Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
5 / 9
toh alhmdl yace toh muntari ka turo manya ayi magana nan ya dinga godia,ni kuwa tuni na fada daki zai tashi baba yace zauna ina zuwa,ko minti 10 baiyi ba ya dawo tare da baba auta auta abnd yasa nayi kirnka shine.nan ya kwashe kaf ya fada masa.cikin frnck baba auta yace Allah ya tabbtr da alkhri.muna hangen yaya sai yan sunne sunne kai yake yi sbd kunya,a gsky ina son halin baba auta,akwai shi da tawakkali ga rywrsa komai ckn sauqi,bai dauki duniya da zafi ba tare da shi suka fita,baba kuma ya shiga daki.ba'a fi minti 5 ba ya kirani a waya,haba gmbya sarunyr mata a tausayan azo muyi mgna. Nayi murmushi kana soro ne yace eh na saka hijab dina nayi waje tsaye yake jikn bango.wani asitaccen kallo yayi mani tare da murmsh,ysikar jkna ta tashi yar..kunyr sa ta lullubeni naji kamar zan fadi duk na harde sai kawai na tsaya a bkn qofa Yayi qasa da murya ckn wata irin fasali na shauqin soyayya yace shigo sosai mgn zanyi da matata,nayi qasa da kai,ya dan tako zuwa kusa da ni ya fara mgn a hnkli kamar haka meena ina sonki,ina kuma kaunarki.ni kadai nsn ydda sonki ke azabtar da ni tunda Allah yasa na fara snki.dn Allah ki riqe amana.ina son duk rintsi duk wata rigima da ya faruk zai zo da ita,meena ki taimakeni kada ki fada tarknsa wlh meena bake kadai ba ni kaina ina tsoronsa nayi saurin dago kai na kalleshi yace kwarai kuwa,sbd na dade ina kallon sonki a kwayar idonsa,shiyasa tsro ya kamani don nasan akwai matsala kuma bamu san ta inda zata bullo ba,na tabbata da wuya lkc daya ya hakura da ke nasan waye faruk,ba tun yau ba.duk da ba gida daya muka tashi ba uba daya ya wuce wasa,a duk inda yake meena kinga faruk nan da kike gani shuumn mutum ne kuma miskile na qarshe shiyas nake son ki fajmci abu guda wlh zai iya cin galaba akanki ta kowacce hanya,abu daya zaki mani kada ki saki jiki da shi ta kowacce hanya,kada kuma ki yadda ku kebe..ko me yi yake son fada maki kice ya fada maki shi a inda kuke. Nayi murmushi can qasan zuciata ,lallai ya muktar ya rude,wai ni yake ba labarin ya faruk,mutumn da muka tashi gida daya,daki daya meke ban sani ba game da shi. Zan wuce meena gobe tunda asuba zan bar gari,saboda ina da meetn gobe karfe 2 na rana..sannan duk abinda faruk zai zo maki da shi ki sama ranki zaki ga fiye da haka daga wurinsa nace insha Allah zan kiyaye... Ina shirin kwanciya kenan wayata tayi qara alamr saqo ya shigo ne daga ya faruk Allah ya bada hkr akan laifn da nayi,haba meena wai duk ina tausayin da na sanki da shi? A taimaka da karbar kokon barata hakanan na wahala da yawa,idan laifi nayi an rama hakanan.duk da ba'a hakura ba any way abu 2 zan sanar dake na 1 ina tayaki murnar cinye jarabawarki duka congrats.don Allah ko a zuci ne ace thnk u mgn ta 2 kuma danki abba ya damu da rashinki,har yana neman kamuwa da cuta.yanzu haka jiya na dawo da shi daga asibin,don haka idan abn yaqi cinyewa zan kawo maki shi nan,kya samar mashi skul a kauye kusa dake.ayi barci lafia meeenata wayyo abba Allah yasa da gaske zai kawo