Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
samun matsalaba se yau. Har 9:00pm seta d'auki wayanta ta kirashi yanata ringing harya d'auke,zata sake kira kenan setaga call d'inshi,ta d'auka cikin sanyin murya tace hello Shuru yayi baice komaiba Ta sake cewa hello Nanma shuru yak'i yayi magana, tace hello manosh, Karon farko data kira sunanshi kenan,seyaji dad'i har cikin ranshi amma baice komaiba,ta sake cewa "manosh pls talk 2me" yace me kike so nace miki aunt? Tace wai fushi kakeyi danine, shuru yayi uanajin daddad'ar muryanta,ta sake cewa "manosh am talking to you" yace inace ni kike kora agaban marwan ko? Wani iri taji a ranta dan yadda yayi maganan batasan lokacin datace "am so sorry manosh i din't main to hurt you pls?" Nanma shuru yayi,ta sake cewa manosh wai bazaka min magana bane kuma kanajina? Yace "yes" take jikinta yayi sanyi tace manosh am sorry pls,nanma shuru yayi seta katse wayan. Hankalinta ya tashi sosai tayi dana sanin yimasa hakan. Har 10pm manosh bai sake kirantaba,seta tsinci kanta cikin damuwa sosai sam ta kasa sakewa,dan tana son manosh sosai acikin ranta. K'arar shigowar texs tayi a wayanta da sauri ta d'auka ta bud'e taga _Am sorry too apple_ _I love you so much_ _Nd i will call you leta_ _Am talking with my dad now okey,manosh loves you so verry much apple_. Maryam tana gama karanta texs d'in taji dad'i sosai a ranta tayi murmushi tana mai k'ara jin sonshi na ratsa jikinta,tace i love you too peach tare da rufe idanunta tana murmushi..... [7:10am, 4/2/2017] Sadiya Taheer: 😔🎈AUNTY'N YARA🍧🎁AUNTY'N YARA🍧🎁 Written by sad-nas & Hama gee muh'd *Dedicated 2 sarah katagum*💋 23-24 Seda manosh suka gama magana da dad nashi,sannan ya koma d'aki ya kira maryam har gurin 11:00pm. Maryam har tayi bacci,ta jiyo wayanta na k'ara da d'auka tare da sawa a kunnenta amma idonta a rufe yake tace hello,cikin muryan bacci, yace "apple am sorry for waking you up"tace "don worry manosh am fine"muryanta ya kashe mishi jiki gabad'aya atake yaji inama tana kusa dashine. Sakeyin k'asa da muryanshi yayi yace "are you sure" tace "yeah am fine"ai manosh aiseya fara juyi akan gadonshi yace "no apple you have to sleep"zan kiraki da asuba kinji,tace "okey good night" yace sweet dreams apple,murmushi kawai ta mishi tare da katse wayar. Manosh ya sauke ajiyar zuciya yace "ooh my apple"Allah ya nunamin ranar da zan mallakeki a matsayin matata,da wannan tunanin bacci ya kwasheshi. Wannan karon manosh baiyi tfy ba,har akayi nisa da azumi sannan suka kaiwa 'yan matansu kayan sallah a d'inke kuma masu tsada,da kuma redimate ga fashions ga takalma da jaka da turare komai dai suka had'o musu kowa da irin nashi,sannan sukayiwa iyayensu,harta abdallah seda manosh da marwan suka mishi kayan sallah. Almajirai sam basa so azumi ya k'are,gashi indai a girene to kusan rabinsu sunsan maryam. Daidai da sabulun wanki ko omo haka zatayita raba musu 1/1 tace suyi wanki dashi,dan haka suna sonta sosai. Azumi gashi wanke wanke ya k'are yau gobe sallah se murna akeyi su maryam ansha kitso gata da amma sam ita tafi so tayi kitso akan tabar kanta haka,su rashida kuwa kai kawai sukayi amma zahida kitso tayi da ameena babale,su samirane