Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 9
Kardam: BABBAN KUSKEREN DANA TAFKA NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-156~160. Ba yan gama wanan shagalin, Falmi ita da tawaganta suka koma gidanta. Yayin da Hajiyansu Haiydar ta kira Amarya d’akinta, ta bata wani abu a cofi tasha. Hajiya tace”ki k’wanta ki huta sosai. Sai da a kayi sallan magriba Hajiya tasa ta gaba taci abinci mai yawa. Hajiya ta saka ruwa a murhu, tare da lalle da magarya ya dahu sosai, sanna tasaka ruwa daban wanda ba komai aciki, ta juye farin ruwan a bokiti ta surka ta kai bayi. Kafin ta d’au wani bokitin ta tace ruwan lallen nan, da rariyan ta, sannan ta d’auko madaran turaruka kala-kala tasaka mata madaran turaren wanka acikin ruwan lallen. (Shi ruwan lallen ba’a cika ruwa da yawa sosai, d’an dai- dai za’a saka). Ta kai bayi tace”Aisha tashi kiyi wanka zaki ga ruwan biyu ne, kiyi wankan sabulu da farin, ki tabbatar ki dirje ko ina. Bayan kingama wankan sabulu, sai ki d’auki ruwan lallen nan zakiga ba yawa, ki tabbatar kin game jikinki dashi ta ko’ian. Aisha Indo ta amsa da”to Hajiya nagode. Saukowa tayi tashiga bayi, wanka sosai tayi kafin ta yiwankan lallennan. Tun daga bayi k’amshi ke tashi har falo. Hajiya ta taho da kasko k’arami, Indo na fitowa tace”zo nan. Fallen zani ta bata, ta lulub’u dashi kafin ta samata kasko tare da zuba turarukan wuta aciki masu kamshi.(masu k’aratu amfanin wannan wankan lallen, da turare yana saka jikin mutun yayi k’amshi, sannan k’amshin yana kama jiki, yana sa mutum kara haske da kyau. Sannan a zuba turare aciki zaki ringa kamshi ne sosai. Idan mutum ya fito daga wanka, bazai bari jikinsa ya tsan- tsame ba. Da ruwan zaki saka turaren wuta a kasko ki luluba jikinki, sannan ki tabbatar kamshin turaren na bin jikinki, in turaren ya k’are ki k’ara sakawa har sai kin tsan-tsame.zakiji k’amshin ya kama jikinki). Hajiya ta d’auko atamfa riga da zani, acikin a kayan Indo ta d’auko kwalban turare yar mai duguri, ta juje akan kayan, hatta ina wears d’inta saida suka sha turare masu sanyin kamshi, wanda duk namiji lafiyaye in ya shaki kamshi, sai ya yaba. Hasna ne ta turo qofa tashigo, ita ta tsara ma Indo kwaliya, kafin tasaka kayan. Masu k’aratu tundaga haraban gidan zaku iya jiyo kamshin da indo takeyi. Waya hajiya ta d’auko lokacin tara da rabi, Haiydar takira tace”kazo yanzu ina son ganinka. Cikin girmamawa yace”to Hajiya gani zuwa. Bai dad’e ba ko sai gashi, cikin shaddarsa ja sai maik’o takeyi. Ko da yazo Main falo, bak’ine aciki sai tsokanarsa sukeyi, murmushi ya musu ya nufi cikin d’akin Hajiya. Qofar tura tare da yin sallama. Tsayawa yayi cak dan ganin Indo a bakin madubi tana saka sarka. Sam ya kasa d’auke kansa daga gareta, ji yake kamar yaje ya rungumeta, amma jinkai da girman kai bazai barshi ba. Wata zuciya tace”to mai zakayi da bak’ar mace ma. Wata zuciyar ko cewa take”ai kuma duk randa tayi gayu sai ta fi falmi kyau. “Mtss kai k’aryane, yama za’ayi tafi Falmi kyau. Yana wannan tunani Hajiya tashigo da sallama tace”yauwa Babana ka iso. Sosa keya ya fara tare da rusunawa ya gaidata, Hajiya ta zauna abakin gado, Haiydar ya zauna akan dadduman dake kasan d’akin. Hajiya tace”Aisha zo nan. Cikin nutsuwa Indo ta tako zuwa kusa da k’afar Hajiya ta zauna. Hajiya tayi gyaran murya, tare da fara musu nasiha mai shiga jiki. Harda yan ayoyinta takawo musu, wanda yake nuni hakkin miji akan matarsa, tare da hakkin mata akan miji. Bayan ta gama tace”Aliyu!”