yace sosai ma dalibatace itada meenat da ita zan aura
Laila da suby suka dau salati suna kallon kallo
Hajiya rukayya kuwa zufa yajikata sharkaf
Saboda rashin gaskiya
Hakeem yayi murmushi gefen baki
Ya kalli husnah yace baby kinsanshi daman tace a copper ne a school dinmu
Yace daga bawani Abu takalli bash ta kalli meenat da jikinta yake bari
.tace bakomai bayan wannan
Bash yace karkice haka asmau nasan ban kyauta miki ba
amma Dan Allah karkice ba komai a tsakaninmu
Cikin bacin rai husnah ta kalleshi tace dan Allah malam dakata karkasake min maganar wani alaka
A ina nasanka da harwani Abu yashiga tsakaninmu bayan malami da dalibarsa
Bashir yazube gaban prof yace wallahi ba a hayyacina nafasa aurenta bansan meyake faruwaba
A lokacin ba abinda nake gani sai amina
Hakeem ya kalli husnah yace daman shine Wanda kike bani labari amina ma itace kawarki da kike bani labari
Tunda akafara maganar kuka baizowa husnah ba sai yanzu
Ta fashe da kuka data tuno da abinda suka mata
Dagudu tabar falon
Hakeem yakai kallonshi ga amina yace ke inason kifada min gaskiyar abinda kefaruwa bana son kimin karya kinsan halina
amina tafashe da kuka ta kalli bashir tace Dan Allah uncle kayafemin
Hajiya rukayya tace ke karkice komai tashi kitafi daki
Hakeem yace ba inda zakije sai kin amsa min tambayata
Cikin kuka meenat ta kwashe komai tafadamusu
Kunyar duniya hajiya rukayya da su hajiya suwaiba da laila sunshashi agun
Bashir yadago idonshi kaman garwashin wuta ya kalli meenat yace amina kuncuceni duniya da lahira
Ninasan dama duk abinda na aikata wa asmau
Ba a hayyacina na aikata ba
Ba abinda zance saidai nace Allah ya isa tsakanina dake da kakarki
Ya kalli Hakeem yace kamin aikin gafara wallahi bazan iya zama da amina a matsayin mataba
Nasaketa saki uku kuma a hayyacina nasaketa
Bana bukatar ta a ruyuwata
Ya tashi yay ficewarsa daga gidan baki daya
Hakeem yace kunga abinda kukajawa kanku ko
Yanzu wannan wani irin abin kunya ne haka
Yayi mun dai dai wannan shine hukuncin da yadace da ita
Kuma kunga dayake Allah ba azzalumin bawansaba ne kuncuci husnah kuna Ganin kunci bulus ko
To kunga aikin Ku saigashi duk abinda kuka yi nikuwa tanadi
Dan kuwa samun mata irin husnah a yanzu sai antona
Dole bash yamiki abinda yafi haka
Banga laifinshi ba Dan asarar mace kaman husnah bakaramin asara bane
Ya tashi yayi dakin husnah ya kullo kofar yanashi baiganta a faloba
Direct yawuce zuwa bedroom dinta
Ya hangota kwance kuka sosai takeyi kaman Allah ya aikota
Ya karasa yazauna dab da ita yakamo hanunta yace baby look in to my eyes
Husnah takasa kallonshi
Yace kukan mekikeyi
Tace bana son tuna abinda suka min ne
Saboda nashafesu a tarihin rayuwata
Yace idan hakane kidaina kuka
Kokinsan nigata suka min da bashir ya aureki ina zansameki baby
Kodaya banji haushin su ba
Saima godewa Allah da kuma hajiya rukayya
Duk abinda ta aikata karshe kan 'yarta yadawo
Dan haka kidaina kuka bana son kukan ki kinjiko
Tadaga kai sama yahau bed din dakyau yajanyota jikinshi yana shafa bayanta yace kokinsan bashir yasaki amina yanzu
arazane Husnah ta tashi tace meyasa zaisaketa bayan komai yawuce
Allah yabani Wanda yafishi
Baikamata yayi hakaba wannan ai cin amanar soyayya ce
Hakeem yamaida ita kan kirjinshi yace ai dama soyayyarsu bata Allah da annabi bane
