Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 9
yace sosai ma dalibatace itada meenat da ita zan aura Laila da suby suka dau salati suna kallon kallo Hajiya rukayya kuwa zufa yajikata sharkaf Saboda rashin gaskiya Hakeem yayi murmushi gefen baki Ya kalli husnah yace baby kinsanshi daman tace a copper ne a school dinmu Yace daga bawani Abu takalli bash ta kalli meenat da jikinta yake bari .tace bakomai bayan wannan Bash yace karkice haka asmau nasan ban kyauta miki ba amma Dan Allah karkice ba komai a tsakaninmu Cikin bacin rai husnah ta kalleshi tace dan Allah malam dakata karkasake min maganar wani alaka A ina nasanka da harwani Abu yashiga tsakaninmu bayan malami da dalibarsa Bashir yazube gaban prof yace wallahi ba a hayyacina nafasa aurenta bansan meyake faruwaba A lokacin ba abinda nake gani sai amina Hakeem ya kalli husnah yace daman shine Wanda kike bani labari amina ma itace kawarki da kike bani labari Tunda akafara maganar kuka baizowa husnah ba sai yanzu Ta fashe da kuka data tuno da abinda suka mata Dagudu tabar falon Hakeem yakai kallonshi ga amina yace ke inason kifada min gaskiyar abinda kefaruwa bana son kimin karya kinsan halina amina tafashe da kuka ta kalli bashir tace Dan Allah uncle kayafemin Hajiya rukayya tace ke karkice komai tashi kitafi daki Hakeem yace ba inda zakije sai kin amsa min tambayata Cikin kuka meenat ta kwashe komai tafadamusu Kunyar duniya hajiya rukayya da su hajiya suwaiba da laila sunshashi agun Bashir yadago idonshi kaman garwashin wuta ya kalli meenat yace amina kuncuceni duniya da lahira Ninasan dama duk abinda na aikata wa asmau Ba a hayyacina na aikata ba Ba abinda zance saidai nace Allah ya isa tsakanina dake da kakarki Ya kalli Hakeem yace kamin aikin gafara wallahi bazan iya zama da amina a matsayin mataba Nasaketa saki uku kuma a hayyacina nasaketa Bana bukatar ta a ruyuwata Ya tashi yay ficewarsa daga gidan baki daya Hakeem yace kunga abinda kukajawa kanku ko Yanzu wannan wani irin abin kunya ne haka Yayi mun dai dai wannan shine hukuncin da yadace da ita Kuma kunga dayake Allah ba azzalumin bawansaba ne kuncuci husnah kuna Ganin kunci bulus ko To kunga aikin Ku saigashi duk abinda kuka yi nikuwa tanadi Dan kuwa samun mata irin husnah a yanzu sai antona Dole bash yamiki abinda yafi haka Banga laifinshi ba Dan asarar mace kaman husnah bakaramin asara bane Ya tashi yayi dakin husnah ya kullo kofar yanashi baiganta a faloba Direct yawuce zuwa bedroom dinta Ya hangota kwance kuka sosai takeyi kaman Allah ya aikota Ya karasa yazauna dab da ita yakamo hanunta yace baby look in to my eyes Husnah takasa kallonshi Yace kukan mekikeyi Tace bana son tuna abinda suka min ne Saboda nashafesu a tarihin rayuwata Yace idan hakane kidaina kuka Kokinsan nigata suka min da bashir ya aureki ina zansameki baby Kodaya banji haushin su ba Saima godewa Allah da kuma hajiya rukayya Duk abinda ta aikata karshe kan 'yarta yadawo Dan haka kidaina kuka bana son kukan ki kinjiko Tadaga kai sama yahau bed din dakyau yajanyota jikinshi yana shafa bayanta yace kokinsan bashir yasaki amina yanzu arazane Husnah ta tashi tace meyasa zaisaketa bayan komai yawuce Allah yabani Wanda yafishi Baikamata yayi hakaba wannan ai cin amanar soyayya ce Hakeem yamaida ita kan kirjinshi yace ai dama soyayyarsu