Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
2 / 9
wani Dan akwati ta gani yamata kyau sosai Garin ta gyara mashi zama sai yafafo kayan ciki cuka zubo Ba abinda tafara gani sai fuska(masks)/kuma da ya mu'alim yake kama sak abin har yaso yabata tsoro zata gudu idonta yakai kan nokia yarsa wacce tasha dauri da roba Cikin tsananin mamaki husnah tace badai ya Hakeem shine ya mua'allim dina bansaniba To meye hujarsa na boye kansa Tasake bincika kayan taga zoben data bashi Wanda sukayi canji yabata tabashi Nan tasake tabbatarwa kanta ya Hakeem shine ya mu'allim Taga wani diary kamar yadda taga anrubuta a bayan littafin Nan ta hau karanta abinda ke rubuce Nan ta tababbatar Abdul Hakeem shine ya mu'allim dinta Kukan dadi suka gangaro mata Sosai tayi kuka ammafa na murna ne Tace meyasa zaka cutar da kanka har haka meyasa baka fada minba kabari har na dauki alhakinka ya mua'llim amma bakomai insha Allahu zakasan kayi auren soyayya Ya Allah ka karemin mijina Daga sharrin wadan nan mutanen tabas a labarin dake rubuce cikin diary dinshi mummy hafsat da daddynsa sunbata tausayi Dole ya mua'llim yayi taka tsan tsan gurin sake Neman matar Baka da laifi kuma na tabbatar kosu umma da ya shamsu bazasu zargekaba idan sukaji Kaine ya mua'llim kuma suka ji dalilinka Wani irin son mijinta yadawo sabo fil azuciyarta tareda tausayinsa Dana iyayensa tashare hawayenta tashiga yin abinda yakawota cikin farinciki da dokin dawowar mijinta Acikin mitoci kadan daki yakoma kaman bashiba kafin tashiga bathroom dinsa ta wanke mishi kayansa tsaf da kananun kayansa na ciki Taje farandar saman shi ta shanyasu tsaf tasaka abin kamawa ta kamasu karsu fadi kasa Tagyara bathroom dim ma tasaka kayan kamshi koina ya San anayi Kafin kuma ta koma falon tagyara tsaf yadawo kaman bashi ba sai sanyayyar kamshin dake tashi akowani lungu da sako na falon Sai da ta tabbatar ba inda bata gyara ba kafin tafito key din dake jikin kofar tacire ta cire ta kullo saman abinta Ta wuce da keyn har yanzu su Laila suna inda tabarsu Zata shige dakinta hajiya rukayya tace ke zonan yanzu agidanku haka kikewa manyanki Husnah tadago ido takallesu Batayi magana ba tayi shiru Dan taga ba abokan yinta bane Suby tace ke 'yar marasa kunya ba magana akemikiba Husnah ta kalle suby sama da kasa tace kekuma fa 'yar masu kunya ya akayi Laila tace kutuman uba lalle yarinyar nan ma kinsamu guri Uban me yakaiki saman dakin mijina Husnah ta tashi tsaye ta kalli Laila sama da kasa tayi dariya Tace ai gwamma da kika nuna min kece matar gidan Dan gaskiya na kasa tan tancewa acikin Ku hudun nan amma yanzu kinga nasani Maganar miji kuma point of correction mujimmu zakice please kina saka munjaye idan zaki furta kallma kamar haka Kafin ta kalli suby ta banka mata harara tace kekuma 'yar cin arziki banda lokacinki Tabuga tsaki tashige part dinta ta banko kofar Cikin tsananin tashin hankali Laila tace me yΓ rinyar nan take nufi da wai bata San matargidan acikin muhuduba Hajiya rukayya cikin takai ci Tace abinda kunnenku yabiya muku shitake nufi harda mukenan namuke nan ai mu hudu Suby ta yashi tana haki tayi kofar husnah tashiga bugawa da karfi Tace kifito Dan ubanki kiga yadda ake rashin kunya karamar 'yar iska yar talakawa kawai shasha Ita kuwa husnah ko jima batayi ba saboda tana bathroom