mani shi din,nima kewarsa ta dameni Na bugawa yaya na fada masa sakamakon jarabawata yayi kyau,yayi murna kwarai,sai dai baiyi mini maganar mkrnt ba,ni kuma naki sanar dashi maganar abba. Mun dade muna hira har na fara gyan gyadi da hamma sannan mukayi sallama na kwanta. Karfe 10 na safe ina kwance daki,ban dade dayin waya da ya mukhtar ba wadda itace ta wajen hudu a safiyar. Haka mukeyi tun ranar daya tafi sai munyi waya tafi sama da goma a rana. Babban abin dake damuna shine,yadda sam hafsa ta fita harkata,kwata kwata yanzu ko 'yar hirar da muka sabayi ta daina,sau 2 ina yi mata magana,kullum sai tace dani,banason yin surutu da yawa,kiyi hkr. Ko daki muke zaki sameta da kara2n littafai na hausa da turanci.ni gani ba gwana ba,dama itace mai kokarin yi,koda yaushe. Ni kuwa off n on ne karatun nawa. Sako ya shigo naga sunan ya abdullah ina dubawa saiga kalaman yabo da taya murna duk akan cinye jarabawata da nayi. Na maida masa amsar gdy,ina cikin turawa hafsa ta shigo,da Allah ko kinga kwalbar onga? Nace uhm uhm. Ba tre da na kalli inda take ba. Bata kara magana ba ta fice. Ina nan kwance har aka kira azahar,na mike naje waje don yin alwala.mikar da hannun da zanyi in dauki buta,sai naji muryar abba ya shigo da gudu yana fadin "got you aunty",na kamaki....... . Toh pa! YayaFarrukh ko YayaMukhtar??? Hada Hausa Book stories GIDA BAI KOSHI BA ¤¤8¤¤ Da gudu na taroshi muka makalkale juna,yana ta kyalkyatar dariya,nima na kama dariyar,kawai sai naga yaro ya fashe da kuka yana fadin, ba kece kika ce ba zaki koma abuja ba,sjine kika gudu kika barni. Ya kara rushewa da kuka, haba ban ankara ba,naji kwalla na shatato mini,yaron ya wani rikeni gam! Kamar bazai sakeni ba. Inna da hafsa sukayi sokoko!! Fuskarsu ta nuna alamun tausayawa yaron. Kukan da abba keyi ya kara hargitsa tunani,hankalina ya tashi matuka. Da yake yau lahadi baba na gida,sai gashi ya fito daga daki yana salati. Wane yaro ne yakeyi mini kuka daga zuwa? Hafsa ta karkata kai,abban ya faruk ne baba. Da sauri ya karasa fitowa yana fadin wani farukun kuma? Inna tace faruku nawa gareku malam? Naka dai wanda ka sani na habuja. Tsohuwa kawoshi nan... Abba ya makalkaleni yana matse kafada,alamar bazai je ba. Ganin haka na sungumeshi mukayi fa'o,kada yaya ya shigo ya ganmu a hakan. Na rungumeshi ina goge masa hawaye,nima na goge nawa, to ya isa haka nan,bazan kara tafiya na barka ba.... Zaki koma gida? Gabana ya fadi amma na dake nace, eh tare zamu tafi. Kaga baba fa! Oh baba,sorry. Ya ruga wurinsa yayi,takadari, nikake cewa sorry? Ina baban naka ya tsaya ne halan su mai rake sun rikeshi.... Yana fa abuja. Ya fada yana dariya. Duka muka hada baki, kai dawa kazo? Yace, uche ya kawoni yana waje.munyi hutu ne,sai bayan six weeks kuma bani lafiya,jiya nayi masa a kawoni wurin aunty, shine ya hado mini kayana duka yace,to mu koma kauyen duka nida ita,saita samu wata skul din ko aunty? Baba ya dauki salati,yana tafa hannuwa,inna tace ke hafsa shigo da bakon yaci abinci,ya kuma huta tunda su ba sallah.... To ina ruwanki da