Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
amince zan aureta idan ba hakaba kuwa bazata k'arayin sallahba. Cikin sauri nace mata na amince zan aureta,tace tofa lallai inda gaskene sena tara da ita kafin ta yarda. Nace mata addina ya haramta hakan bazan iya aikatawaba, tace toshikenan muje amana aure,nan naji zuciyata tak'i amincewa da dahan,nace mata bazaiyuba,idan zaki bautawa Allah tofa kiyi dan tsoronsa amma badan son da kike minba,dan haka inhar kinaso in aureki dagaske tofa sekin koma ga Allah da zuciya d'aya. Tacemin zatayi tunani akan hakan,tofa wannan tunanin nata yakai kusan wata d'aya bata gamashiba. Kuma kullum irin abincin dana sabaci takebani,da farko wani abinci takawomin wanda bansanshi,amma sena k'i nace mata bansanshiba nafison irin wanda na saba ci tace min a ina kenan? Amma sam na kasa bata amsam dan bansaniba bana iya tuna komai na kaina. Murmushi tayi taje ta kawomin abinci irin wanda na saba ci,koda ci abinci senaji irin girkin mum d'inace,da sauri na kalleta harzanyi magana,seta katseni da cewa irin abincin mum d'inkako,nace mata eh ina mamakin kaina,tace karka damu natane acan naje nad'ibo maka dan nasan bazaka iya cin namuba kuma banaso karame. Nidai inada niyan tambayanta akan mumdin nawa,ban sake tunawaba kuma. "Kullum haka muka kasance har tsawon wata guda kuma bata salla. Idan zanyi baccima irin wannan kumbonne dai aciki gadona na alfarma yake da kayan sawa,komaida akwai. Bayan wata guda tacemin ta'amince dan haka ta fara salla,amma bata yadda muyi tare sedai kowa yayi nashi,sannan bansan a inda take kwanaba sesai kawai inganta aduk lokacin da nake da buk'atar ganinta kawai zan ganta kusa dani. Ranan take cemin zata nunamin wani abu amma sena tsunbaceta,sam nak'i senaga hoton aunty agunta,idanuna na bud'e sosai ina kallon fiskan amma nakasa gane wacece,harzan karbi hoton seta b'oye tace dani idan kana so kasake gani dole seka tsunbaceni,nikuwa nak'i,se kuma nagane cewa auntyce,sannan na tuna komai nawa awanan lokacin,da sauri na juyo gareta nace wannan auntyce ai matatace apple nawane meyasa kika rabani da dangina kimaidani kinji? Murmushi tayi tace bazan maidakaba kamadena b'ata bainka. Har zai sake magana setace ka tsunbaceni zan maidake,babu yadda na iya haka na tsunbaci bakinta cikin rawar jiki. Tun daga wannan lokacin ban sake gane komaiba jinta kawai nakeyi acikin jikina,tana cewa kayi hakuri my manosh,wayan aunty ta kira tanata magana da ita amazaunin nine,wanda babu yadda na'iya bare inkaryatata cewa banike magana jikina ta shiga tun lokacin danayi kissing nata. Haka kuma ta sake kiran ibrahim amma cikin ion Allah shiseya gane cewa banine ke maganaba,itace. Taji haushi sosai,dan cewa tayi seta had'akar da rayuwan aunty,shima batai nasaraba saboda irin addu'oin jama'a dasuketayi min. Dan kanta ta bar jikina inda naji ta janye leb'enta daga nawa ta zauna afusace. Inda yake a matsayin d'akin kwanciyana na nufa na kwanta ina haki. Hakadai muka kasance wataran sena tuna da dangina,amma na k'ank'anin lokacine kuma na sake mancewa kenan se kuma wani lokacin harna shafe wata kusan uku a haka,kuma bana ganinta sosai kamar da. Idan na tambayeta ina take zuwa se tacein mutanenka ne suka sani agaba dan haka bani da zama nima. Ma'ana dai addu'oin kune 'yan'uwana dan wataran gabad'aya kwakwalwarta toshewa yakeyi kamar ba itaba gabad'aya