yan kai,gashi suna lalle gayu dai sosai sukayi. Manosh bai samu zuwa rananba dan haka maryam tayi *cake* mai dad'i kuma had'ad'd'e dama duk sallah tanayi. Mhaifinta kuwa drinks ya sayo kala kala dan yasan 'yar tashi da jama'a bugu da k'ari suna son maryam sona hak'ik'a zai iya kashe duk dukiyarsa dan farin cikin maryam,shiyasa ma idan ka shiga d'akin maryam wlh bazaka tab'a zatan cewa a cikin gidansu d'akinta yakeba dan yadda mahaifinta ya gyara mata shi,gurin zuba littattafaima na musammanne,ga computer komai dai se wanda ya gani. Yau take sallah kowa se murna su maryam suka shirya shirya tafiya *idi* anko suka sha ita da rashida da samira da himar nasu neavy blue toyobo dogaye har k'asa masu hannu sunyi ado sosai se k'amshi sukeyi. Mama tazo tace to maryam kinyi bak'o a waje,tace bako kima mama,tace eh,da sauri ta mik'e ta fita kawai setaga drivern manosh ne da *406* ash wai yazo ya kaisu masallaci. Mamaki ya kama maryam tace wlh kaje kawai masallacin fa babu nisa da k'afa zamu tafi,yace a'a madam idan na koma fad'a zaimin kiyi hakuri. Shuru tayi tace to ina zuwa,nan ta koma ta sanar da mamanta,mamanta tace to maryam kuje kawai tunda haryazo, haka suka fito abdallah ne a gaban motan su kuwa ukun suna baya sunata salati zikiri har suka isa, sannan yayi pakin a gefe shima yaje akayi sallah. *Allahu Akbar Allah ka k'ara dauwamar damu a musulunci ameen* Bayan an idarne sukaita hotuna a wayansu,ai se suka hango uncle ibrahim da friends nashi nan suka wuce aka gaisa sannan sukayi pictures da uncle ibrahim da kuma friends nashi yana tsaye kusa da maryam hotunan sunyi kyau sosai,shima driver se d'aukansu yakeyi a tap batare da sun saniba,amma sam bai d'auki su ibrahim ba. Bayan sun gama ne sukayi sallama sannan suka zo gun drivern ya maidasu gida. *cake din* maryam ta zuba mishi a kula tare da soyayyen naman kaza da kuma ruwan faro mai sanyi ta bashi,karb'a yayi tare da godiya ya tafi. Bayan tfyanshine ta kira manosh tace mun godefa,yace bamun b'ataba meyasa kika kirani,tace godiya na kira in maka sannan kuma....yace sannan kuma me, tace inaso ka kawo min *miher* anjuma mu yini,yace coman kike bani kenan,tace *no captain* alfarma nake nema,yace nak'i bazan kawotaba,tace haba mana pls ka kawota,yace nak'i d'in,tace to shikenan ni zanzo gurinta anjuma,murmushi yayi yace zan turo azo a d'aukeki sannan ya katse wayar ya sake kiranta. Ta d'auka tace bana bukata dama zamuje gun zahidane se mu wuce gurin ameena. Yace wa kika tambaya babu inda zakije,tace saboda da me,yace ra'ayinane hakan,shuru tayi tace to shikenan ka kawomin miher dan tace seka yadda kafin take fita wani girin pls ka barta,yace sekin ce *am sorry peach* dariya tayi tace menayi to,yace nidai na gaya miki,tace ok am sorry peach,murmushi yayi yace tosekin fad'a da muryana,tace ni mace kai miji ai muryanmu dabanbanci bazan iya ba,yace to bazata zoba,tace pls mana captain,yace wlh sekinyi muryana, nan dai ta gyara muryanta wai a dole zatayi irin nashi,ai tun bata k'arasaba take dariya shima haka take ta katse wayar tanata dariya shima hakanne muhsin yace ku kamashi muje gun malam mahmud yayi mishi ruk'iyya inaga yad'an samu matsala ne,daroya sosai manosh