. Kansa asunkuye yace”na’am Hajiya. Taci gaba da cewa”ga *AMANA* Aisha na baka, ban yarda matarka ta takura mata ba. “Itama matarka ce kamar yarda Fatima take matsayin matarka. Ko da tagama musu nasiha ta sanya musu Albarka tare da cewa Indo d’auko gyalenki. Hajiya ta d’auko Hijab tace”tashi muje da kaina zan kaiki d’akinki. Hannuta hajiya ta riko suka fito falo, sai tsokanar su akeyi. Haiydar shi ya jasu har zuwa gidansa, ko da suka shiga duk yan biki sun watse sai Falmi da taci riga da wando, tayi shirin ko ta kwana, don yau a shirye take da in dakuwa ne ma suyi a gidan. Ganim Hajiya yasa ta rusuna,, bata ko gaida ta ba sai wani hararan da ta aika musu. Hajiya ta shigar da Indo d’akinta kafin ta fito Haiydar yazo ya rakata yace”zai maidata gida. Hajiya tace”a’a na yafe driver ya maida ni. Sai da suka bar gidan, sannan ya nufi gida. Yana shiga Falmi ta ja ta tsaya a dai- dai qofar shiga side d’in Indo. Dake shi ba ma niyayar sa shiga gun bane ko kalonta baiyiba yanufi side d’insa. A dai-dai bakin qofarsa ta kwanta, wai dan karyazo ya wuce d’akin Indo bata sani ba, a haka har bacci ya d’auketa. Haiydar ko yana shiga d’aki kayansa ya cire ya watsa ruwa, ya sanya kayan bacci ya kwanta. Ko da ya rufe idonsa photon suran Indo ke masa yawo a idonsa. Da duk al’amuran dasuka faru a tsakaninsu. Sai juyi yakeyi gashi duk yana hannu, amma yasan in ya tink’ari Falmi, bala’i zai ne mo ma kansa haka yayita juyi har bacci b’arawo ya d’aukesa. *DEDICATED TO* *AISHA MUHAMMAD* *(MAMAN ABDUL SHAKUR)* *RASH KARDAM * [7/5/2016] Rash Kardam BABBAN KUSKEREN DANA TAFKA NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-161~163. Gari na wayewa Falmi ta tura d’akin tasamu Indo tana bacci. A fili tace”eyeh lalle fa kin samu kanki acikin bak’ak’en labarawa. “Har wani lokacin bacci kika samu. “Lalle ko zanyi maganinki yanzunan. Cikin hanzari ta juya zuwa kitchen d’inta, ruwa mai sanyi ta d’auko a fridge, in kunga ruwan har wani tururi yakeyi na sanyi. Tana zuwa tasamu har yanzu Indo bata farka ba, cikin zafin nama cike da masifa Falmi ta shek’a mata ruwan sanyi a jiki. Cikin razana indo ta farka, sai wuk’i- wuk’i take da ido. Falmi tace”ke waya baki damar yin bacci a gidan nan ko kin manta matsayinki ne. “Na yar shege kuma yar aiki maras amfani ke da babu duk d’aya kuke a gidan nan. “Maza sauk’o ki had’a mana breakfast. Indo ji take kamar ta kurma ihu, ba wai watsa mata ruwa, da masifan da Falmi ke ta mata bane ya dameta ba, ila cemata da tayi yar shege, wannan maganan ya na k’ona mata zuciya. In dai zagi ne kam inda sabo ya kamata tasaba. Tsawa Falmi ta sake mata wanda yasata dirk’owa daga kan gado, da sauri ta nufi hanyan falo. Kitchen d’in dake baban falo ta shiga ta had’a musu breakfast, sai da ta jera komai kafin ta d’ibi na ta, cikin d’akinta ta koma, tayi wanka tare da yin brush kafin