki Kubra tayi murmushi tace nagode mijina dafatan kasamesu lafiya yace kowa lafiya Husnah tashigo falon ganin yana waya yasa ta haura sama gurin mummy can falon daddy Clashing sukayi da meenat zata sauko husnah tace kai matan yaya kinyi kyau wallahi kar ki safa saikuma tayi shiru tana murmushi meenat tace karnasa me kinganki Kina nan sai tsokana ko am kinsan meye husnah wallahi kunya nakeji sosai Husnah tadafa kafadarta tace kisawa kanki kwarin gwiwa kefa mace ce haba yakikeson badani ne kaman ba meenat din Dana sani ba Kinsan Allah saikinyi da gaske kafin kisamu kan yayana wannan kunyar duk bazai fishshekiba wallahi Saboda bahaka antyna take mikishiba Beside ma fa namiji baya son yawan kunya Saboda kunyar yana cutar dasu dayawa Meenat tace nagode da shawararki yar uwa kuma small mama na Zanyi aiki dashi Ta kalli ledar hanun husnah tace karfa kishanye kekadai please nasan cinki Nasan wannan furrar tunda kika damu dashi zaiyi dadi over wallahi Husnah tace jeki fa kinshanya min yaya na a falo Meenat tayi murmushi ta karasa sauka Cike da ladabi da kunya ta durkusa kasan carpet tana jiran yagama wayar sa Shikam ya shamsu soyayya sosai suke zubawa a waya da anty kubra Yadau kusan minti talatin kafin kubra tace Dan Allah idan kana kusa da kanwata ka kashe wayar nan Ba dadi wallahi cin fuskane Ya shamsu ya kalli gefen da meenat take tunda ta ajiye kanta kasa bata dago ba saita bashi tausayi Yacewa kubra gata nan yamika wa meenat wayar batayi tsamma niba taga wayar dago kai tayi suka hada ido yace karba Ta karba suka gaisa da anty kubra meenat ta tambayi umma kubra tace umma lafiya qalau Kafin sukayi sallama kubra ta kashe wayar Dan karma yakarba wayar yasake wata maganar Meenat ta kalli screen din wayar ya shamsu hoton taga hoton anty kubra dashi sunsa kaya iridaya suna murmushi hoton yamata kyau sosai Ya shamsu ganin bata mika mishi wayar ba yasa ya kalleta da kyau yaga metake kallo yaga dai tazubawa Wayar ido Meenat tamika mika mishi wayar Tace ya shamsu ina wuni yace lafiya ya mutan gidan Tace kowa lafiya yace madallah Daga nan kowa yayi shiru Tsawon minti goma daga baya yace amina bakya maganane ko kuma nine bakyason ma magana Meenat tace bahakabane to bakaci komai na gashi ankawo ma komai Ya shamsu ya kalli kayan gurin yace ai bakiso naciba tunda baki bani komaiba haka ake barin bako Meenat tagirgiza kai tamatsa kusada abincin ta saving dinshi komai Tace bissimillah ya shamsu yace to anty meenat Tayi murmushi batace komaiba kasa yasauka yafara cin abinci Meenat haka kawai tatsinci kanta da sahanu tadauki wayar ya shamsu Ya shamsu ganin tadauki phone dinshi murmushi yayi kawai yacigaba da cin abincinsa Meenat kallon hotuna take sosai daga hotunan shi saina kubra saina husnah da su umma Ta dauki wayarta tayi connecting ta xender tayi ta tura pic masu kyau na shi Dana anty kubra Ya shamsu yace mekike turawa tace hotuna Yace nawa kenan tace na anty kubra Yace banyarda ba inga wayar idan dagaske kike Meenat tayi murmushi yabashi wayar duka yaduba yaga abinda ta tura Yadauki number dinta yabata wayar Yaciro kudi bai Masan tawansuba ya ajiye yace ga wannan kiyi