Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 9
tace tabbas basobane sai yanzu nasan soyayya anty na amma tazo min a inda bai kamaceni ba Husnah tayi murmushi tace indai tayi wari maji ai Meenat tayi murmushi tace seson gulma Husnah tayi murmushi tace bakida kunya ko wace meson gulmar meenat tayi saurin kama kunne tace am sorry my mum Husnah tace an miki afuwa Tayi kamar bazatayi da dariya ba sai kuma suka kwasheda dariya gaba dayansu Hakeem ne yashigo falon da sallama ganin suna dariya yace dariyan me kukeyi Kuncika wa mummy kunne Meenat ta tashi da sauri ta karbi brief case dinshi tace sannu da dawowa daddy yace yauwa 'yar daddy Dariyar mekuke keda antyn taki Meenat tace wallahi daddy abincin data ci yau muke kirgawa ga kuma dashishi mummy tamata yanzu tana kan ci Hakeem ya kalli husnah datake cin abincinta bata kulashi ba saboda yayi laifi yau kafin yafita tace yabarta taje taga ummanta ya hanata Murmushi Hakeem yayi yasan fushi takeyi Meenat ta wuce zuwa can part din daddynta takai mishi jakar Hakeem yamaka mata kallon so Matsawa yayi gabanta yadauke plate din abincin Cikin shagwaba ta tace kabani abincina Yace anki abaki meyasa baki min sannu dazuwa ba Tace yau she kashigo aini bangan kaba ma Yanayin yadda take maganar yamatukar bawa Hakeem dariya yazauna kusa da ita yace mama food Inga cikin naki wai a ina kike ajiye abincin ne Husnah tajuya kai abinta batason hirar Hakeem ya janyota jikinshi yace baki huceba Tayi shiru Yace shikenan ina dai kano ne kishirya gobe kaiki Bata San lokacin data dada rungumeshiba Dan tama manta inda take Tace yauwa my Prince kokaifa wallahi har naji dadi sosai Cikin shagwaba tayi fari da idonta tace amma naga yau kadawo da wuri lafiya kuwa Yayi murmushi yace nazo mugaisa da babyna nane Husnah tasan irin gaisawar dayake nufi Dan haka kawai watarana idan taraya mishi zaibar office yadawo gida ya fitineta Murmushi husnah tayi tace naki wayon wannan gaisawar taka Hakeem yakalleta Wanda idonsa tuni yacanja kala Yace nima kuwa nafasa zuwan naki kanon tunda hakane yayi murmushi Mummy tasauko daga sama tace a a Ashe Kaine Hakeem yace a mummy wannan acicin ne Mummy tayi murmushi tace wayafada maka son kanta ne yasa take cin abincin dayawa ai dankane yake sata cin Hakeem yayi murmushi Mummy tace katashi kaje dining mana akwai abinci Hakeem dashi kadai yasan meyadawo dashi gida Yace wa mummy zanyi bacci tukun nadan huta kafin abincin Mummy tace afito lafiya to Hakeem yatashi yanasatar kallon Husnah Yaga dai bata daniyar tashi tabiyoshi Yace kizo kibanin number din inason nakirasune Husnah taji mamakin wannan karya daya mako Mummy tace tashi kije kibashi number idan kindawo saiki karasa ci kisha magani Husnah tace to atare suka fito Mummy tayi murmushi tace kai wai kahaifi 'da acikinka yace zai maka wayo Allah yadada zaunar Ku lafiya yabaku zuri'a tagarai aini idan duk shekara Husnah zata Haifa maka 'da Son murna zanyi naga gidan koina da jikokina Mummy nata zancen zucinta meenat tazo tazauna tace Uwargida sarautar mata Mummy hafsat tace to sarkin surutu kinfito meenat tace nafito wai yaushe wannan tsohon zai dawone Mummy hafsat tace kinga wallahi kifita a idona dacewa mijina tsoho Meenat tayi murmushi tace tsufa kuma aikungama tsufa nan sukayuta dariya Hakeem kam yanashan yana hutawa kamar yadda