ta karya. Hajiya sai da tabari Indo tayi 3 days tasaka driver ya kaimata ak’watunanta. Rayuwan Indo ya canza a gidan ba’abinda ta ke fuskanta ila tsangwama da tsana daga gun Falmi da Haiydar. Tun da ta fahimci duk ranar da sukayi karo da Haiydar sai ta gane kurenta. Hakan yasa indai taji yana falo to bata fitowa sai ya fita. Kwanaki sun tafi yau ki manin 2 month da yin bikinsu. Hajiya ce ta had’a goma na arziki tasaka Hasna ta zo duba lafiyar d’iyarta Indo. Hasna tana zuwa ta wuce d’akin Indo tasamu tayi tagumi. Ta rame ga wani bak’in da ta k’ara, cikin hanzari hasna ta yar da jakanta, taje tace”Aunty na mai ya sameki haka?. “Kinyi rashin lafiya ne?. Cikin dauriya Indo ta k’ak’alo murmushi tace”lau na d’anyi zazab’ine amma na warke yanzu. Sam Hasna bata gamsu da maganarta ba, suna cikin haka, sai ga Falmi ta shigo tana kiran Indo harda ashar d’inta. Sam bata san da zuwan Hasna ba kasancewar daga yawonta ta fito. Hasna ne tace”kar ki amsa wannan kiran yan tashan. Falmi jin Indo bata amsa ba tasan kuma tana jinta, abun sai ya kular da ita. Har zata tura qofar ta fasa ta koma d’akinta, zuk’ek’iyar bulala ta d’auko, ganin jikin bulalan yasata sakin wani murmushi, don tasan wannan bulalan in har yashiga jikin Indo zata gane shayi ruwa ne. Cike da isa da gadara, tana wani wawwaina bulalan a hannuta. Ta iso falon Indo, Kiran yantasha ta sakeyi. Hasna kuwa ta hanna Indo amsawa harda tushe ma Indo baki. Falmi a harzuke tashigo falon, sam bata lura da Hasna ba tayi kan Indo da bulala. Cikin sa’a ta tsula mata na d’aya, ta kai na biyu kenan Hasna tayi saurin shiga tsakaninsu. Falmi ganin Hasna ta razana amma sai ta dake tace”kee bani guri inyi abunda nayi niya. Hasna tace”ke Fatima kike kowa, kar ki kuskura tsautsayi ya gifta miki kice zaki sake dukan Indo. Falmi cikin fushi tace”ke ce mai tare mata ko. Cike da gadara Hasna tace”eh da abunda zakiyi ne.. Tsautsayi yasa Falmi ta d’aga bulala wai zata zuba ma Hasna. Amma kash ina ae ta makara Hasna tayi saurin k’wace bulalan tashiga tsula ma Falmi, iya karfinta, Kan kuce mai ta cika gida da ihu. Sai da Hasna ta mata lilis sai ihu take, karar motan Haiydar ne ya dawo gida, hakan baisa Hasna ta daina ba, Haiydar jin ihun Falmi ko mota bai rufe ba ya shigo gidan da gudunsa. Falon Indo yaji muryanta cike da mamaki yayi side d’in da gudu. Masu karatu bari mu huta a nan, ina muku murna da zagowan k’aramar sallah. Allah ya amsa mana ibadun mu ya kumasa muna daga cikin wa’yanda aka ‘yanta daga wuta zuwa aljannah ameen. *HAPPY SALLAH IN ADVANCE* *DEDICATED TO* *AISHA MUHAMMAD* *(MAMAN ABDUL SHAKUR)* *RASH KARDAM * [2:32PM, 9/14/2016] Rash Kardam: BABBAN KUSKEREN DANA TAFKA NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-164~166. Cikin hanzari Haiydar ya tura qofar d’akin. Cike da mamaki ga takaicin abunda ya gani, wai Hasna ke dukan Falmi. Kanta yayi ya bata lafiyayen mari, tukun Hasna ta koma gefe. Falmi ko ganinsa ta k’ara sautin kukanta. Cikin b’acin rai Haiydar yace”ke husna mai ya kawo ki gidan nan?. “Wa ya baki daman dukan matata?. Hasna tace” Yaya baka abu….. “Ke ni sa’anki ne ina magana kina magana. Ganin yanda ke huci, ya nufo kanta