Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
cikin maroon less daya mata bala'in kyau sannan taje suka gaisa dasu yapendo. Hadiza da nafisa sukace amma dai jiya acan kika kwana yau da asuba kika dawo nan ko? Murmushi takeyi tare dace musu eh acan na kwana. Dariya sukayi sukace ehen dan har mukayi bacci baki dawo gaskya akwai aiki da captain d'innan naki,maryam tace bafa nason sa ido kun dameni wlh bari inmishi waya azo a maidaku kawai,dariya sukayi dukkansu tare da cewa base anzo kaimubama,zamu tafi da kanmu. Nafisa tace bari inje naji ana kirana,da sauri ta fito taga abokin angone,bayan sun gaisane yace dan Allah kiyiwa amaryanmu magana captain yana kiranta wayanta a kashe,tace ok tareda komawa tace hmm wannan angonka wai kije ki bashi na safe ya kira wayarki a kashe,dariua maryam tayi tare da dukan nafisa tace wlh kina da aiki yanzu badama ya kirani seda wani abu?tace eh mana tome zai niki aidai ya hak'ura semun bar gidan. Maryam ta d'auki farin gyalenta mai kauri ta yafa tace kanki akeji 'yar sa ido sannan ta fita. Ahankali take sauka daga saman,amma bata hangoshi a palonba,tace kodai yauma a d'akin yake? Daga bayanta taji yace apple,juyowa tayi ta ganshi sanye da kakin sojojinsa yana zaune kan daining. Ta k'ara inda yaja mata kujera ta zauna tare da cewa ina kwana,yace lfy kin yashi lfy tace lfy lau,yace yasu yapendo dasu hadiza,tace duk lfyansu lau. Kallonshi takeyi da alamun tambaya ganinshi sanye da kaki,murmushi ya mata yace yadai,tace zakaje wani gurinne,ya rik'o hannunta yana wasa dashi da hannunsa masu laushi gashi sunyi sanyi yace eh zan fitane amma zuwa azahar zan dawo. Tace lfy dai ko,yace lfy lau sema alkhairi idan na dawo zakiji komai kinji,tace toh Allah ya taimaka Allah yasa ka fita a sa'a,yace ameeen thankyou sannan ya mik'e tsaye itama ya mik'ar da ita tare da rungumeta tsam,tace dan Allah ka bari idan wani ya shigofa,yace babu wanda zai shigama ki saki jikinki kinji,jin hakan yasa ta sake sosai a jikinsa tanajin k'amshi jikinsa. D'agowa yayi yace kardai har kin fara bacci,mirmushi tayi tace bacci kuma anan,yace eh mana gashi naji kin sake kamar kin samu gado,kunya sosai taji tare da k'ok'arin janye jikinta amma sam yak'i,tace toni ka barni tunda har tsokanata kakeyi,yace nifa wasa nake miki,murmushi tayi tace to muje,ya saketa tare da cewa ina kenan,suna kallon junansu,taace muje ku gaisa dasu yapendo kafin ka tafi,yace apple a hakan tare da nuna jikinshi,tace eh mana aiba komai,yace wlh dai bazan iyaba tare da rik'o hannunta suka wuce d'akinshi. Agado ya zaunar da ita tare da mik'a mata flower mai kyau yace naso in baki jiya amma sena mance har kika tafi,tayi murmushi tace thankyou tarr da sashi a hanshinta tana jin kamshinsa,yace bari in canja kaya idan naje muka gaisa se inzo inmaida kakin ko,tace to tare da mik'ewa zata fita yace ina zakije,tace zanje in sanar dasu zaka shigone,yace a'a kijirani mu tafi tare dawo ki zauna,bata soba amma haka taje ta zauna,shi kuwa wall drop ya bud'e ya d'auko jallabiyarsa fara tas mai adon glod sannan ya cire kayansa daga shi se boxer da singilet,sam maryam tak'i kallonsa harya saka jallabiyar yasa turare,inda taji kamshi seta juyo dan taga turaren nan suka had'a ido shi kanshi ya lura da abinda take kallo sannan ta juya,zuwa yayi har inda take yace kinason turarenne? Kai ta d'aga mishi alaman