yakeyi harya shiga gida,mum da miher se binshi da kallo sukeyi,miher tace the prince lfya kuwa,yace wlh maryam ce take haukatani uama manta mum nashi tana palon,ai take ya seta kanshi yace mum dama kina nan ne,yad'an sosa k'eya,tace nidai inaso akawomin maryam d'innan inga mai sunana kuma sirikata,miher tace dama yau nake so inje in bro ya yadda zuwa jibi kuma se inje mu taho tare. Manosh yace a'a ki bari dai jibin se driver ya kaiki ku taho tare,miher bata so hakanba amma tasan manosh magana d'aya yakeyi dan haka ta sanar da maryam cewa baza samu zuwaba se jibi,maryam bataji dad'iba dan batayi zaton manosh zaik'iba. Da yamma su manosh sukaje gaisuwa gun surukansu tun daga gun mahaifin ameena suka fara har na zahida sannan suka wuce gire mota 3 masu zafi. Kyakkyawan k'arb'a aka musu dama ansan da zuwansu. Koda sukaje gidansu rashida da samira sannan suka wuce batare dasunyi hira da 'yan matanba. Bayan sun komane ya kira maryam se fushi takeyi waidan ya hana miher zuwa. Babu irin rarrashin dabai mataba amma tak'i tanata fushi. Yace am sorry apple zan kawota jibi da kaina kinji,tace banso indai kai zaka kawota bazaniko inaba,yace to shikenan bazan zoba zan kiraki anjuma pls zan d'auki wani kiran kinji,tabace komaiba ta katse wayan shi kuwa ya d'auki wayan oganshi. Kamar yadda manosh yace yau miher ta shirya driver ya kaita gun maryam,mirna sosai maryam tayi bayan sun gaisa da mamane se suka wuce d'akinta,ita kanta miher d'akin ya burgeta dukda dai ita 'yar masu akwai ne. Hira sukayi kad'an maryam ta cikawa miher ciki da abin mak'ulashe sannan tace bari in yiwa mama sallama semu tafi dan in dawo da wuri koh,tare suka mik'e sukai mata sallama tace a gaishesu sannan suka tafi. After dress ce red a jikin maryam tayi kyau sosai taga sun tsaya a wani katafaren gida. Koda aka bud'e gate se taga ashe cikin yafi wajen had'uwa,bayan sun k'arasane taketa ganin flawers kala kala masu kyau sosai. Miher tana rik'e da hannunta se gaisheta gards din sukeyi har suka k'arasa palo, me zata gani...hoton miher da manosh ne da kuma iyayensu,jikinta yayi sanyi tanata fad'in *innalillahi wa'inna ilaihirraji'un* tabbas maryam bazata tab'a mance fiskan wannan mutumin da take tunanin shine mahaifin manosh ba,acikin ranta kuwa tace wlh bazan tab'a b'oyewaba koda hakan zaisa in rabu da manosh peach d'inaba. Miher tace yanaga kina ta kallon hotonmu da iyayenmu nadai fi bro manosh kyau,murmushin kawai tayi tace nidai bance komaiba,miher ta kaita d'aya palon sannan ta zauna tace ina zuwa bari na kira mum sannan ta wuce wani kofa,ita kuwa tana zaune kanta a sunkuye tana tunani. [7:10am, 4/2/2017] Sadiya Taheer: 🍭🎈AUNTY'N YARA🍧🎁AUNTY'N YARA🍧🎁 Written by sad-nas & Hama gee muh'd Dedicated 2 FIDDY G MUH'D 💋😘😘 25-26 Mum da miher sun fito a tare kan maryam a sunkuye, tayi saurin durqusawa qasa ta gaishe da mum din manosh cikin fara'a da sakewa sosae mum ta amsa mata gaisuwa tare da tambayanta ya mutanen gidan, sun dae gaisa sosae amma kan maryam a sunkuye yake. Mum tace ki saki jikinki fa , nan kaman gida ne haka dae sukaci gaba da hira mum ta kama hanya ta tafi ta barsu ita da miher. Miher ta kawo mata kayan maqolashe kala kala, maryam bata