Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
6 / 9
had’iye da ya tuna yanda take sarrafa mazaunanta, da k’irjinta. Tabbas Allah yayi halita a gun, cikin zuciayrsa ko cewa yake”wannan taci a kirata da zallaziya ko zank’aziya hmm wannan tamk’ar ita tayi kanta. “Gaskiya ta had’u ba k’arya. “Gashi ta had’a duk wani abunda nake so ajikin mace amma taya zan tink’areta?. “Hmm ni shakkanta na ke ji ma yanzu. Wata zuciya tace”to ko kana jin shakkanta sai ka tin k’areta, ai girmanka zai zube. Yana tsaye tazo ta wuce sa, motarta tashiga sai da ta yi ribas, kafinta ta da kura ta bule Haiydar ta wuce da gudu. Haiydar ko gizau baiyi ba ila bin motarta da kallo. Zuciayrsa tana masa wani irin abubuwa nai wuyan fasaruwa, kasa motsi yayi don duk jikinsa ba k’wari. Masu karatu wai shin wata yarinyace wanna, da har zata iya taka Haiydar, ta masa wannan wargin batare da ya d’au mataki ba?. Don son jin wannan amsar ku biyo ni. *DEDICATED TO* *AISHA MUHAMMAD* *(MAMAN ABDUL SHAKUR)* *RASH LUV * [2:32PM, 9/14/2016] Rash Kardam: [7/8/2016] Rash Kardam BABBAN KUSKEREN DANA TAFKA NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM ®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION. Pg-180~183. Da k’yar Haiydar ya iya jan k’afarsa, zuwa gun motarsa ya shiga. Yana shiga motar sai da ya d’an zauna, don gabad’aya ganin Aisha, ya haddasar masa da kasala a jikinsa. Kansa ya d’an jingina a steering motar, ya lumshe idanunsa, ba abun da ke gani illa fuskan Aisha, da suran jikinta, suna masa gizo a idonsa. Imagine ya farayi, wai ga Aisha tazo, cikin tafiyarta mai burgewa, kusa da shi tazo, tana masa k’wark’wasa, sai da ta matso kusa dashi, kiss ta manna masa a baki. Shiko sai wani murmushi ya saki, tare da k’ara lumshe ido, wayarsa ce tayi k’ara, sai da yaja karamin tsaki, don bai so ya katse tunanin da yakeyi ba. Ni ko Rash nace”da ka tafi sabgar gaban ka ne, da zaifi maka wanna kayan jaki da karan. “Don yanzu Indo ta maka nisa, yanzu Indo matar manya ce. Wayarsa ya zaro, sunan Falmi ya gani akan scream d’in wayan, tsaki yayi kafin ya d’aga wayar. Cikin muryansa da ba yabo ba fallasa yace”hello ya akayine?. Daga b’an garen Falmi tace”Haiydar pls ka turan kud’i a cikin account d’ina, ina….. Bai bari ta k’arasa ba ya katse kiran. Ransa duk ya gama b’aci, sai huci yakeyi, cikin zuciyarsa ko cewa yake”wai ya rinyan nan tana da hankali kuwa?. “Bata san hakki na da ke kanta, ta sauke ba amma ta iya tambayan kud’i?. “Rabon da Falmi ta zo d’akina na manta, wai sai kasuwanci ta saka a gaba. “Dole in d’au mataki akan ta. Motarsa ya ja ya fice abunsa, zuciyarsa ko sai zafi take masa, don shi yanzu ya gaji da halin Falmi, ta soma hawan masa kai sosai. Aisha ko tana fita daga gidan, gidan Hajiya ta wuce, tana shiga ta perker motar ta fito. Masu aikin gidan sai sannu suke mata, cikin girmamawa ta amsa musu. Cikin falon ta nufa, da sallamarta ta shiga falon, Hasna da ke goge TV da gudu tazo ta rungumeta, tace”haba Aunty eeshat kinanan kwana biyu?. Aisha tace”washhh nikam sakeni karki karyani, gwamma ke. Hasna