tashiga wanka Hajiya suwaiba da tsufa yakamata sosai tace kai kai kedawo nan bakuda hankali ko Duk abinda kuka mata za ace mu ne muka saku Kuma kunga zasugane ba tuban Allah mukayiba Abinda nakeso daku kibari sai randa bama nan bamuzo ba sai Ku hadu kumata shegen duka dakanta zata gudu Kunga idan mukazo sai murufeku da fada sosai akan abinda kukayi Baku kyauta ba Hajiya rukayya tayi murmushi tace kai hajiyata Ashe haryanzu da sauranki a tunani kuma wallahi wannan shawarar tayi dari basa Dari Suby tace ai gaskiya idan nakama yarinyar nan saina fasa mata baki wallahi wai nice 'yar cin arziki Nan dai sukata gulmacensu Husnah kuwa wanna tafesa cikin wani tsadaddan material Wanda ummanta ta kawo mata Daga Sudan Ya hadu iya haduwa gashi dinkin ya kwanta ajikinta Daga tundaga samanta a matse yake Sai Daga kasan gwaiwarta aka sake irin dai dinkin amare idan zasu dinner Ta gyara gashinta cikin mayuka masu kamshi da dadawa Tasaka ribbon tadauki sarka ta metsada tasaka Rabin kirjinta awaje suke amma cikin net Wanda akayi ado dashi har wuyanta Wanda akecewa high neck Sai da tagama komai tay sallar magriba Dan taji anata kira Ta dauki tiren abinsu tayi waje saida ajiye akasa tasaka ta kullo sashinta kafin tayi saman mijnta Dining din saman tajera komai cikin wayewa da Jan hankalin mecin abincin Kafin ta dauko remote din TV kunna ta dauko tasaka tashar sunna TV Kafin ta fito bayan ta kullo kofar da key guri tasamu itama zauna a falon ganin ta zauna yasa duk suka dawo da kallonsu kanta Itakuwa husnah bata San Allah yayi ruwan tsiransu ba Tadauki wayarta tana watspp tashiga group din mutuniyarta wacce tazama mata kamar roll model dinta wato ummu afan Wani littafi ake turowa maisuna 'YAN BIYU NE kuma husnah tana bin novel din daki daki Tana balain son NANA DA SAMHA jarumar cikin novel dinne Gaskiya itadai zata iyacewa novel biyune sukamata a rayuwarta Daga 'YAN BIYU NE Sai kuma 'YAR MAKARANTA wacce ficacciyar marubuciyar nan ta rubutashi wato UMMY KHALEEL Gaskiya mutanen biyu tana matukar alfahari da littafinsu Tana ta karatunta na novel dinta inda Nana tama Hussain karyan rashin sallah Sai kawai taga ankarbi wayar an rada da kasa Husnah tabi wayar da kallo kafin ta kalli wacce ta karba wayar Laila ce tsaye tana karkada jiki tace nafasa kozaki yi magana nane Husnah tayi murmushi tace kodaya abinda baninasayaba Wanda yasai wannan shizaisaje sayan wani kinga kuwa ai basai nayi magana bako Laila tayi tsaki saiya saya mugani ai wallahi bai isa yasai miki waya a gidan nan ba saidai kizauna haka ba wayar Husnah tace to Allah yakawo sauki Kafin Laila tace wani abu prof yayi sallama yashigo Idonshi direct kan babynsa suka sauka itakuwa Husnah ta shi tayi cikin tafiyanta mai kara rikitashi Ta isa gurin prof ta fada kirjinshi Cikin tsananin mamki Prof ya ajiye jakar hanunshi shima ya rungumeta da kyau yana ajiyar zuciya Husnah tadago kai tace sannu da dawowa Kasa amsawa yayi saboda mamakin Husnah Itakuwa husnah ganin haka yasa ta sunkuya tadauki brief case Dan daya yar takama hanunshi shikuwa prof binta kawai yake harzasu haura sama husnah tace sweet baka gaidasu hajiya ba Har ga Allah prof bema san da mutane a falonba Laila datayi suman tsaye baki kawai tasake da ido tana kallon ikon Allah Hakeem yayi murmushi yakalli su hajiya suwaiba da hajiya