seta canja kamanni tayita ihu tana wasu irin abubuwa wanda bana iya jure kallonsu sedai ingudu zuwa d'akina inyi kwanciyata harsena dena jinta. Saboda dazaran nashige makwancina tofa bana iyajin komai datakeyi,watarana tace min inzo zata maidani gida amma sena rungumeta,bamusu na rungumeta tak'e tace inrufe idona,bayan a rufe idonane nad'an mintina setace in bu'de. Kodana bud'e sebangantaba kawai dai naganni a wani shop tsaye ajikin mota se dubata nakeyi da idanuna ina ganin kayanjikina da kuma agogon hannuna wanda bansan ya akai nagansu ajikinaba. Kawai senaga aunty dasu ibrahim sunzo suketamin magana amma sam nakasa ganesu sebinsu da ido nakeyi musamman aunty. Haka dai har suka fara fad'a duk bansan meya had'asuba danna d'auka duniyar tasuce muke har yanzu. Sedata rik'e hannunane tace min ind'awa aunty hannu tayi min nuni da hannunta,shine kuwa nayi yadda ta gayamin sannan tace inyi sauri in rufe ido,kawai sena gammu a nasu duniyar inda tamin masauki. Bayan mun nitsune kuma sena tuno da komai sakamakon b'acewar motanu a idon mutane wanda kowa ya tsorata sekace a film. Dalilin hakanne masu yimin addu'a suka sake yawaita tundaga ranan ban sake mance komaiba game dani harta kaimu wani guri wanda har yanzu bansan ina bane gurin nakasa gane gurin... manosh ya tsaya daba lbrnsa anan saboda razana dayayi yace muhsin wlh nagana marwan. Tabbas naga marwan da rashida awannan gurin kuma suma sun ganni danhar na kirashi ama sam tak'i ta barni muhad'u daga karshema bansan inda takainiba sedana bud'e idonane naganta tana kuka tana cewa wlh bazai yuba my manosh, bazantab'a yarda a rabani dakaiba idan bazan kasance tare dakaiba to wlh auntyma sedai tarasaka......... _inna lillahi wa'inna ilaihirraji'un_ manosh ya furta lokacin dayazo nan da lbrnsane ya tuna da abinda shukrah ta zuba mishi akan dick nashi wanda yayi sanadiyar sumewansa tare dayi ihu mai karfin gaske. Da sauri manosh yasa hannunsa akan dick nashi yaji dai yananan,sanan ya kalli mai d'aukansa yace da wannan nake godiya ga dukkan 'yan'uwa musulmai Allah yasaka muku da gidan aljannah aminnn..... [7:18am, 4/2/2017] Sadiya Taheer: 🍭🎈AUNTY'N YARA🍧🎁AUNTY'N YARA🍧🎁 Written by sad-nas 91-92 Manosh yace what!?? Muh'am kugayamin meke damun aunt! Muhsin yace haba abokina katsu mana kasan dai dolene bazamub'oye maka komaiba amma yana da kyau ka huta. Majid yace kana nufin zai samu sukunine batare dayasan inda aunty takeba,abokina aunty bata da lfy shine aka fitar da ita waje domin duba lfyarta dakyau. "Kafin manosh ya sake musu tambaya muhsin yayi saurin cewa karka d'aga hankalinka rashinkane yasata cikin damuwa harta kamu da ciwon...muh'd yayi saurin cewa ciwon mantuwa. Manosh dai bai gamsu da bayanin nasuba se kallon tuhuma yake musu d'aya bayan d'aya wayar muh'd ya ciro daga aljihun gaban rigansa yayi dailing numbern aunt amma sam baya tfy,hakan yasa ya kira mum nashi ta d'auka tare da cewa hello,manosh yace mum nine wai ina aint ne?" Mum tayi ajiyar zuciya tace son karka damu aunt tana lfy sun tafi indiane domin duba lfyarta,kayi hakuri zakaji komai agida gaji,barka da dawowan my son. Murmushin karfin hali yayi yace to mum,sannan ya ajiye wayan inda alfiya tace daddy ina ka tafi ka barmune kullum idan muje gire gun mummy kuka kawai takeyi waidan baka dawoba. "Murmishi yayi yace tobaganinadawoba,kigayamin medame mummy take