ta saki dariya. Aisha tace”Hasna ina Hajiyata ban ganta ba?. Hasna tace”ta tafi dubiyar maralafiy. Aishat tace”Allah ya dawo da ita lafiya. Hasna ta kalli Aisha sama da k’asa tace”Baby Eeshat irin wannan wanka haka?. “Gaskiya zaki rikita Yayana. “Hmm Aishat duk gayuna yanzu kin d’aramin sosai, sai dai mu biyo bayanku. Wani lalalusar mirmushi Aishat ta saki tace”ke ban son iskanci fa. Hasna tace”gaskiya ne ae, ko da yake hausawa sunyi gaskiya da sukace, bakauye bai iya wayewa ba. Cikin zolaya tayi maganan, dariya suka saka dukkansu. Aishat tace”barin je gidansu Sanah suna jirana zamuje saloon ne. Hasna tace”okay! To sai kin dawo. Har jikin motarta Hasna ta rakata, tashiga ta ja motar ta bar gidan. Hmm masu karatu kenan Indo mu na da ne tawaye. Gidansu Sanah ta shiga, tana ajiye motar tashiga gidan, Sadeey tace”ae na d’auka bazakizo ba. Rausayar da kai Aishat tayi, tare da had’a hannu alamar ban hakuri, tace”tuba nake amin afuwa. Sanah ne tafito da gyale suka wuce, sai yamma suka dawo, sai da ta ajiyesu a gida ta nufi gidanta. Tun a harabar gidan, taga motar Haiydar yadawo, cikin zuciyarta ta fara tsara irin rikitasa da zatayi yau. Tana shiga gidan bakowa a falo, side d’inta ta nufa, kaya ta cire tukun tayi wanka, saida ta tsane jikinta, tukun ta zauna a gaban madubi, ta kusa d’aukan awa d’aya tana k’waliya. Three quarter ta d’auko tare da wani riga marar hannu, irin wanda ake d’auresa a wuya, rigan kalar ja, sai ta d’auko ribom ja ta d’aure kanta, bak’aramin k’yau tayi ba. Main falo ta fito, sai da ta kunna CD, ta d’auko kaset d’in waka tasaka, don niman magana ta k’ure speaker, don ta san Haiydar baya son hayaniya sosai. Kitchen ta shiga ta had’a zob’o, daman tayi girki kafin ta fita, a plate tasako a binci ta fito falo, ta zauna abinci taci ta k’oshi, ta tattara plate da cups d’in ta mayar kitchen. Falo ta dawo sai da ta huta, ta je gun speaker ta k’ara volume a hankali tafara rawanta, cikin salon k’warewa take gir- giza jinkita. Haiydar ko na bacci ya ji kid’a na tashi, har sai da ya toshe kunnesa, cikin masifa ya nufo falon, ko da ya iso falon kasa motsi yayi, don gani irin rawan da Aishat takeyi. Aishat kuwa ganin Haiydar da gan-gan tasoma matsowa kusa da shi tana rawa. ®NWA. *DEDICATED TO* *AISHA MUHAMMAD* *(MAMAN ABDUL SHAKUR)* *RASH KARDAM * [2:32PM, 9/14/2016] Rash Kardam: [7/8/2016] Rash Kardam : BABBAN KUSKEREN DANA TAFKA NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. ®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION. Pg-184~186. A hankalin take rawa, mai d’aukan hankali, harta iso gun Haiydar, hannusa ta kamo tana rausayawa tamkar yanda turawa suke in suna rawa. Kwanto da fuskanta tayi akan k’irjinsa tare da lakace hancisa, ta d’ago da kanta tazo dai-dai kumatun Haiydar, ta sakar masa lafiyayan kiss, wanda sai da numfashin sa ya kusa d’aukewa. Salon rawan ta canza zuwa na India, da gudu tayi side d’inta, don tasan in ta k’ara minti biyar agun, zata gane kurenta, don yanayin Haiydar ya canza. Haiydar gani ta yi side d’inta gashi duk ta gama rikitasa, da