rukayya ya ce sannunku hajiya hankalina yayi gaba bangankuba Sam Hajiya rukayya tace inazaka ganmu ai hankalin ka baya taredakai Nan ya gaishe su kaman karsu amsa amma dai gudun tuhuma yasa suka amsa mishi Suby tsabar haushi ko gaishe shi batayiba bare uwar gayya datakasa magana Kota Kansu baiyiba yajuya zai haura sama saiyaga wayar Husnah a tarwatse akasa Yace garin yaya kuma wayarta yafashe Caraf hajiya rukayya tayi tace ai da gangan tafasashi munata mata magana tace ai tagaji dashi tana ce Kasai mata wata zaka saya Shine fa Laila ta mata magana akan abinda tayi fa almubazzaranci ne shine fa tahau zagin Laila Laila zatayi magana nace tabarta yarinya ce ai Tana gama was Hakeem wannan bayani Yayi murmushi yace oh baby rigima aidata fada ma da nataho matadashi amma bakomai barin ci abinci nayi wanka saimuje nasaya mata wani Ya kalli Laila yace kekuma data zaga kiyi hakuri kamar yadda hajiya tabaki hakuri Dan yarinyace Ya kalli suby yace ke tashi kigyara wajen data fasawayar Yayi haura sama abinshi Dan tunda yatsaya gaisuwa husnah tashige da brief case dinsa Yana shiga falomshi nasama yaji wani sassanyar kamshi mai ratsa zuciya Tabbas yasan aikin husnah ce wannan Dan tunda aka zuba kujerun falon nan yana jinma ba ataba share waba duk da ba azama sosai amma ai yana bukatar gyara Yana shiga bedroom nan ma mamaki yakasheshi ganin yadda komai tas Ya kalli koina fes Husnah tafito Daga bathroom din shi tanufo shi tashiga cire mishi takallmimsa da cire mishi bottle din suit dinshi Har neck tied ita tacire mishi Shidai Abdul mamakinta yakeyi kuma yakasa magana saida yarage saura farin naciki da wandon suit din Ta kwashe Sauaran ta ajiyesu Indayakamata Kafin tace kashiga wanka kafito kacin abinci Tana fadar haka tayi hanyar kofa Hakeem yayi wuf yakamota Suna fuskantar juna ya kureta da ido takam takasa kallonshi Yakai bakinshi kun nan ta yace thanks my wife Husnah dai kanta a kasa yazaunar da ita bakin gado yace bana son kitashi kijirani harsai na fito OK Husnah tadaga kai Ya sumbaceta kafin yashige bathroom Husnah tana dubawa kan side bed taga phone dinshi Tadauka tahaye gadon tana kallon hotuna duk yawancin hotunan natane abin ya matukar bata mamaki yaushe yasamu wadan nan hutunan Dan itadai bata san lokacin daakayisuba Ganin hotunan meenat taredashi ranar graduation dinsu Abin yamatukar bata mamaki Kardai AMINA ABDUL HAKEEM itace 'yar shi Caf ai idan haka ta kasance zanji dadi duk wani masoyina dole yaji min dadin wannan Abu Tana ta murmushi itakadai har prof yafito Daga wanka yaga tana kallon wayar tana dariya koba fada mishiba hotuna take kallo Karasowa da ruwan jikinshi ya hauro gadon ya kwanto da ita akan kirjinshi Yace meyabaki dariya baby Tace bakomai Ta budo hoton amina tace wannan fa kasantane Yayi murmushi yace kice kinga kawarki ko Maganar taba husnah mamaki daman yasan amina kawarta ce Husnah tace muna dai gaisawa amma bakawata bace Sai ta wayance tace kasanta ne Yace 'yarkice she is my daughter Tana aure a kano sunyi tafiya da mijinta Zakiganta wataran ,ita kadai Allah yabani Kidage nan da nine months kibani baby kaman ke Husnah ta boye fuska Ta yi saurincewa muje kaci abinci Hakeem yashirya cikin farar jallabiya Kafin yaja hanunta sukayi dining Sosai yaci abinci amma fa saida yatabbatar takoshi kafin yafara