Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 9
mijinta Dana surukanta Hakeem kuwa Wanda yasanshi ada yaganshi yanzu balalle yaga neshi ba saboda kwanciyar hankali da yasamu Ga bunkarsar arzikinsa ta kota ina Samun karuwa yakeyi ****** Meenat zaune satinsu kusan daya da dawowa amma bashir ya hanata zuwa Kaduna Yace saiyaga dama zataje Tana zaune hajiya rukayya tazo gidanta meenat nakwance kan cinyarta tana kuka hajiya rukayya Tace yanzu wannan yaro haka zaimana dubi dan Allah yadda kikabi kikarame Waike kina auren mekudi ina wallahi dasake dole zamuyi maganinsa Zaidawo kamar yadda yake da sai abinda kikace mishi Meenat tace yauwa hajiyata daman nasan zakimin komai wallahi bashir yacanja sosai Hajiya rukayya tace yanzu yaudin damukayi zanbiyo tanan mutafi Kaduna dake baibariba Meenat tace yaki wallahi yace idan nasa kafa natafi karnadawo mishi gida Hajiya rukayya tadafe kirjin har abin yakai haka a a gaskiya dole mutafi yau dan nayi niyar tafiya dake Meenat tace tayaya hajiya ai yakine Hajiya tayi murmushi tace badai yana ganin kiman baban ba Meenat tadaga kai sama tace kwarai kuwa Hajiya rukayya tace to kyale nidashi Bashir yadawo gida daga office Yagaji sosai yanashigowa falon yaga hajiya rukayya ya tamke fuska sannan yace sannu hajiya zaiwuce hajiya rukayya tace bakaji ba bashir Yace inajinki tace mahaifinta akakwantar a asibiti yau kwana daya kenan Shine nake nema mata izinin zuwa dubashi dan nima can na nufa yanzu Bashir ta ambaci mahaifintane balafiya yasa yace Allah sarki zata iya zuwa zanzo jibi na dubashi sai mudawo tare Meenat cikin zumudi tace nagode ya maka mata harara yawuce bedroom dinshi Meenat tace ajedai tunda kabarni aishikenan Nan suka shirya sai kaduna **** Laila da suby da masu aikinsu suna ta shirshiryen zuwan su meenat gida ya kaure da kamshi ta kota ina Husnah kuwa tana can part din mummy tana tayata shirya kayanta cikin akwati zasuyi tafiya zuwa madina Dan duk azumi acan dadi yake yi har sallah ma sai bayan sallah suke dawowa Husnah ta kalli mummy ta ce yanzu mummy gobe warhaka fa kuna can ko Mummy ta ce sosaima Tace yaufa 'yarki tana hanya Husnah tace haka yaya yafada min allah yakawosu lafiya mummy ta ce amin Next page Your comment is needed fans Love u all 😘😘😘 πŸ“–πŸ“–πŸ“πŸ“ [05/05, 10:18 PM] UMMU AFAN 🌹: πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ— BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Story & written By The special writer UMMU AFAN πŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ“š 🌹FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION🌹 🌹🌹 (F.C.T.W.A)🌹🌹 🌹HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION🌹 πŸŽ—I DEDICATE THIS PAGE TO YOU AGAIN MY SWEET TWINS SISTER UMMY KHALEEL ( HAJARA)πŸŽ— Ina alfahari dake wallahi kina kashani da wannan nice comments din naki Allah yabar kaunaπŸŽ—πŸ˜˜πŸ˜˜πŸ˜˜πŸ˜˜πŸ˜˜ πŸŽ—AKWAI LOKACI πŸŽ— πŸŽ—PAGE 136 to 137πŸŽ— HUSNAH tana gamawa mummy komai ta koma sashinta Tana shiga kara gyara dakinta sosai kasacewan yau itace da prof kuma asabarce Tafesa wanka tazauna tana shafa mai itakai take ta jin dadi saboda yau meenat zatazo taganta amatsayin matar ubanta Tayi murmushi itakadai ta tashi taje wajen English wear's dinta Tazabo wasu Riga da wondo Wandon Jean's me adon pink flower ajikinshi Sai rigar shima pink tayi matukar kyau ita da kanta sai data yaba da kayan Ta dauko pink ribbon dinta tagyara gashinta yayi kyau sosai kamar wata 'yar india kwalliya tayi Normal