eh,murmushi yayi tare da bud'e gun ajiye turarensa ya d'auko mata guda d'aya a cikin kwalinsa yazo ya bata,murna tayi tare da cewa nagode,yace bakomai tashi muje,mik'ewa tayi kuma yana tsaye a gabanta da turarensa a hannunshi,yace bari in fesa miki nawa tunda a bud'e yake,to tace dashi sannan yahau fese mata harda cire lullub'inta da hannunshi yayita fesa mata yana k'arewa kirjinta kallo,kunya sosai tajitace aiyi haka,yace kin tabbata tace eh,nan ya ajiye turaren batare dayaje ko inaba sannan ya d'auki gyalenta ya yafa mata kamar yadda tayi,kallon juna sukeyi suna murmushi tace nagode,yace nima nagode sannan ya d'auki takalminsa yace muje yana rik'e da hannunta suka k'arasa gun steps. Anan ya tsaya ita kuwa ta haura yanata kallonta taje ta sanar musu sannan ta dawo tace mishi bismillah,yace ok sannan yaa rike da ita a kafad'a har suka isa gun k'ofa shinefa ya saketa tayi saurin wucewa d'akinta shi kuwa ya tsuguna yana gaishesu. Maryam tana shiga ta ajiye turaren da kuma flower tana mai murmushi,hadiza tace tofa hmmm wato seda kika sakeyin wanka acan harda turare,tace eh d'in banafa nason sa ido ni inadai yazama mijina tofa ku kiyayeni kuma kar wanda ya bud'e turarennan bare kuma ku tab'amin flower yara sesa ido kuka iya tana murgud'a musu baki ta fice sunata binta da kallo. D'akinsa ta shiga da sallam harya maida kakin sojojinsa,seya ganta da tea a hannunta da kuma bread ga blueband duk a tirei tasasu ta ajiye tace kasha kafin ka fita. Hakan yayi mishi dad'i sosai data nuna kulawarta akansa,shi kuwa manosh baya shan tea mai madara amma dayake ta had'o bayaso yak'i sha haka ya zauna ta mik'a mishi cup d'in take yaji zuciyarsa tana tashi da madaran dayaji,yannunsa yasa a kirjinsa,tace lfy,yace zuciyanane yake tashi wlh,tace toko in had'o maka lipton kawai,yace wannan kuma fa,tace nise insha,yace ok sannan ta fita taje ta had'o ta kawo nishi. Ya karb'a tare da cewa thankyou yasha kuwa sosai tanata kallon yadda yake cin abinchi abin birgewa,kunnenta yaja yace banace miki banaso kallo ba,hannunta tasa akan nashi tace kayi hakuri nifa bakai nake kalloba,seya saki kunne yace nayi karya kenan,tace a'a haka yaci gaba tanata kallonshi harya gama. Sannan yace tokisha,tace zansha amma ba'a nanba,yace toshikenan nizan tafi,ta mik'e tace to Allah ya dado da kai lfy,yace ameen sannan ya mik'a mata kud'i yace karb'i wannan maybe zaki aiken wani abu kasuwa kodai wata buk'ata,tace wlh a'a bana buk'atan komai kuma akwai kud'i a hannuna sosai wlh,yace sam seta karb'a take ta b'ata rai tace ni wlh bana so wlh akwai kud'i a hannuna mai yawa,yace nawane,tace 70k,yace apple kin tabbata,tace wlh kuwa,yace toshikenan gadai kud'i anan ya nuna mata walldrop nashi yace idan kina da buk'ansu kina iya d'auka koma nawa kinji jealousy nah,nan ta b'ata rai yayi saurin rungumeta yace am sorry sunanne kawai yazomin a baki yanzu sorry my luv,shuru tayi,yace haba apple yanga zakiminne to shikenan na fasa fita mukwanta muyi bacci,ido ta zaro tare da cewa na hakura wlh,dariya yayi yace dama kina da idanu manya haka,kunya taji tace muje karkayi late,yace ok tare dasa takalminsa se kallonshi takeyi tanajin dad'i tare da godewa Allah,d'agowa yayi yace apple pls bana son yawan kallo kinji,itadai abin yana bata mamakiyi kuma taga da gaske yake,tace meyasa to? Yace idan na dawo zan gaya miki,tace to tare