sallarsa? Baba ya katseta. A'a malam,wai gani na yi.... Kifa iya bakinki dije,ina kwatanta miki wata rana lallai za ki.....na bari malam,na bari. Tuni hafsa tayi waje, ni kuma naja aab muka yi daki, baba yace,uhm kaji mai da. Inna tayi dariya,yo mal don ma bakaga lkcn daya shigo ba,yau naga soyayya,alwala fa zatyi kaga buta inda aka wantsalar mini da ita. Ina ji suka kra yin dariaya. Murna ga uche kmr zai daukeni,muka gaisa yace yau zai koma. Baba yace sam ya bari sai gobe ya zaro idi, baba na oga say i de go bck 2day. Ganin ya dage baba yace to ai saiya tashi yayi harama. Muka rakashi mota ya dago hannu alamar in matso zaiyi magana dani nace yo, saida ya dan rusuna sannan ya langabar da kai, abeg aunty,mek u help oga ny mrryng him,bcoz he done bcm mad n crazy,nw 4 ur love,pls! Pls!! Dariya kawai nayi na juya tareda fadi safe jrny uche,thnk u. Ranar wuni mukayi daki nida abba,babu abin da kake ji sai dariyarmu. Na dauko kayansa dana cire na linke,na bude aljihun jakar daga sama na saka na dawo muka cugaba da hira,yace aunty tsaya kiji kuma wani labarin,kin san ina muke kwana nida daddy? Na gigiza kai, yo dakinki,yama kwaso kayansa duka na sawa ya dawo da sunan..... Me mummy tace? Na bukata cikin dabara. Yayi murmushi,irin na yarinta mai nuna alamar bai san ciwon kansa ba yace mummy ta tafi hutu gidan mummy hauwa sada,ai kin santa ko?wannan mai yawan dariyar? na kakaro yaken dole nace eh kwarai na ganeta,abba yaushe zata dawo? Ya watsa hannuwa,daddy yace ba rana. Sai dai lkcn da hafsa ta shigo, irin kallon da tayi mini ya tabbatar da cewa, ta ji hirar da mukeyi. Na bita da ido naga ta suri littafinta tayi waje. Abba yaci gaba da yi mini sokanarsa yana cewa,kinga daddy yanzu shi kadai ne a gida, tare da uche da uncle abdullah,sai su uche ko aunty? Nace uhm, kawai. Hirar tasa ne neman damuna,don haka naja shi mukayi tsakar gida inda su inna ke zaune. Hakan ya kwantar mini da 'yar damuwar dake neman taso mini,sbd yadda hafsa taje shi suka fara 'yan wasanni. Ganin haka yasa na koma daki don samu nayi dan tunanin dake neman tarwatsan kwalwa. Hafsa ya kamata ki fahimce........ Bana son tone tone yanzu mene ne matsalarki? Ta katsen, na hade wani busasshen miyau daya taru a wuyana, ina son sanin maanar wannan 'yan fizge fizgen da kike mini,sbd nace ina son ya mukhtar? Kwalla suka zubo mini,wlhy kin bani mamaki hafsa ita fa rayuwa idan kika duba gaba dayanta hakuri da fahimta ce, daga ba wadannan ta zama shirme. A duk duniyar nan ina mai tabbatar miki ina cikin layin farko dazan fayyace halin ya faruk,nasan waye shi, kuma na rantse miki bana sonsa ko alama,hakan bai taba faruwa ba,to ballantana tausayi. Hafsa tunda nake rayuwata ban taba jin ina tausayin ya faruk ba. Kwata kwata baya burgeni,ko irin abin nan na kanwa da yaya,dama can bama shiri dashi,ina ga yanzu? Ta kalleni alamar maganata ta fara tasiri a wurinta,sai sai ba taceklala ba. Ganin haka yasa na sami kwarin gwiwar cigaba da fadin. Kiyi la'akari da halinsa yanzu haka idan kika lura yanayi mini tayin kansa cikin gadara da isa,aure