nashi Tundaga kan dining din wasa yafara canja salo Cak yadauketa zuwa bedroom Daga nan kuma sukayi bathroom Dan yin alwala Hummm Next page Your comment is needed fans Love you allπŸ‘πŸ‘πŸ€²πŸ˜˜πŸ˜β€ [05/05, 8:59 PM] UMMU AFAN 🌹: πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ— BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Story & written By The special writer UMMU AFAN πŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ“š 🌹FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION🌹 🌹🌹 (F.C.T.W.A)🌹🌹 🌹HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION🌹 πŸŽ—I DEDICATE THIS PAGE TO YOU sis Fatima Umar ina alfahari dake wajen comments mai Allah yabar zumunciπŸ‘πŸ˜˜ (πŸŽ— πŸŽ—AKWAI LOKACIπŸŽ— πŸŽ—PAGE to116 to 120πŸŽ— DUK wani taimako da uwa yakamata ta wa 'yarta mummy tama Husnah Ta hada mata hadaddan tea maikauri da farfesun kayan ciki Yasha kayan sirrin na mata Ta lura husnah kunyarta take sosai Sai ta wayance Tace ai zazzabi ba dadi husnah bama saimunje asibitiba Zazzabin nan nayanzu ai sai a hankali Sannu kinji Ganin kaman mummy bata gane ba yasata saki jikinta taci abincinta Tasake komawa bacci a gadon mummy Ranar dai Husnah taga tattali da gata Kuma alhamdullila gaskiya taji dadin jikin sosai Mummy taki tabarta tafito ma ko falo Laila kuwa tana farfadowa tafara kuka jikin hajiya rukayya Tana shiga uku hajiya shikenan sun rabani da Abdul Hajiiya rukayya tace audama sabodashi kike kuka asararrariya Ni ma dauka saboda dukiyarsa kike kukar wani so ana zaune kalau Nan sukayita mata fanfo Hakeem zaune a office sai Ahmad yace amma gaskiya natayaka murna wallahi Dasamun kan madam yanzu zaka bani labarin yadda zama da mata biyu yake konima zansamu nakara Hakeem yayi murmushi yace baka da hankali kai kuma wani aure zakayi sha'awar yi Ahmad yace wallahi ba abun da Aisha ta rageni dashi kawai dai sunna nakeson cikawa Hakeem yace tonidai baruwana Nan Hakeem yadauki wayarshi yakira mummy yace mata yajikin Husnah tace Bansaniba marakunya Hakeem yayi murmushi yace haba daliba toshikenan ina babyn Mummy tayi murmushi tace tana bayana Hakeem sosai yayi dariya Dan yasan mummyn shi da caka magana Mummy takashe wayarta Ahmad yace waye balafiya Hakeem yayi dariya yace Husnah Yana murmushi ya lumshe ido kawai Ahmad yace wallahi young Prof kabimusu 'ya a hankali fa she is very young fa Hakeem yabude idonshi tar yace innan bita a hankali ai bazata saba da mijinta ba kullum tsorona zataji amma intariga ta saba she is always welcome me Ahmad yace lalle ma mutumin nan Allah yataimaki 'yar mutane daba ita kadaibace aida ka karar musu da yarinya Hakeem yayi murmushi yace bazaka fahimta bane Nifa Allah Allah nake ma daddy sugama ganawar nan da shugaban kasa yazo mutafi gida Ahmad yace taresuke da daddyna ko Hakeem a suna tare Ahmad yace OK nima barinjirashi kawai muwuce tare Ahmad yace wallahi kabar yarinya nan nayau dai karka koma Hakeem yayi murmushi yace caf ai hakan ma ba zai yiwuba Tashi muje karani nasiya mata waya Nata ya fashe MEENAT kwance kan bed dinta suna waya da antynta suby tana ta bata labarin abinda kefaruwa da uwarta Meenat ta fashe da kuka tace meyasa daddy zai ma mummy haka duk da dadewar dasukayi tare saboda yayi are shine zai wulakanta ta Suby tace kedai bari kawai ai daddynki ya canja hali sosai