zai daketa, ta d’au wayarta da gudu, tayi bayi tasaka key. Ganin ta gudu Haiydar ya dawo kan Indo yace” wato kece munafukar gidanan nan ko?. Belt d’insa yasoma zarewa, nan Indo tasoma kuka tana basa hak’uri. Hasna jin Haiydar zai daki Indo, da sauri ta kira Hajiya ta saida mata ga Haiydar zai daki Indo. Hajiya ta kira wayan Haiydar dai-dai lokacin da ya d’aga belt, zai zuba ma Indo wayarsa tayi k’ara, yana cirowa sunan Hajiya ya gani. Ya d’aga tare da fad’in “Assalamu’alaiku. Hajiya ta amsa masa da”Ameen Wa’alaikumusalamu. “Ali wallahi karka kuskura ka daka min ‘ya’ya, mai suka maka ne haka?. “Ka jirani ina zuwa yanzu, tunda Abba ku baya gari, bare yazo da kansa. Bata jira amsan shi ba ta kashe wayar, Hijab ta zara da waya ta fito driver ta kira, suka d’au hanyan gidan. Haiydar ko wani takaici ne ya tokaresa, tabbas Hasna ne ta fad’a ma Hajiya, cikin zuciyarsa ko cewa yake”lalle duk randa na rike yarinyan nan, bansan wani irin duka zan mata ba. Falmi ya d’auketa, tare da kaita falo. Itako ta wani sakan jiki, da baki tana kuka kamar yarinya. Hajiya ne ya shigo da sallaman ta, Haiydar ya amsa mata, kalon tambaya ta tsaya masa, kai ya sunkuyar k’asa. Hajiya tace”ina yarana?. “Wallahi in ka duki d’aya a cikinsu, ranka sai yayi mumunan b’aci. Bata jira amsansa ba ta nufi side d’in Indo, tana shiga taganta, ta had’a kai da gwiwa, tana kuka mai ban tausayi. Hajiya da sauri ta yi gunta tana cewa”Indo ya dakeki ko?. Hasna jin muryan Hajiya yasa ta bud’e qofa ta fito. Hajiya tace”mai ya kaiki bayi?. Hasna tace” Ya Haiydar ne ya tashi zai buge mu. “Na gudu toilet. Hajiyan tace” muje falo tukun inji komai. Hasna ta kama hannu Indo suka nufi falo, Haiydar na ganin su Hajiya sun fito, ya sauka kasa ya zauna, Hajiya ta zauna a kujera, su Indo suka zauna a kasa suma, Falmi ko tana zaune a kujera taki saukowa. *DEDICATED TO* *AISHA MUHAMMAD* *(MAMAN ABDUL SHAKUR)* *RASH KARDAM * [7/6/2016] Rash Kardam BABBAN KUSKEREN DANA TAFKA NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-167~169. Hajiya ta kalli Haiydar tace”mai ke faruwa?. Cikin in ina Haiydar yace”Hajiya na dai dawo ne, naji muryan Falmi na ihu, ko dana shigo gida da gudu, sai naji sautin kukanta a side d’in Indo. “Ina zuwa sai na samu Hasna tana dukanta. Hajiya tace”shine ka tashi zaka da kamin yara?. “Shin kayi bincike akan mai ya had’asu?. Kai ya gir-giza alamar a’a, Hajiya taci gaba da cewa”haka babba ya kamata ya yanke hukunci, ba tare da binkiken mai ya faru ba. “Haiydar bana son ka da hakan ba adalci bane. “Yanke hukunci batare da bincike ba. Ta juya ta kalli Hasna tace”ke Hasna mai ya faru har kika daki matar wanki?. Hasna ta fara basu bayani tundaga shigowarta, harda kiran da Falmi tayi ma Indo, bata rage ko wasali ba. Hajiya ta saki salati tace”daman kuntata ma yar mutane kukeyi?. “Matarka har tasamu daman dukan yata?. “To bazaiyiwu ba. Hasna tayi sauri cewa”Hajiya ina rokon alfarma da amayar da Indo makarantar boko da islamiya. ” Tayi karatunta taga ma, kuma hakan zai bata daman samun sakewa, da samun ‘yancinta, da wayewa, batare da wata ta takura mata ba. Hajiya tace”rufe mana baki manya na magana kina saka baki. Hajiya