Naji dadi dayawa amina wannan sakin
Hakan shizaisa tagane abinda yake dai dai
Tadaina bin zugan kakaninta Dana uwarta
Idan amina ta nutsu tagyara halinta
Zan maida ita makaranta insaku tare kucigaba da zuwa school dinku kamar yadda kuke da
Husnah tayi murmushi ta kara rungumeshi sosai tace idan kamana haka zamuji dadi sosai Allah yasaka da alkairi
Allah yakara daukaka da arziki mai amfani yakara mana lafiya yabaka ikon ciyar damu da halak
Yakara wa su mummy da daddy Nisan kwana da lafiya
Hakeem cikin tsananin son matarshi ya kara kankameta sosai a kirjinshi yace adduoinki agareni suna sani nishadi
Dani da su mummy duk muna alfaharin samun ki cikin rayuwarmu
Husnah tace Dan Allah sweet karkace zaka matasawa meenat
Kabarta na tabbatar zatayi nadama abinda tayi
Hakeem yace kedai kice kina bin bayan kawarki ko
Husnah tayi murmushi tace tun bayan rabuwata da meenat bansake wata kawaba daman nima bamai son tarin kawaye bane
Naso meenat zuciya daya itace dai tadaukeni da guda biyu
amma koyanzu takeson mucigaba da zumuncin mu
Ina son haka saboda ina son meenat sosai
Hakeem bai barta tacigaba da maganartaba yahada bakinsu guri daya
Nan fa wasa yacanja salo
Gashi ankusa kiran magriba kuma ba itace dashiba
Tayi kakorin kwatar kanta amma takasa tashiga hanun maza sosai Hakeem yafara fita a hayyacinsa yana kokarin rabata da kayan jikinta
Husnah tayi tunanin idan tabari fa ba takyauta Dan anshiga hakkin uwargida
Cikin kuka Husnah tafara wash Allah cikina cikina
Cikin sauri Hakeem yafara tambaryata meyasameta tace cikina nane yake ciwo
Dasauri yasauka daga kan bed din Dan dauko magani husnah naganin yafita ta tashi dasauri tashiga bathroom
Tasaka key
Yadawo yaga wayam bata kan bed murmushi yayi yace zan kamaki
Kifito nayi alwala kinga zantafi masallaci Husnah tace naki wayon kaje dayan bedroom din kayi acan
Murmushi yayi yasan idan zai biye mata bazata budeba
Meenat zaune gaban uwarta da kakanta kuka sosai takeyi
Laila tace duk abin ma ai kaina yadawo niyakama ta ace ina kukan bakeba
Hajiya rukayya kuwa cewa tayi share hawayenki Dan yasaki ke
ai bashine karshen mazaba
Dan haka kiyi shiru miji sai kin ce bakya so
Keda ba mummuna ba
Meenat tace wallahi ina son shi gashi harsaki uku yayi min
Yazanyi nayi rayuwa ba bashir
Husnah kincuceni bazan taba yafe miki ba sai na dau fansar abinda kika min
Laila tace dakuwa kincika 'yar halak mekishin kanta ban amince kibarta tasha ruwaba agidan nan zanso kizama kece kishiyarta baniba uwarki zan nuna mata ina da kamarki
Hajiya suwaiba tace gaskiya ne idai kujininane ban amince kubar maganar nan ba
Tunda saboda ita aka sakeki
Itama inason saboda ke ubanki yasaketa
Nan sukaci gaba da mummanar shirunsu
Hakeem yafito daga dakin husnah yayi waje batareda ya kallesuba
Husnah kuwa sai da ta tabbatar yafita kafin tayi alwala tayi sallarta hade da adduointa
Ta dauki alkuraninta tafara karantawa har aka kira isha
Kafin ta ajiye tayi sallarta
Tana idarwa ta ninke kayan sallarta tashiga bathroom tay wanka kafinta fito tashirya cikin wasu Riga da skirt din atanfa dinkin yayi matukar zama ajikinta tafesa turararukanta
Tayi parking din gashinta
Tadaura Dan kakwalin ta das kaman wacce aka dasa akanta
Tasake gyara dakinta kafin tafito falonta
Daman kafin Hakeem yakirata tagama abincinta mai rai da lafiya