gudu yaje don ya tura qofar, amma kash! Saijin qofar yayi ansa key. Cikin dashashiyar murya ya fara k’iran”Aishat! Aishat! Aishat! Please ki taimaka min ki bud’e qofar nan, inason inga rawanki yamin kyau kuma ya burgeni, nayi miki alkawarin zan miki kyautar da baki tab’a tsamani ba. Ko mai kikeso nayi alkawarin zan bakishi dan Allah”. Aishat na jinsa ta shek’e da dariya, tazo jikin qofar tace”Ya Haiydar naki d’in ko ka manta bak’ar macece kuma ‘yar aiki ke rawa a gabanka, mai zata burge ka dashi a jikinta?”. Haiydar ya marairaice fuska tamkar mai shirin yin kuka Yace”komai zakice na yarda, ko wani irin horo zakimin, bazan damu ba, amma rawan ki ya burgeni”. Aishat na jinsa tayi banza dashi, ta hau kan gado ta kwanta tana murmushin mugunta. Haiydar ya jima ajikin qofar, kafin ya ja tsumar k’afarsa, ya bar qofar d’akin, don Aishat tak’i bud’e qofar, gashi duk ta d’aga masa hankali”mtss”. Ya ja tsaki, cikin zuciyar shi cewa yake”to mai yasa na fito ne ma?”. “Gashi na ja ma kaina ae, ita kuma ko tausayina ba zata jiba?”. Da wannan tunanin ya koma d’aki ya kwanta, duk abun duniya ya ishesa, don yanzu baida burin ganin kowa a gaban sa, sai Aishat dake rikitasa. Haka ya k’araci zamansa har lokacin sallah magriba yayi, sai da ya jira akayi isha’i kafin ya dawo gida, yau sam yaki shiga d’aki, jira yake ko zaiga Aishat ta fito, sai da ya kusan kwashe awa d’aya, a gun bata fito ba, har yana shirin tashi yaji alamar tana bud’e qofa, da sauri yaje ya b’uya yanda bazata ganshi ba. Aishat ko yunwa ne ya dameta, shiyasa ta fito ta had’a tea, mini skirt ne ajikinta, wanda dashi da babu duk d’aya ne(wai an karya matacce). Bata sa riga ba, sai yar bra top tasa, wanda ko cibiyarta bai rufe ba, duk k’irjinta na waje. Tafiya take duk ilahirin jikinta motsawa yakeyi, ta shiga kitchen ta had’o tea, falo ta dawo ta zauna, kafa ta d’aura d’aya a kan d’aya. Wanda hakan yasaka duk wanda ke saitinta zai iya hango kalar pant d’inta. Ganin irin zaman da tayi, saida Haiydar ya had’iye miyau, ji yake tamkar ya rugo da gudu, ya rik’eta, amma yana tsoron masifarta. Aishat ta gama shan tea ta d’ibi kayan taje kaiwa kitchen, Haiydar na ganin tashiga kitchen, sauri yayi yashiga d’akin ta ya kwanta akan gadonta. Aishat tana yar wakanta ta shigo d’aki, sam bata lura da mutum ba, harta tura qofar amma bata rufe ba, ta juya zata hau gado kenan, taga Haiydar a kan gadonta, ba k’aramin razana tayi ba, ta juya da niyar zata gudu kenan ya diro daga kan gado ya biyo ta. ®NWA. *DEDICATED TO* *AISHAT MUHAMMAD* *(MAMAN ABDUL SHAKUR)* *RASH KARDAM * [2:32PM, 9/14/2016] Rash Kardam: [7/9/2016] Rash Kardam BABBAN KUSKEREN DANA TAFKA daga www.hausaebooks.com.ng NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. *®NAGARTA WRITERS ASSOCIATION*. Pg-187~189. K’ofa ta ru fe, ta ju ya za ta hau kan gado ke nan, ta ga mutum a kwan ce, ba k’aramin razana ta yi ba, ci kin sauri ta ju ya za ta fita, Haiydar ya yi saurin dirowa da ga kan gado, ya kai ma ta cafka, amma kash! Ka fin ya iso, cikin za fin na ma ta fita. ‘Dakin da ke