ta musu fad’a tace”duk randa wani ya sake ya daki Indo a gidan. “Tabbas zakuga bacin raina. “Kuma daga yin aure, bazan so yata tafara yaji ba. “Amma komawa makaranta yazama dole ta koma. “Haiydar yanzu zan tafi da matarka, za’amata registration sai angama komai ta dawo. “Inaso gobe kazo ka kaita, amma sai mun zab’i makarantar da zatayi karatu. Kafin Hajiya tak’ara magana Falmi tasaki ihu, tana fad’in Hajiya ki taimakeni karta koma makaranta. Nayi alkawarin bazan daketa ba, gwara ta zauna a gida, In Har Indo ta koma makaranta to nakad’e nikam. Magana Falmi takeyi ba uwa k’wab’a. Hajiya ta mata kalon bakida kunya. Hajiya tace”Hasna kuje da Indo ta d’au hijab d’inta, da kayanta kala biyu, kuzo mu tafi. Hasna kamar jira take, da sauri ta kama hannu Indo suka nufi d’aki. Basu dad’e ba suka fito, Hajiya tace”mun tafi. Haiydar ya rako su, har gun mota suka tafi. Haiydar yana dawowa ko kalon Falmi baiyi ba, ya wuce d’akinsa. Hajiya suna zuwa tasaka Indo tayi wanka, ta bata abinci taci, sai da suka huta Hajiya tace”Hasna yanzu wani makaranta ne yakamata a yi registration ma Indo?. Hasna tace”inaga *SABIL SUNLIGHT* za’a mata. “Don makaratan yana da kyau ana karatu sosai. “Kuma sabon skul ne. Hajiya tace”to ba matsala gobe zamuje tare kawai. “Tunda Haiydar na fita aiki. Hasna suka shiga d’akin da Indo, suna hira, Hasna tace”kin san me aunty na? Indo tace” a’a sai kin fad’a. Hasna tace” ina rokon Allah yasa in anje registration d’in nan su baki science class. “Kinsan sabida mai yasa nake son abaki science class. Indo tace” a’a sai kin fad’a. Hasna tace”sabida ina so Falmi tayi regret cos taki ya auro mai aikin asibiti. “Ni kuma tun randa aka yi bikinku, na d’au alwashin da ikon Allah sai nayi hanyan da kika koma school. “Sannan inaso ki waye ki zama kikakiyar likita ba nurse ba. Indo tace”nima ina da burin karatu da, sai dai rashin mai taimaka min. “Gaskiya nagode Allah ya barmu tare. Hasna tace”Aunty Jiddah tana kirana a waya tana tambayarki. “Wai tanaso inta dawo zatazo ta koya miki abubuwa dayawa. “Basa k’asan ne ita da Yaya Ghali sun fita yin wani course a waje. Indo tace”ayya ni ae suna burgeni da Ghalinta dukansu Doctors. Hasna tace”wallahi kam ae sai kinji labarin soyayyan su gwanin burgewa wanda aurensu, yazo musu a *BAZATA*. Haka sukayita hira a tsakaninsu. Washe gari Hasna ta jasu a mota suka nufi *SABIL SUNLIGHT*. duk wani abunda ya dace suyi anyishi. Anyi interview ma Indo ganin k’ok’arinta, yasaba suka bata Science class. SSS1 daman tayi JSCE ta. SSS1A aka bata, nan suka bata uniform da komai hatta books, da text book suke bayarwa. Malamin da kansa ya kaita ajin, ya kira wata Sadiya S Adam, bayan da Sadiya tazo yace”Sadeey ina k’awarki?. Wacce aka kira da Sadeey tace”yau batazo ba, bata jin dad’i. Uncle d’in yace”ga frd nan na muku. “New comer ce gobe zata fara zuwa, inaso ku zauna tare da ita. Sadeey tace”okay sir!. Malamin yace”sunanta Aisha Muhammad. Nan suka gaisa Sadeey ta koma aji. Su Hajiya kuma suka dawo gida, Indo in banda murna ba’abinda takeyi, wai yau itace ta koma makaranta. Masu karatu ku shirya yazu ne gurmin zai fara, don Indo zata shigo gari, zata