Couscous ne tadafa fari da miyar kaza
Sai zobo drink mesanyi
Wanda yasha flavour masu kamshi
Da yakan kamshin
Nan tadauki plate tadeba abincinta tasa miya
Tadauki Dan karamin glass jug tazuba zobonta aciki
Taduki karamin cup tayi waje
Main falon gidan taje center table tajawo ta ajiye kayan abincin ta akai kafin tazauna zaman ci
Bakowa afalon sai TVdake kunne
Can saiga su sunfito gabadayansu kowa tanemi kujera tazauna
Husnah tace barkanku da fitowa
Duk zuba mata tsaki
Husnah ta kallesu tace to Ashe abin nan
To Allah yasauwake
Tacigaba da cin abincinta
Can sai mai aikin laila tace anty nashirya dining din
Laila tace jeki kawasu nan muna a nan zamuci
Husnah tayi murmushi batace komaiba
********
Bayan wata hudu meenat tadade da gama iddarta da kusan watadaya kenan
Kuma a kano tayi iddarta yau take shirin komawa Kaduna gidan ubanta
Dan tadau matakin datake da niyar dauka akan husnah
Tuni driver yadukota zuwa kaduna
Laila tuni tasa angyara wa meenat dakinta
Komai yaji
Ita kawai dakin yake jira
Husnah kuwa yau ta tashi da kewan gidansu ne
Tunda tayi aure sau biyu taje
Kuma bai barta takwana ba
Yau tafita girki tana zaune kusa Hakeem tana mishi rigima ita sai yabarta taje takwana biyu agida kuma yau takeson tafiya
aikin dayakeyi a computer ma kasawa yayi
Ajiyewa yayi gefe yakamota yace baby bakya tausayina kinsan bazan jure rashinki kusadani bako
Husnah tasake shagwabewa
Tace aishiyasa nace natafi yau jibi da yamma insha Allah sai na dawo
Kaga yau dagobe bani bace da kai antyna ce
Hakeem yace kedai kimin wayo ne kawai tashi kishirya
Sainasa driver yakaiki
Jibin zanzo na daukoki yau muna da meeting ne
Inkuma zaki bar tafiyar sai gobe to saina kaiki da kaina
Husnah tayi saurin cewa a a kaje meeting dinka kawai
Yayi murmushi yace wato murna kikeyi zaki barni harna two days ko
Husnah tasa hanunta a kumatunshi tace mezaisa nayi murnar barin minjina abin alfaharina
Hakeem yashafa cikinta Yakama ta muje aduba min kefa
Ina son yara baby yaushe zaki Haifa min yara masu kyau kamarke murmushi husnah tayi tace nikuma masu kaman kai nakeso su dauko
Yace dagaske kikeyi tadaga alamar a
Yace sai kidage sosai kinsan abin kokarine
Tabashi full attention dinta Dan yamata bayanin yadda kokarin yake
Yace kina son sanin yadda zakiyi 'ya'yan my suyi kama dake tace a
Yace OK yatashi yacire singled din jikinshi itadai husnah dai kallonshi takeyi da zuciya daya bata kawo komai aranta ba
Gani tayi yacire mata Dan kwalinkanta aikuwa ta gane meyake nufi
Cikin shagwaba tace wallahi nabar maka suyi kama dakai kawai
Hakeem yace a a kibarni kawai nayi kokarina Dan insamu mai kama dani kuma kice kinyafe
ai kokarin danake nufi kenan
Kibani hadin kai sosai kigani inbazaki samu masu kama dani ba
Husnah dai talura da gaske fa yake
Tace shine abinda kake bukata yace yes my Queen
Tace OK ina zuwa barinsha sha ruwa a fridge zanbaka mamaki yace really tace yes
Bani minti daya naje nadawo
Tasamu tamishi wayo tagudu shiru shiru bata dawo ba yatashi tafita zuwa part dinta
Yaga har ta fito daga wanka ma tana drying gashinta da hand drayer
Hanu yasa a kirji yace kimin lefi kinshiga min aiki tunda kinsan ina gida aikina nane namiki komai
Husnah tadago suka hada ido tasan bakaramin aikinshi bane yasata sake wanka yanzu