daci gaba da kallonshi,rungumeta yayi tare da tsotsar lips nata sannan ya saketa yace idan na dawo zan naidasu yapendo kinji,tace to sannan ya tafi ita kuwa ta d'auki tirai ta fice ta dawo ta gyara mashi ko'ina sannan ta rufo kofan ta taho da key d'in d'aki. Lubna ce agun miher tanata kuka tace yanzu shikenan wanda zuciyata take k'auna ya zama mijin wata,kuka sosai takeyi miher amarya se bata hakuri takeyi tace haba lubna tunfa jiya kike abu d'aya,kiyi hakuri kibarwa Allah komai idan bro manosh mijinkine tofa dole seya aureki. Lubna ta bud'e jajauen idanunta tace pls kidena zolayata nafasan irin k'aunar da captain yakeyiwa maryam,baya iya 5minit baiji muryantaba kuma bro marwan yacewa mum wlh manosh yayi alk'awarin cewa maryam ita kad'aice manosh yake kauna duk fad'i duniya. Miher tace hakane amma ai komai yana gun Allah ne bagun bro manosh,lubna dai sam tak'i se kuka takeyi tare dajin haushin maryam kuma ayanzu. Azuciyarta tace wlh dabadan saddam ya cuceniba dasena auri manosh kota wace hanyace danni shi kad'ai nake so,ibrahim kawai dan dai asirina zai rufune badan ina sonshiba wlh,kai amma maryam kinyi sa'an samun miji kamar bro manosh,mik'ewa tayi ta shige toilet tanata kuka sannan ta wanke fiskanta ta fito miher sebinta da kallo takeyi tare dajin tausayinta gashi duk sunyi aure banda ita. Abinci lafiyayya aka kaiwasu maryam daga gidansu manosh,na safe daban na rana ma daban. Tunda manosh ya fita bai kira maryam ba se 3:37pm yace da ita albishirinki,tace goro,yace fari ko ja,tace fari tas kamar fiskarka. Murmushi yayi yace toshikenan ganinan dawowa nafiso inga fiskarki lokacin da nake sanar dake,murmushi tayi tace to seka iso. Zuwa 4pm manosh ya iso gida,wayanta ya kira taje d'aki ta sameshi,ya cire kayanshi harya shiga wanka,kayan nashi ta nad'e ta mayar walldrop,sannan ta fito mishi da wanda zaisa. Tana zaune ya fito da towel a west nashi,sam tak'i d'agowa har seda yasa data fito mishi dashi yace nagode,tace dame,yace da fito min da kayan sawana,murmushi tayi tace kaci abincine? Yace nachi wlh acan akoshe nake apple "thanks for d care" zama yayi kusa da ita yace juyo kina kallona,ba musu ta fiskance,yace k'iran da akamin bana koai bane sena k'arin girma daga captain manosh zuwa asistan major,kallonsa tayi har cikin ido cikin mamaki tace kad'in,yace wlh kuwa, rungumeshi tayi sosai sedaya fad'i akan gadon. Kunya taji tayi saurin tashi tace kayi hakuri murnane yamin yawa,alhamdulillah Allah ya tayaka rik'o akan gaskya da adalci peach nah,yace ameen my luv tare da kissing d'in hannunta yace su yapendo sun shirya,tace eh tun d'azu,yace ok muje bari abokina yaje ya musu magana,tace to tare da komawa d'akinta. Bayan isarta da 5minit abokin yayi sallama yace hadiza wai kufito muje inkun gama,tace to sannan ta gayawa su yapendo suka shirya tsaf suka fito,nan maryam ta fara kuka dataga zasu tafi a barta ita kad'ai. Su nafisa kuwa se zolayarta sukeyi haka suka tafi aka barta ita kad'ai agidan tanata kuka. Manosh bai dawoba harse bayan magrib abokanshi suka rakoshi lokacin maryam tana karatun qur'an yashigo d'akinta da sallamarshi...... [7:12am, 4/2/2017] Sadiya Taheer: 🍭🎈AUNTY'N YARA🍧🎁AUNTY'N YARA🍧🎁 Written by sad-nas *dedicated 2 amal aliyu & ummul aliyu*❤💕💕 ❤)*❤)* ❤❤ 57-58 Gidan majid duk an watse amma banda lubna,tanata kuka tana jiran shigowan majid. Bayan ya