iya cin komai ba in banda ruwa da tasha. Suka dan yi hira kadan daedae lokacin dad din manosh ya shigo yana kiran miher da sauri tace naam dad, sannan ta fita taje wurin dad dinta, yace ke da wa kuka shigo?? Tace nida wanda bro manosh zae aura ne. Tazo gaida mom ne nan dae tace dad bari tazo ta gaishe ka, tayi sauri ta koma taje ta kira mrym da sauri ta fito kanta a sunkuye ta durqusa har qasa ta gaishe da dad shima ba laifi cikin fara'a ya amsa. Koda suka gaisa ya wuce dakinshi ita kuwa maryam tana kallonsa a nitse ta sake tabbatarwa wannan shine mutumin da nan da bazata taba mantawa dashi ba a rayuwarta. Jiki sanyaye ta koma falo suka zauna dae, ita kanta miher ta lura da sauyi daga gareta amma bata ce mata komai ba. Maryam ta dan zauna na kusan 30 mins tace to gaskiya zata tafi saboda batason dare yayi miher tace bazaki tafi ynxu ba dole se bro manosh ya dawo dan shine zai maida ke gida maryam tace aa ni bamuyi haka dashi ba dan allah ki tashi ni zan koma gida. Miher taga dae da gaske takeyi dan haka ta kira bro manosh a waya ta sanar dashi bada jimawa ba yazo daedae lokacinda suka fito tayi sallama wa mum zata tafi, mum ta hada mata goma ta arziki ta rako ta har kofar falo sannan ta juya , shi ko dad daman ya riga da ya fice. Ko da ta iso wurin mota tana tsaye shi ko manosh ya danno shi da marwan kallonta yakeyi tun daga sama har qasa saboda kayan ya bala'in mata kyau murmushi kawae takeyi tare da gaishe da marwan bayan sun gaisa ne manosh ya matso kusa da ita yace wato bazaki gaishe ni ba kenan?? Shuru tayi batace mishi komai ba tace nidae ka kaini gida yace ae ba ni na kawo ki ba wanda ta kawo ki saeta maida ke,maryam ta maida kallonta gun marwan tace marwan kaji abinda yace ko,marwan yace rabu dashi muje in maidake,duka manosh ya kaiwa marwan tare da cewa ina ruwanka acikin hidimata,marwan yace da ruwana mana aunt muje in kaiki gida kinji tare da dannan keyn mota ya bud'e mata gaba ta shiga ta zauna sannan manosh ya karb'e keyn a hannun marwan yace zaka zauna a baya kenan,marwan yace eh ba matsala,maryam tayi mirmushi yayinda miher tasa mata goma na arzikin da mum ta had'ota dashi sukai sallama manosh yaja mota suka tafi. Tunda suka fara tfy manosh da marwan ne suketa hira itakam tayi shuru tana ta tunani a ranta. Manosh ya lura cewa akwai sauyi tattare da ita,yace kira sunanta a hankali apple,juyowa tayi suka had'a ido sannan ta mayar da kanta gefe,shuru yari bai sake cewa komaiba har suka iso girei,marwan yace jirani abokina bari naje gun rash a tsatstsaye yanzu zan dawo. Bayan marwan ya tafine su kuwa suna zaune a cikin mota manosh yace apple meyake damunki? Murmushi tayi tace bakomai,yace no apple karmu fara haka dake pls ki gayamin dan nasan akwai wani abu,tace gaskya naji dad'in yadda aka karb'eni a gidanku mum naka tana sona sosai nagode sosai tana murmushi tare da kallon kyawawan idanunsa,shima idanun nata yake kallon yayi da yakejin shaid'an yana zugashi da cewa kayi kissing nata manosh,maryam taga kallon da yake mata ya fara wuce gona da iri dan haka tayi saurin kawar da kanta tare da cewa zan shiga gida. Manosh ya dawo hayyacinsa yace bakomai apple kin cancanci a k'aunaceki domin kina da