bata Allah da annabi bane Naji dadi dayawa amina wannan sakin Hakan shizaisa tagane abinda yake dai dai Tadaina bin zugan kakaninta Dana uwarta Idan amina ta nutsu tagyara halinta Zan maida ita makaranta insaku tare kucigaba da zuwa school dinku kamar yadda kuke da Husnah tayi murmushi ta kara rungumeshi sosai tace idan kamana haka zamuji dadi sosai Allah yasaka da alkairi Allah yakara daukaka da arziki mai amfani yakara mana lafiya yabaka ikon ciyar damu da halak Yakara wa su mummy da daddy Nisan kwana da lafiya Hakeem cikin tsananin son matarshi ya kara kankameta sosai a kirjinshi yace adduoinki agareni suna sani nishadi Dani da su mummy duk muna alfaharin samun ki cikin rayuwarmu Husnah tace Dan Allah sweet karkace zaka matasawa meenat Kabarta na tabbatar zatayi nadama abinda tayi Hakeem yace kedai kice kina bin bayan kawarki ko Husnah tayi murmushi tace tun bayan rabuwata da meenat bansake wata kawaba daman nima bamai son tarin kawaye bane Naso meenat zuciya daya itace dai tadaukeni da guda biyu amma koyanzu takeson mucigaba da zumuncin mu Ina son haka saboda ina son meenat sosai Hakeem bai barta tacigaba da maganartaba yahada bakinsu guri daya Nan fa wasa yacanja salo Gashi ankusa kiran magriba kuma ba itace dashiba Tayi kakorin kwatar kanta amma takasa tashiga hanun maza sosai Hakeem yafara fita a hayyacinsa yana kokarin rabata da kayan jikinta Husnah tayi tunanin idan tabari fa ba takyauta Dan anshiga hakkin uwargida Cikin kuka Husnah tafara wash Allah cikina cikina Cikin sauri Hakeem yafara tambaryata meyasameta tace cikina nane yake ciwo Dasauri yasauka daga kan bed din Dan dauko magani husnah naganin yafita ta tashi dasauri tashiga bathroom Tasaka key Yadawo yaga wayam bata kan bed murmushi yayi yace zan kamaki Kifito nayi alwala kinga zantafi masallaci Husnah tace naki wayon kaje dayan bedroom din kayi acan Murmushi yayi yasan idan zai biye mata bazata budeba Meenat zaune gaban uwarta da kakanta kuka sosai takeyi Laila tace duk abin ma ai kaina yadawo niyakama ta ace ina kukan bakeba Hajiya rukayya kuwa cewa tayi share hawayenki Dan yasaki ke ai bashine karshen mazaba Dan haka kiyi shiru miji sai kin ce bakya so Keda ba mummuna ba Meenat tace wallahi ina son shi gashi harsaki uku yayi min Yazanyi nayi rayuwa ba bashir Husnah kincuceni bazan taba yafe miki ba sai na dau fansar abinda kika min Laila tace dakuwa kincika 'yar halak mekishin kanta ban amince kibarta tasha ruwaba agidan nan zanso kizama kece kishiyarta baniba uwarki zan nuna mata ina da kamarki Hajiya suwaiba tace gaskiya ne idai kujininane ban amince kubar maganar nan ba Tunda saboda ita aka sakeki Itama inason saboda ke ubanki yasaketa Nan sukaci gaba da mummanar shirunsu Hakeem yafito daga dakin husnah yayi waje batareda ya kallesuba Husnah kuwa sai da ta tabbatar yafita kafin tayi alwala tayi sallarta hade da adduointa Ta dauki alkuraninta tafara karantawa har aka kira isha Kafin ta ajiye tayi sallarta Tana idarwa ta ninke kayan sallarta tashiga bathroom tay wanka kafinta fito tashirya cikin wasu Riga da skirt din atanfa dinkin yayi matukar zama ajikinta tafesa turararukanta Tayi parking din gashinta Tadaura Dan kakwalin ta das kaman wacce aka dasa akanta Tasake gyara dakinta kafin tafito falonta Daman kafin Hakeem yakirata tagama abincinta mai