na yiwuwa a haka? Sam baya saurara mini,ga dizgi da rainin hankali ki fada mini macen da keson ta sami irin wannan mijin. Yana takama da kyau da kudi,kyan dan maciji ko kuwa kudi da balai? Hausawa na cewa,arziki da tashin hankali gwamma tsiya da kwanciyar hankali. Ni a yadda na lura tsabar sonkai ne yasa shiyin wannan kudirin tare da jin zafin ya mukhtar,sbd idan kika lura daman can basa shiri. Ya farul wulakancin da izgilanci tareda girman kai,shi kuma ya mktr baya barin kota kwana. Na kalleta sosai, bana son yaya,kuma ban taba tunanin sonshi a zuciyata ba, sbd kwata kwata baya cikin tsarin irin mijin da nakeso. Mts!!! Rayuwa kenan,haba hafsa,shifa ya rikeni,na daukeshi tamkar mahaifi,sai kuma.... Nayi shiru raina ya gama baci. Ji nayi ta dafa kafadata, baki fahimceni ba, maganar da nayi miki idan zaki tuna bance doleki so ya faruk ba,shawara ce na baki cewar,a duk duniyar nan yafi cancanta ki aura,sbd zaifi ko wane namiji daukarki da muhimmanci,yafi sanin darajarki akan ko wane sannan bazai taba gajiya dake ba. Kibar ganin ya mukhtar nata rawar kai dake yanzu,wlhy baki shiga gidan shi bane,amma da..... Bana tunanin haka hafsa,kema kuma ki cire hakan a zuciyarki. Uhm!!! Meena kenan,ya kamata kiba kanki shawara amma kiiyi amfani da kwalwarki wajen aikata hakan,sbd zuciyarki ta gama karaya ko ince tsorataki,ta anyar zugaki kina yi masa wani mummunan zato,wanda na tabbatar ba gsky take ayyana miki ba. Magana ta karshe itace,ki tuna cewa,ko da ya faruk kullum safiya dukanki yakeyi idan dare yayi kuma ya kara miki wani,ya kmt ki tuna da dawainiyar da yake dake,sbd ana son duk laifin da wani yayi maka kafin ka dauki hukunci,sai ka fara komawa baya kayi tunanin,shin kafin hakan ta faru wane alheri ne ya taba yi maka? Sannan ka dawo kan wannan abu Na kakaro wani busasshen murmushi mai nuna alamar maganarta ba tayi tasiri ba, na ce, "godiya nake malamata". Ta kyalkyace da dariya, Allah ya kyauta miki wannan taurin kan, nayi murmushi, "Hafsa kenan, kina tunanin akwai wani kalamai dazai sa na so ya Faruk?" na girgiza kaina, " wallahi haka nan Allah ya dasan kiyayyarsa a zuciyata, sam baya burgeni...." daidai lkcn da Abba ya shigo da gudu yana fadin "aunty boyeni, kawu zai amshe mini ball" kafin na kai ga mgn yaron ya shigo shima a guje. Abinka da yaro ya cachukuni, Abba kiki-kiki yana son kwace kwallon, wlh sai ka bani abata. Abba ya riketa gam, tare da fashewa da kuka yana fadin, uhm-uhm. Har da make kafada. Hafsa ta kamo yaron " zo nan kawu, ya akayi ne kai da dan abokin naka ko kaima baka so ya hau da kai kekensa idan babansa ya kawo masa gobe? Yaro sakarai! Wai daga wannan 'yar mgnn har ya hakura, ita kuwa tare da biscuit ta rakashi kofar gida. Tana dawowa ta hau babbaka mana dariya, ni sa abba. Sai kuwa ya rike ball(kwallo) kamar rikon san dake neman guduwa a garke. "Wannan shine uwa da da sun kasa fadin mazuru" ta fada tare da kara fashewa da dariya. "Hafsa banson sharri" kya ji kamar dgsk, ynz danki aka biyo yayi rashin gsky amma kin kasa tabuka komai, har gara abban da