yacewa mummy Bayan sunfito daga wanka ne suna zaune akan resting chair dake bedroom din Hakeem husnah kwance kan kirjinshi yana shafa gashinta itakuma tana wasada gashin kirjinshi Yace sai kitashi muje kimusu shopping ko Husnah tace a a wallahi kabarshi karyazama barnar kudi tunda ba adade da kaimusu tsaraba ba Hakeem yayi murmushi yace ba abinda zanwa su umma yazama barnar kudi Dan Wallahi banajin ban bancin umma da mummy agareni Dan haka kidauka nima umma mahaifiyatace yadda kika dauki mummy na amatsayin uwa nima haka umma take agurina Husnah tace banida bakin dazan gode maka akan yadda kake kula da mu gabadayanmu Allah yakara arziki my Prince Hakeem yace nifa banason wannan godiyar da kike min Dan komai nawa nakine kina da damar dazakiyi yadda kikeso da komai nawa nariga nasa hanu Nan dai suka shirya sukatafi shopping Sai dare suka dawo Washagari meenat tace itama zata Hakeem yace tashirya suje suyi kwana biyun Husnah taji dadi kuwa dazuwan meenat ***** Sun isa kano wurin la'asar Ya shamsu da anty kubra suka taresu suna murnar ganin su Meenat tadurkusa har kasa tagaida ya shamsu Yace a a mutanen Kaduna yasu mummyn meenat tace lafiya kalau suke Husnah tace kai anty kubra wannan irin kyau wallahi komawa baby kikeyi Anty kubra tayi murmushi tace keba kiga yadda kika koma ba ko Anty kubra ta ruko hanun meenat tace meenat sannun dazuwa kinji husnah ta tareni dashirme hanun meenat rike da hanun anty kubra suka Shiga Umma tayi murna sosai da zuwansu Abinci kala kala a ka saukesu dashi Meenat dai takasa sakewa kwatata Washagari husnah nazaune a falo itada umma meenat da anty kubra kuma suna kitchen suna abinci Sungama suka jera komai kafin nan kuma kowacce tawuce wanka Meenat dakin dasuka sauka tawuce Itada husnah ne dakin anan suka sauka Bayan salar isha abba da yashamsu sunshigo husnah sai shagwaba takeyi yadda ranta yakeso kowa naji daita anzauna za afara cin abinci Sai umma tace Husnah tashi kikira amina tazo taci abinci itama cikin mutane Narasa takasa sakin jikinta ai komai yawuce tunda anzama daya Husnah ta tashi zataje kiran meenat Kubra tace zauna abinki zankirata anty kubra ta na Sakai cikin dakin tadawo dabaya tatsaya turus Kunnenta takunnenta sosai Meenat dabatasan anshigo ba tace ya Allah narokeka kacire min son Wanda nasan bazan taba samunshi ba ya Allah nasan ya shamsu yafi karfina Ba abinda zaiyi dani yana da mata kamar wacce yake da ita Nasan yafi karfina ya Allah kai kajarrabeni da kaunarsa Allah ka yaye min Allah natuba Allah kacire minshi acikin arayuwata ya Allah Tana kuka mecin rai Anty kubra kasa jurewa tayi cikin tsananin tashin hankali tajuya zata koma dabaya Sai kuma tayi tunanin to idan antambayeta mezatace Sai kawai ta daure tashiga dakin aikuwa meenat naganinta tace sannu anty Kubra tace yauwa kanwata kifito muci abinci kinji Meenat tayi murmushi tace to anty Da daddare anty kubra kasa bacci tayi tana ta tunanin abinda kunnenta yaci mata Can tayi tunin haba kubra kiduba fa gidan nan basu da wadatar yara umma zataso taga 'ya'yan shamsu amma bawanda yataba maganar rashin haihuwarta kowa nuna mata kauna yakeyi Kuma tabbas sunje asibiti an tabbatar itace da matsala Dan meyasa zata zama meson kanta dayawa Yakama itama tarama hallacin da mijinta da iyayenshi suke mata arayuwa Kuma ai meenat ta shiryu ta tabbatar