kusa da na ta, ta shi ga, key da ke ji kin k’ofar ta murd’e, cikin sa’a ya kullu. Haiydar ya na zu wa, ya sa mu har ta sa key, ya tsa ya ci za, sam bai so ha ka ba, d’akin ta ya ko ma ya kwan ta. Rigan baccin ta ya ga ni, hannu ya sa ka ya d’auko, kan hancin sa ya kai, ya na shin-shinan dadda d’an kamshin da ke jikin rigan. A haka har bacci b’arawo ya d’au ke sa. Aishat ko duk illahirin jikinta rawa ya ke yi, sai da ta kusa awa d’aya, ta zauna a bakin gadon, sai da ta yi addu’a kafin ta kwanta. Asuban fari ta mik’e tayi sallah, sai da ta ji Haiydar ya fita, kafin ta lallab’a ta koma d’akinta ta kulle. Wanka ta shi ga sai da ta ga ma ta fito, sama-sama ta shirya, uniform ta sa ka, ta d’au bag d’in ta, ko karyawa ba ta tsaya yi ba, ta fito bakin gate, Napep ta tare sai gidan Hajiya, da sallama ta tura k’ofar falon ta shi ga, da Hasna su ka fara karo, ci ke da mamaki Hasna ta ce”lafiya dai na gan ki da sassafe nan?. Murmushi Aishat ta yi ta ce”lafiya lau wallahi, yau sauri na ke yi shi ya sa ko ka yan breakfast, ban tsaya had’a wa ba”. Hasna ta ce” ina Bros d’ina fa?”. Aishat ta ce”ke barni yau ina sauri ne, yi ki had’a ma na breakfast ka wai, Hasna Hajiya fa? Tana ciki ne?”. Hasna ta ce”eh! Ta na d’aki”. “Okay! Barin shi ga gun ta, na gaida ta”. Da d’an gudunta ta haura step d’in, da sallama ta shiga d’akin Hajiya, ta samu tana karatu, a gefenta ta zauna, sai da Hajiya ta idar da karatun, Aishat ta ce”Hajiya an ta shi lafiya?”. Hajiya ta ce”lafiya lau, ya karatu?”. Aishat ta ce”Alhamdulilah! Mu na kai”. Hajiya ta ce” ya Haiydar d’in? Ina fatan ba ku na zaman lafiya, bai ta ku ra mi ki?”. Aishat ta ce”lafiya mu ke zaune ba wata matsala”. Hajiya ta ce”Alhamdulilah!”. Aishat ta ce” barinje na karya don zan wuce school daga nan”. Hajiya ta ce”to in kin gama karyawan ki min magana”. Aishat ta amsa mata tare da fita falo. Ita da Hasna su ka karasa aikin, su na hira har Aishat ta karya, lokacin Hajiya ta sauko, kud’i ta mika ma Aishat ta ce”ga shi ki rik’e ki na b’atarwa”. Aishat ta yi godiya ta fita. Driver ne ya kaita makaranta. Haiydar na dawowa da ga masallaci, ya ko ma side d’in Aishat ya na tura k’ofan d’akin da tashiga, sai ganin k’ofar ya bud’u, sa kai ya yi cikin d’akin amma me?. Sai ganin d’akin empty bakowa, d’akinta ya sa ke zu wa shi ma k’ofar a bud’e, sai ya d’auka ko wanka tashiga, kan gadon ta ya sa ke kwanciya, ya na za man jiran fitowarta. Shiru-shiru ba bai ji Aishat ta fito ba, bare ya ji karan ruwan wanka, tashi ya yi ya nufi bayin, k’ofar bayin ya tura, nan ma ya ga empty bakowa a ciki, tsoro ne ya kama Haiydar to ina Aishat ta je?. Ko dai ta na kitchen ne?. Da sauri ya yi hanyar kitchen, ko da ya je nan ma ba kowa. Ba karamin razana ya yi ba, ga shi time d’in fitar sa aiki ya yi, da sauri ya koma d’akinsa ko wanka bai tsaya yi ba, ya saka kaya, ya fito mota ya d’auka ya nufi gidan Hajiya, Ko da ya shiga a falo ya sa me su a falo, ya rusuna ya gaida Hajiya, Hasna ma ta gaida shi, Hasna ta sa ma sa abinci, sam kasa cin abincin ya yi, hankalinsa ya tashi, tunani ya