amma fa Wanda tayi dominshi ta tabbatar zai yaba sosai Kara fesa turare tayi kafin nan tadauki chocolate din ta da katuwar Teddy dinta Wanda Prof yasaimata a super market dasuka fita kalakala tasaya masu kyau sosai manya kuma Tafito a daga part dinta ta kullo ta haura sama tasauko saukowarta taga su Laila ansha kwalliya itada suby an harde a kujera Husnah tanemi two sitter tazauna tana shan chocolate din ta gefenta kuma katuwar Teddy dinta saikuma wayarta a hanunta Tana game Suby ta kalli Laila tace dan dubeta saikace aljana Laila tace ina marabarsu da aljanun ai babu Suby tace daga yau dai duk wani iyayi yakare dan za asamu dai dai daita dan meenat ba daukar raini zatayi Laila ta buga tsaki zuciyarta FAM da da haushin kyau dataga Husnah tayi cikin kayan datasa koina yaji kuma yafito ajikinta Husnah kokulasu batayi ba kuma tasan da ita sukeyi Wayarta yayi kara tadauka cikin shagwaba tace Ya bakudawo ba sweet kasan muna da bakuwa ko Yace sorry baby Kinsan da asuba su mummy zasu tashi shine nake musu booking din komai Husnah tace amma yanzu a ina kake Yace ina mota zandawo gida insha Allah Tace allah yadawo mindakai lafiya barinje najiraka a sama yace yauwa my baby Love you ya mata kiss kamar tana ganinshi takashe wayar Ko kallon inda suke batayi ba Ta haurasa da Teddy dinta da wayar sauran chocolate din ne tabari a falon Ta haura sama tasake feshe dakin dakin da turare mai kamshi Kafin tazauna tana kallon tashar wato zee aflan Ana wani film ne na soyayya yanayin soyayyyar jaruman saiyake mata kaman nasu itada sweet dinta sosai film din yamata dadi Can taji ihu daga kasa na murna Tana tunanin su meenat sun iso kenan Meenat sosai ta rungume mummynta tana murna tace wallahi mummy nayi missing dinku Laila tace nima haka my daughter kinrame Meenat tayi murmushi tasake uwar ta rungume anty suby suna murnar ganin juna Hajiya rukayya tace wato kunga 'yarku bakwa tani ko tana dariya Laila ta ce ya hakuri hajiya Kinsan meenat da surutu sannunku da zuwa Nan meenat ina ita hakeemar take Suby tace yanzu tagama mana karuwanci anan ta haura sama Kafin meenat tayi magana Hakeem yashigo cikin falon yana ganin meenat yasaki fuska itama da murnarta tatashi taje gabanshi takama hanunshi tace sannu da zuwa daddy nayi murnar ganinka Yace nima haka kakata ya magidan naki tace kowa lafiya yaja hanunta sukayi sama Laila dadi yakasheta ganin yadda Hakeem ya nuna murna daga yarshi guda daya Suna shiga falon kamshi hade da sanyin AC ya doki hancinsu a falon suka zauna meenat tazauna kusa da daddynta yana tambayarta rayuwa Husnah tana daga bedroom Hakeem yadauki wayarshi yakira husnah yace baby kina ina kifito ga 'yarki ta isofa muna falo tare Husnah tace ganin zuwa nima inan ina bedroom ne Ta kashe wayar ta Meenat kuwa takaici yakamata ganin yadda ubanta yake kashe wa wata banza murya wai harda kiranta baby Husnah tafito cikin yanayin tafiyarta medaukar hankali tana murmushi tace Ashe ma sun iso Hakeem yajuyo jin kamshinta murmushi yazuba mata Ita kuwa meenat jin muryar kaman tasan inda tasan muryar nan tayi saurin juyowa itama aikuwa sukakyi eyes to eyes da juna cikin tsananin rudewa meenat tace nashiga uku Asmau meyakawoki gidan mu Husnah tayi murmushi kawai tace sannu da zuwa ya hanyar tazo tazauna daf da Hakeem Meenat cikin tashin hankali ta buga wa husnah tsawa tace meya kawoki gidan nan Tajuya gurin daddynta tace tadurkusa tadafa gwiwowinsa tace dan Allah Daddy karkace min asmau ce matarka