zasuyi zama na girmama juna Sai dai kuma ta yaya zata hada wannan Abu bayan tasan balalle bane su amince mata Juyawa tayi takalli yaya shamsu dayake baccinsa Take tausayinsa yakamata tasan yana balain son yara Kuma gashi ita bata halin bashi wannan farincikin Tana da yakinin ya shamsu bazai taba juya mata baya ba koda ya auri meenat ta Haifa mishi yara Tayi murmushin dole tace meenat Allah zaibaki abinda kikeso fatana Allah yasa muzauna lafiya Kubra ta Dan taba ya shamsu kadan yatashi yace a a honey mekike yi baki kwanta ba Tace katashi muyi magana Dan Allah Dayake ya shamsu yana matukar bawa kubra muhimmanc acikin rayuwarsa Yatashi yace Allah yasa lafiya kubra tayi murmushi tace Alkairi nema Next page Your comment is needed Fan's Love you all πŸ“πŸ“πŸ“πŸ“πŸ“πŸ“–πŸ“–πŸ“–πŸ“–πŸ“– [06/05, 11:18 AM] UMMU AFAN 🌹: πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ— BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Story & written By The special writer UMMU AFAN πŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ“š 🌹FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION🌹 🌹🌹 (F.C.T.W.A)🌹🌹 🌹HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION🌹 πŸŽ—I DEDICATE THIS PAGE TO YOU MAMAN MUFIDA Ina alfahari dake wallahi kina kasheni da wannan nice comments din naki Allah yabar kaunaπŸŽ—πŸ˜˜πŸ˜˜πŸ˜˜πŸ˜˜πŸ˜˜ πŸŽ—AKWAI LOKACI πŸŽ— πŸŽ—PAGE 153 to 155πŸŽ— YA SHAMSU yace inajinki honey Kubra tace wallahi inasha awar naga yara agidan Koda kuwa bani zan haifesu ba inason ganinsu Ya shamsu yace bangane mekike fada ba kubra Kubra tace nazauna nayi tunani Halaccin da kukayi min a rayuwa Dan me nima bazanso abinda zai faranta ran ka Dana su umma ba Wallahi koba afadamin ba nasan yadda kakeson yara Koba kaiba ma su umma fa girma ya kamasu zasuso suga yaranka kafin sukoma ga mahallincinsu Saboda son dasukeyi min da nuna kulawa agareni yasa bantaba jin umma tayi magana akan rashin haihuwataba Kuma nasan dole abin zai dameta Kaga idan har nacika masoyiyarka ta gaskiya dole ne nayi kokarin ganin farin ciki arayuwarka idan har INA da damar hakan Ya shamsu yace duk meyakawo wannan maganar kubra mekike nufi kenan Kubra tace ina nufin kayi aure Dan Allah muna bukatar muga yara acikin gidan nan Dan Allah karki yadda da bukatuna Kayi tunani mai kyau akan magana bakai zaka duba ba su umma zaka duba Ya shamsu Wanda mamakin kubra yakeyi tubaran Yace anya kina cikin hankalinki kuwa kubra Meyasameki Bantaba ganin macen datake jawa kanta kishiya ba saike Kokuma kindaina sonane yasa kike fatan nakawo wata cikin rayuwarmu Please banason sake jin wannan maganar a bakinki Dan Allah bana samum sabani dake amma akan wannan zan baki mamaki Kubra tasauka kasa tazuba gwiwarta akasa tana kuka tana rokanshi akan yacika mata burinta Yaga abin nata ma dagasake ne yafita daga dakin yakoma dayar dakin yasaka key Kubra kuwa ganin yabar mata dakin Yasa tama rasa tunanin dazatayi ahaka bacci yadauketa rana nafarko dasuka fara raba shimfida kenan da mijinta Washagari da safe bayan sungama karyawa meenat tace zata ta kwanta Dan tana komawa baccin safe falon yarage daga husnah sai umma sai anty kubra Umma ta lura da kubra yau kaman bata lafiya takasa yinshiru tace khadijah lafiya kuwa Kubra tayi murmushi tace umma ina da magana amma keda Abba nakeson magana daku Umma da husnah