rai da lafiya Couscous ne tadafa fari da miyar kaza Sai zobo drink mesanyi Wanda yasha flavour masu kamshi Da yakan kamshin Nan tadauki plate tadeba abincinta tasa miya Tadauki Dan karamin glass jug tazuba zobonta aciki Taduki karamin cup tayi waje Main falon gidan taje center table tajawo ta ajiye kayan abincin ta akai kafin tazauna zaman ci Bakowa afalon sai TVdake kunne Can saiga su sunfito gabadayansu kowa tanemi kujera tazauna Husnah tace barkanku da fitowa Duk zuba mata tsaki Husnah ta kallesu tace to Ashe abin nan To Allah yasauwake Tacigaba da cin abincinta Can sai mai aikin laila tace anty nashirya dining din Laila tace jeki kawasu nan muna a nan zamuci Husnah tayi murmushi batace komaiba ******** Bayan wata hudu meenat tadade da gama iddarta da kusan watadaya kenan Kuma a kano tayi iddarta yau take shirin komawa Kaduna gidan ubanta Dan tadau matakin datake da niyar dauka akan husnah Tuni driver yadukota zuwa kaduna Laila tuni tasa angyara wa meenat dakinta Komai yaji Ita kawai dakin yake jira Husnah kuwa yau ta tashi da kewan gidansu ne Tunda tayi aure sau biyu taje Kuma bai barta takwana ba Yau tafita girki tana zaune kusa Hakeem tana mishi rigima ita sai yabarta taje takwana biyu agida kuma yau takeson tafiya aikin dayakeyi a computer ma kasawa yayi Ajiyewa yayi gefe yakamota yace baby bakya tausayina kinsan bazan jure rashinki kusadani bako Husnah tasake shagwabewa Tace aishiyasa nace natafi yau jibi da yamma insha Allah sai na dawo Kaga yau dagobe bani bace da kai antyna ce Hakeem yace kedai kimin wayo ne kawai tashi kishirya Sainasa driver yakaiki Jibin zanzo na daukoki yau muna da meeting ne Inkuma zaki bar tafiyar sai gobe to saina kaiki da kaina Husnah tayi saurin cewa a a kaje meeting dinka kawai Yayi murmushi yace wato murna kikeyi zaki barni harna two days ko Husnah tasa hanunta a kumatunshi tace mezaisa nayi murnar barin minjina abin alfaharina Hakeem yashafa cikinta Yakama ta muje aduba min kefa Ina son yara baby yaushe zaki Haifa min yara masu kyau kamarke murmushi husnah tayi tace nikuma masu kaman kai nakeso su dauko Yace dagaske kikeyi tadaga alamar a Yace sai kidage sosai kinsan abin kokarine Tabashi full attention dinta Dan yamata bayanin yadda kokarin yake Yace kina son sanin yadda zakiyi 'ya'yan my suyi kama dake tace a Yace OK yatashi yacire singled din jikinshi itadai husnah dai kallonshi takeyi da zuciya daya bata kawo komai aranta ba Gani tayi yacire mata Dan kwalinkanta aikuwa ta gane meyake nufi Cikin shagwaba tace wallahi nabar maka suyi kama dakai kawai Hakeem yace a a kibarni kawai nayi kokarina Dan insamu mai kama dani kuma kice kinyafe ai kokarin danake nufi kenan Kibani hadin kai sosai kigani inbazaki samu masu kama dani ba Husnah dai talura da gaske fa yake Tace shine abinda kake bukata yace yes my Queen Tace OK ina zuwa barinsha sha ruwa a fridge zanbaka mamaki yace really tace yes Bani minti daya naje nadawo Tasamu tamishi wayo tagudu shiru shiru bata dawo ba yatashi tafita zuwa part dinta Yaga har ta fito daga wanka ma tana drying gashinta da hand drayer Hanu yasa a kirji yace kimin lefi kinshiga min aiki tunda kinsan ina gida aikina nane namiki komai Husnah tadago suka hada ido tasan bakaramin aikinshi bane yasata sake wanka yanzu Karasowa tayi cikin shagwaba ta kwantar da