gayamiki dabanan?" Alfiya tace ai suna dewa,abdallah dake gun muhsin a baya yace toba se ki gayamishi wanda tafi gaya manaba,tace ina ruwanka aini aka tambaya bakaiba,daddy cewa takeyi munyi kewankako,semuce mata eh,setayi hawaye tace mana itama tana kewarka sosai amma karmu damu kakusa dawowa muyitayin maka addu'a Allah ya dawo dakai lfy,Allah ya kareka daga sharri duk wani abu mai cutarwa afad'in duniyannan semu karanta maka *qulhuwallahu ahad da falad da nass* sannan muyi maka addu'oi wani addu'anma bamu iyaba mummyce takeyi munace ameen. Abdallah yace wlh nidai na iya daddy alfiyace bata iyaba setayita yin jagwalgwale wai ishcibisshaa setace ameeen. Ba manosh kad'aiba dukkansu seda sukayi dariya,inda alfiya tace wlh daddy ka'arya yakeyi na'iya kuma idan mummy ta dawo a tambayetama. Manosh yace ainasan duk kun iua,amma alfiya kinsan abdallah yayankine ko,tace eh tare da d'aga kanta sama,yace to bakyau k'anwa tacewa yayanta yana k'arya kinji? Tace to daddy nadena bazan sakeba,yace yawwa maisanyi na yana mata dariya,tace mutafaaa daddy,ai kuwa seya mika mata hannu suka tafa,sannan ya juya ya dunk'ulawa abdallah hannu suka buga duk suna jin dad'i tare dajin k'aunar yaran nashi yana sake shiga jikinsa musammanma dayasan apple nashi batanan. Muhsin yace saukeni anan muh'd zanje gidan radio goyel domin musanar da al'umma cewa captain ya dawo sannan muyi musu godiya kuje zanzo na sameku. Sukace ok sannan sukaci gaba da tfy hankalin manosh duk baya kansu yana can tunanin apple nashi saboda bala'in missing nata dayayi gashi kuma koda tanananma baisan ya abun zai kasanceba. Majid yace wai lfyanka ko prince,tunanin me kakeyine haka munata magana?" Manosh yace me kukace,wai ina marwan yajene? Muh'd yace wlh bamu saniba dan numbernsa bata shiga sam. Manosh yace kamar yafa? Majid yace pls kabar duk wani magana semunje gida zakaji komai. Babu wanda ya sake cewa komai har suka isa gida Tun daga gate suka fara hango mutane dasuka yiwa manosh barka har suka shige,masu gadi da sauran mutanen sukazo gun da sauri sunayiwa dad d'in manosh barka tare da gaishe da manosh,ba laifi ya sake sukayi musabaha daduk jama'an yana rik'e da alfiya a hannusa sannan suka wuce gefenshi dake gidansu nan yace da alfiya taje gun mum zaiyi wanka,ba musu suka tafi itada abdallah seya wuce toilet. K'arewa kansa kallo yadingayi sannan yayi wanka ya fito ya shirya yayi sallolin da baiyi wato azahar da la'asar. Bayan ya idarne ya fito sanye da jallabiya,dan yana da kaya kad'an a gidan nasu. Abinci aka kawo musu suka ci amma sam dukda yadda manosh yake son fruit yak'isha seya koma kan kujera ya zauna tare kiran abdallah da alfiya ya ajiuesu akan cinyarsa. Daidai nan miher ta shigo da gudunta ta rungume manosh tana kuka" Wani sanyi yaji aranshi dan base nagaya muku irin son da yake tsakanin yaya da k'anwannanba. Manosh yace haba kuma miuena kukan tunda ga bro naki ke kad'ai ya dawo,murmushi tayi tace Allah sarki bro manosh darabon bazan mutuba ashe zan ganka,yace haba sis kidena fad'an haka mana inba kinaso inyi kukaba,take ta share hawaye tana rik'e da hannusa tace yaya ina suka ajiyeka dan Allah? Yace miher ba yanzuba dan Allah kimin bayanin akan aunty bazan iya jiran bayanin su dad ba,kekad'aice zaki gayamin komai. Nan take tace bro Allah sarki aunty taga jarabawa iri iri wlh idan kaganta dole ka rausaya mata danma