ke, kardai ace Aishat ta gudu ne?. Tabbas da ya yi hauka, don yanda ya ke jin sonta a cikin zuciyarsa ba zai iya hakuri da rashinta ba, mikewa ya yi, ya mu su sallama ya nufi gun aiki. Ko da ya shiga office, bai iya tab’uka komai ba, key d’in motarsa ya dauka, ya nufi hanyan makarantarsu Aishat, ya na zuwa, bai wani samu matsala da mai gadi ba, don kakin police ne ajinsa. Ya na shiga harabar makarantar, ya ga mu da abokinsa Malami ne a makarantar, suna zuwa office ya masa bayanin Aishat Malamin ya ce”oh! Head girl ka ke fad’a?”. Haiydar ya ce” eh ita ce”. Malamin ya aika aka kirata, bata dad’e ba ta zo. Malamin ya basu guri a office d’in, Aishat wani mugun kalo ta masa, ta ce”lafiya Malam mai ya kawoka makarantar mu?. Miye alakarka da ‘Yar aiki, kuma ‘Yar shege?. Haiydar ba na son ganinka, i hate you”. Nan ta ke ya ji zuciyarsa na tafarfasa, don jin kalamanta ya ke, har cikin kwakwalwan kansa, cikin tsawa ya ce”ya isa haka!, Aishat mai ya sa bakya tausayina ne?. Aishat in kinji yanda zuciyata ke bugawa a kan k’aunarki. Please ki taimaka ma rayuwata, ki yi kahuri da abunda ya faru, ki manta komai dan Allah!”. Wani kalon banza ta sama nai nuna alamar baka da wayo, juyawa tayi za ta fita, cikin hanzari ya sha gabanta, matsawa ta soma yi, shima ya na binta, cikin dakiyar zuciya tace”wai lafiyanka kuwa? Wannan wani irin iskanci ne haka?”. Haiydar ya yi wa ni murmushi, ya ce”Aishat ko kin manta matsayina a gunki? Ni fa mijinki ne na sunnah, kuma ina son inji d’umin jikin matana a tare da ni”. Cikin tsiwa Aishat ta ce”Allah ya sauwake wa ye za ta had’a jiki da kai? Wai ko ka manta Aishat ‘yar aiki ce? Cikin zafin na ma Haiydar ya matso kusa da ita, hab’arta ya kamo. Kuyi hakuri da wanna ba yawa, yau ina bussy ne. *®NWA* *DEDICATED TO* *AISHA MUHAMMAD* *(MAMAN ABDUL SHAKUR)* *RASH KARDAM * [2:32PM, 9/14/2016] Rash Kardam: [7/10/2016]Rash Kardam BABBAN KUSKEREN DANA TAFKA NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. *®NWA.* Pg-190~193. Cikin tsiwa Aishat ta ce”Allah ya sauwake, wace zata had’a jiki da kai?. Wai ko ka manta Aishat ‘Yar aiki ne? Kuma ba’kar mace, wanda bata waye ba, marar ilimi. Mai zakayi da ni Indo?”. Cikin zafin nama Haiydar ya riko hab’arta, ya ce”mai ki ka ce?”. Aishat ko alamar tsoro babu a tare da ita, ta sake mai-maita abunda ta fad’a. Haiydar ya sassauta murya ya ce”Aishat always be the first to forgive the other person”. Wani mugun kalo ta masa ta ce”oh! Yanzu ne kasan da haka? Ko ka manta irin tsa….. Bai bari ta k’arasa ba, ya toshe mata baki da hannusa. Aishat hannu tasa tare da zage iya k’arfinta ta turesa, sai da Haiydar ya d’anyi tangal- tangal kamar zai fad’i. Aishat tana kaiwa bakin k’ofar office d’in, ta juyo tare da rike k’ugu, ta ce”Haiydar ni Aishat ba tsaranka ba ce, a yanzu ne na dawo mutum? Kasani kwarya ta bi kwarya, kuma *DAI-DAI RUWA DAI-DAI GARI*. Ni Aishat Yar shege ce kuma bakace ni, sai kuma nayi sa’a baka son ba’kar mace, to mai za kayi dani?. Haiydar duk ya rasa inda zai sa kansa, hannusa ya had’a biyu alamar hakuri. Aishat ta