kanta a kirjin tace na tuba my prince Dan Allah karka bata min wanka na wallahi dokin ganin umma yasa nake sauri Hakeem yace ban yarda ba saikin min Abu daya Tace mezanma Yace kekisani murmushi husnah tayi tasan idan yafara haka rigima yake nema Tace OK kan bed tahau taga Kansu yazo dai dai tahada bakinsu guri daya Sosai take kissing dinshi Dan tasan abinda yake bukata kenan Batayi aune aune ba taganta yakwantar da ita duk yadda taso yakyaleta yaki Sai daya samu nutsuwa kafin yabarta Cak yadauketa tare sukayi wanka suka shirya Dakanshi yahada mata kayansawarta kala biyu cikin wani Dan karamin jaka mai kyau da sha'awa ~~~~~~~~~~ Husnah kwance falon ummanta kanta akan cinyar umma suna hirarsu Anty kubra ta shigo falon tace kinsan Allah husnah kikiyayeni fa zaki karyamana cinyar umma ne katuwa dake Husnah tayi murmushi tace to kwana nawa bangantaba banga ya shamsu ba ai dole na damu nayi kewarsu saura ya shamsu zaizo shima yasameni yamin alkawarin zai dinga zuwa sosai yana ganina Amman bai cika ba Husnah tace wallahi danwake zanci da dambu da kuma tuwan alkama Kubra ta rike baki duk acikin ki kekadai tace sosai makuwa amma dai yanzu tuwon nake bukata tukun Anty kubra tace OK bani minti na muna da miya daman tuwon kawai zanmiki Husnah tace yauwa matan yaya daga ke bawata Husnah taci tuwo sosai umma da kubra sunyi mamakin Umma dai murmushi tayi itakadai tasan dalilin murmushinta Duk abinda takeso shi ake mata agidan su Yaya shamsu kafin yadawo sai yatambayeta abinda take sha'wa ya taho mata dashi Ranar da zata tafi tun azahar YOUNG PROFESSOR ABDUL HAKEEM ABUBAKAR Ya isa kano gidansu husnah yazarce direct danshi jinshi yake kaman bashi da lafiya Dan kwana biyun datayi bata nan Saida yaci abinci agidan shida ya shamsu kafin suka wa ummu sallama suka fito suka dau hanya Hakeem yakasa boye zalamrsa akanta saida. Yayi parking a gefen titi Komeyasa oho Suna isa Hakeem yayi parking yazago yabude wa husnah kofa duk abinda kefaruwa a idon meenat da suby Dan suna lambun gidan suna hutawa Takaici Yakama meenat tace wallahi anty suby danasan husnah zata auri daddy Dana wallahi da banbar hajiya taje gurin maganin ba Yanzu gashi nibada bash itakuma da auren ubana har bayaganin kowa sai ita Suby tace ai wallahi zamu koya mata hankali basu rufe bakiba Hakeem yadauko bag din husnah da Yakama hanunta suka shiga ciki Suna zama husnah ta ce wayyo Prince zansha nun tsamiya zansha kuma nagaji dayawa beside ni idan nayi ma balle nashaba Cikin sauri yazauna kusada da ita yace kobakida lafiya ne Dan naga kincan minfa sosai Hanu takai ta lakuce hancinshi tace nidai ba abinda yake damuna Kawai kasamomin kunun tsamiya Waya yadaga yakira Ahmed yace kana gidane yace a Hakeem yace kasa Aisha ta min kunun tsamiya zanzo na dauka Kafin Ahmad yayi magana Hakeem yakashe wayarshi Dan yasan sai yamishi tsiya Hakeem yajuya yaga hartafara bacci a mota gabadaya ma baccin tayi Tashi yayi yamatsa kusa da yakura mata ido sosai Can zuciyarshi tace anya yarinyar lafoyarta kalau kuwa Yadauki waya yakira family doctor dinsu macen yace tazo da kayan aikinta Yafada mata abinda yake zargi tace OK tagane gatanan zuwa Hakeem cikin tsananin farin ciki yayi sujjadar Allah yatabbatar mishi da abinda yake zargi Next page Your comments is needed fans Love all πŸ“πŸ“πŸ“πŸ“πŸ“πŸ“–πŸ“–πŸ“–πŸ“–πŸ“–πŸ“– [05/05, 