suka kalli juna Dan basu taba ganin kubra cikin wannan halin ba Umma tace to kutashi mutafi can falon abban naku sai kiyi maganar acan Tare umma da kubra suka wuce sukabar husnah da damuwar rashin sanin maganar da kubra zatayi Can husnah tace kodai fada sukayi da yaya shamsu Tace haba ya shamsu me anty kubra zata maka da har zai kasata adamuwa irinhaka Haka ta tashi ta wuce part dinsu anty kubra tanazuwa tasamu ya shamsu a falo yana kwance fuskarshi nakallon sama husnah tashiga Husnah tayi sallama ya shamsu ya amsa tare dayin yaken dole Husnah tace ya shamsu wai meke faruwa kaida anty kubra ne Yatashi da sauri yace tafada miki wani abunne Husnah tace a a amma yau bata cikin walwala kuma tace tanada magana da Abba Ya shamsu yace ita kubaran yanzu tana ina husnah tace suna falon Abba Dasauri ya shamsu yafita yayi hanyar falon Abba yanazuwa yace kubra wai meyasa bakya jin maganane Dan Allah Abba yace karaso mana ubana yafi nakowa sham sudden Ya shamsu yashiga yasamu guri yazauna Abba yayi gyaran murya yace matarka tasamemu da wata magana wacce da bamu amince da itaba sabida ganin rashin dacewar hakan amma kuma tafimu hujja da da dalilu masu yawa Ya shamsu yadaga kai yace Abba yanzu inbanda shirme irin na kubra ta ina zanfara Neman matar aure Abba yace ai har matar ma tariga tasama maka ita Dasauri yadago kai yakalli kubra wacce tamaida kanta kasa Yace bangane tasamamin matar aureba Abba yace wannan yarinya amina Ya shamsu yace amina kuma wacece wannan kuma Husnah dake bakin kofa tace meenat kenan Duk suka kalleta anty kubra tace a itanake nufi Na tabbatar a yanzu duniya ta mata karatun tanutsu zata zauna lafiya Kuma meenat bakowa takeso sai yayanki Tana son ya shamsu kobadan itaba ai zamu duba babanta da kakaninta tashiryu duk abinda tayi da ina da tabbacin yarinta ce amma yanzu hankali yazo mata Dan Allah ke ma husnah kifahimce ni Husnah tace yanzu anty kubra dakanki kikeson janyo meenat ajiki bayan munsan ta musan halinta Anty kubra tace sanin da kika ma kuma kema na San kinyarda meenat ta canja Abba yace duk kuzauna mufahimci juna Nan Abba yayita musu nasiha Sannan kuma yanuna musu faidar yin abinda kubra tace Umma tace gaskiya khadija samun mace irinki awannan zamani maison farinciki Wanda take taredashi koda ita zata rasa nata farincikin Kai kuma shamsu idan wannan aure dazaka yi zaisa kubra tayi farinciki to kaje kanemi auran amina Abba yace wannan banyarda kabata wa kubra ba shamsu a rayuwar ka mace ce tagari Wacce samun irinta a rayuwa sai antona Kubra tace nagode dakuka fahimceni Abba yace Allah yamiki albarka yabaku masuyi muku abinda kukamana Anty kubra ta tashi tafita Abba yakai kallonshiga shamsu dayayi suman zaune Abba yace abinda yakamata yarinyar tayi a yanzu tabbas lokaci yayi dayakamata karamawa kura aniyarta ba abinda zamuce ga wannan yaro Abdul Hakeem da iyayensa saidai Allah yasaka musu da gidan aljanna Kaduba yadda suke kula da 'yar uwarka ba abinda tanema tarasa Baka tunanin hanyar dayakamata kaima kamishi wani Abu dazaiyi jidadi a rayuwarshi To Allah ne yabaka damar dazaka sakamasa shima shine ka auri yarinyar nan amina kariketa kamar yadda yake rike maka naka 'yar uwar Nan dai su Abba sukayi ta fahimtar dashi faidar yin hakan Da daddare kubra da yashamsu sunyi shirin kwanciya Sunkwanta kubra kallon kayan