ke to wlh kiyi gaggawar sai mishi nashi, in ba haka ba gobe zan kyaleki da shi. Na kara tsuke fuska, ki kyale din na kalli abba, je ka mayar musu tsiyatakunsu, gobe idan munje katsina gidan baba Abdulkadir zan shiga da kai central market na zabo maka wadda kake so kaji my love? Da gudu abba yayi waje yana tsallen murna ita kuma hafsa har lkcn bata daina sauri ba. Sauri kawai mukeyi mu bar gidan kada su baban kano su kai ga iso wa lallai idan hakan ta faru zanji kunyarsu matuka. Sanye nake da atamfa super wax fara mai ratsin zanen ganye jajaye, daga rigar har skirt din sai ka rantse da Allah dinkakke tazo sbd yadda dinkin ya dace da ita ni kuwa dana saka a jik a rantse da Allah zanen na jikna aka dinka sbd dacewarsa. Daurin kallabina turai 'yar adua ba wata uwar kwalliya nayiwa fuskata ba illa yan jan baki na zizara daga saman idona da kasan kadan,(har dai zuwa karshen kwalliyarta) dubu goma haka na saka a jaka, na kuma fiddo dubu biyar na ba hafsa nace ko zata sayi wani abu a kasuwa ita ma idan taje karfe gama da rabi mukayi sallama dasu inna, sai kuma mun dawo gobe ko jibi kamar yadda ya fada. Yanayin gidan baba Abdulkadir da yadda suke tafiyar da rayuwarsu ta burgeni matuka. Duk yaran gidan manya suna mkrnt wanda aka bari ita kadai ke pri. Wato autarsu kuma ynz ajinta biyar ta kusa gamawa. Babbansu da mai bimasa kadai suka fara aiki, daya a kaduna zenith bank, daya kuma Rigasa teaching hsptl a kadaunar. Matarsa daya gwaggo baraka, mace mai mutumci da son addini, mgn daya ka ji ta sako sunan Allah, ko ta kawo hadisi. Da niyyar kwana daya kawai muka je kamar yadda baba yace amma sai gashi mun share wajen kwana takwas. Ana gobe zamu tafi ya hadamu da driver ya kaimu kasuwa ko wacce ya bata dubu goma goma, abba kuma dubu takwas a sai mishi keke, muna cikin zagayar kasuwa, Allak ya hadamu da wani hadadden sago babu abinda babu na kyauta (gift) munga hakan tun a saman shagon , daman an rbt haka da manyan baki MAMU GIFT CENTRE. na fizgi hannun hafsa ina fadin taho muje shagon can muma shiga na ida rudewa, lallai katsina ta hadu don shagonnan ko a Abuja wallahi yayi. Wani kwandon flower ya ja hankalina wanda aka rubta 'im yours foreverl jikin kowace flower daga sama, na ce "don Allah nawa wannan?" "dubu hudu", ya fada yana murmushi. Banyi gardama ba na balle jaka, hafsa ta kalleni galala . "Me zaki saya"? Kafin na bata amsa, mai shagon ya ce, "ke ba za ki saya ba ne? Jibi fa ranar masoya, wato valantines day, nayi saurin dago kaina sam na manta da ranar, lallai soyayya ta dibeni, nan fa na dage ina sayen flowers, card da turaruka irin na badawa,sai dana kashe dubu goma sha takwas da dari biyar. Ganin na yi masa wannan cinikin yasa yi mini ragin mutunci. Har muka fito shagon hafsa na yi mini mitar, ki yi a hankali meena, shi fa ya kamata ya baki, ba kece zaki.... No don't say that, don me ake kyuata, ba don so ba? Yana yi min don na gane hakan, why not nima bazan mishi ba? Abbaa ya damko hannuna yana dariya "aunty wa kike so zaki ba? Na yi murmushi na ce "abbanka ko kada na