shigone yaga motarta,yana shiga yaga se kuka takeyi,yace sis lfy kike kuwa meya faru? Nan miher ta bashi lbrn duk abinda yake damunta game da bro manosh. Shuru majid yayi tare da tausayawa lubna,yace amma sis kinsan kina sonshine shine koni baki tab'a gayaminba,idan bazaki iya gayawa marwan ba aini seki gayamin ko muhsin ko muh'd,gaskya ina tausaya niki sosai dan wlh lokaci ya k'ire yanzu tunda kinga manosh yayi aure,sannan kwata kwata captain bayi da ra'ayin yin mata biyu a rayuwarsa dan yana kaunar aunt fiye da tunani wlh sannan koda marwan d'in kika gayawa nasan hakuri zai baki danmune shaida akan irin k'aunar da manosh yakeyiwa aunt. Banaji ance ibrahim brothern su rash yana nemankiba,ai shima mutumin kirkine sis dukmun yaba da halinsa wlh ga addini zakiji dad'i sosai agunshi,amatsayina ya brothernki shawaran dazan baki shine kiyi hakuri ki cire captain a ranki dan wlh wahala kawai zakisha bazai yaddaba,dama ace ace baiyi aure bane toyariga dayayi aure sis. Lubna cikin muryan kuma tace pls bro majid kayiwa daddy magana wlh ni shikad'ai nake so dan Allah ka taimakamin,tausayinta ya kama majid sosai yace kiyi hakuri sis amma gaskya nake gaya miki idan kikaci gaba dasashi a ranki to wlh zakisha wahalane kawai gara kiyi hakuri kici gaba da addu'a. Wayan manosh ne yashigo majid ya d'auka hello abokina yane,yace lfy lau ina k'anwata,yace gatanan,nan majid ya mik'awa miher ta karb'a tate dacewa hello bro,yace yakike,tace lfy ina aunt,yace gata zakuyi magana,nan maryam tace hello amarya,miher tayi dariya tace amare dai,tace ina ango majid,tace gashinan,maryam tace ok yadawo gida kenan shima,tace eh,maryam tayi murmushi tace toshikenan seda safe,miher tace to Allah ya bamu alkhairi sannan ta mik'awa majid,yace ango shikenan,manosh yace aunt ce tace waina dawo gida da wuri bayan ku baku komaba,shine na kiraka danta tabbatar da cewa kana gida,dariya majid yayi yace a isarmin da gaisuwa,yace tana jinka ai seda safe yace okey. Majid yace lubna muje in maidake gida se driver ya dawo dani dan bazan barki kiyi driving a hakaba,cikin kuka ta mik'e suka tafi. Manosh ne zaune kusa da maryam a d'akinta yace meyasa kikayi shuru agaban friends nawa? Tace tomezance aidai na musu godiya bayan sun gama jawabin ko,murmushi yayi yace to kici kazan mana,tace nifa ak'oshe nake,yace niban uardaba kici,tace wlh nak'oshi bazan ciba. Yace kinaso mu b'ata ko,ta e Allah peach akoshe nake,yace to shikenan nima bazanciba. Kazan ta bud'e tasa musu a plate tace to bismillah seta d'auki k'oda taci,sannan shima yaci amma itakam bata sake cin komaiba se ruwa datasha. Dama tunda yaje raka friends nashi ta shirya tasa rigan bacci dogo iya gwiwanta ya tsaya se hula dayake kanta mara nauyi,shi kuwa 3quater ce kawai ajikinsa jikinshi babu komai,hakan yasa takejin kunyanshi da kuma tsoronshi. Bayan ya gamane seya shiga toilet nata da sauri ta kwace komai takai kichine tanata sauri ta dawo karya fito daga toilet amma setaga harma ya kwanta kuma yasa riga k'arami a jikinsa yayinda ya rufe rabin jikinsa da bargo. Dad'i taji aranta tace Allah yasama bacci ya d'aukeka dan tsoronshi takeji sosai yaud'in. Ahankali ta kwanta gefe tare dajan bargon itama ta rufe dukkan jikinta dan d'akin yayi sanyi,sunkai kusan 10minit shuru kamar wanda sukayi bacci amma kuma idonsu biyu,juyowa yayi yana ganinta yayi magana batare