Karasowa tayi cikin shagwaba ta kwantar da kanta a kirjin tace na tuba my prince Dan Allah karka bata min wanka na wallahi dokin ganin umma yasa nake sauri
Hakeem yace ban yarda ba saikin min Abu daya
Tace mezanma
Yace kekisani murmushi husnah tayi tasan idan yafara haka rigima yake nema
Tace OK kan bed tahau taga Kansu yazo dai dai tahada bakinsu guri daya
Sosai take kissing dinshi Dan tasan abinda yake bukata kenan
Batayi aune aune ba taganta yakwantar da ita duk yadda taso yakyaleta yaki
Sai daya samu nutsuwa kafin yabarta
Cak yadauketa tare sukayi wanka suka shirya
Dakanshi yahada mata kayansawarta kala biyu cikin wani Dan karamin jaka mai kyau da sha'awa
~~~~~~~~~~
Husnah kwance falon ummanta kanta akan cinyar umma suna hirarsu
Anty kubra ta shigo falon tace kinsan Allah husnah kikiyayeni fa zaki karyamana cinyar umma ne katuwa dake
Husnah tayi murmushi tace to kwana nawa bangantaba banga ya shamsu ba
ai dole na damu nayi kewarsu saura ya shamsu zaizo shima yasameni yamin alkawarin zai dinga zuwa sosai yana ganina Amman bai cika ba
Husnah tace wallahi danwake zanci da dambu da kuma tuwan alkama
Kubra ta rike baki duk acikin ki kekadai tace sosai makuwa
amma dai yanzu tuwon nake bukata tukun
Anty kubra tace OK bani minti na muna da miya daman tuwon kawai zanmiki
Husnah tace yauwa matan yaya daga ke bawata
Husnah taci tuwo sosai umma da kubra sunyi mamakin
Umma dai murmushi tayi itakadai tasan dalilin murmushinta
Duk abinda takeso shi ake mata agidan su
Yaya shamsu kafin yadawo sai yatambayeta abinda take sha'wa ya taho mata dashi
Ranar da zata tafi tun azahar YOUNG PROFESSOR ABDUL HAKEEM ABUBAKAR
Ya isa kano gidansu husnah yazarce direct danshi jinshi yake kaman bashi da lafiya Dan kwana biyun datayi bata nan
Saida yaci abinci agidan shida ya shamsu kafin suka wa ummu sallama suka fito suka dau hanya
Hakeem yakasa boye zalamrsa akanta saida. Yayi parking a gefen titi
Komeyasa oho
Suna isa Hakeem yayi parking yazago yabude wa husnah kofa duk abinda kefaruwa a idon meenat da suby Dan suna lambun gidan suna hutawa
Takaici Yakama meenat tace wallahi anty suby danasan husnah zata auri daddy Dana wallahi da banbar hajiya taje gurin maganin ba
Yanzu gashi nibada bash itakuma da auren ubana har bayaganin kowa sai ita
Suby tace ai wallahi zamu koya mata hankali basu rufe bakiba Hakeem yadauko bag din husnah da Yakama hanunta suka shiga ciki
Suna zama husnah ta ce wayyo Prince zansha nun tsamiya zansha kuma nagaji dayawa beside ni idan nayi ma balle nashaba
Cikin sauri yazauna kusada da ita yace kobakida lafiya ne Dan naga kincan minfa sosai
Hanu takai ta lakuce hancinshi tace nidai ba abinda yake damuna
Kawai kasamomin kunun tsamiya
Waya yadaga yakira Ahmed yace kana gidane yace a
Hakeem yace kasa Aisha ta min kunun tsamiya zanzo na dauka
Kafin Ahmad yayi magana Hakeem yakashe wayarshi Dan yasan sai yamishi tsiya
Hakeem yajuya yaga hartafara bacci a mota gabadaya ma baccin tayi
Tashi yayi yamatsa kusa da yakura mata ido sosai
Can zuciyarshi tace anya yarinyar lafoyarta kalau kuwa
Yadauki waya yakira family doctor dinsu macen yace tazo da kayan aikinta
Yafada mata abinda yake zargi tace OK tagane gatanan zuwa
Hakeem cikin tsananin farin ciki yayi sujjadar Allah yatabbatar mishi da abinda yake zargi
Next page
Your comments is needed fans