bashi?" ya kara tuntsirewa da dariya, ina so aunty a ba shi, na lura abba na son ya mukhtar kwarai dgsk, kuma duk dangi shi kadai abban ke kira abbanah, saura kuwa duk baba yake cewa, ko uncle, hafsa kuwa a english wears kudunta ya kare, daga nan muka yi wa abba tashi siyayyar, ba mu koma gida ba sai karfe shidda. Bayan sallar isha'i muna zaune falon mu. Gwaggo na dakin baba, muna ta hira ta ce, wasa wasa kayan can fa sun hadu, ji don Allah yadda aka kawaa su cikin leda, ni na ma rasa yadda akayi wannan kwantenar har da tayoyi kama jaka. Don Allah kuma leda a sama duk ana ganin komai, Nayi murmushi cikin jin dadi "ai yanzu matsa masa zanyi jibi yazo don na bashi". "Uhm yaya dan gatan meena"duk muka kyalkyace da dariya, washe gari karfe biyu muka bar katsina, amma uku saura muna falon inna Garhi. "Ynz muka gama fadin ko sai mun bi sawu?" duk muka yi dariya, hafsa tace "wlh baba kansu basu so muka taho yau ba". Indan haj. Bata ki ku koma can da zama ba inji inna. Abba ya hau rigima dole sai na tashi na hada masa kekensa da yake cikin kwali yake, ba arzik na mike su inna kuwa sai dariya suke yi mini. Washe gari nayi kuri da ido ina jiran isowar ya mukhtar kamar yadda ya yi alkawari. Sannan ga rudani da na shiga na mgnr iya yensa shin ko sun zo? Na ji daga inna har baba ba wanda ya yi mina mgnr. Wai meena ba zaki fito mu hada abincin ba, ko so kike sai ya kai ga zuwa muji kunya? Na dan ya mutsa fuska "wlh tunani nakeyi, me za muyi masa? Nasan shi da son cin dadi..." waye zai zo kuma marassa kunya? Hafsa ta kyalkyace da dariya "inna ki yiwa Allah ki bar shiga harkarmu irin wannaa...." wuf ta yunkuro zata cafkota tayi waje da gudu, haba yarinya zan kamaki ne. Ta fada tana 'yar dariya. A kitchen muka karasa shawararmu. Inna dai ta sanya mana idanu sai idan dayan mu ya gitta ta bishi da harara, tare da fadin kwa ji da shi idan kaya ne, karfe daya komai ya rikece mana, muyi wannan muyi wancan, baba na zau ne tsakar gida bisa tabarma yana duba littafinsa,na hadisi mai suna bulugul maram, inna a kusa da shi ta sa manan ido. Abba kuma sai yan zagaye zagaye yake yi bisa keke. Agogo ya buga karfe sha biyu na kalli hafsa cikin damuwa "gsky aikin nan baya sauri kinga ko rabi fa bamu yi ba" ta sanya cokalin juya abinci ta ci gaba da juya fride rice din data ji kayan hadi, ba tare da ta kalleni ba tace "ki kwantar da hankalinki in don yaya ne sai kiga har biyu ta wuce bai iso ba. Kinsan kuwa ba ko ma fatan mu kara awa daya a nan...." sallama muka jiyo kamar daga sama, wani kallo na wa hafsa nai nuna alamar tambaya. Da gudu abba ya saki keke yana fadin "Daddy!!!" cikin kara irin ta yara "daddy? Yau kuma daddy ya samu?" na fada ina kallonta. "ya Faruk?" hafsa ta fada da karfi na gwalo ido sam banji dadin zuwansa ba yau sbd ban so haduwarsu da ya.... Maraba maraba muryar inna kenan, baba ya ajiye littafinsa tare da cire gilashin fuskarsa "dan halak kaki ambato, wlh ina karatunnan ka fado min a rai, ashe kana tafe?" daidai lkcn ya kara so ya zauna gefen tabarma "wallahi kua na so yin waya amma