halayya na gari masu kyau daban sha'awa,dad'i taji tace ai kaima haka,dan azamanin yanzu da kyar asamu namijin da baya iya tab'a koda hannun budurwansa shiyasa kullum nake k'ara sonka manosh nasan cewa kana min so na gaskyane kuma mai tsafta. Jikinshi yayi sanyi dajin kalaman maryam,yayi hamdala a cikin zuciyarsa yace Allah nagode maka danafi k'arfin shaid'an a wannan lokacin Allah ka k'ara kareni akan sha'awar da nakeyiwa maryam ameen. Ta katseshi da cewa ya naga kayi shuru,yace bakomai kawai bana so ki tafine harse marwan ya dawo,murmushi tayi tace toshikenan kamin hira,yace kedai zaki min,tace ni nawa sun k'are ai,yace to mata biyu nake sofa in aura dake da kuma wata kin amince? Murmushi tayi tace eh na amince mana ai halal ne kana iya yin hud'uma,dariya sosai manosh yakeyi,wanda yake burge maryam dan manosh ya had'u wlh sedai sam bai fiye yin dariyaba wanda ta lura hakanma dan itace yakeyi se kuma dasu marwan ko miher. Manosh ya tsargu da irin kallonsa da maryam takeyi yayi sauri tsayawa da dariyan nashi yace "apple why are looking at me like that?" Kunya sosai taji dan batama san ya akai taketa kallonshi hakaba,kuma aduk lokacin take kallonshi sha'awarta tane kawai yake kamashi. Maryam tace ina son ganinka aduk lokacin da kake dariya dan kanamin kyau sosai manosh,jiyayi kamar ya rungumeta dan yadda yake ji,amma seya daure yayi d'an murmushi tare da d'aukan wayarsa ya kira marwan yace ganinan zuwa mutafi sannan ya katse wayar maryam tana kallonshi,shi kuwa bai sake kallontaba hannayenshi suna kan siterin mota yace apple am goying,mamaki taji amma setace tonagode Allah ya kiyaye hanya yare da bud'e kofar mota ta fita se nanne shima ya fito tare da d'aukan abubuwan da mum ta bata yake mata har zauren gidansu ya ajiye. Tace nagode tana murmushi,kallonta yayi batare dayayi murmushi yace *minfu miyatti* sannan ya wuce motarshi ya shiga yaja yana mata bye,ita kuwa murmushi kawai take mishi daga k'arshe ta d'aga masa hannu sannan ta wuce gida. Maman maryam tayi farin ciki sosai dajin yadda aka k'arb'i maryam hannu bibbiyu,ga kuma zannuwa da less masu tsada ga sarka da turare da mum din manosh ta bata. Maryam ta koma d'aki tana kwance se kuma ta tashi ta bid'e kit nata ta d'auko memori tasa a wayarta ta sake tabbatar da cewa lallai wannan shine mahaifin manosh,hawayene suka fara zuba a idanunta se taji wayanta na k'ara,koda ta duba *peach &cream* ne seta d'auka tare da share hawayenta tace hello,manosh yace apple mun tafi,tace to Allah kare nagode,yace ameen *i luv u* murmushi tayi tare da cewa *she luvs u 2* dad'i yaji yace thankyou apple,tace always *peach* wayyo Allah manosh kamar zaiyi hauka yana mirmushi ya katse wayar yatana lumshe ido,marwan yace bari in karb'eka dan naga kamar ka gaji,dariya sukayi dukkansu sannan manosh ya fizgi motar kamar zasu fire sama,marwan yace a'a mudaije a hankali kaga dukkanmu tuzuraire hhhhhh Maryam kuwa wasu zazzafan hawayene suke zub'o mata tinda ta ajiye wayar. Tace inason sosai manosh,yanzu ya zanyi kenan? Wayarta ta d'auka ta kira uncle ibrahim bayan sun gaisa tace dam inaso miyi magane in baka cikin mutane,yace ok bari na kiraki. Bayan ya katsene ya sake kiranta yace yes