Love all
πππππππππππ
[05/05, 10:18 PM] UMMU AFAN πΉ: πππππππππππππππ
ππππππ
πππππ
ππππ
πππ
ππ
π
BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM
Story & written
By
The special writer
UMMU AFAN
πππππππ
πΉFIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATIONπΉ
πΉπΉ (F.C.T.W.A)πΉπΉ
πΉHOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATIONπΉ
πI DEDICATE THIS PAGE TO YOU Aisha Ibrahim ina matukar jin dadin comment din ki wallahi keep it up ina alfahari dake over my sister πππππππ
πAKWAI LOKACI π
πPAGE 143 to 145π
Bayan gwaje gwaje da likita tawa Husnah ta tabbatar mishi husnah tana dauke da cikinshi
Cikin tsanin farin ciki hakeem yace alhamdulillah Allah nagode maka da cika min burina cikin gaggawa
Allah kasauketa lafiya likita tayi murmushi tace gaskiya wannan babyn zaiga gata prof irin wannan doki da murna haka
Yayi murmushi tare da rungume husnah ajikinshi tunda likitar tafada cewan ciki ne da ita
Ta rufe Idan kaman me bacci
Ita kanta takasa sanin meyasata jin kunyar
Hakeem yace wa likita kizuba ido kiyi kallo aranar da Queen dina ta haifamin baby a ranar zan yi abinda za bakowa mamaki
Kuma kema fa baza abarki ba zaki ga goron albishir a account din ki
Likita tayi murmushi tace kai amma nagode Allah yafito mana da wannan babyn lafiya
amma Yakama ka kawota hospital gobe Dan mumata scanning a tabbatar cikin wata nawa ne Dan kasan lokacin da zakafara tsammanin babayn ka
Hakeem yace ai bazan bari sai gobe ba yanzu zamu biki muje Nagani da idona
Doctor tayi murmushi tace ina jiranku to
Hakeem cak yadauki Husnah zuwa bedroom yasamata kataton hijabinta
Sannan kuma ya sunkuya wai ta hau baya
Husnah taga dagaske yakeyi fa
Taware tace a a Dan Allah Prince kabarni maka ganin bamu kadai bane
Hakeem yace ai ni mutane da maganarsu bai cika damuna ba ko agaban mummy zan iya goyanki ballantana 'yata
Husnah tace naji inkai bazaka ji kunya ba aini zanji
Ta kwasa dagudu tabar dakin
Yafito hankalinshi a tashe yace Dan Allah baby kidaina gudu karki samin baby yagaji
Husnah tatsaya cak taki juyowa
Ya tako ya iso har gurinta yajanyota jikinshi yace oya mutafi ko kinga doctor tana jiranmu a waje
Cikin shagwaba husnah tace tun ba aje ko ina ba kafara nuna min iyakata ko
Shine zaka ce wai kar babyn ka yagaji
Wato ma bani bace damuwarka babyn ne ko
Cikin murmushi Hakeem yajuyo da ita suna fusakanta juna yace Haba baby kema kinsan you are my one and only
Taya za ayi nace bandamu damu da lafiyarkiba
ai dake da abinda yake cikin ki
Inkincire mummy da daddy to kune rayuwata kune komai nawa
Husnah tace nidai banyarda ba
aikuwa sai ganin prof tayi gwiwa biyu agabanta
Cikin sauri itama tayi kasan takama hanunshi tace la nifa wasa nakema
Yayi murmushi yaja hancinta yace kinji tsoro kenan tace sosaima wace dasa zuciyata kneeling a kasa ai dole tsoro yakamani yayi murmushi yatashi yadagota cak
Dakyar tabashi hakuri yabarta ta tayi tafiya da kanta
Bayan scanning da akayi wa husnah aka ta babbatar musu da tana dauke da cikin sati bakwai wato getting to two months kenan
A gurin Hakeem yadauki wayarshi yakira mummy da daddy yasanar dasu
Mummy kaman tayi tsuntsuwa tazo taga 'yarta husnah haka take ji
Tayi murna sosai haka ma daddy
Dan mummy hafsat kam ma cewa tayi tundaga can zata fara sayayyar kayan jarirai