dan Allah kace min ba ita bace Yace kina Haukane Amina wani irin magana kikefa matata ce fa Jin abinda daddynta yace yasa tafa sa wata uwar kara tafadi kasa sumammiya Husnah tayi kanta tana jijjagata Jinkara daga sama yasa su Laila dasu hajiya rukayya suka hauro a gigihusnahSuna shigowa sukaga meenat kwance a kasa kanta a hanun husnah Tana yayyafa mata ruwa Suby ta bangaje husnah tace matsa dallah dangin mayu Daga zuwanta ankama mana ita Laila kuwa batayi watata ba badauki hanu ta tsinke Husnah da mari dai dai fitowar Hakeem daga kitchen dinsama dan dauko ruwa mesanyi a kwara ma meenat aikuwa yasaki robar ruwar akasa baiyi watata ba ya damko Laila yazabga mata mari har sau uku hajiya rukayya da suby suka saka salati Hajiya rukayya tacewa wa suby yimaza kije kikira hajiyarsa tazo Suby tatafi bangaren mummyn Hakeem dan kiranta Hakeem kuwa da sauri yasa hanu yadago husnah yana rarrashinta Husnah tafashe da kuka tace To mena mata zata mareni Yace kiyi hakuri baki ga na dau hukunci ba Ya kwantar da Husnah ya akirjinshi yana rarrashinta Laila kuwa hanu tasa akai tace yanzu saboda wannan yarinyar kamanta da rayuwar 'yarka Kamareni saboda namata abinda yadace Meenat dake kuka sosai a hanun hajiya rukayya tace Asmau kincuceni kincuceni kirasa Wanda zaki aura sai baba na Wallahi sai kinbar gidan nan inba haka ba zankasheki wallahi ta tashi daga kwanciyar datake Hakeem yace Ashe rashinkuyarki yakai haka Zaki dubi tsabar idona kice zaki kashe matata tobari kiji akan matata dagake har uwarki dama Wanda yake da hanu wajen daga mata hankali zan Baku mamaki wallahi Yaja hanun husnah sukayi bedroom Ya rufo ko Hakeem yadago fuskakarta yace kiyi hakuri kinji ko bamai sake mai maita abinda ta tayi akanki ina fatan kinji ko Husnah tadaga kai yace yauwa my sweet amma daman meenat kawarki ce Husnah tace nifa bansanta ba ma a school sosai sai lokacin da akabata prefect Hakeem yadaga kai yace OK Nasan aikin kakan kane zata zugata zanyi maganinsu Mummy tashigo falon tace wai meyake faruwa ne agidan haka Meenat tanaganin mummy ta taso da gudu ta rungume mummy tace Granny Dan Allah kisa daddy yasaketa Wallahi zuciyata zataiya fashewa Mummy tace wai mekefaruwa ne Laila tace bata labarin komai Mummy tace ina suke Laila tace yajata zuwa dakin yabata hakuri Mummy takira wayar Hakeem yadauka tace kufito falo dukanku ina da magana daku Hakeem yakamo hanun husnah zuwa falon Mummy ta kalli husnah tace 'yata dama kunsan junane da meenat Husnah ta girgiza kai tace a a mummy Ina dai ganinta a school dinmu amma gaskiya bawani sani na mata ba Amina tace karya kikeyi kifada musu gaskiya Granny wallahi babbar kawatace a school nasanta tasanni cin amana ne kawai ta auri babana na Dan Allah daddy karabu da ita wallahi kawatace komai namu tare mukeyi A school Taya zatayi tazama kishiyar uwata Hakeem yace kewai bakida kunya ko oya get out of here stupid girl Dasauri meenat takama husnah Tace wallahi kifada musu gaskiya Dan wallahi bazan taba barinki kizauna agidan a amatsayin kina auren baba na ba Husnah ta kalli mummy Mummy tace was husnah kiyi hakuri kinji husnah Koma dakinki kizauna kawai Husnah tace to mummy Tajuya zata fita amina ta fincikota ina zakishiga gidan ubanki ne Ko anfada miki nan ma scholarship akeci kamar yadda kikasamu har kika yi makaranta mekyau Kafin husnah tayi magana taji wasu gigitaccen mari da duka tako ta ina Daddynta yace Ashe bakida kunya matata kikefadawa haka Ashe zaki iya fadawa