aunty ina jinki,tace ka tuna da wannan vedion dana tura maka a wayarka,yace ai devio d'aya kika tab'a turamin na wanda ya buge mahaifina ko? Hawaye ya sake zubowa a fiskarta tace eh shi,yace eh har yanzu yana wayana ai,tace bakowa bane wannan mutumin illa mahaifin manosh yah ibrahim. What! Mahaifin manosh kikace,tace eh shine na tabbatar da hakanne yau danaje gaida mahaifiyarshi yah ibrahim bazan iya b'oye makaba dannima mahaifinka mahaifinane sannan mun dad'e muna nemanshi se gashi kuma ashe shine mahaifin manosh,kukane yaci karfin maryam take ta katse wayar. Hankalin ibrahim ya tashi sosai ya rasa meyake mishi dad'i musamman dayaji maryam tana kuka,don ya dad'e dasa son maryam a ranshi tun mahaifinshi yana raye ya sanar dashi,amma se mahaifinshi yace karka damu ibrahim ka gama karatunka tukunnan maryam 'yace aguna nima zafin samun kwarin gwuiwa idan ka gama karatu ka samu aiki se inyiwa mahaifinta magana tunda amininane. Hakan yasa ibrahim ya hakura yabar abin a ranshi amma kash *muna namu Allah yana nashi* hankalin ibrahim atashe ya wuce gidansu maryam..... [7:10am, 4/2/2017] Sadiya Taheer: 🍭🎈AUNTY'N YARA🍧🎁AUNTY'N YARA🍧🎁 Written by sad-nas & Hama gee muh'd Dedicated 2 *ANEELURV*🌹 27-28 Uncle ibrahim yana isa yayi sallama,maryam ta fito tare da amsa sallamar,tunda ganin fiskarta ya tabbatar tayi kuka. Kallonta yakeyi mai cike da kauna,yace ina mama,miryarta k'asa ba tare data kalleshiba tace tana d'aki. Ibrahim yace aunty meyasaki kuka,shuru tati ta kasa cewa komai,ya sake cewa aunty pls banaso in sake ganin hawaye a fiskarki wlh na yafewa mahaifin camtain amma saboda kece kawai wlh dabadan keba danayi k'aransa,aunty kin wuce duk yadda kike tunani aguna sannan babanki ya rik'emu kamar uba tun bayan rasuwan mahifinmu dan haka ki wantar da hankalinki kinji wlh komai ya wuce zan samu baba anjuma muyi maganan. "Maryam ta d'ago da kanta tana kallonshi tace nagode sosai yah ibrahim,basan dame zan biyakaba a duniyannan Allah yabar zumunci. Murmushi yayi mata tare da cewa ameen aunty pls kicire komai a ranki karki nunawa captain wani canji sannan karki sanar dashi kinji,to tace dashi yace to ai seki murmushi dan fishi bai kamacekiba,dariya takeyi wanda yake kara mishi kaunarta a ranshi nan sauyin kallon da yake mata ya canja,wanda ita ita da kanta ta lura da hakan,take jikinta yayi sanyi,shi kuwa juyawa yayi ya tafi batare daya sake cewa komaiba. Tunani sosai maryam ta shiga akan yanayin yah ibrahim tace kodai sona yakeyi to? Kai a'a da sona yakeyi aida ya dad'e da fad'a kawai dan kila dan kokarinane yasa yake sona haka amma kuma meyasa yakemin wannan kallon da manosh yake min sannan ya tafi babu sallama? Wayanta ta d'auka ta kirashi bugu d'aua ya kayse ya kirata ta d'auka da sanyin murya tace yah ibrahim katafi babu ko sallama? Yace am sorry aunty bazan iya tsayawa inaci gaba da kallonki bane,tace todai ai semuyi sallama koh kamar dai yadda muka saba. Murmushi yayi yace tokiyi hakuri aunty nayi laifi,murmushin ta mayar mashi tace ba komai ya wuce dama shiyasa na sake kiranka. Yace tona gode aunty ina so in miki wata tambaya pls ki gayamin karkiji kunyana,tace to inaji, "you love camtain right?" Shuru tayi dan bata