hidima dasu Meenat tace wallahi kabarsu niba abinda zanyi Sai walima kuma mummy ce zatayi komai Yace yace nariga nayi niyya Tayi godiya kawai daga nan ya kalli agogo yaga time yace zan wuce kinsan sainabi office din daddynki Dan baimasan na zoba Meenat dai tana ta wasa da hanunta Duk wayoyin ya kwashe yazuba a aljihunshi meenat kuma takasa magana Yace kikara su mummy muyi sallama Meenat ta wuce yabita da kallo harta sama amma batasan yana kallon ba Sunyi sallama da mummy tace Dan Allah kagaishemin da umma kace mata munga tsaraba mungode tabashi aika yakaiwa umma Husnah tace to yaya sai munkawo ma amaryar ka Yace shikenan yar kanwata kikula da kanki Tace insha Allah yaya sakon gaisuwa na zuwa ga antyn data fikowacce anty aduniya Ya shamsu yayi murmushi yace zataji insha Allah meenat tadauki kayan da mummy tabayar akaiwa su umma Tarakashi hargurin mota tabude tasaka kafin ta jingina da jigin motar tana son tambayar wayarta tana kunya Ya shamsu kuwa baimasan tanayiba tashiga motar shiyace to amaryar shamsu sakin kinzo ko yana gama fadar haka yaja motarshi yayi gaba Murmushi meenat tayi tace nasan bakasona ya shamsu amma ina fatan kasoni a ranka koda bazai kai yadda kakeson anty kubra ba daman bankai kaina nanba Saiga hawaye yana zubo mata Saiji tayi ana share mata hawayen Tabude ido taga husnah ce Meenat bata San lokacin data fada jikin Husnah tana kuka ba Kukan datarasa namenene shi Da daddare YOUNG PROF da husnah falonsu Hakeem yace sweet albishirin ki Husnah dake kwance jikinshi tace goro Prince Yace saikinfada min goron albishir dazaki bani idan nafada miki husnah ta tura baki tace kaifa Prince nasan irin goron ka fa tayi maganar tana shagwaba Yayi murmushi yace to aike kekadaice me iyabani wannan goron Husnah tasake kwantar da kanta a shimfudaddan kirjin mijinta tana shakar kamshinsa Tunda tasamu ciki itakuma takeson kamshin Hakeem sosai kullum suna manne da juna idan yadawo daga office Tace inajinka yace angama miki gidan marayun nan da asibitin saboda haka bayan biki Saimuje mukwaso su umma suzo sugani susa albarka aciki Baiyi aune auene ba yaji hawaye a kirjinshi Yadago kanta yace lafiya sweet meye kuma na kuka husnah tace bansan mezan maka nabiyaka Prince kamin komai a rayuwata kacika min burina danake dashi tun ina yarinya Allah ya Kafin takarasa godiyar dai Hakeem ya hade bakinsu guri daya saidaya kusan minti biyar kafin yace karkisake min godiya Wallahi aini bawan Allah kuma ni bawankine kiyi yadda kikeso dani bayan su mummy banida samada ke Itama dai husnah ganin bazai barta tamishi asalin godiyaba Yasa tafara nuna mishi farincikinta tahanyar abinda yafiso ***** Hajiya rukayya da hajiya Laila suna kasa metsarki tun bayan faruwar alamarin nan suke saudiya Suna ta ibada da Neman yafiya agurin Allah Daddyn Hakeem suna waya sosai dasu danshi yake musu komai shida Hakeem Daddyn Hakeem kuwa shiyake sanar da su zancen auran meenat da wan husnah Sosai suma sukaji dadi sukasa albarka To shine yanzu suke shirin dawowa saboda auran meenat *** Ya shamsu Yakoma gida lafiya anty kubra ta tarbeshi da murnarta takai mishi ruwan wanka Yayi wanka yaje part din su