uwarki kenan Laila tace kadaina hadani da wannan jinin mayun Mummy tace wai maiyasa hakane Towaima menene dalilin dazaku dage Saiya saki matarshi Ke meenat idan kawarkice shiya haifeta To bari nafada muku bawanda ya isa yatakurawa yarinyar nan agidan Idan kinsan rigima zakiyi da matar mahaifinki kiwuce kikoma gidanki Hakeem yace mummy rabudasu dasu duk zanyi maganinsu koma jeki huta abinki Mummy tawuce zuwa part dinta Amina tasauka kasa dagudu tana kuma mecinrai sosai Hajiya rukayya tace gaskiya gidan nan ba adallaci Laila tace bakomai Allah zaimana sakayya Dan yana ji kuma yanagani Hakeem yajuya yamaka mata wani uwar harara yace idan kikasake ambatar Allah sainabuge bakin ki wallahi kinsan Allah zaki dinga abinda kukeyi Ya juya yashiga bedroom dinshi yaga husnah kwance tana kuka Yasunya dai dai kunanta yamata rada amma taki shiru cak yadauketa zuwa bathroom Tare sukayi wanka saida ya tabbatar ta huce sannan suka fito daga bathroom din dakanshi yashiryata zai mayar mata dakayan data cire tarike hanunshi tace zanje nasa wasu Yace wadannan bayanzu kikasaba tace ai idan nayi wanka bana son maida Wanda cire kobaiyi datti Yace duk yadda kikeso haka za ayi amma saikin gama shirya ni kinsan zanfita magriba tadaga mai gira tace angama sweet Tsaf tashiryashi cikin wani farin jallabiya kowa yaganshi yasan yanada kwanciyar hankali Zaifita tace bakajiba yatsaya yana kallonta ta tako tazo har inda yake Tayi tsalle manna mashi kiss tace I LOVE YOU Murmushi Hakeem yayi yakamota yace I love you too Ya rungumeta tsam a kirjinsa Yadago kanta ya hade bakinsu guri daya yashiga kissing din sosai sun Dade a haka Hakeem sai dayaga hankalinshi na shirin barinjikinshi yasaketa da kyar Dan yaji anakiran sallah yace mune kikaini nasake auwala Murmishi husnah tayi taja hanunshi zuwa bathroom Dan taga rigima yakeji Sai daya sake alwala kafin nan ya manna mata kiss Yayi waje Murmushi tayi tabishida kallo Meenat kuwa tana can falo tana kuka Laila tace kifada min gaskiya meenat a ina kika San wannan yarinyar yanayin kukanki yaban tsoro fa Kaman akwai wani Abu akasa Cikin kuka meenat tace mummy wallahi kawatace nasanta tasanni Kuma wallahi nayi alkawarin bazata kwana agidan nan ba Yayi dai dai da saukowar husnah daga sama daga ita sai karamin tawul zata je part dinta tasa kaya ne Duk suka bita da kallo Next page Your comments is needed fans Love you all πŸ“–πŸ“–πŸ“–πŸ“πŸ“πŸ“ [05/05, 10:18 PM] UMMU AFAN 🌹: πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ— BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Story & written By The special writer UMMU AFAN πŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ“š 🌹FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION🌹 🌹🌹 (F.C.T.W.A)🌹🌹 🌹HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION🌹 πŸŽ—I DEDICATE THIS PAGE TO YOU ABDUL AZEEZ (KHALEEL) & HAJARA (YUSRAH) INA ALFAHARI DAKU 'YA'YANA NAKAINA ALLAH YA RAMINKU DA IMANI 😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘😘 πŸŽ—AKWAI LOKACI πŸŽ— πŸŽ—PAGE 138 to 140πŸŽ— HUSNAH takallesu tayi murmushi tace sannunku da hutawa Meenat tazabura zata biyota Hajiya rukayya takamota tace rufamana asiri Mezaki mata Meenat tace kibarni naje na nuna mata ita karamar Mara kunyace hajiya Laila tace karuwai ba inba karuwa ba mezaisa tasauko daga ita sai karamin towel Husnah tayi murmushi tace Dadin abin aduk inda kiga karuwa saikunga abokin tambadewarta Kaman yadda kuka ganshi yasauko yayi masallaci yanzu