tab'a tunanin jin wannan tambayan daga garesaba,yace aunty kinyi shuru,tace yah ibrahim yana da wani haline mara kyau kodai kasan wani abu mara kyaune game dashi? Yace "aunty" namiki tambaya kimin tambaya,cikin sanyin murya tace yah ibrahim bazan iya b'oye maka komai a duniyannan ba "yes ina sonshi" amma wlh idan yana da wani aibu kagayamun ko kuma baba,tunda dama ai nace kayi bin ike akanshi. Ibrahim yace hakane aunty wlh bayi da wani aibu ko hali mara kyau kawai dai na tambayekine,tace tomeyasa kamin tambayan? Yace yanzu nayi laifi kenan,yace bakayiba nima ina so ka gayamin me dadilin tambayan? Yace idan muka sake had'uwa zan gayamiki yayinda nake kallon fiskarki kinji,tace toshikenan nagode,yace ok bye sannan ya katse. Maryam dai da tunanin maganansu ta kwana a rai kuma daahi ta tashi. Rashida ce taje gun maryam,lokacin tana zaune a gaban *computer* tana sanye da blue jeans da kuma jan top mai dogon hannu ta nad'e kanta da *light brown* gyale k'arami,rashida tace kai amma kinyi kyau a kayannan bari in miki *picture* ai kuwa maryam tayi dariya fararen hakwaranta suka bayyana rash ta dauka tare da cewa gaskya ki turawa captain wannan pic din dan yayi kyau sosai wlh. Murmushi maryam tayi tare da kab'ar wayan rash tana ganin pic din, nan suka koma kan k'aramin gadonta tana shirya books nata rashida se d'aukata takeyi,maryam tace ke ya isama mana. Dariya rash tayi sannan suka fara hira nanne maryam take gaya mata cewa mahaifin manosh ne ya buge mahaifinta kumata gayawa yah ibrahim,hankalin rashida ya tashi sosai ta mik'e tsaye tace mahaifin manosh fa kikace,maryam tace eh wlh wlh shine kinsan jiya naje gaida mum nashi acan naganshi. Rashida tace wlh bazai yuba,ya rabani da mahaifina shikenan aahe manosh bai sami mahaifi nagari wlh tunda har zai iya yin kissa sannan kuma ya gudu mugu mara imani wlh Allah ya isa mana. Maryam tace dan kiyi hakuri rash kidena fad'a haka,rash tace ai wlh ba mutumin kirki bane tunda haka yake Allah yasa camtain karya d'auko halinsa dan wlh indai halinsu d'aya to ina tausaya miki maryam. Maryam tanata bata hakuri amma ina rash se kuka takeyi harta fara cewa to yanzu kinsan hakan tome kuke ciki da captaim maryam? Maryam tace kamar ya rash? Rash tace har yanzu kina son captain, maryam tace rash wani irin magane haka kuma pls kiyi hakuri ki nitsu pls,rash tace in nutsu,hakan ya nuna har yanzu kina tare da captain kenan maryam mahaifina fa mahaifinkine,kuma har zaki iya ci gaba da soyayya da d'ansa,lallai nagode danke mahaifin na raye shiyasa keto marwan d'inma daga yau bani bashi tunda shi abokin manosh ne koma ince amininsa dan haka kema daga yau *bani bake maryam* tana kaiwa nan ta ta fice tanata kuka sosai. Mamakine sosai ya kama maryam dajin kalaman rash,dan tunda suka taso ko musu bai tab'a shiga tsakaninsuba kowa ya sansu kuma yasan shak'uwarsu sannan maryam tana son rash sosai fiye da sauran k'awayenta dan haka se abin ya dameta sosai, dama mamanta ta tafi angiwa dan haka ta rufe gida tabi bayan rash. Kuka sosai rash takeyi itama mamanta bata gida dan yare suka fita da maman rash d'in sunje barkan haihuwa. Maryam tace haba rash yau har zaki iya furta cewa *bake bani* akan