daya kira sunantaba yace dawuta kike bacci ne,amsa tabashi batare data juyoba tace a'a,tashi yayi ya kashe wutan sannan ya koma ya kwanta. Bayan tayi addu'ointane ta tofe ko ina sannan tayi niyanyin bacci,shuru babu wanda yace komai har kusan 1hr,itadai maryam tanata mamakinshi sam baice suyi nafila ba,dan haka tayi niyan yin bacci abinta se taji yace wai bacci zakiyine,eh tace dashi,setaji yace bacci kikazoyi? Tambayar yayi mata wani iri amma setayi shuru kamar batajishiba,ya sake cewa dake nake *maryam*bacci kikazoyi gidanna,mamakine sosai ya kamata dajin irin kalaman manosh,gashima yau ya kira da sunan mum nashi kai tsayae wanda sam bai tab'a kiranta dashiba tunda suke. Batada amsan da zata bashi dan haka tayi shuru tana jiran mezai k'ara cewa. Sunanta ya kira a tsawace maryam! Ina miki magana kinajina,take tsoro ya kamata tayi saurin cewa naga kamar bacci kakeji shiyasa,yace aikin banza tare da tashi ya d'auki wayanshi yabar mata d'akin zuwa nashi d'akin. Maryam ta tashi ta kunna wutan d'akin tana mamakin abinda ya faru yanzu kamar a mafarki take gani. Wani zuciya yace ta tashi ta bishi,wani zuciyan kuma yace mata kwanta abinki,haka takasa kashe wutan ta kwanta tanata tunanin abun aranta daganan bacci ya d'auketa ba ita ta farkaba se asuba. Koda maryam ta farka bataga manosh ba,hakan ya tabbatar mata da cewa bai dawoba kenan a d'akinsa ya kwana. Mikewa tayi tayi alwala tayi sallah tare dayin addu'ointa sannan ta wuce d'akinshi dake sama ta shiga da sallama,yana kwance akan sallaya inda yayi sallah,harma ya fara bacci seya farka tare da amsa sallamarta idanunshi sunyi jah. Tunda taganshi tasan cewa baiyi bacciba jiya,sunkuyawa tayi har k'ara tace ina kwana,yace lfy kin tashi lfy,tace lfy lau yanaga idanunka sunyi jah haka,yace bacci nakeji sosai apple kuma na gaji wlh ban ganewa jikin nawaba,tace subhanallahi bakayi bacci jiyabane? Jajayen idanunsa ya d'ago yana kallonta yace bakin barni nikad'aiba kink'i kizo,mamaki sosai tayi tace muna kwancefa ka tashi ka fito peach kodai fushi kake dani dan nak'i cin kazan jiya,yace a'a taimakamin inhau gado pls apple,kallonsa takeyi kamar dai bugegge haka ta rikoshi ya kwanta tare da janyota jikinshi ya rungumeta yace i luve apple,wani sanyi taji a ranta ta kwanta lub ajikinshi. Shuru taji alamun bacci yayi,ahankali ta d'ago da kanta setaga yayi bacci,mamaki abun yabata tace tomeya hana peach yin bacci jiya,abun ya d'aure mata kai sosai setayi yunk'urin tashi,amma sam ya k'ank'ameta da hannayenshi daya had'asu a bayanta,idan tayi yunk'urin tashi seyace pls apple let sleep okay? Tace okay peach amma na takuraka ai a hakan bari mu gyara kwanciya,sam yaqi hakata kwanta harseda baccin nashi yayi nisa sannan tajanye jikinta tare da rufeshi tanata k'are mishi kallo sannan ta fita zuwa d'aki itama baccin tayi bayanta gama tunani. Manosh bai farkaba har se azahar,maryam ta damu sosai da irin baccinshi. Har aka kawo musu abincin safe dana rana duk yana bacci. Yana tashi yayi toilet yayi wanka tare da alwala yayi sallah ya shirya cikin kananan kaya ya fito,abincine jere akan daining na palourn shi amma seya wuce d'akin apple inda take kwance akan gadonta,shigowarshi yasata mik'ewa ya qare mata hannayenshi da sauri taje ta rungumeshi tana murmushi shima haka,yace kiyi hakuri apple inata bacci nabarki ke kad'ai yaushe kika tashi,tace