So kuringa sanin abinda zakufada Dan bakusan abinda za'amayar maku ba Kekuma daughter meenat Mekike tunanin zakimin duka na zakiyi ko Lalle kuwa Ashe zaki iya dukan ubanki kenan Mara kunya kawai Kifito fili kifada musu abinda kike boyewa fa Ta kallisu hajiya rukayya tace tabbas meenat kawata tace kamar yadda tafada muku Sauran bayani zata muku Tawuce abinta cikin part dinta Daga Laila har hajiya rukayya baki sukabita dashi Cikin kuka meenat tace kunganiko dakunganiko nafada muku kawatace Wallahi dakun barni naje naci ubanta Laila tace rabu da ita dole musam abinyi tunda abin yakai haka Hakeem nafitowa daga massalaci yaga motar Ahmed Yakarasa gurin motar Ahmad tafito yace kaganni kenan Hakeem yayi murmushi yace ai inafitowa naga motarka Yace mukarasa ciki mana Ahmad yace a a mushiga mota kawai muyi maganar Nan suka shiga Hakeem yaba wa Ahmad labarin komai zuwan meenat Ahmad yasauke numfashi yace kasan mena fahimta a wannan labarin Hakeem yace saika fada Ahmad yace Husnah tasan meenat zai iya yuwuwa kawartace kaman yadda meenat tace Akwai dai dalilin dayasa husnah taki nuna tasan meenat Yakamata ka lallabata tafada maka komai Hakeem yace hakane nima naso nafahimce hakan amma maizaisa meeanat ta dage ita saina saki matata Akan husnah zansaba mata wallahi daga ita har uwarta dansu suke Dada bata min yarinya Ahmad yace a dama aibazaka rabuda matarka saboda Wannan daliliba amma inaso kasani fa akwai takaici kawarka ta auri mahaifinka Dole meenat zataji ba dadi Hakeem yace kuma husnah bata taba sanin nineahaifin meenat ba sai ranar dataga ta a hoto amma naga tayi murmushi Dana tambayeta murmushin metake tace min bakomai Ahmad yace ganiba tabbas akwai wani Abu Hakeem yace kwarai kuwa amma nasan yadda zanyi zangano koma menene Nan sukayi sallama da Ahmad Shikuma Hakeem yatsaya a massalaci don sallar isha Husnah tashirya cikin wasu arnar kayan bacci masu matukar kyau tafeshe jiki ta da turare Takoina yadau kamshi ta hada gashinta guri daya da ribbon Kafin tabude fridge din kitchen dinta tadau fruit salad din data hadawa mijinta tadauki dogon hijabinta tasaka Tadauki abinda zata dauka tayi waje tayi sama abinta cikin farin ciki Hakeem yadawo daga massallaci yabi wajensu mummy Mummy tace Dan Allah kaba wa husnah hakurin abinda tagani yau Mutanan basuda imani fa Ni anya bazan fasa tafiyan nan bakuwa Hakeem yace saboda mezakifasa mummy Mummy hafsat tace sunban tsoro ne ai karama susata agaba amana ce fa a hanunmu idan muka bari wani Abu yasameta Allah bazai barmu ba Yarinyace karama Hakeem yace karkidamu mummy Insha Allah ba abinda zaifaru mummy Mummy tace shikenan Allah yadada karewa yace ameen Mummy tace tashi kaje gurin matarka kabarta itadai Yama mummy saida Yana Shiga falon baiga kowaba Ya wuce saman shi Yanashiga kamshin ta yadaki hancinsa Tana zaune kafanta daya kan daya Rigar mesharara ce sai yana da siririn hanu sannan kuma dai dai cinyarta yatsaya ba abinda ba gani a jikinta Ga sambala balan cinyoyinta masu tsantsi da laushi Da kuma daukar ido Cikin yanga da Jan hankali ta taso tarungumshi Hakeem sumane kawai baiba saboda gaskiya shigar ya kayatar dashi sosai Nan da nan kwadayinshi yatashi akanta Sosai ya matseta ajikinsa Yana shin shinnanta yamata rada akunne tayi murmushi tace saikaci abincinka Yace ai nakoshima Ganin wannan wanka ma ai wadatar dani sosai Husnah takama hancinsa tace naki wayon ta matsa cikinshi tace ji cikinka bakomai kaman wani silipas Shima dariya yayi