umma sukaci abinci da shi ya shamsu indai badasu umma yaci abinciba anaci anahira kamar dai yadda suka saba ada Sunyi shirin kwanciya sai akakira wayar yashamsu Yace kubra tamiko mishi Anty kubra tayi murmushi ganin wayoyi biyu a aljihunshi Takwaso duka tace honey wannan wayarfa batareda yakalleta ba yace nawane Tace amma dai wayartayi kyau tana danna screen din wayar wani hoton meenat ne ya bayyana ajiki tayi kyau kuwa Cike da mamaki anty kubra tasake kallon wayar tace lalle ma namiji kaman bashinake ta matsamai yaje gurintaba Ganin ta tsaya kallon wayar yace kikawo min mana Honey Kafin kubra tayi magana har ankira wayar ya shamsu akarona biyu Kubra Tamika mai yaga lovely sister husnah kenan Bayan tamishi yagajiyar hanya tace yaba anty kubra itama suka gaisa tace abawa kanwarta Suka gaisa da meenat Kafin husnah takarba anty kubra taba ya shamsu wayar husnah tace yaya shine baka ba meenat wayarta ba itakuma takasa maka magana ko aikuwa ya shamsu yatashi daga kwancen dayake yace subhanallah ai nazaci tadauka nema amma gobe zan bayar akai mata Husnah tace OK kasan zama bawaya ba dadi Sukayi sallama Ya shamsu yakai kallonshi kanwayar dake hanun kubra yace wallahi basan nataho mata da wayaba Honey Kubra tayi murmushi tace badamuwa ai hakan ma yanuna min kai karbi meenat sosai Allah yabaka ikon aldalci atsakaninmu Ya shamsu kunyar anty kubra ce ma shitakamashi Dan yasan bashida bakin kare kansa anty kubra talura da hakan yasa tashiga mantardashi wanann kunyar **** Rana bata karya yaune daurin auren SHAMSUDDEN DA AMINA next page 😘 Your comment is needed fans Love you all πŸ“’πŸ“’πŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–Š [06/05, 11:24 AM] UMMU AFAN 🌹: πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ— BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM STORY & WRITTEN BY THE SPECIAL AUTHOR /WRITER UMMU AFAN πŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–Š 🌹FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION🌹 🌹F.C.T.W.A.🌹 🌹HOME OF QUALITY AND TRUSTED WRITERS OF THE NATION🌹 πŸŽ—I DEDICATE THIS PAGE TO YOU SISTER MAMA AL'AMIN Ina alfahari da comment dinki over kina kokari sosai wajen suburbudo comment Allah yabar zumunciπŸŽ—πŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉ πŸŽ—AKWAI LOKACI πŸŽ— πŸŽ— PAGE 161 to 162πŸŽ— YONG PROF yayi rawan gani sosai Dan abinda yawa meenat shiyawa anty kubra colour ne kawai ya ban banta su Anyi biki an watse kowa Yakama gabanshi Husnah tayi tayi Hakeem yabar takai amarya yace Sam baiyadda tabi rubibiba kar ature mishi hancin baby Sosai taji haushi amma haka ta hakura ba yadda zatayi Su anty Aisha matar Ahmad da su hajiya rukayya suka kai amarya gidan mijinta dake kano Tarba sosai aka musu yan kawo amarya sunji dadin tarbar sosai komai cikin girma akayi shi Yarage saura amarya itakadai adakin ta bakowa Can anty kubra tashigo tace sannu dazuwa kanwata Dan Allah meenat wannan kunyar kirageta mijinkifa ba maison kunyabane Kizage kinuna wa mijinki so yadda shima zaisan yes yayi amarya karkiji kunyata munzama daya tunda yanzu mundawo karkashin adalin miji kamar mijinmu Dan haka kirage indan