Daga hospital sai gidan su Aisha da Ahmad Hakeem yayi dasu
Suna zuwa kuwa Aisha takawo mai kunun tsamiyar dakan yazauna kan carpet ya hada mata sosai tasha kuwa duk sunyi mamaki
Ahmad yace amma natayaka murna abokina Allah yaraba lafiya
Aisha da itama haihuwar ko yau ko gobe
Tayi murmushi tace Allah sarki 'yar kanwata Allah yasaukemu lafiya ko
Husnah tace anty nifa bani da komai
Wasa fa yaya yake muku
Aisha da dariya yaso barke mata tace sosai Nagani kuwa
Wannan tulun kunun da kika shanye ai kowa yasan bake kadai bace
Husnah tayi murmushi tace ai saboda ina sone shiyasa
Hakeem yace sannu da kokari madam kema kina fama da kanki mun hada kida aiki
Tace bakomai wallahi bana ma son zaman
Nan Ahmad da Hakeem sukafita
~~~~~
Bayan sati biyu duk wannan abinda kefaruwa na maganar cikin nan baizo kunnen su Laila ba
Husnah zaune a falonta mai kamshi da sanyun Ac
Kaman daga sama taji murya kaman na anty kubra
Da sauri ta tashi taduba anty kubra ce kuwa tasha kyau cikin wani tsaddan less Dan shima ya ashamsu yanzu kudi yazauna mishi sosai shiyake juya dukiyar husnah Wanda tabashi ragamar komai a hanunshi
Kuma shiyazama manager a company Hakeem
Husnah tayi tsalle ta rungume anty kubra tace wayyo anty na wallahi naji dadin ganin
Anty kubra tace kai Husnah bakida hankaline wayafa miki meciki tana tsalle haka husnah tarufe ido tace anty nifa banida komai
Kubra tace ai Allah zata sake magana husnah taja sukayi part dinta
Laila dake zaune jin abinda anty kubra tace
Ya mugun daga mata hankali sosai
Tace kai ina karya ne wallahi ba zaki taba haihuwa gidan nan ba matsuyaciya
Meenat ce tafito daga part dinsu
Dauke da glass cup a hanunta na drink
Sai mummynta na hawaye
Sai Takaraso a tace meyafaru kuma mummy
Suby tace wannan 'yar talakawar ce wai cike ne da ita
Meenat batasan sanda tasaki cup din hanunta ba
Tace karya takeyi wallahi bata isa ta haifi wannan Dan iskan cikin nata agidan nan ba
Tayi hanyar dakin husnah suby tayi saurin tarota tace inazaki
Meenat kibarni naje anty suby wallahi sai namata dukan dazaisa cikin yazube inga tafadi
Suby tace idan kikayi haka daddynki zai dauki babbar mataki akanki
Kibari mubiyo musu tabayan gida
Ina tabbatar muku husnah bazata haifi cikin nan ba
Nan dai suby taringa basu shawarwari
Husnah takawo wa anty kubra gashashshan namar kaza da drink saikuma fruit
Ta zauna kusada anty kubra
Anty kubra tace anya wannan husnah ummace kuwa
Kinganki kuwa kinyi fresh dake kaman ba mai cikiba
Husnah tayi murmushi kafin tayi magana wayarta yayi kara tana dubawa taga Prince ne cikin shagwaba ta amsa sallamar
Anty husnah baki kawai tasake tana kallon husnah yadda tazage tana soyayya da mijinta ba alamar kunya cikin kawarewa da iya wa Hakeem yace to ya antyn mu
Husnah tace LA ya akayi kasan tazo yayi murmushi yace karkidamu ki isar min da gaisuwa na kafin mukaraso yanzu
Husnah tace kukaraso kaida wa kuma
Yace naki fada yayi murmushi yace bani baby na muyi hira naji abinda take bukata
Murmushi husnah tayi tace anty nan
Yace kibani baby muyi hira
Taga dagaske yake
Tayi murmushi ta kashe wayar
Sai da tagama taga anty kubra tazuba mata ido
Kubra tace anya wannan Husnar ummace kuwa towai Husnah ina kunyar ne wannan soyayya haka
ai sai kisa yakasa aikin
Husnah tayi murmushi tace anty kenan wallahi tun inajin kunyar ya Hakeem wallahi har na daina