aika masa da harara ta ce” Aliyu kake da suna ko? To ka sani wutsiyar rakumi tai nesa da kasa, da ga yau sai yau, karka kara shiga sabgata, kayi hanyarka nayi tawa mtsss”. Ta saki tsaki ta fita abunta ko ta wai- wayesa. Haiydar dafe k’irjinsa yayi, don zuciyarsa wani irin zogi take masa, kujera ya nima ya zauna, ya lumshe ido, a haka Abokinsa yazo ya samesa, fuska yayi ya b’oye damuwarsa, sallama yayi ma Abokinsa tare da masa godiya ya fito ya bar makarantan. Aishat ta na shiga class da Sadeey suka fara karo, Sadeey ta ce”ya dai lafiya? Mai ya sameki?”. Aishat batace komai ba, Sanah ce ta shigo class d’in, da sauri ta k’araso gurinsu ta ce”Aishat lafiya kuwa yanzu naga Haiydar zai shiga motarsa a school d’in nan? Ko dai shi ya aika a kiraki?”. Aishat taso ta b’oye musu amma jin Sanah taga Haiydar, kawai ta sanar musu komai. Sanah ta ce”Aishat ba wai ina had’a ki da mijinki ba, gaskiya karki kuskura ki basa fuska, yanda ya wulakanta ki, ya kamata ki rama kema, ki basa wahala har sai ya gane kurensa, don baiyi nadama ba tukun da sauransa”. Sadeey ta ce”gaskiya kam”. Haka sukayita hira har lokacin tashi yayi suka fito. Haiydar ko da kyar ya iya jan motar ya koma gida, don ko ya koma office ba zai iya aikata komai ba. ‘Daki yaje ya kwanta tunani yake kala-kala, cikin zuciyarsa ko cewa ya ke”ya zanyi da k’aunar Aishat da ke baraza ga rayuwa ta? Duk wanda yayi yunkurin rabani da Aishat, to tabbas na san baya k’aunata, barema in Allah ya yarda ba abunda zai sa na saketa, ko da zatayi ta gallaza min a haka”. Aishat ko tana tashi daga makaranta gidan Hajiya ta wuce, a gun ta yini, sai yamma ta koma gidanta, ta na zuwa d’akinta ta shiga, wanka tayi kafin ta fito, kitchen tashiga ta girka kuskus da miyan stew, falo ta fito ta zauna tana cin abinci, Haiydar ya d’an kwaso yun warsa ya ga Aishat tana cin abinci, cike da isa ya ce”ke tashi ki zubo min nawa”. Banza tayi dashi kamar bata jishi ba, ganin bata da niyar tashi, ya ce”in fa bazaki zubo min ba, to zan kwace naki”. Nan ma bata ce masa ba, ganin haka yayi kanta zai kwace abinci da gudu ta mike ya bi bayanta. Dai-dai lokacin Falmi ta sanyo k’afarta cikin falon, dai-dai lokacin kuma Aishat ta iso gabanta, turus suka tsaya dukkansu a gabanta cike da tsoro a fuskansu, jakan da ke hannuta ne ya fad’i a kasa, ba k’arami gir-giza tayi da ganin su haka ba. *®NWA* *DEDICATED TO* *AISHAT MUHAMMAD* *(MAMAN ABDUL SHAKUR)* *RASH LUV * [2:32PM, 9/14/2016] Rash Kardam: [7/11/2016]Rash Kardam BABBAN KUSKEREN DANA TAFKA daga www.hausaebooks.com.ng NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. *®NWA.* *Pg-194~196* Ba k’aramin razana tayi da ganinsu cikin wannan yanayi, Aishat ta razana amma shirin ko ta kwana da tayi, hakan yasa ta shanye damuwarta, ta juya sai murgud’a jiki takeyi, ta kama hanyan komawa falo, Haiydar ko yanuna damuwarsa, shima ya juya da niyar komawa cikin falon. Falmi da sauri tasha gabansa, cike da masifa ta fara ce wa”Haiydar asai baka da mutunci? A sai kai d’an iska ne? Maciyi *AMANA*. To asirinka ya tonu, karasa wacce zakana bi sai Yar aiki na?”