yashafa cikin nata yace harkura zatace wa kare maye Ji cikin kifa Tace aini hallittace duk abinci da zanci cikina bazai tashi amma kaifa idan kaci abinci sosai katoto cikin ka yakema Hakeem yayi murmushi yadauketa cak dining dakanta tayi feeding dinshi Shima yabata kafin suka tashi zuwa bedroom wanka suka fara Indai suna tare komai tare sukeyinsa Shiyasa wani shakuwa metsanani yashiga tsakanin su takama idan baranar kwananta bane Hakeem cikin kunci da kewa yake Sosai yasamu abinda yakeso agurinta tacire mishi duk wani damuwar dasu meenat da uwarta suka sashi Sai da komai yakammala sannan Hakeem yadawo hankalinshi Cikin tsananin son matarshi yarungumeta Shikanshi yasan tana kokari dashi sosai bata taba hanashi kantaba Duk da yasantana wahala sosai danshi din yasan Jan gwarzo ne Yana rumgume da ita ya kalli beautiful face dinta ya manna mata kiss abaki Nan yashiga tunanin abinda yasa husnah taki amincewa tasan meenat Yasan tabbas akwai wani Abu haka kawai husnah bazata nuna mata haka Kuma yana da tabbacin husnah ce da gaskiya Dan yasan halin 'yarshi sarai Agogo yaduba yaga time shabiyu darabi nadare Badama yakira ya shamsu yanzu amma zaibari zuwa gobe yakirashi yamishi tambaya Yarungemeta sosai ajikinta sosai ahaka bacci yayi awungaba dasu Dasafe bayan husnah da Hakeem su shirya cikin shigata alfarma Cikin wani rantsatstsan less Maroon colour yayi matukar kyau tasaka farin mayafi da farin takalmi Shima Hakeem cikin dark maroon shadda Yayi balain karbarshi Husnah kuwa ta maka wata dambareriyar sarka tasaka na zinari Tare suka fito zuwa kasa Meenat suka hada ido husnah tasakar mata harara Itakuma husnah tasakar mata murmushi Meenat tace ina kwana daddy Yace lafiya qalau Suby ma tagaisheshi ya amsa yace wa meenat bataga antynta bane bazata gaisheta ba meenat tayi shiru Husnah tayi sauri tace Dan Allah sweet kabarta bakomai wallahi watarana zata gane Hakeem yafita abinshi Husnah takalli Laila tace mama zamuje kai mummy air port sai mundawo kafin suyi magana tafita Laila kuwa inbanda kallon takaici ba abinda take bin su dashi Shiyasa ma Hakeem yayi banza da ita sukayi waje zuwa part din mummy Mummy tace ina suke subazasuzo muyi sallama ba Hakeem yace muje kawai mummy Daddy yace a a ke 'yata kiramin matata muyi sallama Husnah tayi murmushi tace to daddy Tasan meenat yake nufi kenan Tawuce zuwa falonsu tace amina Hakeem daddy na kiranki kafin amina tace wani Abu husnah tajuya abinta Meenat tace wallahi mummy idan nabar yarinyar nan nacutu Laila tace kedai kwantar da hankalinki kije kiji medadin zaimiki kidawo ai nata yazo karshe agidan nan Meenat tana zuwa falon daddyn Hakeem yace haba amaryata shine bazakizo nagankiba muyi sallama Meenat ta kakalo murmushi tace yahakuri grand wallahi kaina yake ciwo yace asha kinsha magani kuwa meenat tace nasha yace to Allah yakara sauki ko Wannan in Allah ya dawo damu lafiya Zanzo hargidan ki kinji ko 'yar albarka Meenat tace to grand Allah yadawo daku lafiya yaciro cheque yayi signed yabata na zunzurutun kudi jar 1 million Sosai meenat tayi godiya tafita Dan bata San Ganin husnah da ubanta ***** Da yamma Hakeem nazaune shikadai a falonshi yakira ya shamsu a waya suka gaisa Hakeem yace Dan Allah ya shamsu wata yar tambaya zanmaka Koka kasan wata kawar husnah mesuna amina wacce sukayi makaranta tare Ya shamsu yace kwarai inajin sunan sosai agurinta sai dai bamu taba haduwa daitaba Hakeem yace nagode kwarai amma har suka bar school suna tare