Dan shi baruwanshi ko agaban waye baya kunyan nuna min soyayya
Anty kubra tayi murmushi tace to ai gwamma dai da kika nuna mishi kema kwararriya ce fanni kula miji kar kiyarda kece zaki kunyar wasu
Husnah tace wallahi anty kaman kinsan ni
Wallahi Allah yagani tsoro suke bani kawai nuna musu nakeyi kaman bana jintsoronsu
amma wallahi suna ban tsoro
Anty kubra tace ai karkisake Susan kina tsoronsu
Wato ita meenat din har yanzu bata sadudaba duk da irin jarabawar data gani na rayuwa
Husnah tayi murmushi tace wallahi anty sai abinda yakaru inda kikasan zata kasheni agidan nan haka take min
Dam tana tsoron daddynta ai da abinda zata min dayafi haka daga ita har uwarta
Anty kubra tace ai sai kigodewa Allah ma mijin ki nasonki
Husnah tayi murmushi tace ai ni wani zubin har tsoron nuna min son dayakeyi gabansu nakeyi
Anty kubra tace inbanda abinki ai hakan shine zaisa duk sukone da ruwan jikinsu
Nan dai anty kubra tayi ta bata shawarwari zaman duniya
YOUNG PROF da Ahmad da ya shamsu sukayi sallama suka shigo falon
Masu falon ne hakimce abinsu
Suby da meenat suka gaishesu amma banda madam laila
Direct dakin husnah suka shiga
Wani kamshi ne yadoki hancinsu yasa farin ciki a zuciyar Hakeem yasan kadan daga aikin husnah bata zama ba kamshi
Husnah cikin tsananin murna tace LA yaya shamsu daman harda kai kukazo shima ya shamsu
Cikin tsananin farin cikin ganin 'yar kanwar tashi
Yayi murmushi yace ai daman mamaki nakeson baki
Sosai husnah take murna ganinsu
Hakeem yace lalle ma baby wato kinga ya shamsu kin manta dani ko
Ahmad yayi dariya yace kai Dan uwa wasane ballantana su biyu kawai
Kokaima dakana da kanwa haka zaka nuna jin dadin ganin ta alokacin da kuka hadu bayan kun Dade Baku haduba
Young prof yayi dariya yace wayafada maka duk shakuwarsu
ai yanzu munfi shakuwa Dan nasan kozaba zatayi yanzu
Ya mu'allim zata dauka
Ya kalleta kobahakaba Queen dina
Husnah tashi tayi tabar gurin zuwa dining Dan hada musu komai
***********
Hajiya suwaiba tawa bokanta magana akan aikin datakeso yamata
Shine yabasu tabbacin sai sun zo dakansu baya son aika
Shiyasa da hajiya rukayya da hajiya rukayya suka shirya tafiya zuwa karbo maganin daza a wa husnah cikin yazube kuma ta haukace tabi duniya
******
Bayan wata daya da sati biyu
a yaune ake sa rai da dawowar su daddy da mummy
Husnah tagama gama hadawa su mummy abincin su mai rai da lafiya kusan kala hudu banda drinks kala kala
Da su farfesun kaji gasunan dai
Hajiya suwaiba da hakiya rukayya sundawo wajen satinsu uku kenan yau suke son aiwatar da nufin su akan husnah
Husnah da Hakeem sungama shiryawa kasancewar ranar girkintane
Har sunfito zasuje air Port dauko su mummy Sai taji kanta yasara mata tadafe kan nata
Hakeem dake bayanta yayi saurin karasowa yakamata
Yace yadai Queen tace kai nane yake ciwo
Yace o to sannu kinji kizauna kawai zanje na daukosu
amma barin kawo miki magani kisha kafinko
Duk wannan abinda me faruwa a idonsu meenat
Hajiya rukayya takashe mata ido daya
Meenat ta tashi da sauri tace daddy kaje kawai zan kawo mata maganin
Kaman daga sama yaji maganar abakin amina
Kafin yayi magana wayar daddy ya shigo wayar Hakeem
Hakeem yace sun sauka baby
Husnah tace badamuwa kaje kadauko min mummy na nafi bukatar ganinta akan