hakan...." muryar Abba muka jiyo yana fadin "Daddy ga abinka inji aunty, kai ta sawowa a katsina zata baka a yau ranar masoya, kuma gata can tana yima na abincin partu, duk saboda kai...". ada Hausa Book stories GIDA BAI KOSHI BA ¤¤9¤¤ "Laha'ilaha illalllah, muhammadan Rasulullah" salatin dasu bab keyi kenan. Na kwaso da gudu a firgice. Me zan gani haka? Gift din da zan ba ya mukhtar ne. Ina fitowa nayi turus bakin kofa ckn wani irin burkitaccen yanayi. Shi kuwa ya tsareni da wani munafukin kalla. Hafsa na gani kusa da ni ita ma kamar tayi karya, da gudu Abba ya kara so " aunty ga daddy to ki fada masa abinda kika cen wanda zai sa shi dariya da farin ciki, kuma harda ilove you ko aunty?" ai sai na ida rikicewa, wane dan banza yace Abba ya saurari hirarmu? Wa ya fada masa babansa nake nufi? Kallon da baba da inna ke yi min na kasa gane manufarsu, take kwalla suka fara biyo mini a kumatu, wanda zan kirasu dana tashin hankali. Nasan arina,sbd tun safe naga yarannan suna kuminiya,magana kawai ce tawa,amma hafsa...... Na rushe da wani rikitaccen kuka, izihi sittin na alkur'ani inna ba shi....ke rufan baki kada nazo nan.... A'a tsaya tsaya,ke tsohuwa taso nan inji gskyar al'amarin. Baba ya fadi haka cikin natsuwa,amma har lkcn yana yi mini kallon tsarguwa,kamo hannun hafsa nayi don ita kadai zata shaideni akan wannan. Kika wani kamo hannunta,ai duk bakinku 1 marasa kunya. Ban wani damu da mgnr inna ba,ga Allah kawai na dgr,sai kuwa hafsa,shi kuwa kallona kawai yakeyi yana murmushi.abba rungume jikinsa yana shafa kansa,ko kunyar su baba bayaji sam. Irin zaman da mukayi gabansa,kai kace wani gagarumin laifi ne muka yi,munzo gafara,babu abinda zuciyata takeyi,sai zafi da rugugin tashin hankali. Tsohuwa! Nayi saurin cewa,na'am tare da kura masa ido kamar wacce aka kama da dukiyar wani a hannu. Ya dan muskuta, koda yake bada ke ya kmt na fara ba,sbd krntrki. Lkcn da ya fadi haka hnklnsa ya koma ga kallon yaya. Shi kuwa harda sunkuyar da kai kasa don yaudara. Faruku zan tambayeka sbd Allah,shin tsohuwa tasan da zuwanka? Eh baba,kwarai kuwa. Nayi saurin dago ido,amma mugun idanunsa kasa kara kallon fuskar abba dake kwance bisa kafrsa, sbd Allah fa baba yace? Na fada a rude,ina kara kallonsa cikin nutsar da idanu. Ya dago muka hada ido,ya daure alamar ba wasa,sannan ya maida kallonsa ga baba, tin satin sama taso nazo,amma na kasa aikata hakan,sbd yawan aiki daya rutsani a office shine fa tayi mini waya,lkcn suna katsina tace idan ban zo ba yau ba....... Na rushe da kuka, don Allah ya.... Ke banason mgnr banza kya barshi ya karasa kafin zuwanki ko? Baba ya fada a kule. Na sunkuyar da kai kawai ina zubar da hawaye, ya cigaba da cewa, ganin tana neman tada hankalinta yasa na karaso yau din duk da cewar akwai sauran aiki,zawan shi yafi amfani a gareni,sbd nema mata farin ciki kamar yadda tace. Gudun faruwar matsala irin ta baya, wacce ta nemi na kawo mata abba naki aikata hakan,cewarta har ciwon zuciya sai da ya kusa kamata,sbd kukan zuci. Ba abun ta tunkareku da mgnr ba tana tsoron hukuncin