da akaturo mata nasiyarwa ne wata kawarta ce take kawowa daga Dubai Ya shamsu yakarba yana kallo shima yace kai amma sunyi kyau wanne kikazaba Kubra tayi dariya tace daga ganin Abu a waya kuma saina hau zaba kawaidai ita tafara nunamin ne inga irin kayan data saro kuma nagani kaga nace mata ma sunyi kyau sosai Yace hakane to ninace kizaba muku masu kyau keda asmau Kubra tace a a fa wallahi bada niyar kasayamin nabude kaganiba kawaidai nabudene Dan nasan ta turo sai dai nazabawa Husnah dai tunda kayi niyya saya Ya shamsu yace kizaba muku banason musu Kubra tace to ai kabari muji kudinko Ya shamsu yace bakyajin magana ko Kubra tayi murmushi tace shikenan angama rankayadade Saikuma tace muka saya mana kanwata fa meenat kagafa tunyanzu yakamata ka kafara kwatanta adallcin fa Ya shamsu yace yasalam kubra rigima wai ba anwuce wannan shafin bane Kubra tayi murmushi tace yanzu aka bude shafin kuwa kasan fa jibi zasu koma gida yakamata kagabatar da kanka agurin meenat Ya shamsu yace Ashe kuwa saidai afasa kenifa barin fada miki wallahi bayadda na iya ne yasa na amince muku keda su Abba amma wallahi duk abinda yafaru dake zanyi kuka Kubra tayi murmushi tace ba abinda zaifaruma sai alkairi Yanzu dai mu uku zan zaba mana ko Ya shamsu yakwanta yace yadda kikace Murmushi kawai anty kubra tayi tace shikenan Tace nazaba mana nida husnah katashi kazabawa meenat nata Duk kubarshi amfasa indai nizan zaba mata anty kubra ta kunshe dariya acikin bakinta Dan yadda yayi maganar yabata dariya Husnah da meenat suna kwance sunyi shirin bacci Husnah tacewa meenat duk da kinfada min Wanda kikeso yanzu idan Allah yacika miki burinki kika aureshi Wanda kikeso yazakiyi wani irin tanadi kika mishi wurin faranta mishi Meenat ta tashi tazauna tayi murmushi tace hmm wannan sirri nane tsakanina da mahaliccina Dan Allah yaga niya ta akan shi idan Allah yacikamin burina Wanda banma taba mafarkin cikansaba amma wallahi Allah yasani inason shi sona hakika so mai tsabta Husnah tayi murmushi tace Allah yacika miki burinki Zaki auri Wanda kikeso meenat Cikin tsananin mamaki meenat tace taya akayi kikasan Wanda nakeso bayan nasan banfada mikiba Husnah tace labarin zuciya a tambayi fuska kawata kuma nima antyna a yanzu amarya agurin anty kubra mace daya tamkar yadubu Mata agurin masoyinki ya shamsu Meenat da mamaki take kallon husnah tace ya akayi kika fahimci asirin zuciyata Husnah tayi murmushi tace karkidamu Allah dai yanuna mana lokacin Ni husnah nafi kowa gata da samun matan yaya guda biyu masu sona Allah yabaku zaman lafiya Bana son tambaya bacci zanyi idan kika dameni zanfada wa dad dinki Kin hanani bacci ta kwanta abinta tana cike da farincike Meenat tarasa abinyi murna zatayi kokuma akasin haka To kodai shima ya shamsun yanasonta ne kai a a akwai dai wani Abu Kuma mai bata amsar taki fito da daita daga duhu Tashi tayi tashiga bathroom alwala tayi tana Neman zabin Allah Washagari da safe meenat takasa fita falo tayi takasa hada ido kowa inba husnah ba Umma ana cin abincin rana Anty kubra ta kalli husnah tace wallahi baki kyauta ba yanzu gashi kinsa tunsafe takasa fitowa cikin mutane Husnah tayi murmushi tace ai dole takasa fitowa tunda bata da gaskiya takarasa maganar tana dariya Umma tace tashi wa husnah kitashi kije kikiramin ita Husnah tace to ta tashi ya shamsu