. Wani mugun kalo ya sakarmata, bai tanka mata ba yabi gefe zai wuce, da sauri ta sha gabansa tare da shan kwalar rigansa. Hannunsa yasa ya b’amb’are hannuta daga jikin rigarsa, da sauri tasake tare gabansa, Haiydar ya ce” Falmi ki bini a hankali duk wani rashin kunyar da kike take, tsaf zanyi maganinsa, karkiga na kyaleki kina yanda kikeso, kice zaki takani son ranki, a k’ark’ashina kike”. Wuceta yayi ya nufi d’akinsa, sam shi baya son hayaniya. Falmi ganin ya tafi, ta juya gun Aishat daniyar mata rashin mutunci. Aishat ko ta d’aura kafa d’aya akan d’aya, Falmi ganin irin zaman da tayi gashi k’ananan kaya ne ajikinta, don duk suran jikinta ya bayyana, hakan ya k’ara b’ata mata rai, ta iso gaban Aishat ta ce”ke Yar aiki kuma Yar shege wa ya baki daman saka wa ‘yannan kayan?”. Aishat tayi banza da ita bata amsa mata ba, hakan yak’ara kub’ular da ita. Ta sa ke ce wa”ke k’aramar ‘Yar iska da e fa nake magana”. Aishat ta saki lallausar murmushi, ta mik’e tare da gir-giza jikinta ta tak’o har gaban Falmi, sai da tamata kalon ido cikin ido, ta sake k’ara taku biyu zuwa uku, kafin ta juyo ta ce”Fatima kike ko Falmi? Ko ma dai wa kike duk ba damuwa ta insan sunan bane”. Falmi kasake tayi don tsananin mamaki, ko motsi ta kasa, sai bakin da ta sake tana kallon Aishat. Aishat ta ci gaba da cewa” ina sane da duk wani wulakancin da kika min tun daga tasowa ta, harda cin mutuncin da kukayi ma uwata, kin wulak’anta ni wulak’ancin da ko kare baza’a masa ba. Falmi ki sani da da yanzu ba d’aya yake ba, ki sani biyu yafi d’aya, kamar yanda uku tafi biyu. Ki sani wutsiyar rak’umi tai nesa da k’asa, kamar yanda na tsere miki yanzu. Ki sani a da kin taka Indo ta kyaleki, a yanzu na canza daga Indo zuwa Aishat, kuma Aishat bata juran wani raini da wargi. Samun kwanciyar hankaliki da zaman lafiyanki a gidan nan, shine kiyi sabgarki, banda shiga hark’an Ashanty baby, domin bana juran wani wargi. A hankali tasoma takawa tana sarrafa mazaunanta da k’irjinta, taku uku ta k’ara ta juyo ta ce”oh! Na manta ban sanar da ke, ko da gigin wasa karki ce zaki ne mi Aishat da fad’a, don bana had’a k’irji da kishiya kuma banga wannan kishiyarba, kuma ina fatan kinji duk abunda na fad’a miki?. Ta juya idonta ta ce” na manta ban miki godiya da karamcin da kika min, gaskiya kin can-canci in gode miki, kin had’a ni aure da gwarzon Mijiki Haiydar kuma kin iya had’i sosai, don ni kaina na san, nasamu mijin nuna wa sa’a gashi kyakyawa, jarumi a kowanne fage nagode”. Hannu Aishat tasaka akan bakinta tare da yin kiss ta hura ma Falmi, ta saki wani murmushin mugunta, don yanda taga Falmi ta dawo, juyawa tayi ta nufi d’akinta tana rangwad’a. Falmi batan lokacin da ta d’aura hannu aka ta fara ihu tana cewa”lalle yau nasan na *TAFKA BABBAN KUSKURE* wato d’an hakin da na raina…… Na raina Indo sai ita ce zata gasa min aya a hannu”. Ni ko Rash ina gefe na ce”gaskiya wannan show d’in yayi Aishat ta burgeni. Lalle wannan shi ake kira da *BABBAN KUSKUREN DA KI KA TAFKA* Falmi”. Gyara zama nayi don inci gaba da kalon wannan gurmi mai k’ayatarwa, kashh! Sai ga wayata tana nuna battery low. *®NWA.