10:18 PM] UMMU AFAN 🌹: πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ— BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Story & written By The special writer UMMU AFAN πŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ“š 🌹FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION🌹 🌹🌹 (F.C.T.W.A)🌹🌹 🌹HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION🌹 πŸŽ—I DEDICATE THIS PAGE TO YOU Aisha Ibrahim ina matukar jin dadin comment din ki wallahi keep it up ina alfahari dake over my sister πŸ˜˜πŸ˜˜πŸ˜˜πŸ˜˜πŸ˜˜πŸ˜˜πŸŽ— πŸŽ—AKWAI LOKACI πŸŽ— πŸŽ—PAGE 143 to 145πŸŽ— Bayan gwaje gwaje da likita tawa Husnah ta tabbatar mishi husnah tana dauke da cikinshi Cikin tsanin farin ciki hakeem yace alhamdulillah Allah nagode maka da cika min burina cikin gaggawa Allah kasauketa lafiya likita tayi murmushi tace gaskiya wannan babyn zaiga gata prof irin wannan doki da murna haka Yayi murmushi tare da rungume husnah ajikinshi tunda likitar tafada cewan ciki ne da ita Ta rufe Idan kaman me bacci Ita kanta takasa sanin meyasata jin kunyar Hakeem yace wa likita kizuba ido kiyi kallo aranar da Queen dina ta haifamin baby a ranar zan yi abinda za bakowa mamaki Kuma kema fa baza abarki ba zaki ga goron albishir a account din ki Likita tayi murmushi tace kai amma nagode Allah yafito mana da wannan babyn lafiya amma Yakama ka kawota hospital gobe Dan mumata scanning a tabbatar cikin wata nawa ne Dan kasan lokacin da zakafara tsammanin babayn ka Hakeem yace ai bazan bari sai gobe ba yanzu zamu biki muje Nagani da idona Doctor tayi murmushi tace ina jiranku to Hakeem cak yadauki Husnah zuwa bedroom yasamata kataton hijabinta Sannan kuma ya sunkuya wai ta hau baya Husnah taga dagaske yakeyi fa Taware tace a a Dan Allah Prince kabarni maka ganin bamu kadai bane Hakeem yace ai ni mutane da maganarsu bai cika damuna ba ko agaban mummy zan iya goyanki ballantana 'yata Husnah tace naji inkai bazaka ji kunya ba aini zanji Ta kwasa dagudu tabar dakin Yafito hankalinshi a tashe yace Dan Allah baby kidaina gudu karki samin baby yagaji Husnah tatsaya cak taki juyowa Ya tako ya iso har gurinta yajanyota jikinshi yace oya mutafi ko kinga doctor tana jiranmu a waje Cikin shagwaba husnah tace tun ba aje ko ina ba kafara nuna min iyakata ko Shine zaka ce wai kar babyn ka yagaji Wato ma bani bace damuwarka babyn ne ko Cikin murmushi Hakeem yajuyo da ita suna fusakanta juna yace Haba baby kema kinsan you are my one and only Taya za ayi nace bandamu damu da lafiyarkiba ai dake da abinda yake cikin ki Inkincire mummy da daddy to kune rayuwata kune komai nawa Husnah tace nidai banyarda ba aikuwa sai ganin prof tayi gwiwa biyu agabanta Cikin sauri itama tayi kasan takama hanunshi tace la nifa wasa nakema Yayi murmushi yaja hancinta yace kinji tsoro kenan tace sosaima wace dasa zuciyata kneeling a kasa ai dole tsoro yakamani yayi murmushi yatashi yadagota cak Dakyar tabashi hakuri yabarta ta tayi tafiya da kanta Bayan scanning da akayi wa husnah aka ta babbatar musu da tana dauke da cikin sati bakwai wato getting to two months kenan A gurin Hakeem yadauki wayarshi yakira mummy da daddy yasanar dasu Mummy kaman tayi tsuntsuwa tazo taga 'yarta husnah haka take ji Tayi murna sosai haka ma daddy Dan mummy hafsat kam ma cewa tayi tundaga