yayi kaman yayi magana sai yabasar kawai Next page Yau kunga typing din kadan watspp ne yakebani matsala Please marasa comments ina ganinku fa kara nake muku Masu comment ina alfahari daku Allah yasaka da alkairi Love you all 😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘 [06/05, 11:21 AM] UMMU AFAN 🌹: πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ— BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM STORY & WRITTEN BY THE SPECIAL AUTHOR /WRITER UMMU AFAN πŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–Š 🌹FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION🌹 🌹F.C.T.W.A.🌹 🌹HOME OF QUALITY AND TRUSTED WRITERS OF THE NATION🌹 πŸŽ—I DEDICATE THIS PAGE TO YOU SISTER SHAFA'ATU (UMMU KHALEEL) Ina alfahari da comment dinki over kina kokari sosai wajen suburbudo comment Allah yabar zumunciπŸŽ—πŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉπŸŒΉ πŸŽ—AKWAI LOKACI πŸŽ— πŸŽ— PAGE 156 to 157πŸŽ— HUSNAH tashiga dakinsu da sallama tasamu meenat kwance dawa a hanunta Tana chart husnah tace anty meenat umma nakiranki Meenat tadafa kirji tace nashiga ukuna Wallahi ina matukar jin kunyar 'yan gidan nan Husnah ta ballawa meenat harara tace saikizaba Ko zuwa kiran umma ko jinkunyar Meenat tayi saurin saka hijabin dogo har kasa Tace muje amma Dan Allah ya shamsu yana falon wallahi banason hada ido dashi kunyarshi nakeyi wallahi Sosai dariya yakama husnah tace yaukuma kece da kunya meenat Meenat tazunburo baki tace bake kika fada ba kuma alhalin niban fada miki da bakina ba Husnah tayi murmushi tace to ai labarin zuciya atambayi fuska Husnah taja hanunta suka fito alokacin ya shamsu yadauki cup din tea dinshi Yayi gefen kujera yazauna yana shan abinshi Meenat suka fito da taga baya falon tayi hamdala azuciyarta Ta durkusa harkasa tazauna gaban umma tace umma ina kwana Umma tayi murmushi tace haba amina kinbuya adaki kinki fitowa kisha iska Meenat tayi murmushi tace ba komai umma tace umma azumi nakeyi Kafin umma tayi magana anty kubra tafito daga part dinta tace yauwa kokefa meenat amma kinki fitowa kisha iska Meenat kanta akasa tace anty ina kwana anty kubra tace lafiya qalau antashi lpy Umma tace wani irin azumi yau lahadi Husnah tace au umma har kinyarda ma azumin takeyi Wayace tayi ringing kan dining din dasuke husnah tace ya shamsu ankiran wayarka azabure meenat ta kalli bayan ta kan kujera aikuwa caraf suka hada ido Tayi saurin saukar da fuskarta kasa tana Shima ya shamsu baisan lokacin da yakalleta ba yakau da kansa Husnah ta kallesu tayi murmushi kawai Umma talura da yadda meenat tarikice tace tashi mana kici abinci Meenat tace to umma amma kasa yafi min dadin cin abinci Anty kubra tadauki wayar ya shamsun takai mai Yakarba yace tazauna anan Tayi murmushi tace ina karyawa nefa honey Ya tashi yadauki wayarsa da yace biyoni Anty kubra tabi bayansa sukatafi part dinsu meenat ganin sunbar falon yasa tadan sake kadan Prof da Ahmad ne sukawa kano diran bazata Ya shamsu sosai yakarbesu a falonshi prof yakira wayar husnah yace baby kufito mutafi ko Husnah tace badai kunzo kanoba Murmushi prof yayi yace naki wasane ke atunaninki zan iya barinki har kwana hudu ukun ma dakyar nayi Yashamsu yashigo falon yaga Hakeem nawaya Ahmad yace kaga wannan romeo din barnar kati baya mishi wahala Wai kuna gida dayama amma kana