Kuma duk ba laifinsabane akan wannan 'yar figigiyar yarinyar da yakawo ne Kokefa zaki girmi yarinyar nan Meenat tace nashiga uku wallahi nazo gidan nan saidai daddy yazaba ko mu ko shegiyar yarinyar Suby tace gaskiya dai kam tunda ke 'yarsa sace ai watakila yaji maganarki tunda ai duk haukarshi bazai zabi mata yabar 'yaba Meenat tace munkusa da wowa muna sauka a kano zanyi Kaduna inzo karuwar da ake wa mummyna wulakanci saboda ita Bayan sunkashe wayar ne Meenat tacigaba da kukanta Ita abin ma yamata yawa ga wulakancin da bashir yakemata Dan idan baidaketa sau biyu to zaikai uku kullum Baya cin abincinta baya hira da ita Inya zauna bashida magana saina Asmau Asmau Tana cikin tunaninta bash yashigo Yana ganinta yadauko ruwa mai tsananin sanyi a fridge ya kwarama ta tashi ra wan jiki Tace Dan Allah uncle menamaka ka tsanani haka auren soyayya mukayifa bana kiyayya ba Bash yamata wani matsaya cin kallo yace wallahi bansan ya akayi har nawa masoyita wulakanci saboda jaka irinki ba wallahi Ke wai dan uwarki ma ya akayi har naji banason ganin kowa saike ne har na aureki na bar asmau Meenat ta yi tsilli tsilli da ido Yace ba magana nake mikiba bazaki ban amsaba yashakota idon meenat yafito tace wallahi ba abinda namaka Bash yasaketa yace wallahi duk ranar da na tabbatar da abinda nake zargi tattare dake zanbaki mamaki Mutum daya nakejin kunya shine babanki Mutumin kirkine Da Dan uwarkice da kakanki da na Dade da kada ki gida wallahi amma yanzu zanmiki uziri har na tabbatar da zargina akanki tukun Maganar auren da babban ki yayi audole yayi aure indai mata irin uwarkice saikace akuya namaga kokarinsa da ya iya hada jini da dabbar matar Cikin tsawa meenat tace ya isheka haka bashir kamin komai amma karkasa uwata aciki Kafin ta rufe baki bashir yakai mata duka abakin fas Aikuwa ta kwalla kara saboda azaba Yace kuma kifara hada duk wani tsummo karanki Sati maizuwa zamu koma gida Yasa kai yafita abinshi Sosai amina take kuka ba mai rarrashinta Dadin data jima sati maizuwa zasu bar kasar Zataje takakkarya wacce tayi kasadar zama kishiyar uwarta *** Hakeem da daddy sukayi sallama suka shigo Mummy da Husnah suna hira a falon Husnah tagaida daddy ya amsa cike da kulawa Tareda mata yajikin Hakeem kuwa kureta yayi da kallo Dan sake canja mishi tayi wuni daya kawai Husnah kuwa tana gaida Hakeem tayi sama dakin mummy abinta Tana shiga bedroom din mummy tafada kan bed abinta Hakeem kuwa suna gama cin abinci yaki tafiya har daddy ya haura sama Yazama daga shi asai mummy hafsat mumme tace wai bazaka je ka kwanta bane Hakeem yasosa keya yace mummy tafito mutafi mana Mummy ta harareshi tace da tare kuka shigo Tariga tayi bacci katafi kawai abinka Hakeem zaiyi magana mummy tace kaga nikam saida safe indan kafita kaja min kofa Hakeem badan yasoba yaja kafarsa yayi part do shi Yana shiga ya tarrar da suby da Laila sunkasa sun tsare Dama abinka da wanda yake wuya Yanashiga yafara musu masifa Yace waiku bakuda falo ne kullum kuna falona saboda tsaban fituna ko Laila tace au dama akwai inda aka mana iyaka dashi ne agidan Ya kalleta ya balla mata harara Ya haura sama Suby ta kalli Antin tata tace yaufa abin ya motsa miskilancin Laila ta tabe baki Hakeem bayan yagama shirin kwanciya Ba abinda yake tunanin husnah Da irin farin cikin dayasamu tattare da