tana da tawakkali. Bro aunty tana da matsalan *kidney* dukka biyu nata sun lalace ce bro anje mata dashe k'odane bro abinda ya kaisu kenan broo...seta fashe da kuka, mik'ewa manosh yayi yace what!!? Dashe fa kikace nawa za'a dasa mata badai na ibrahim ba!? Miher ta tsorata dan yadda taga hankalin yayanta ya taahi,itama mik'ewa tayi tace karkasa damuwa aranka na *lubna* za'a samata. Manosh ya juya yana kallon miher cikin tuhuma yace lubna kuma? Tomeyasa sena lubna? Meyasa aka tafimin da matata batare dana saniba meyasa!? Abdallah da alfiya se suka fara kuka dan ganin yadda daddynsu ya sauya cikin k'ank'anin lokaci. Muh'd ya mik'e yace miher shiga dasu abdallah gun mum,bamusu ta kamosu sunata kuka kafin su fita manosh yace miher ina marwan rai ab'ace? Tace yaya bro marwan bamusan inda ya tafiba dad nashima yana kwance a hoapital din su bro muh'd. Majid yace my luv jeki ciki dasu pls. Bayan ta tafine majid yace za'a sawa aunty kidney'n lubna sabida su sisters kuma twince ita da aunty,akwai sirri babba wanda hajiya iya kakan marwan da kuma mum d'in marwan suka b'oye wanda se yanzu muka sani,tuk kafin mu sani ashe shi marwan mum nashi tagaya mishi lbrn shine silar rashin lfyanshi daga bisani kuma yayi tfy wanda komuma bamusan inda yakeba har yau. Mamakine bayyane k'arara a fiskan manish ji yake kamar a mafarki kallonsu kawai yakeyi inda dukkansu suka rasa abunyi kowa da abinda yake tunawa aranshi. Sallamar muhsin ne ya katsesu, yace lfy kuwa naganku haka? Manosh yace mekuje nufi da wannan lbrn ne nakasa fahimtar komaifa,meya samu dad din marwan kuma? Sukace hawan jini,sannan dagaskene aunty da lubna ciki d'aya sukafito duk yaran alhaji muh'd atta ne... Wayan muh'd manosh ya karb'a ya kira numbern oganshi sau biyu kafin ya d'aga yace hello sir manosh ne. Ogan yace what! Manosh kana ina? Yace sir ina gida pls sir visa nake so ka taimaka in samu zanje india. Sir yace manosh yanzu haka akwai wanda zai tafi india jibi amadadinka,amma bazan iyabakaba saboda kana bukatan hutu ina nan zuwa gidanku... manosh yace no sir pls aunty tana cikin wani hali sir natabbata tanada bukatana acan,yace manosh _i know everything but you need to rest gaskya_yaushe ka dawo? Yace yanzu sir,pls sir i'm alright wlh just help me,ogansa yace ina zuwa gidanku yanzu. Manosh ya shiga d'aki ya cire jallabiyan jikinsa yasa kananan kaya ya fito yace dasu muhsin muje hospital muga dad d'in marwan,muh'd yace no manosh ka zauna mutane biyu suje gunshi amma kai ana buk'atanka anan,yace ina bazai yuba ai yanzu zamu dawo idan kuma bazakujeba toni na tafi. Sunsan dagaske yakeyi dan haka suka fito inda dad yake waje suna zantawa da wasu malamai. Manosh ya nufi gunsu suka gaisa sannan yace dad zanje duba daddyn marwan yanzu zamu dawo,dad bazai iya hanashiba dan yasan yadda marwan da manosh suke,yace kuje pls majid ku dawo da wuri,yace insha Allah dad sannan suka juya zasu tafi muhsin ne mai driving. Abdallah ne ya fito yanata kuka wai zaibi daddynshi,daga mirrow manosh ya hangoshi dan haka muhsin ya tsaya muh'd yace zomuje abdallah. Acinyar babanshi ya zauna idan uban ya rungumeshi yana hawaye yana cewa insha Allah zan tafi india zanje gurin mummynka abdallah nasan tana buk'atana akisa da ita,ya Allah kakaremin matata Allah ka bata lfy yana hawaye akan d'ansa abdallah su majid suka amsa da ameeen ya rabbi... [7:18am, 4/2/2017] Sadiya Taheer: 🍭🎈AUNTY'N YARA🍧🎁AUNT'YN YARA🍧🎁 Written by sad-nas *Zanyi anfani da wannan dama domin inyi muku godiya masoyana,nagode sosai da addu'oinku domin kuwa Alhamdulillah na samu lfya Allah yabar zumunci ameeen!