tun lokacin dakayi bacci,yace wato kinmin wayoko,murmushi tayi tace muje kaci abinci mum ta aiko mana tun safe ga kuma naranama. D'aukanta yayi cak yayinda kunya ya kamata shi kuwa ko'ajikinshi har suka isa daining sannan ya ajiyeta akan cinyarsa ita kuwa ta zuba musu abinci tare da spoon 2,tana bashi yana bata abin sha'awa take ta mance abinda ya faru jiya sunci abinci sosai sannan sukasha fruit,ya sake d'aukanta se d'akinta can suka kwanta akan gado ita kuwa tana kwance a jikinsa. Yace apple meya faru jiyane,tace bakomai,yace ya akayi banci amarcinabane,kunya taji sosai batace komaiba,ahankali ya fara shafata ita kuwa tsoro ta faraji,yace menene apple,tace babu,yace akwai mana gashi jikinki yana rawa,kina jin tsorone,kaita d'aga alamun eh,yace kidena tsoro bazan miki komaiba kinji? Shuru tayi tanajin yadda yake tab'ata,yawu ya had'iya tare da cewa yau kam ai zanci amarcina ko apple,kaita girgiza alamun a'a,murmushi yayi yace haba apple d'ina meyasa,cikin wata irin murya tace inajin tsoro,matseta yayi ajikinshi tare dayin k'asa da muryanshi yace kidena tsoro bakomai kinji,batace komaiba yace apple dakenakeyi,nidai banso,yace toni ai inaso apple bakya tausayinane,akunnenta yayi maganar a hankali qanda ya sake kashe mata jiki ta lume sosai ajikinshi,shi kuwa rikicewa yayi dosai aise yahau kissing nata tun tanajin kunya harta sake. Da dare kuwa manosh yana d'akinshi sam baizo gun maryamba. Ita kuwa tayita jiran shigowarshi amma shuru har 9:30pm,kuma bataso takai kanta dan haka ta kwanta har tayi bacci baizoba aeda taji kiran sallah seta farka tare da mamaki yauma manosh a d'akinshi ya kwana kenan,abun ya fara damunta yanzu kam,bayan tayi sallah ne taje taga yana bacci tare da jallabiyarshi a jikinshi da alamu tunda yayi sallah ya koma bacci. Hakan yasa ta koma d'aki tanata tunani,gashi su samira sunbata lbrn yadda sukasha wuya agun mazajensu,dukdadai basu gaya mata komaiba amma tasan duk sunci amarcinsu inbanda rash da take period nata. Hakadai manosh da maryam suka kasance har tsawon 3days batare da wani abu ya shiga tsakaninsuba. Yaune kwana na hud'u kamar kullum maryam tace bari dai taje ta duba meyasa manosh baya zuwa da dare seda rana yayita romancing nata. Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un ta fad'a tare da k'arasawa inda yake kwance yana juyi tare da rik'e cikinsa da hannayensa. Maryam ta rik'oshi tana hawaye peach lfy,meke damunka,hannunta tasa adaidai nashi tace cikinkane,cikin wata irin murya yace apple tashi ki tafi d'aki,tace meyasa zan tafi d'aki bayan gashi kanafa da ciwon ciki,ita a tunaninta dan yaga tanajin tsoronshine baya so ya kusanceta harya ja mishi ciwon cikin. Cikin kuka tare dajin tausayinshi tace peach dan Allah kayi hakuri wlh daga yau nadena jin tsoronka bansan ina cutar dakai har hakaba pls kayafemin. Yace apple pls ki tashi ki fita! Cikin tsawa wanda sedata razata amma sam tak'i barinsa se kuka da takeyi tana tofa mishi addu'a a cikin nashi sannan ta cire rigan baccinta daga ita se wandon tace peach kayi hakuri wlh nadena daga yau,jinta a jikinshi kuma yaji babu riga yasashi tasowa idanunsa kamar atarugu yana kallonta rai b'ace,take tsoro ya kamata tace peach miye kuma haka kake min irin wannan kwallon,wuyanta ya kamo yana cewa wato ke gaki mara kunya 'yar iska ko,take maryam ta fara tari da kuma kuka tana