ita Wayar da yasiyo mata yadauka yacire yasama a acaji Dan yacika wayace metsadar gaske **** Washagari da daddare karfe takwas na dare bayan sungama ma dinner Mummy ta haura sama gurin husnah tace Tace kinkunta ne husnah tace a mummy Mummy tace Allah yatashe mu lafiya kafin husnah ta amsa wayar mummy yayi kara taduba taga Hakeem Nan dai mummy tayi murmushi bayan sungama wayar ta kalli husnah tace kije mijinki na kiranki wai yasayo miki waya Husnah gabanta yafadi ras tace mummy yabari gobe zankarba Mummy tace kedai jekikarbo kidawo kiyi kwanciyarki Husnah tace to mummy tafita zuwa falon mummy baya falo ta wuce sashinsu Dan tasan yanacan Tana shiga taga su Laila da suby suna kallon Hausa film Tace sannunku Duk suka kalleta suka buga mata tsaki Husnah bata bitakansu ba ta huce zuwa saman gurin kiran mijinta Suby tace anty yau bakwanankibane naga wannan 'yar talakawar ta haura Laila tace kwarai kuwa barinje naga ikon Allah Husnah tana shiga bedroom din taganshi kwance daga shi gajerar wondo Yana danna waya ganin shigowarta ya kura wa mata ido itadai bata son suhada ido Tanemi gefe ta zauna tace gani yaya Yatashi ya ajiye wayar agefe Yakamota yace wai guduna name kikeyi ne baby Husnah tayi shiru yace bazaki magana ba ko Kafin husnah dake kwance kan kirjin Hakeem tayi magana Laila tashigo dakin ko sallama babu Hakeem yace o my GOD wai yaushe zakiyi hankali ne Laila bance karkisake shigo min daki a wannan lokacin ba Laila tace taya za ayi nayi tunanin yin sallama bayan kana kokarin cin amanata Hakeem kalleta yace kamanya cin amanarki dawata kika kamani koda matata Tace duk da matarka ce ai yakamata kasan yau kwanana ne Yace OK dama abin kenan Saikije kifara kirgawa daganan zuwa 5 day's saikufara raba kwana Dan ita yanzu take amarya Kinga kuwa sai ta min 7 day's kafin kufara raba kwanan So fita kiban waje ganin da gaske yakeyi Ta juya hade da banka wa wa husnah harara Ta banko kofar tayi waje Hakeem yabita da kallon takaici Ya dawo kan husnah yace nadawo kanki kekuma meyasa jiya kika gudu dakin mummy Husnah tace nima fa gigin baccine bani najeba Hakeem yayi murmushi yace ko Tadaga kai sama ya dauko wayarta da yasayi mata yabata cikin nuna jin dadi da wannan kyautar da yayi mata tace Allah yakara budi Bata gama godiyar ba ya hade bakinsu guri daya yashiga sarrafata Duk yabi yagigitata da salon soyayyarsa kafin yatashi yaje yasamusu key a can kofar falon Yauma fa basauki husnah takwashi kashinta a hanu saidai da sauki zafin bakan nafarko ba Sosai tasha tattali itakuma sai shagwaba take zabawa son ranta Da asuba bayan yadawo daga sallar asuba sunyi karatun alkur'ni maigirma Yajata kan bed yace baby kinbani komai arayuwata ba abinda zance saidai Allah yabar minke mutukaraba Yadauko wasu files da takardu acikin yace karba wanna tace nameye wannan Yace tukwicin first night dinki ne Tabude taga takardun company ne da takardun gidaje guda biyu Saikuma mukullin motoci guda biyu Sai kuma kufi a account har Naira million goma Husnah ta tashi daga kwanciyar datake Ta ajiye mishi takardun tace haba yayana ta durkusa agabanshi tasa hannayenta kan laps dinshi tace karkamin haka hakkin ka nefa danme kenanma kabiyani karkasa Allah yayi fishi dani fa Kuma ma wallahi abubuwan nan sunyi yawa sungirmi tunanina aikosu mummy ma saisuma fada Dan