kile. Masu karatu ya kuke ganin Haiydar zai yi akan Indo nan gaba, k’iyayar zata ci gaba ko zai k’are?. Shin Indo zata ci gaba da d’aukan rainin da suke mata?. Shin ya rayuwan Falmi yake kasancewa nan gaba?. Ku biyo yar *JARAWA* don ji yanda zata kaya. *HAPPY SALLAH IN ADVANCE* *DEDICATED TO* *AISHA MUHAMMAD* *(MAMAN ABDUL SHAKUR)* *RASH KARDAM * [2:32PM, 9/14/2016] Rash Kardam: [7/6/2016 Rash Kardam] BABBAN KUSKEREN DANA TAFKA daga www.hausaebooks.com.ng NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-170~173. Ko da suka dawo gida, Hajiya ta zaunar da Indo tayi mata nasiha, game da aurenta, sanan ta k’ara da cewa”Aisha kiyi hak’uri ina sane, da duk irin abunda Aliyu yake miki. “Abunda yasa ba zan takurasa ba a kwai lokacin dana ke jira, zan ramamiki duk abunda ya ke miki, inaso ki nutsu kiyi karatu nan gaba sai Haiydar yazo da kansa yana baki hakuri. “Alokacin ne zamu rama duk abunda ke mana, Hajiya wani murmushin mugunta tayi, kafin taci gaba da cewa”zan saki a makaranta islamiya, don ki rage yawan zaman gida. “Sannan ki k’ara hak’uri da duk abunda zasu miki, wataran zakici riban hak’urin ki, har sai ni da kaina nazo, ina cewa Aisha ki d’an ji tausayin Yayanki, ki sassauta ma Haiydar. Hasna ne tayi murmushi don itama tanason ta ga wannan ranan. Hajiya tace” a kwai motar da Abban na, Sarkin Fulani(Gakansu Haiydar ) ya ban range rover zan baki ita, tadawo naki halal malak. “Zansa Hasna ta koya miki mota amma sai naga kunyi jarabawa, da irin sakamakon da kika fito da shi kafin na damk’a miki motarki a hannuki. “Sai gobe zaki fara zuwa school, in kin dawo da kaina zan maidaki gida, kuma zansa driver yana kaiki makaranta. “Ku tashi kuje ku huta Allah ya muku Albarka. Suka amsa da”ameen. Gidan Haiydar ko yau ya dawo da niyar ko ta kwana, don yau yayi niyar karb’a hakkinsa a gun Falmi. Don yayi hak’uri har ya gaji, rabonsa da ya kusanceta har ya manta. Wanka yayi ya nufi d’akinta, yana zuwa ya tarar ta baje a gado, tana sharan baccin ta. Hawa gadon yayi, yazo kusa da ita ya kwanta. Salon sa da yake rikitar da mace, ya fara aika mata sak’onsa. Cikin bacci Falmi taji ana shafata, farat ta farka ganin Haiydar yasa ta rik’e hannusa, tace”mai kake shirin yine?. “Ko ka manta dokata ne?. “Matsawan kana son biyan buk’atarka sai ka ajiye min kud’i. Cikin da shashiyar murya Haiydar yace”haba Falmi anya kina tsoron Allah kuwa?. “Matar aure na na sunnah, don zan kusanceki sai na biya kud’i. “Kisani fa hakan haramun ne. “Kisani mala’iku su tsine miki fa?. Falmi tace”ai yau in har kaga ka samu abunda kakeso to kasaka min kud’i har 200k. Haiydar yace”Falmi bayan kud’in sadakin dana biya?. “Ki sani bana son miki ta k’arfi. “Ina rok’onki da kiji tausayina, ba wai don bana da kud’in da zan baki ba, a’a saidan hakan baida kyau. “Kuma duk irin k’yautata miki danakeyi ba k’ya gani?. “Yaushe na baki 300k fa falmi?. Tsaki ta ja ta mik’e, za ta sauk’a daga kan gadon, ya fincikota, sak’onni yasoma aika mata dashi. Duk iya k’arfinta ta kasa kwacewa sai tasoma masa ihu. ( kira gareku mata masu irin wannan halin, kusani baida kyau, Allah da mala’ikunsa, suna tsine wa duk matar da mijinta ya nimeta, ta juya