magana da kyar tana cewa pea..ch menay..i ma..kane zaka kashe..nine.wuyana pea...ch sannan taci gaba da tari,flower gefen gadonshi ta d'auka ta buga mishi awuya sannan ya saketa da sauri ta gudu zuwa d'akinta tana kuka tare da sauke numfashi tana mamakin manosh,tabbas manosh yaba cikin hayyacinsa,riga ta d'auko a walldrop tasa setaji yanata buga k'ofa yana cewa ki bud'e kofannan *maryam* tsoro sosai taji da yadda yake buga kofan,toilet ta shiga tayi alwala tazo tayi sallah raka'a 2 ta zaunayin addu'a sosai. Manosh ta jiyo yana cewa wlh idan kika yadda na bud'e kofannan tofa gawanki za'afitar. Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un taketa yi tare da addu'uoi. Yah ibrahim ne kawai ya fad'o mata arai,nan ta d'auki waya ta kirashi lokacin 10:5pm bugu d'aya ya d'auka baice komaiba tace yah ibrahim dan Allah kazo yanzu,akwai matsala amma pls karka gayawasu mama komai,hankalinshi atashe dajin yadda take kuka yayi saurin zuwa gun babanta yace abashi aron mota yanzu zai dawo,batare da b'ata lokaciba baba ya bashi keyn hondansa,dan motar maryam kam tun ran biki yakai mata shi gida. 15minit sega ibrahim a gate d'in gidan manosh,amma maigadi ya hanashi wucewa seda ya kira maryam ta waya ya had'asu kafin yabar ibrahim ya shigo da saurin. Jin tsayuwar mota yasa manosh yadawo daidai, take ya fara cewa apple meyasameki ,meyasa kike kuka bud'emin kofan kinji apple, ita kanta taji sauyin mura tattare dashi, mamakine ya kamata amma sam tak'i bud'e mishi. Bugun kofan falon k'asane yasa manosh barin gurin yaje ya bud'e kawai seyaga yah ibrahim ne a tsaye suna kallon juna cikeda mamaki,manosh baisan babu riga ajikinsaba sedayaga irin kallon da ibrahim yake mishi sannan yalura da jikinsa dagashi se boxers..... [7:12am, 4/2/2017] Sadiya Taheer: 🍭🎈AUNTY'N YARA🍧🎁AUNTY'N YARA🍧🎁 Written by sad-nas *this ❤)* ❤)* page is dedicated to fans of tana raina,i luv u all* ❤💞❤💕💐🌺🌹 59-60 Bismillah yace da ibrahim,cikin jin kunya ya wuce sama domin sa kaya. Ibrahim ya zauna yana jiran fitowan maryam. Bayan manosh ya sako jallabiyane yaje kofan d'akin maryam saboda kukanta dayakeji,take hankalinsa ya tashi yanta cewa apple pls apen d door,ahankali ta bud'e tana rakub'e ajikin kofa sanye da doguwar riga da kuma gyalenshi. Rungumeta yayi sosai dan ganinta wani iri,ita kuwa sam takasa sake jikinta se fama kwacewa takeyi,manosh ya lura da hakan yace apple meke faruwane meyasa kike kuka,kallonshi ta tsayayi cike da hawaye tace bakaivabe ka shak'eni kace zaka kasheni dak'ar na kwaci kaina agunka dubi wuya kaga yadda kamin peach mena maka hakane, kallon wuyanta yake ga alamun hannun mutum kuma yayi jah shatin hannun ya zauna a wuyanta sosai. Hannu manosh yakai yana tab'a tare da cewa apple ni kuma,yaushe na miki hakan,kallonshi ta tsayayi cikin mama da kuma tsoro tace ka matsamin zanje gun yah ibrahim,se anan ya tuna da yah ibrahim yazo,tace nina kira yah ibrahim a waya nace yazo dan ka biyo har nan kashe idan ka shigo kasheni zaki nikuma ina jin tsoro shine na kirashi. Rungumeta yayi yana magana cikin nadama yace apple wlh bansan komai akan abunda kike gayaminba pls apple kiyi hakuri karki gayayawa ibrahim komai,yaushe akayi airen har za'a fara jinmu,pls apple wlh niban miki komaiba taya za'ayi in miki haka kuma? Itadai gabad'a bata gane mishiba dan haka tace to muje gun yah ibrahim,yace kimin