*😊_ ❤ ❤)*❤)* 95-96 sannan ya sake cewa ina sake neman wata alfarma agareku jama'a dakusa matata acikin addu'oinku domin an fita da ita waje domin yimata aiki fatanmu shine Allah yasa ayi aikin a sa'a ameeen nagode. Da sauri abdallah yace nima zanyi jawabin,akace mezakace to? Yace Allah yabawa mummyna lfy,Allah yabarta tare da daddynah har mutuwa ameeen... Dariya akayi tare da amsawa da ameen sannan manosh ya d'aga d'ansa sama suka fito waje yana cewa baka so in kawo muku aunty amarya kenan? Abdallah take ya b'ata rai yace bana so. Muhsin yace yanzuma kuwa gurin amaryan zamuje kafin mu wuce gida,abdallah yace tosedai idan bana nan dan bazan tab'a yadda daddy yaje wani gun babuniba kuma itama amaryan zata gane kurenta ciwonta anyi kuma zance mata sam bana kaunarta nida alfiya. Hakadai suketa hira har suka iso gida. Ai kuwa se suka sami maigidan manosh harya iso dan dama sun zauna suna kallon bayanin da manosh yakeyine a gudan TV GOTEL wanda akeyi kai tsaye,hakama gudan radio. Duk wanda yaji lbrn se san barka,hatta almajirai saboda aunty itana kowane. Bayan awanni biyu maigidan manosh ya tafi inda akace manosh bazaijeba ya zauna ya samu lfy sosai. Wanda shi kuwa sam baiji dad'in hukuncin da aka yankeba. Rashida zaune da marwan suna cin abinci,tace yaudai dan Allh kabani wayata inkira jama'a kodan asan inda muke. Anitse yasa hannu a aljihunsa ya fito da wayansa ya kunna. Texs ne wanda babu adadi sukaita shigowa,sam bai bud'e ko d'ayaba yayi saurin kiran number'n mum nashi,lokacin ta idar da sallan la'ar kenan a hospital da sauri ta d'auka tare da cewa hello mum,wani sanyi taji a ranta tace marwan inaka shiga haka anti neman numbernka amma shuru kaida rashidan fatan dai kunanan cikin koshin lfy? Shi kanshi yayi missing na mum nashi yace lfy lfyanmu lau mum ya kuke,tace lfy k'alau ina kuka shigane haka? Yace muna nan a abuja mum. Tace Allah sarki marwan kayi hakuri ka dawo gida dan Allah domin komai ya wuce yanzu,marwan yace to mum zamu dawo ya dad,mum bansan me zan fara cewa dad ba gabad'aya tsoron kiransa nakeyi wlh. Mum tace marwan karkaji tsoro domin daddynka yana buk'atanka ayanzu yana kwance a asibiti yana fama da jinya abokanka suketa fad'i tashi akanshi mahaifinka nada buk'atan ganinka marwan dan haka kayi gaggawan dawowa sannan kuma...innalillahi mum meke damun dad? Marwan kaidai ka dawo gida cikin sauri,badamuwa mun,ganinan akan hanya insha Allah kigaida dad d'in. Marwan yana katse wayan ya tashi hankalinsa dukya koma gun dad nashi ba shiri ya shirya suka fito. Abokinsane ya musu hanya suka samu jirgin karfe biyar se yola. Suna isowa kusan 6 ya tara musu adaidaita sawu suka shige ya sauka a hospital yacewa mai nape ya wuce da rashida gida taje tayi abinci sannan tazo da mota. Mahaifin manish da kuma mahaifiyarsa agun dad d'in marwan sunje dubashi ana zaune ana hira se sukaji sallaman marwan. Wani ajiyar zuciya dad d'in marwan ya sauke lokacin dayaga d'an nasa ya rame sosai kamar wanda yayi ciwo. Bayan yayi musu sallamane ya wuce gunda mahaifinsa yake kwance ya tsuguna tare da rik'e hannunsa yace sannu dad,ya jikinnaka,dan Allah dad kayi