can zata fara sayayyar kayan jarirai Daga hospital sai gidan su Aisha da Ahmad Hakeem yayi dasu Suna zuwa kuwa Aisha takawo mai kunun tsamiyar dakan yazauna kan carpet ya hada mata sosai tasha kuwa duk sunyi mamaki Ahmad yace amma natayaka murna abokina Allah yaraba lafiya Aisha da itama haihuwar ko yau ko gobe Tayi murmushi tace Allah sarki 'yar kanwata Allah yasaukemu lafiya ko Husnah tace anty nifa bani da komai Wasa fa yaya yake muku Aisha da dariya yaso barke mata tace sosai Nagani kuwa Wannan tulun kunun da kika shanye ai kowa yasan bake kadai bace Husnah tayi murmushi tace ai saboda ina sone shiyasa Hakeem yace sannu da kokari madam kema kina fama da kanki mun hada kida aiki Tace bakomai wallahi bana ma son zaman Nan Ahmad da Hakeem sukafita ~~~~~ Bayan sati biyu duk wannan abinda kefaruwa na maganar cikin nan baizo kunnen su Laila ba Husnah zaune a falonta mai kamshi da sanyun Ac Kaman daga sama taji murya kaman na anty kubra Da sauri ta tashi taduba anty kubra ce kuwa tasha kyau cikin wani tsaddan less Dan shima ya ashamsu yanzu kudi yazauna mishi sosai shiyake juya dukiyar husnah Wanda tabashi ragamar komai a hanunshi Kuma shiyazama manager a company Hakeem Husnah tayi tsalle ta rungume anty kubra tace wayyo anty na wallahi naji dadin ganin Anty kubra tace kai Husnah bakida hankaline wayafa miki meciki tana tsalle haka husnah tarufe ido tace anty nifa banida komai Kubra tace ai Allah zata sake magana husnah taja sukayi part dinta Laila dake zaune jin abinda anty kubra tace Ya mugun daga mata hankali sosai Tace kai ina karya ne wallahi ba zaki taba haihuwa gidan nan ba matsuyaciya Meenat ce tafito daga part dinsu Dauke da glass cup a hanunta na drink Sai mummynta na hawaye Sai Takaraso a tace meyafaru kuma mummy Suby tace wannan 'yar talakawar ce wai cike ne da ita Meenat batasan sanda tasaki cup din hanunta ba Tace karya takeyi wallahi bata isa ta haifi wannan Dan iskan cikin nata agidan nan ba Tayi hanyar dakin husnah suby tayi saurin tarota tace inazaki Meenat kibarni naje anty suby wallahi sai namata dukan dazaisa cikin yazube inga tafadi Suby tace idan kikayi haka daddynki zai dauki babbar mataki akanki Kibari mubiyo musu tabayan gida Ina tabbatar muku husnah bazata haifi cikin nan ba Nan dai suby taringa basu shawarwari Husnah takawo wa anty kubra gashashshan namar kaza da drink saikuma fruit Ta zauna kusada anty kubra Anty kubra tace anya wannan husnah ummace kuwa Kinganki kuwa kinyi fresh dake kaman ba mai cikiba Husnah tayi murmushi kafin tayi magana wayarta yayi kara tana dubawa taga Prince ne cikin shagwaba ta amsa sallamar Anty husnah baki kawai tasake tana kallon husnah yadda tazage tana soyayya da mijinta ba alamar kunya cikin kawarewa da iya wa Hakeem yace to ya antyn mu Husnah tace LA ya akayi kasan tazo yayi murmushi yace karkidamu ki isar min da gaisuwa na kafin mukaraso yanzu Husnah tace kukaraso kaida wa kuma Yace naki fada yayi murmushi yace bani baby na muyi hira naji abinda take bukata Murmushi husnah tayi tace anty nan Yace kibani baby muyi hira Taga dagaske yake Tayi murmushi ta kashe wayar Sai da tagama taga anty kubra tazuba mata ido Kubra tace anya wannan Husnar ummace kuwa towai Husnah ina kunyar ne wannan soyayya haka ai sai kisa yakasa aikin Husnah tayi murmushi tace anty kenan