baba,sbd furucinka na farko a kaina....ya karasa makircinsa da maida kallonsa ga baba. Gsky hausawa da suka ce,idan kaga ana kuka(kundai san karashen)...to nima haka ta faru dani a wannan lkcn dif! Naji kwallan dake zubowa sun kafe kaf! Babu ko alamunsu. Biri yayo kama da mutum inji inna, uhm uhm bana kaiga cewa haka ba,ita ma bari ta bamu tata hujjar... Baba na ratse da Allah wanda ya halicceni,ban san zai zo ba. Allah ke shaidata,hafsa na shaidata kuma tun a katsina mukayi waya da ya mukhtar cewar,yau zai zo kuma wlhy shina siyowa kayan nan. Kada ku biye maganar abba,wlhy karya yakeyi kuma idan..... Dakata tsohuwa,ban tari numfashinki ba,abin nan idan kin san da matsala ki rufa mana asiri kada ki bamu kunya,gara kawai ayi shi cikin mutunci. Baba wlhy har yanzu ina son ya mkhtr. Yanzu dai kince yau zi zo ko? Nayi saurin cewa eh. To mu jira zuwan nasa shi kuma. Meye nasa a ciki baba? Wlhy ni duk abinda yaya ya fada bansan anyi shi ba,na ratse...... Ke na gaji da wannan rantsuwar taki ta banza,amma tunda kin dage da hakan,wlhy ke kika sani babu ruwana. Kai faruku sai ka kara hakuri,sai.... Hana! Haba! Babu komai baba,haka Allha ya rubuta,wlhy na kuma gamsu da byninka, allah yasa hakan shine mafi alkhairi baki 1n din mu. Yanzu mgnr sa ranar na biya ta kano,alhajin yace wata 4 yayi muku? Jin hakan yasa nayi saurin kwasar kayana mukayi ciki. Abba ya biyoni, aunty kawo nasan wa daddy a motar.... Wani kallo na fara jefa masa kafin na damko kunnensa. Zaka kara yi mini shishshigi da surutun banza akan harkokina? Ya kwala kara na daka masa tsawa,rufen baki kona maidaka toka da garwashi a wurin nan mara kunya,sai na zane maka jiki sosai,idan bakai wasa ba. Na wurfa shi bisa katifa,kwanta nan, Allah ya sa naga ka motsa a wurin ko ka fito kaga yadda zanyi dakai idiot. Tunda ya kwanta baiko motsa ba,sbd tsabar tsoro da fargaba,sbd tunda muke dashi ko tsawa ban taba yi masa ba. "Hafa tayi zugum! Kafin tace yaya fa ya ba ni mamaki..." kuma mamaki kuka bani, nayi zumbur na mike tare da kura masa ido cikin bacin rai. Ya kyalkyace da dariya, "matsoraciya, ina sa ne da abinda nayi, kawai ni ma don na rama razanar da ki ka yi mini yasa ko haka nan zan hakura da ke? Ya kalli Hafsa " meena ta kini, kuma na hkr dole tunda abu har an kai ga sanya ranar biki, kinsan mu ba a taron nan na mata, su Alhaji sunce 27 ga wata za a daura auren nan da wata hudu" na dan matso kadan, "Allah dgsk kakeyi yaya?" akan me? Ya bukata tare da dan tsuke fuska."ka hakuran?" na fada kaina a sunkuye. Yayi dan murmushi, ba dole ba, tunda kin nuna mukhtar kikeso Amina? Nayi 'yar dry cike da jin dadi na ce ngd yaya, Allah ya saka da alkhairi, kaga ynz sai mu sakata mu wala, sbd domin kai ne matsalarmu. Na kalleshi ido da ido har da kara nutsar da idanuwana ckn nasa, don ya gasgata da abinda na fada "kayi hkr kasan komai muqaddari ne daga Allah, sannan shi ke haifar da soyayya a zukatan bayinsa, wlh kaji na rantse da Allah ban taba jin sonka cikin raina ba baka taba burgeni ba ko makamancin haka. Kasan

Chapter 5 of 9