hakuri karka ce komai,kawai nayi abinda nake tunanin shine mafita agareni shiyasa,amma dan Allah kayafemin? Dad nashi ya shafi kansa yace bazance komaiba marwan,domin bakayi laifiba hakan da kayi shine daidai domin na fahimceka d'ana Allah ya maka albarka,sanyi marwan yaji a ranshi yayi nurmushi tare da cewa ameeen dad nagode,toya jikinka? Dad yace nayi sauki ai yanzu dana ganka kusa dani,ko kuma ince tun dawowan abokinka na fara samun lfy,abokanka sunyi k'okari dani sosai sedai muce Allah ya saka musu da alkhairi Allah ya masu masu musu suma, aka amsa da ameen. Amma zuciyar marwan tana nanata abinda mahaifinsa ya fad'a wai tun bayan dawowan abokinka,yace dad prince ya dawone? Yace eh ya dawo yau kwanansa d'aya kenan da dawowa. Tsantsan farinciki marwan baisan sanda ya rungume mahaifinsaba yana cewa Allah sarki abokina Alhamdulillah,ina yake dad? Dad d'in manosh yace suna can gida. Sallamar dr muh'd ne ya katse su,shima ya tsaya kallon marwan cikin mamaki yace dama zaka dawo ashe? To ai ka koma domin bana bukatar dawowanka. Marwan yace haba dr kuyi min uzuri dan Allah,muh'd ya mik'awa dad maganinsa sannan ya kalli marwan yace uzurifa kace? Ai babu wani sauran uzuri kuma domin kanuna mana cewa bamuda muhimmanci agurinka har zaka iya mana haka. Dad d'in manosh yace yanzu dai tunda ya dawo kuma yasan yayi laifi toku mishi uzuri. Muh'd yace dad gaskya semunyi zama danba haka kukeba run yaranta amma gashi alokaci d'aya ya canja mana tsarinmu dan haka dole semunyi zama shima yasan hakan. Babu wanda ya sake cewa komai haka marwan ya gaidasu dukkansu sannan ya nemi gafaran mahaifiyarsa sannan suka fito shida muh'd inda suka wuce office nashi yana cewa waime hakane muh'd? Amma ai a tunanina ban d'auka zakumin hakaba tunda kunji dalilin yin hakan nawa. Muh'd yace sosai munji dalilinka amma kuma ai abinda kayi bashine mafitaba kuma kanuna mana cewa mu abin baishafemuba kenan sekai kad'ai. Marwan zaiyi magana muh'd yace nazo bawa dad maganinsane dan haka zan koma idan mun had'u dukkanmu semuyi magana. Marwan yace shikenan muje ka saukeni agida,tare suka fito suka shiga motan muh'd amma babu wanda yace komai har suka iso gidan marwan ya fita shima muh'd ya wuce gidansu manosh inda suketa hira. Bayan marwan yayi wanka yaci abincine suka sake fitowa shida rash suka kawowa dad abinci. Se marwan yace zaibar rash a hospital d'in bariyaje gunsu manosh ya dawo. Suna hira amma hankalin manosh gabad'aya yana india saboda har yanzu su yah ibrahim basu kira kowaba. Slm marwan ya fad'a tare da k'arasawa ciki inda suka amsa salamarsa suna kallonshi cikin mamaki dan sam muh'd baigayamusu cewa marwan ya dawoba. Abdallah yanadaga jijin babanshi yace oyoyo uncle marwan sannu da dawowa,marwan ya k'arasa gun manosh cike da murmushi manosh ya mik'e suka rungume juna suna farinciki abdallah se kallonsu yakeyi yace daddy dama manyama suna rungumar junansune? Dariya sosai manosh yayi tare da sake marwan yace sosaima kuwa musamman idan sun dad'e basu had'uba. Marwanma dariya yakeyi sannan ya d'aga abdallah sama yace ina alfiya? Yace tayi bacci tun d'azu ko sallan isha batayiba,marwan yace haba to idan ta tashi gobe ka tabbata tayi gashi? Abdallah yace insha Allah zatayi,marwan ya ajiyeshi yace jeka ka kawo min abin tab'awa kaji? Da sauri abdallah ya fita sannan ya mik'awa sauran hannu suka gaisa harda muh'd. Yace