alkawarin bazaki fad'a,shuru tayi tace muje bakomai,nan suka firo a tare tana sauka k'asa tayi gudu taje inda ya ibrahim yake ta zauna kusa dashi tare dayin kuka tace yah ibrahim ka d'aukeni mu tafi gida wlh kasheni zaiyi kaga abinda yaminfa. Afusa ibrahim ya mik'e dan yasan maryam bazata tab'a mishi karyaba,yace captain meke faruwane,metayi haka da irin wannan shatin dake wuyanta? Manosh ya juya a sanyaye yana kallon maryam yace haba apple yanzu haka zakimin,wlh ibrahim niban mata komaiba meyasa kikamin haka apple? Maryam tana kuka tace wlh yah ibrahim shine,sedana buga mishi flower a wuyansa sannan ya sakeni wlh kaine peach babu yadda za'ayi inyi maka karya wlh yah ibrahim cewa yayi zai kasheni kuma wlh banyi ishi komaiba. Manosh kamar zaiyi kuka se rantsuwa yakeyiwa ibrahim yace shi wlh baiyi mata komaiba,ibrahim yace yanzu maganan waye zan kama acikinkune kaina ya d'aure wlh. Maryam tace yah ibrahim na tab'a maka karya,kuma menene ribana idan nayiwa mijina karya,wlh Allah shine ya shakeni tare dayin wasu maganganu wlh yah ibrahim ba karya nake mishiba. Manosh yayi shuru danya rasa mema zaice,ibrahim ya kira marwan a waya yace kazo ina gidan manosh yanzu pls. Marwan ya kalli rash da take kwance ajikinshi yace kiyi hakuri zanje gun ibrahim in dawo kin,tace pls karka dad'e dan tsoro nakeji,yace bazan dad'eba my darling sannan ya shirya ya tafi. Cikin k'ankanin lokaci ya iso cike da tunanin komeya faru ibrahim ya kirashi kuma gidan captain. Da sallama ya shigo tunda yaga maryam kusa da ibrahim yasan akwai matsala,bayan ya zaunane yace captain,manosh yace yane,sannan suka gaisa da yah ibrahim. Yah ibrahim yace marwan wani abune ya d'aure min kai sosai gaskya shiyasa na kiraka ko zamu samu mafita,marwan yace okey meya faru yana kallon maryam kanta a sunkuye,ibrahim ya gaya mishi,mamakine bayyane a idon marwan yace gaskya kozaka kwana kana gayamin bazan tab'a yadda abokina zaiyiwa aunty hakaba saboda mune shaida akan irin k'aunar da yake mata taya kuma za'ace manosh ya shak'eta da sunan zai kasheta a wani dalili? Ibrahim yace kamar yadda ka yarda da manosh ka kuma san halinshi,tonima haka na yarda da aunty na kuma san halinta bazata tab'amin karyaba wlh,sannan idan ka dubi wuyanta zaga shaidan abinda take fad'a,kuma lokacin dana shigo da kuma yanayin danaga captain ya tabbatar min acewa akwai matsala,kodai manosh yana da wata matsala ko kuma wani abu da baya so? Marwan yace gaskya bayi da wata matsala ko damuwa,abu d'ayane muka san baya so shine mace tayita kallonshi sam bayason haka. Ibrahim yace bayasan mace ta kalleshi,to saboda me? Marwan yace shidai haka nashi tsarin yake kuma komu bamusan dalilinba kawai dai yace mana shi kawai baya sone. Ibrahim yace to aunty kodai kallonshi kiketayi,dariya abin yabaiwa marwan yace to idan aunty ta kalleshi kuma seya shaketa? Ibrahim yace eh mana tunda dama baya so,marwan yace amma kuma harda aunty gaskya dai ban ganeba abokina meke faruwane? Wani irin mugun kallo manosh yakeyiwa maryam wanda tsoro ya kamata tace yah ibrahim kaga kallon da yakemin ko,wlh ni bazan zaunaba zan bika mu koma gida dan idan kun tafi kasheni zaiyi wlh...bata k'arasaba manosh yayi kanta tare da sake shak'eta yana cewa wlh bazaiyuba baki isaba wlh! Ibrahim da marwan suka mik'e domin tsaidashi,amma ina sun kasa ita kuwa maryam se

Chapter 10 of 17