wallahi tun inajin kunyar ya Hakeem wallahi har na daina Dan shi baruwanshi ko agaban waye baya kunyan nuna min soyayya Anty kubra tayi murmushi tace to ai gwamma dai da kika nuna mishi kema kwararriya ce fanni kula miji kar kiyarda kece zaki kunyar wasu Husnah tace wallahi anty kaman kinsan ni Wallahi Allah yagani tsoro suke bani kawai nuna musu nakeyi kaman bana jintsoronsu amma wallahi suna ban tsoro Anty kubra tace ai karkisake Susan kina tsoronsu Wato ita meenat din har yanzu bata sadudaba duk da irin jarabawar data gani na rayuwa Husnah tayi murmushi tace wallahi anty sai abinda yakaru inda kikasan zata kasheni agidan nan haka take min Dam tana tsoron daddynta ai da abinda zata min dayafi haka daga ita har uwarta Anty kubra tace ai sai kigodewa Allah ma mijin ki nasonki Husnah tayi murmushi tace ai ni wani zubin har tsoron nuna min son dayakeyi gabansu nakeyi Anty kubra tace inbanda abinki ai hakan shine zaisa duk sukone da ruwan jikinsu Nan dai anty kubra tayi ta bata shawarwari zaman duniya YOUNG PROF da Ahmad da ya shamsu sukayi sallama suka shigo falon Masu falon ne hakimce abinsu Suby da meenat suka gaishesu amma banda madam laila Direct dakin husnah suka shiga Wani kamshi ne yadoki hancinsu yasa farin ciki a zuciyar Hakeem yasan kadan daga aikin husnah bata zama ba kamshi Husnah cikin tsananin murna tace LA yaya shamsu daman harda kai kukazo shima ya shamsu Cikin tsananin farin cikin ganin 'yar kanwar tashi Yayi murmushi yace ai daman mamaki nakeson baki Sosai husnah take murna ganinsu Hakeem yace lalle ma baby wato kinga ya shamsu kin manta dani ko Ahmad yayi dariya yace kai Dan uwa wasane ballantana su biyu kawai Kokaima dakana da kanwa haka zaka nuna jin dadin ganin ta alokacin da kuka hadu bayan kun Dade Baku haduba Young prof yayi dariya yace wayafada maka duk shakuwarsu ai yanzu munfi shakuwa Dan nasan kozaba zatayi yanzu Ya mu'allim zata dauka Ya kalleta kobahakaba Queen dina Husnah tashi tayi tabar gurin zuwa dining Dan hada musu komai *********** Hajiya suwaiba tawa bokanta magana akan aikin datakeso yamata Shine yabasu tabbacin sai sun zo dakansu baya son aika Shiyasa da hajiya rukayya da hajiya rukayya suka shirya tafiya zuwa karbo maganin daza a wa husnah cikin yazube kuma ta haukace tabi duniya ****** Bayan wata daya da sati biyu a yaune ake sa rai da dawowar su daddy da mummy Husnah tagama gama hadawa su mummy abincin su mai rai da lafiya kusan kala hudu banda drinks kala kala Da su farfesun kaji gasunan dai Hajiya suwaiba da hakiya rukayya sundawo wajen satinsu uku kenan yau suke son aiwatar da nufin su akan husnah Husnah da Hakeem sungama shiryawa kasancewar ranar girkintane Har sunfito zasuje air Port dauko su mummy Sai taji kanta yasara mata tadafe kan nata Hakeem dake bayanta yayi saurin karasowa yakamata Yace yadai Queen tace kai nane yake ciwo Yace o to sannu kinji kizauna kawai zanje na daukosu amma barin kawo miki magani kisha kafinko Duk wannan abinda me faruwa a idonsu meenat Hajiya rukayya takashe mata ido daya Meenat ta tashi da sauri tace daddy kaje kawai zan kawo mata maganin Kaman daga sama yaji maganar abakin amina Kafin yayi magana wayar daddy ya shigo wayar Hakeem Hakeem yace sun sauka baby Husnah tace badamuwa kaje kadauko min mummy na nafi bukatar ganinta akan

Chapter 5 of 9