koku had'a fiskokinku koku sake dai ina cikin farin cikin dawowar prince,saboda haka bazan biye mukuba sannan kuyi hakuri kumin uzuri akan abinda nayi muku... babu wanda yace dashi komai acikinsu,se manosh da yake binsu muh'd da kallo dan yaga duk sunyi shuru suna danna wayoyinsu. Murmushi manosh yayi yace waito me kuma hakan magana yake muku fa? Muhsin yace dan Allah malam babu ruwanka aciki kawai kayi shuru,manosh yace kamar inyi shuru bayan kunyi shuru kowannenku yana danna waya hakuri yakebaku tunda yasan yayi laifi aise ku mishi uzuri. Muh'd yace idan kaine hakan ya faru dakai mezakayi a wannan lokacin dakasan komai? Manosh yace gaskya kusan yadda marwan yayi nima hakan zanyi,amma dai bazaiyu ace na b'oye nukuba tunda mun zama d'aya babu wata boyayya a tsakaninmu ai koma akan menene,amma pls ubar maganan haka ya isa kawai marwan baka kyautaba da abinda kamusu semu kiyaye gaba inaga maganan ta k'are. Muhsin yace bata k'areba prince wannan wulak'ancine ai amintakarmu yazama bayi da ma'ana kenan wai har ace bamusan inda d'aya daga cikinnu yakeba wannan abun kunyane wlh laifikam kayi "dude" kawai dai abar maganar haka nan. Marwan yace nasan nayi laifin ai shiyasa nake so mufahimci juna ai,majid ya mik'e yace to nidai prince kacewa miher ta taimaka tazo mu tafi dan yau bazan barta ta kwana agidaba jiyama da kyar nayi bacci wlh. Muh'd yace kaikuma ana magana ka tashi,majid yace eh ai maganan naku bata shafenibane shiyasa domin nibamma san waya shigo nanba. Bugu manosh yakaiwa majid ta yadda ya isa hargun marwan harya bugeshi,marwan yace me hakane wai baka ganine? Majid yace eh aikasan ni makahone,dariya manosh da marwan sukasa inda majid yakaiwa marwan duka yace wlh sa'a kaci d'an iska albarkacin dad baida lfyane kawai zamu d'agama kafa dabadan hakaba wlh dase kaci kwakwa-kwakwa kamar yadda mukayiwa captain a baya... Hahahaha sukasa dariya dukkansu,manosh yace ai wlh kune kuka dena kulani amma muna waya da marwan ab'oye lokacin. Muhsin yana dariya yana kallon marwan yace to ashe kaine d'an iskan daka karya mana doka tun'a wancan lokacinma bamusaniba,dariya sukeyiwa junansu sosai inda inda manosh yake kallon muh'd yace kodai in fad'i nakane abokina? Muh'd yace ohonka idanka tonama ai kanka ka tonawa... hakadai suketa hira cikin hara da dariya. Can se wayar marwan ta fara ringing,kodaya duba numbern waje yagani hakan yasa yayi saurin amsawa yace hello,muryan yah ibrahim yaji yace marwan,marwan yace yane mutanen india kun isa lfy? Yace lfy lau wlh yawanci numbernku baya tfy kaima da kyar na sameka wlh ka dawo daga tfyarnaka ne? Marwan yace eh wlh yau na dawo yasu mama ya aunty da lubna? Ibrahim yace suna lfy lau wlh auntynema bata jin dad'i wlh zazzab'i taketayi tunda muka bar nigeria wlh. Subhanallah ya jikinnata to? Yace da sauki inasu muh'd,yace kowa lfy kun samu masauki mai kyau ko? Yah ibrahim yace alhamdulillah wlh,manosh yace banishi mugaisa pls? Ibrahim yaji kamar muryan manosh,shi kuwa marwan baisan cewa babu wanda sukayi waya da 'yan india ba shine mutum na farko. Manosh ya karb'i wayan yace hello yah ibrahim,ibrahim ya kira sunanshi cikin mamaki yace manosh dakai nake magane? Manosh yayi mirmushi yace nine wlh ya kun isa lfy ina apple d'ina? Yah ibrahim yaji dad'in aranshi yace Alhamdulillah bari na kaimata kozata ji sauk'i gaskya nayi farincikin jinka captain