manosh,rash nasan ina son manosh amma wlh soyayyar da nake miki yafi wanda nakeyiwa manosh,domin shi zan iya rabuwa dashi amma ke na d'aukeki tamkar k'anwatace da muke ciki d'aya meyasa zakice haka dan Allah? idan rash jajur dan kuka tace wlh karyane maryam dakam nasan kina sona amma banda yanzu dan haka ki fita kibar mana gidanmu ki fita bana bukatan in sake ganinki dake da kowa nakima ki fita anan da k'arfi ta hank'e maryam har waje se jinta tayi ta mannu da mutum ta bayanta. Da sauri ta goge hawayen idonta tare da juyowa se sukayi ido hud'u da yah ibrahim take hawaye yaci gaba da gangarowa a fiskanta ta juya tana kallon rashida da tsoro ya gama kamata dan ganin yah ibrahim datayi. Wucewa maryam zatayi da kukanta se yah ibrahim yayi saurin rik'o hannunta yace auntyn kiyi hakuri meya had'aku? Karon farko kenan danamiji ya rike hannu maryam bata iya cewa komaiba se kokarin fisgan hannunta takeyi agun yah ibrahim tace dan Allah ka sakeni yah ibrahim zan tafi gida,yace no aunty dan Allah ki tsaya yana rike da hannunta ya juya rai a b'ace yana kallon k'anwarshi rash yace ke meya faru,jiki na rawa ta gaya mishi,ya e shine yau da hannunki harkin iya hankad'e maryam rash? Ina ruwanki azan,yana rik'e da hannun maryam harya isa gun rash *belt* d'in jikinshi ya zaro rash ta fara kuka tare da cewa dan Allah yah ibrahim kayi hakuri wlh bazan sakeba. Rash ta tsorata sosai dan tasan halinshi sarai, kukda dai bai tab'a dukantaba tunda take. Maryam tayi saurin shiga tsakaninsu tana hawaye tace dan Allah ya ibrahim karka dake pls,tsawa ibrahim ya dakawa maryam wanda dukkansu seda suka tsorata yace aunty ki matsa! Rash ta rike maryam sosai tana bashi hakuri. Maryam tace kayi hakuri yah ibrahim amma sedai ka dakemu dukkanmu tana kuka sosai. Jikinshi yayi sanyi dan yadda yaga maryam take kuka haka ya sake *belt* din a k'asa rash kuwa da gudu ta fita ta wuce d'akin mamanta ta kulle da key. Maryam ma tazo zata wuce amma seya tareta,kuka takeyi tace yah ibrahim zan tafi gida,yace *aunty am sorry pls akan abinda rash tamiki*,maryam batace komaiba tace pls kaban hanya in wuce,yace sekin share hawayenki,bai jira me zataceba yasa hannunsa yana share mata,tayi saurin kawar da kanta gefe tare da buge hannunsa daga kan fiskanta,amma ina seya sake mayarwa tare da rik'e hannunta yace pls aunty ki dena kuka wlh har cikin raina nake jin kukanki sabo da yadda nake *k'aunarki tunda dad'ewa*. Da sauri maryam ta d'ago da kanta suna kallon junansu sosai har cikin ido,hakan ya sake rikitar da ibrahim sosai aise ya tsinci kanshi da fara matso da fiskarshi dedai nata da niyan kissing nata. Idanunta ta zaro tare da bigeshi gefe tayi saurin barin d'akin da gudu ta wuce gida,shi kuwa wani ajiyar zuciya ya sauke huuuuuh! tare da nadaman abinda yake son aikatawa... [7:10am, 4/2/2017] Sadiya Taheer: 🍭🎈AUNTY'N YARA🍧🎁AUNTY'N YARA🍧🎁 Written by sad-nas & Hama gee muh'd Dedicated 2 *billy tabacco*🌹 29-30 Maryam tana komawa gida ta wuce d'akinta dama mamanta bata dawoba,ta kwanta tana kuka sakamakon tunawa da kalmomin rash agare. Dan bata tab'a zaton cewa wani abu zai shiga tsakaninsuba. Wayartace ta fara ringing kodata duba se taga manosh ne,haka

Chapter 4 of 17