kuwa Ya shamsu gaskiya a a saboda natambayeta akan dalilin dayasa suka rabu taki sanar dani amma lafiya kuwa yallabai kake wannan tambayar Hakeem yace lafiya qalau karkadamu nagode sai anjima sukayi sallama Shigowar Laila kenan yanagama wayar Ta kalleshi sannu da hutawa daddyn meenat Hakeem yace yauwa Yau itace da oga shiyasa take ta rawar kai itaga memiji Hakeem yacigaba da aikin dayakeyi a computer Laila tace na hado ma coffee ne yace no karkidamu Barshi kawai Ya tashi zuwa bedroom yana waya Bashir sirikinsa yake kira Yadauka cikin girmamawa yagaida Hakeem Sannan yamishi yajiki Hakeem yace jiki kuma ni Saikuma kawai ya wayance Yace idan bazaka damuba inason ganinka yau din nan Bashir yace bakomai insha Allah zanzo Allah yakara maka lafiya Hakeem yace ameen ameen nagode sosai yakashe wayar harcikin ran Hakeem yanason bashir sosai saboda baya rainashi kokadan baya duba bawani shima ba wani girman shi yayi Dan zai girmi bashir da shekaru irin biyar zuwa shida Laila tashigo cikin dakin tace baban meenat kai dawaye haka kace kanason ganinshi yau Hakeem yace idan yazo zakiganshi Wajen karfe biyar na yamma YOUNG PROF yasauko cikin jallabiyarsa yagansu gaba dayansu a falon yau harda hajiya suwaiba da hajiya rukayya duk sunzo Meenat ce bata falon yace sannunku da zuwa hajiya Nan suka washe baki ganin yasake musu Zama yayi cikin daya cikin kujerun falon ya kalli suby yace ke kiramin amina Suby ta tashi taje takira amina Meenat tazo cikin doguwar rigar abayanta tazauna gaban daddynta tace gani daddy Ya kalleta yace kinci abinci kuwa tayi shiru Suby tace takicin komai tunsafe Hakeem yace jeki debo min abincinta Suby taje takawo yakarba yace wa meenat zakici nasa arike minke namiki dure ko yakarasa yana murmushi Wanda hakan yasanyaya ran amina da uwarta dama duk Wanda kefalon Amina takarba abinci taci agabanta daddyn ta yabude ruwa maisanyi dakanshi yazuba mata tasha Sallama suka ji Hakeem ya amsa yace karaso ciki malam bashir jin sunan daya ambata cikin meenat yabada wani kulululu Bashir yashigo yagaida mutan falon sannan yazauna yana fuskantar prof Hakeem yadauki phone dinshi yayi dialing number husnah dake cikin dakinta yace Baby fito falo kugaisa da bako ko tace OK sweet Ganin zuwa Fitowar husnah daga part dinta yayi dai dai da dagowar Bashir daga sankuyon dayayi dakai aikuwa a razane yatashi yana nuna ta da hanu Next page Your comments is needed fan's Love all 😘😘😘😘😘😘😘 πŸ“πŸ“πŸ“πŸ“πŸ“–πŸ“–πŸ“–πŸ“πŸ“πŸ“– [05/05, 10:18 PM] UMMU AFAN 🌹: πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ— BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Story & written By The special writer UMMU AFAN πŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ“š 🌹FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION🌹 🌹🌹 (F.C.T.W.A)🌹🌹 🌹HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION🌹 πŸŽ—I DEDICATE THIS PAGE TO YOU FATIMA SUNUSI SANAYA ina alfahari dake wajen nice comments wallahi Allah yabar zumunci keep it up page saboda kina kara min kwarin gwiwa sosaiπŸ˜˜πŸ˜˜πŸ˜˜πŸ˜˜πŸ˜˜πŸ˜˜πŸŽ— πŸŽ—AKWAI LOKACI πŸŽ— πŸŽ—PAGE 141 to 142πŸŽ— HAKEEM yakai kallonshi ga Husnah data nuna kaman bata sanshi Bashir yace mene ke gani asmau Mekikeyi anan Husnah tayi murmushi takaraso tazauna a hanun kujerar da Hakeem yake zaune tace uncle bash Anzo lafiya ya hanyar Bashir kawai yasake baki yana kallonta yadda kasan ba komai a tsakaninsu Hakeem yace kasanta ne bashir yadaga kai da sauri

Chapter 4 of 9