nine wallahi Dazuciya daya nake tare dake kanwata fatana Allah yahada kanmu muhadu mufaranta ran mijinmu banda jin zugan kawaye da zuciya zasu kaimu subaro mu ne kawai Kinji ko meenat tadaga kai tace insha Allah anty na Nagode da kaunarki gereni Anty kubra tace ba komai yanzu kitashi kikara gyarawa kafin angon naki yashigo Meenat taki tashi anty kubra data lura bazata tashi ba Tayi murmushi ta tashi tamata sallama tafita Kubra nakomawa dakinta tafashe da wani kuka mai ciwo yauce rana tafarko dazata kwanta batareda mijinta basa raba shinfida saidai idan tafiya yayi Yau gashi zama sufara raba kwnane dawata Tace ya Allah kasan niyyata na alkairi Allah kabamu zaman lafiya da mijinmu kasa yazama shine mujinmu a aljanna Ta kashe wutar dakinta ta kwanta Ya shamsu yana shigowa direct bedroom din kubra ya wuce yanshiga yasameta tana bacci Wanda azahirin gaskiya ba bacci takeba batason ganinsane kawai Ya shamsu zama yayi dai dai kanta yana shafa gashinta Yace Allah yamiki albarka matata Allah yasa kece uwargidata nagidan aljanna Kinsadaukar da komai saboda ni Nima ba abinda bazan iya yiba saboda ke Allah yabarmu tare mutukaraba Ya manna mata kiss agoshi Yafita zuwa bedroom dinshi yayi wanka yasa kayan bacci aiko yanagama shirin kwanciya ya kwanta abinshi tare da kara karfin AC din abinshi sai muce yashamsu asuba tagari ango Meenat dama tasan ba lalle yazoba Dan talura saitayi da gaske kafin tadan samu hankalinsa Ta tashi itama tayi shirin bacci takwanta Umma kuwa suna hira dawata aminyarta Maisuna hajiya zulai Hajiya zulai tace nikuwa hajiya anya kinlura da yarinyar nan kuwa khadijah dakyau kuwa Umma tace a a lafiya kikace haka Hajiya zulai tace ai daga yarinyar nan tana da juna biyu Bakiga yadda ta dashe tayi kyau ba cikin idonta zaki duba dakyau zakiga zahiri Umma tace nikaina naso nazargi haka Saikuma nace yaran yanzu da suke Neman cikin ido a rufe Da cikin ne zadasu sanar dani Hajiya zulai tayi murmushi tace aiko dai daga shamsu har khadijar bazasu iya ba yarane masu kunya Umma tayi murmushi tace allah nagode maka daka nufemu daganin wannan Abu Allah ka tabbatar da zarginmu akan kubra Hajiya zulai tace saikiyi kuma wani zargi aiko kaffara bazanyiba yarinyar nan cikine da ita Allah dai yaraba lafiya Nan sukayi ta tattaunawa tasakaninsu **** Washagari da asuba meenat tashi tashiga kitchen tafara aiki anty kubra kuwa tanayin sallah gajiyar biki yasa bacci yakwasheta a sallayar Meenat tagama komai tashirya a dining din falon su umma nan taga anacin abinci Kafin tawuce zuwa dakinta donyin wanka Anty kubra kuwa farkawata tayi dasauri ta kalli agogo taga taga takwas saura salati tayi Cikin sauri tafita zuwa kitchen ko hijabin ma bata tsaya cirewa ba Tana zuwa falo taga kan dining anjera komai takarasa da mamakinta ta bubbude Tace tomehakan yake nufi kenan Duk yadda akayi honey ba adaki sa takwana ba Ta wuce bedroom din ya shamsu tana shiga taga yana kwance abinshi Jinbudewar kofar yasa ya shamsu ya farka sukayi ido hudu da juna ya ware hanunshi wai ta taho Kubra ta nuke kafada ya shamsu tashi yayi dasauri yace wayatama min baby na Kubra tace yanzu kayi adalici kenan