Allah abin godia. Shima manosh dad'in yajin a ransa mara misaltuwa yanata so yaji muryan apple nashi,yah ibrahim yayi sallama a d'akin da aunty take kwance lubna ko sallah ko takeyi mama da baba kuwa suna can d'akinsu ko kuma ince masaukinsu yah ibrahim lfy kaketa sauri haka? Yace barima in had'a da gudu aunty kashi zakuyi magana,batare datasan wayeba ta karb'a dan atunaninta ma dad d'in manosh ne. "Tace Assalamu alaikum" wani sautin saukan numfashi taji"sannan akace "wa'alaikumus salam _my one nd only apple_. Wayan ta cire daga kunnenta tana karewa wayan kallo sannan ta sake mayarwa kunnenta tace peach...? Sautin sauk'an kiss kawai taji akunnenta har cikin ranta taji wani ni'ima mara misaltuwa take ta fara hawayen farin ciki tace peach kaine kodai mafarki nakeyi? Manosh ya mik'e daga inda ya zauna kusada marwan ya shige d'akinsa su kuwa sebinshi da kallo sukeyi suna taya abokinsu murnan jin muryan matarsa... [7:18am, 4/2/2017] Sadiya Taheer: 🍭🎈AUNTY'N YARA🍧🎁AUNTY'N YARA🍧🎁 Written by sad-nas 97-98 "Peach yanaji kayi shuru?" "Apple how are u" "Ya jikinki my luv?" Alhamdulillah peach kaine dagaske?" "Nine apple,Allah ya dawo dani tare da taimakon addu'oinku agareni." "Murmushi tayi tace yaushe zakazo india peach,ina shaik'in son ganinka my luv" Karki damu *aunt* zanzo insha Allah kema kinsan nafiki son inganki ko?" Dan haka inaso ki kwantar da hankalinki yanzu haka k'ok'arin da naketayi kenan wlh. Dariya tayi maicike dajin dad'i tace kai Alhamdulillah Allah abungodiya peach nayi matuk'ar farinciki wlh Allah,ina fata dai kana lfy?" "Dariya yayi tare da cewa i'm fine aunt kikwantar da hankalinki lfyata lau jealousynah." Ya k'are maganar yana mata dariya Itama dariyar tayi tace ka fara koh? "Apple yasu mama da fatan duk kuna lfy,ina kuma sisterna lubna?" Shuru tayi nad'an lokaci sannan tace kowa lfya sis lubna ma tanata murnan dawowarka gata tadameni waisedai in bata wayan,amma bazan bataba dan nima bangaji dajinkaba tukun." "Manosh yayi dariya yace toki gaishesu,sannan kicewa sis lubna kawai nagaisheta yanzu bana son jin kowa se apple d'ina,dan haka tayi hakiri senazo magaisa." Dad'i aunty taji,farin ciki ya kasa k'auracewa fiskanta tama mance da yah ibrahim yana tsaye agefe se shagab'a da kalaman soyayya kala-kala suke jefan junansu dashi abin ban sha'awa... Marwan yana duba account nashi seyaga 0.00 "Yace lallai captain wato seda ka tabbatar wayan ta gama amfani kafin ka dawomin da ita koh?" Manosh yace sorry luv ne yayi nisa nama d'auka ko muna tarene ashe awaya muke. Dariya suka sa dukkansu muhsin yace shiyasa naga kamar ma seda kayi wanka kafin ka fito. Hahhhhhh! "Washe gari aka sallami dad d'in marwan dayake ya samu lfy. Gida aka wuce dashi inda mahaifin manosh da sauran 'yan'uwa suka bashi hakuri akan ya maida matarsa wato hajiya khadija mahaifiyar marwan "Cikin saukin kai kuwa ya maidata inda marwan yaketa murna." Sedai hajiya iya tana kwance ba lfy,tunda abun ya faru itama take jinya kad'an kad'an dan tak'i barima asan bata da lfyan se yanzu da ciwon yacigaba sosai. Hakadai aketa faman jinya dan dad d'in marwan ya d'aukota daga girei ya dawo da ita gidansa inda take samun kyakkyawan kulawa daga gun mum d'in marwan. "Manosh kuwa anata kan masa magani akan abinda ya sameshi gameda lfyanjikinsa akan abinda shukrah ta mishi." Maganin *islamic* ake

Chapter 16 of 17