kashe murya a waya Ya shamsu yayi murmushi kawai yana jin dadin yadda Abdul Hakeem yake ba wa kanwarsa kulawa ko agaban wayekuwa Kodan wannan zai auri meenat zai riketa tsakaninshi da Allah Meenat da husnah suka fito cikin rakiyar anty kubra da umma Sosai umma tahadawa meenat tsarabar su humra ne da dai sauransu anty kubra ma tabasu nata Sosai sukayi kewa meenat dai Allah Allah take sutafi Dan ta takura sosai wallahi ******** Bayan sati biyu da komawarsu Abban su husnah da wani abokinshi sukatafi Kaduna Dama daddyn Hakeem yasan dazuwansu Shida daddyn Ahmad suka karbesu Bayan anci ansha Abba yakawo musu bukatarsu Daddyn Hakeem yanisa yakalli daddyn Ahmad yace lalle wannan yarinya amina Allah yanasonta Mutum kamili mai nutsuwa kaman shamsu yanemi auranta bayan duk Abu abuwan datayi abaya Abba yace duk wannan yawuce alhaji muyi maganar yanzu kawai Daddy yace duk da bani ubanta jikatace to amma da ubanta da itadin duk mallakinane wallahi naba wa shamsu ita halak malak Nan sukayi hamdala da godiya Abba yace idan bazaka damuba tunda ba auran farko bane daga ita harshi shamsun zanso a yanka mana sadaki mubiya Daddy yace hakane amma naji wannan alamari sosai Daddyn Ahmad yace tunda hakane ga sadakin nan nabiya wa Dana shamsu Abba yace a a haba alhaji karmuyi haka daku mana wallahi da komai mukazo Daddyn Hakeem yace haba ba komai karka daga hankalinka dan yabiyawa danshi sadaki kuma ma ai shamsu Dan mune kana nufin da wani guri yaje Neman auren aimune masu biyamasa sadaki bawai Dan bashidashi ba sai Dan can cantarsa Hakadai sukata raha abinsu har suka tsaida lokacin aure nan da wata biyu masu zuwa Abban ya shamsu ya fito da kudi yace tunda anbada nasadaki to ga kudin Nagani inaso Dakyar daddyn Ahmad yakarba Da daddare daddy da Hakeem sun gama cin abinci Daddy yace akwai maganar danakeson nayi daku kaida mummynka Mummy hafsat tayi murmushi tace to tasamu kenan tunda naji meeting Daddy yayi murmushi yace sosai kuwa Nan daddy ya sanar dasu komai Hakeem yace daddy kar ayi haka wallahi matar shamsu yarinyar kirkice Aje amina taje tabata musu zaman dasukeyi mai cike da kwanciyar hankali Daddy yace duk namusu bayanin wannan sai suka nuna min matar ma bata da matsala itama tabada goyan baya kuma tayi alkawarin zama da meenat tsakani da Allah Hakeem yace aidama itabata da matsala su laila ne damuwata kunsan halinsu Suje suyita abin kunya mummy tace Gaskiya kam Kuma gaskiya yarinyar nan kubra bata can canci kishiya ba Muna zumuncinmi gwanin sha'awa da mutane azo ana raba mana abin kunya Daddy yace to duk naji baya ninku Nan yadauki waya yafada wa abbansu husnah komai abban su husnah yace bani Abdul Hakeem din Abdul Hakeem ya yakarba da ladabi kaman yana gaban abban sun dade suna magana kafin sukayi sallama Abdul Hakeem yace Allah yasa dai karsu dinga jamana abin kunya a inda ake ganin mutuncinmu Dadddy yafito da sadakin da kudin Nagani inason yakuma fada musu ranar da suka tsayar Mummy tace har cikin raina naji dadin wannan Abu sai dai ita aminar akira ajamata kunne sosai tazauna lpy dasu Hakeem yakira wayar meenat tazo tazauna akasan carpet Ke yaushe kuka fara soyayya da shamsu Mummy hafsat ce ta wurgo mata wannan tambayar duk ta gigice tayi shiru kawai Daddy yayi murmushi yace yanzu dai mamana kinason asake minkafa kenan ko akaro na

Chapter 7 of 9