* *DEDICATED TO* *AISHAT MUHAMMAD* *(MAMAN ABDUL SHAKUR)* *RASH KARDAM * [2:32PM, 9/14/2016] Rash Kardam: [7/12/2016]Rash Kardam BABBAN KUSKEREN DANA TAFKA NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. *®NWA.* *Pg-197~199.* Ta juya idonta ta ce” na manta ban miki godiya da karamcin da kika min, gaskiya kin can-canci in gode miki, kin had’a ni aure da gwarzon Mijiki Haiydar kuma kin iya had’i sosai, don ni kaina na san, nasamu mijin nuna wa sa’a gashi kyakyawa, jarumi a kowanne fage nagode”. Hannu Aishat tasaka akan bakinta tare da yin kiss ta hura ma Falmi, ta saki wani murmushin mugunta, don yanda taga Falmi ta dawo, juyawa tayi ta nufi d’akinta tana rangwad’a. Falmi batan lokacin da ta d’aura hannu aka ta fara ihu tana cewa”lalle yau nasan na *TAFKA BABBAN KUSKURE* wato d’an hakin da na raina…… Na raina Indo sai ita ce zata gasa min aya a hannu”. Falmi ta fara Safa-da-marwa a falon bakinta ta ciza tare da dunkule hannu, tana tunanin mafita yanzu wani mataki zata d’auka gashi taga Aishat da zafin ta take can komai ta tuna tasaki lallausa murmushi ta nufi dakinta wanka tashiga don tasamo ma kanta matakin da zata d’auka. Aishat ko tana barin falo da gudu tayi d’akinta key(mabud’i) tasa ma d’akin ta rufe tare da jin gina a jikin k’ofar dakin tana maida numfashi. Wani sassanyan ajiyar zuciya ta saki a fili ta furta” lalle na iya cika baki duk wannan kurarin kamar zan iya dukan Falmi ai ko yau da ta shakeni sai dai wata Aishat bani ba”. Jin kamar motsi yasa ta zabura jikinta sai b’ari yake ta ce”wayyo yau na janyo ma kaina tabbas yau inta rikeni nikam sunana gawa”. Wani dabara ne ya fad’o mata doguwar kujeran hutuwa dake cikin d’akinta ta janyo zuwa bakin k’ofar ta tokare k’ofar dashi, wai ko da Falmi ta biyo ta bazata iya b’alle k’ofar ba. Sai zufa takeyi ga tsoro da take ji duk a razane take sai zare idanu takeyi tamkar wacce tayi ma sarki lafi. Haiydar ko d’aki ya koma yana tunanin irin rayuwan da zaiyi da matansa biyu, gashi yanzu ba abunda yake da k’auna da muradi kamar Aishat amma sam bai ganin fuska ajiyar zuciya ya sauke a fili ya furta”Allah ka sanya Aishat sona”. Mik’ewa yayi tare da d’aukar key (mabud’i) d’in motarsa ya fita waje don ya samu abunda zai ci. Falmi ko tana fitowa cikin hanzari tasoma shiri make-up (kwaliya) tayi ta d’auko kaya tasaka tare da d’iban kud’i tana wani murmushin mugunta ta fita. Wayarta ta d’auka ta kira wata magana sukeyi kasa-kasa wanda nikai na Rash duk son d’ibo rahoto na bansamu damar naji mai take ce wa ba, dole na hak’ura injira ta gama na bita naga mai take shiri aikatawa. Haiydar yana fita gurin cin abinci yanufa ya sayo guda uku, gida ya dawo ko da yazo falo yaga ba kowa, d’akin Falmi ya nufa yaga batanan da alamar ta fita ledar da yaso nata ya ajiye mata. Ya nufi b’an garen Aishat ko da ya tura k’ofar yaji a kulle sai ya kwan-kwasa k’ofar. Aishat da take ciki jin an kwan-kwasa k’ofa take cikinta ya bada sautin kululuuu! Wani

Chapter 6 of 9