masa baya. Ko kuma ta nimi sai ya bata kud’i kafin ya kusance, ta kamar yanda Falmi takeyi. Dan Allah ku kiyaye inda maiyin haka ku daina. Kisani duk randa kika faranta wa mijinki rai shi da kanshi zakiga canji a gunsa kuma komai kika roka matsawan na dashi zai baki, amma ba kice sai ya baki kafin ki basa hakkinsa ba, hakan haramu ne. Allah ya tsaremu da aikata hakan ameen). Bai k’yaleta ba sai kusan asuba, wanka yaje yayi ya kwanta, yana tunani irin halin Falmi sam baida k’yau. Gidan Hajiya kuwa, da safe Indo tayi wanka tasaka Uniform d’inta purple da light purple, riga da skirt sai barret. Hijab ta d’auko ta d’aura akan kayan, Indo tayi kyau sosai, Hasna ne ta kaita school d’in. Suna zuwa school d’in registration office suka nufa. Bayan sun gaisa da uncle d’in jiya, Hasna tace”gata nan mun kawota. Uncle d’in yace”ok wata yarinya ya kira, yace”ta je SSS1A ta kira masa Sadeey S Adam da Sanah S Matazu. Ko da yarinyan ta tafi, bata dad’e ba saiga su sunzo. Nan ya had’a su yace”su je su zauna tare. Sanah da Sadeey suka kama hannu Indo suka nufi class. Hasna kuma ta wuce school d’inta itama. *MASU NIMAN WANNA BOOK ‘DIN DA WA’YAN DA SUKE MIN MAGANA TA PRVT, PLS KUYI HAK’URI SAK’ONNI YANA YAWA, BA WULA’KANCI BA. KUNA TAMBAYA A GROUP DAN ALLAH. KUMA ‘YAN GROUP MAI SHI KUNA BAYARWA COS MUTANE SUNA YAWA, KUMA GA MESSAGES ‘DIN MASU YIN COMMENTS, SUMA ZAN MUSU REPLY, INA HÀU DA NIYAR INA GA SAK’O IN CIGABA DA TYPING, AMMA SAI NA TSAYA TURAWA MUNAE, WASU IN BAN TURA MUSU AKAN LOKACIBA SUNA FA’DAN BAK’AR MAGANA DUK IYA K’OKARIN DANAKE AMMA BASA GANI, DAN ALLAH FANZ A TAIMAKA ANA TURAWA A GROUPS IN AN TAMBAYA PLS N PLS* GA WANNAN KUYI HAK’URI BAYAWA KAINA YA DAMEN DA CIWONE NASO NAYI YA FI HAKA . *DEDICATED TO* *AISHA MUHAMMAD* *(MAMAN ABDUL SHAKUR)* *RASH KARDAM * [2:32PM, 9/14/2016] Rash Kardam: [7/7/2016] Rash Kardam BABBAN KUSKEREN DANA TAFKA daga www.hausaebooks.com.ng NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-174~176. Sanah da Sadeey suka nufi class da Indo, ni ko Rash ina biye da su. Tun shigarsu class, yan aji suka fara tambayan Sanah da Sadeey wacece?. Sanah suka sharesu ganin sunyi hanyar sit d’in da ke k’usa dana su, wani yaro yace”kai new comer ce fa. “Jiya ina gani aka kawo ta. Wasu sukafara cewa ke kizo nan ki zauna, wani yaro yace”kai gaskiya tana da kyau. “Zamu zama frds ko?. Wani kalo Sanah ta musu, wanda yasaka shi yin shiru yana dariya. Sit d’aya aka bata kasancewa kowa da sit d’insa, had’e da kuma lokansa na ajiye wasu littafa. Sanah ce a farko sai sit d’in Indo a tsakiya sai Sadeey a baya. Ana haka Uncle d’in Biology yazo, darasin da yamusu shine. *CELL* sai da ya gama darasi yayi bayani sosai, ko da yazo yin Evaluation, ya tambayesu kamar haka, “class what is cell?. Shiru ba wanda ya d’aga hannu, sai Indo ta d’aga hannu, ya nuna ta, Indo ta mik’e tafara cewa”Cell is the fundamental total unit of life. Cikin salon da take karatun, abun burgewa ne, bare muryanta tamkar mai yin busa. Tana gamawa tun kafin malamin ya bada umurni a tafa mata, ‘yan class suka d’au sowa da tafi. Jikake raf raf raf, sannan malamin yace”well done good girl clapp for her once