kabar yarinya ta kwana itakadai tana Bakuwa Ya shamsu yayi murmushi yace hoo kubra rigima Yatashi yazo yakamota yace kinsan namanta ma sai yanzu da kika tuna min Kubra ta kalleshi da mamaki tace yanzu akawo maka amaryar kace wai kama man daita Sakeni Dan Allah honey gaskiya baka kyauta ba su haka sukewa husnah ba duba wannan hallaci nasu karikemusu yarinya dakyau Ya shamsu yarungume kubra yace am sorry NY wife nayi tunanin zato zo nan ne Tace amma kace min kaman ta yasosa keya yace a banmantaba Yayi murmushi yanayin yadda yake maganar yabata dariya sosai atare suka fasheda da dariya Tace Dan Allah yau ka gaiyaceta dakin nan dakanka Dan taji itama kadamu daita Ya shamsu yayi murmushi yace yadda kikeso haka za ayi madam tayi murmushi tace kaje kashirya muje muyi break tagama komai yace wa Kubra tace kanawata mana Ya shamsu yayi murmushi yace to zauna kijirani nafito Kozaki tayani Kubra tayi murmushi tace ai kodaya bazanyiba honey Nima wanka zanje nayi kakira kanwata tatayaka Tana fadar haka yafada bathroom abinshi Kubra kuma takebe baki tayi waje abinta Wanka sosai meenat tadauka tayi kyau sosai abinta Kubra ma tadau gayu abinta tayi kyau sosai ba kadan ba Meenat ganin kubra yasa taraina kanta Dan ganin kubra tamata zarra Kubra da murmushi tace sannu da aiki kanwata amma fa kinyi laifi Meenat tadago dasauri ta kalleta kubra ta ce hakkina nane nabaki abinci yau my kanwa meyasa kika shiga kitchen batareda da la'akari dake amarya bace Meenat murmushi kawai tayi tace bakomai anty aikomai namiki banfadi ba Kafin kubra tayi magana umma tafito suka gaisheta ta amsa sosai tace inashi shamsun kubra tace Yana zuwa yanzu nakirashi umma tace kuci abinci mana kinyi shiru Kubra tayi murmushi tace to umma aike muke jira Umma tayi murmushi tace o ni kam zanga ranar dazaku girma keda shamsu wai kuce saida umma kwaci abinci Takarasa maganar tana murmushi Kubra tace umma ai munriga munsaba ne Ya shamsu yashigo da sallamarsa umma yagaisar kafin yace umma Abba yafitane tace yafita yanzu yanagama karyawa Ya shamsu yace amma yayi sammako dayawa Umma tace ai suna dataron dattawan unguwane yau Shamsu yace OK hakane natuna yaja kujera yazauna Ya kalli kubra yayi murmushi yace kekuma bagaisuwa Kubra tace bayan Wanda nama dazu Kafin yayi magana meenat tace yashamsu ina kwana Ya amsa batareda ya kalleta ba abin yaba umma kunya danta Lura ko kallon ta baiba Ya shamsu kam azuciyarshi hamdala yayi daya bashi mata kaman nashi Dan harga Allah sunmishi kyau dukansu **** Da daddare bayan sungama dinner meenat ta tafara tashi tayi musu saida safe umma tace amina har kingudu kenan Meenat tayi murmushi tace umma ai ina bacci da wurine shiyasa Umma tace shikenan jeki kwanta abinki Allah yamaku albarka yabaku masu yimuku abinda kuke mana Ya shamsu yabita da kallo ta wutsiyar ido Umma na kallonshi murmushi kawai tayi anty kubra ma tayi musu saida safe Sai wayajen goma ya shamsu yayi yatafi bedroom dinshi bayan yagama shirin baccin shi daga shi sai gajeran wando Yadauko aikinshi yafarayi a laptop Can dai yaji wani kasala yasaukar mashi Shifa baisaba rabuwada matarshi ba itakuma wannan

Chapter 8 of 9