naga kaman kayi almubazzaranci da dukiyarka Hakeem baki kawai yasake yana kallonta tabbas Allah yabashi matar da iyayensa suke mishi fata Ya kamota yadawo da ita yace baby kinsan wani Abu da izinin daddy da mummy na miki wanna kyautar shima daddy yabaki filayensa guda biyu dake abuja Mummy kuma tasaya miki zinare duk kuma sunabani nabaki aibaki gama kallon kayan ba tukunnan Husnah takai dubanta kan sauran dayake nuna mata Cike da tsnanin son mijinta ta ta kwanta ajikinshi Tace Allah nagode maka daka hadani da mummy da daddy amatsayin iyayen mijina sunasona tamkar susuka haifeni Sanna kuma Allah yabani masoyina alokacin danake tunanin na rasashi Allah na gode maka da kabani ya mu'allim dina a matsayin miji Dasauri Hakeem yadago da fuskarta suka kalli juna tace kayi mamaki ko Next page Your comment is needed fans Love all πŸ“–πŸ“–πŸ“–πŸ“πŸ“πŸ“ [05/05, 8:59 PM] UMMU AFAN 🌹: πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ—πŸŽ— πŸŽ— BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM Story & written By The special writer UMMU AFAN πŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ–ŠπŸ“š 🌹FIRST CLASS TECHNOLOGIES WRITERS ASSOCIATION🌹 🌹🌹 (F.C.T.W.A)🌹🌹 🌹HOME OF QUALITIES AND TRUSTED WRITER'S OF THE NATION🌹 πŸŽ—I DEDICATE THIS PAGE TO YOU HUSNAH ina matukar alfahari dake Allah yabar zumunci Kicigaba da comments dinki mezafin nan πŸŒΊπŸŒΉπŸŽ— πŸŽ—AKWAI LOKACIπŸŽ— πŸŽ—PAGE 111 to 115πŸŽ— Suna idar da sallah bayan yayi adduoin da yakamata miji yayi akan matarsa Cak yadauketa sai kan bed bayan yacire mata hijabin Ganitayi ya bude wani Dan karamin akwati shima maishegen kyau yadauko wasu sleeping dress masu kyau da tsada kamshi ne kawai yake tashi ajikinsu Ya matso dai dai kun nanta yamata rada komai yafada mata oho Gani nayi kawai husnah ta ce a a zansa da kaina Murmushi Hakeem yayi yace oya tashi kisa Tace nidai gaskiya kadaina kallona tukun ya rufe idonshi da tafin hanunshi Can kuma sai yace minti biyu sweet yanzu zandawo Yasauka can kasa har yanzu suna falon basu tashiba aranshi yace wai wadan nan mutanen suna da hankali kuwa Zai wuce yace sannunku hajiya Suka amsa dacewan Yauwa sannu dai anfito kenan Yace a amma yanzu zandawo Abu zan dauka a mota ya wuce yafita Sai yashigo da wasu manyan ledoji guda biyu Yana falon yace wa Laila ganata Ya haura sama abinshi Laila tsaki tayi tace kakusa Shiga hanu Suby tace to wannan ledar da ya haura dashi kuma fa Laila tace ta wannan yar talakawar ne mana Suby tace wallahi kibishi kice ina nasu hajiya tunda ai yagansu a falon aikuwa Laila ta tashi tayi saman Dai lokacin da Hakeem yake ba Husnah nama ta banko kofar tashigo aikuwa Husnah ta tsorata sosai bata San lokacin da kankame Hakeem ba Shikuwa Hakeem kallon kofa yayi yaga Laila ce yace kewace irin dakikiyace Laila Zaki shigo wa mutane daki ba sallama Laila tace nida dakin mijina sainayi sallama zanshigo Saboda kana tare da 'yar matsiyatar Me zubin karuwar yan tasha Cikin zafin nama Hakeem ya tashi yazabga mata mari yace. Kinmanta wanene Abdul Hakeem ko To wallahi zanfada nafarko na karshe duk randa kikasake kiran matata da wannan sunayenda kika ambata ranki inyayi dubu zai baci kuma a ranar ne zakisan waye Abdul Hakeem shasha kawai Get out my room right now Karkisake shigomin daki batare da kinyi nocking

Chapter 2 of 9