again. A haka har aka tashi. School bus ne ya maidata gidan Hajiya. Washe gari ta koma gidanta, Haka rayuwa taci gaba da tafiya, kulum school bus ke zuwa d’aukan Indo ya dawo da ita. Sannu a hankali sun shaku dasu Sanah da Sadeey, anan ne ma take sani asai Sanah yar gidan bababn Malaman nan ne mai wa’azin biki da gyaran Amare. Sai Sadeey kuma gurin gayu ba’a barta a baya ba. Niko Rash nace”lalle abun yayi wato kaya, ya tsinke a gaban mai kaba. Aisha ta soma kilewa, duk da haka ita take aiki a gidan Falmi, ko kad’an bata nuna gajiyawarta, Haiydar ko ya saba da girkinta duk randa bata gida, ko ya je Hotel baya iya cin abincin su. Indo ko mungun kama kanta take bata bari ma ya ganta bare ya nimi takura mata. Falmi ko bala’in yau da ban nagobe da ban, Meesha lurv da Zarah BB sun bata shawaran ta kama kanta, ta fita hark’ar Indo tak’i, sabida duk randa Indo ta waye sai ta gane KUSKURENTA amma fir taki, tana bin shawaran mugayen k’awayenta, hakan yasaka suka zuba mata ido. *DEDICATED TO* *AISHA MUHAMMAD* * (MAMAN ABDUL SHAKUR)* *RASH KARDAM * [2:32PM, 9/14/2016] Rash Kardam: [7/7/2016]Rash Kardam BABBAN KUSKEREN DANA TAFKA daga www.hausaebooks.com.ng NA ©RASHEEDAH .A. KARDAM. Pg-177~179. Rayuwan Indo haka yaci gaba da tafiya, tana zuwa makaranta. Sun had’a kai da su Sanah da Sadeey, da zamansu ta ga na da kyau, bata b’oye musu komai na rayuwanta ba, ta fad’amusu. Sanah tace” mukuma zamu bada tamu gudumawar gurin ganin kin gyaru. Sadeey ita ta dage gun koya mata k’waliayar zamani, Sanah kuma gyaran jiki, hatta yanda Indo zatayi tafiya saida suka koya mata. Bayan kwana biyu suka zo mata da form d’in makarantar kwaliya ta cika, da kanta ta biya kud’in kasancewar tana samu ‘yan kud’i, a haka ta fara zuwa. Hajiya ganin jarabawan Indo yayi kyau hakan yasaka ta bata motarta, ranar da Falmi tasamu labari kamar zatayi hauka a gidan, don saida Hajiya ta tsayar mata ita da Aliyu, don motar Falmi bai kai na Indo ba. Sanah suna hira da Sadeey da Indo, Sadeey tace”Indo gaskiya ni bana son ana kiranki, da Indo nan sai kace yar kauye. Sanah tace”kamar kina raina. “Shawara daga yau duk wanda yace miki Indo, in ba wanda kike jin kunyarsa bane karki amsa. Tun daga ranar sunan Indo ya b’ata yakoma Aisha, nima Rash nace” daga yau na daina cewa Indo sai Aishat.********* 2yrs later Wata k’yak’yawan budurwa na hango, tana fitowa da ga cikin gida ta na k’ok’arin bud’e motar ta, mai k’irar RANGE ROVER, sanye take cikin wani doguwar riga ya d’an kamata daga sama, sai d’an k’aramin cikinta dake a shafe ya fito. Hakan shi zai baka daman gane irin halittan da ubangiji ya mata, harta shiga mota ko mai ta tuna cikin damuwa tace”oh shirt! Da sauri ta fito ta nufi hanyan cikin gidan, gudu-gudu sauri sauri, sam bata ankara da wanda ke fitowa ba, sai jin garam sunyi karo da mutum. Ko ta nuna alamar damuw ta d’ago kai tare da d’an zaro gilashin dake idota, sai da ta d’an rausaya ido, ta wani kashe murya tace”oh i’m sorry! you guy. Bata jira amsan shi ba ta sakai ta wuce abunta, Haiydar da tsananin mamaki kasa motsi yayi, shafa ida ta buge sa yayi, haryanzu dadda d’an k’amshin ta yana tashi. Wani yawu ya

Chapter 5 of 9