Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
7 / 9
wasi kafin ta sake magana sai mukaji anaMaganar tayi tasiri akanta saboda ganin irin yadda tayi kasake tana kallona kuma tana wasi wasi kafin ta sake magana sai mukaji ana kwankwasa kofa ta kalleni na kalleta sannan amina ta sake kallona cikin takaici gumi ya rufeni saboda nasan Amina a shirye take ta damkani a hannun sojojin hawaye ya fara kwaranyowa akan kyakkyawar fuskar Amina alokacin dasu kuma yan dadi bindigar dake waje sukaci gaba da buga kofar ahankali duk da yake kuwa sojojine wannan ba abin mamaki bane idan akayi la'akari da kasancewar Amina yar gidan Kanal muktar dole ne itama abata girma iya nata Allah ya isa soyayya wallahi kin gama dani kin kuma cuceni tunda kika fi karfin zuciyata har kika sa zan ceci ran makiyin mahaifiyata Amina taci gaba da kuka bayan wasu yan lokuta sai ta turani cikin daya daga cikin dakunan dake fuskantar dakin banjira wani karin bayani ba sai kawai na fada dakin na rufe na jingina kunne a jikin kofar dakin ina sauraron abinda ke faruwa a dakin. Ranki ya dade wani kurtun soja wanda cikakkiyar hausa bata isheshi ba yace da Amina Sannunka dai ta amsa sama sama haryanzu ina iya sauraren haushin karnukan dake maraba dani gasashshe awaje kinga motsin wani abu ko kamar gudun mutu anan wajen sojojin suka tambayeta a'a wallahi banji komai ba Amina ta amsa nayi mamakin irin yadda muryarta ke bada amsa batareda tayi rawa ba to shikenan to daman mun dauka ko kinji wani abune sai da safe sojojin sukace da ita. Lafiya dai? Ta tambaya a'a babu komai suka ce da ita sannan naji an turo kofar an rufe bayan yan dakiku saina bude kofar na fito Amina na zaune akan daya daga cikin kujerun dake dakin sai yanzu ne na lura cewa ashe ma wai akwai kujeru a cikin falon nata batayimin magana nima kuma banyi mata ba saboda raina nima yayi matukar baci ganin irin yadda amina ta kasa fahimtata na matsa kusa da tagar dake dakin Amina sai naga wani tsani a tsaye ajikin katangar gidan dake fuskantar dakin ga dukkan alamu sabon fenti akayiwa bangon su kuma ma'aikatan suka bar tsanin ajingine na gane haka ne ta hanyar ganin gwangwanin fenti a makale ajikin tsanin na sami hanyar tsira nace cikin zuciyata batareda na sake duban Amina sai kawai na bude dakin inajin lokacin da amina tayi firgigit ta tashi tsaye amma bacin rai baisa na juyo ba sai kawai na nufi tsanain da gudu inajin lokacin da wani katon kare ya kawowa kafara sura amma nasan nayi masa fintinkau dakiku biyu sai gani akan katangar gidan daga barin gabas a sannan ne kuma naji wani radadi ya bugi hannuna kamar an sokeni da kibiya karar bindigar daya biyo baya shi ya tabbatar min da cewa harbina akayi karfin harsashin bindigar shi yayi jifa dani kasan katangar na fada acikin wani katon kwalabati da kyar nake numfashi juwa na daukata ahaka na lallaba naja ciki na shige cikin bututun kwatar dake fuskantar katon lambatun kwatar radadin da hannuna keyi bai hanani jin kukan Amina ba alokacin da harbeni Fadil ta kira sunana cikin Karaji ** Fadil naji wata siririyar murya tayi kirana duk da yake radadin harbin da akayimin ahannu na damuna saida muryar tasa gabana ya fadi muryar da bazan taba mantawa da ita bace muryar yarinyar da haryanzu zuciyata takasa tantancewa shin MASOYIYATA CE KO KUWA ABAR KINA CE? . Fadil nice BADURA kada kaji tsoro nazone na ceci ranka saboda kaunar da nakeyi ma badura tace dani adaidai lokacin data sunkuyo ta kama hannuna tana niyyar fitar dani daga cikin katon lambatun kwatar da nake ciki Badura nakira sunanta idan kina tsammanin zan sake yarda dake to kin zolayi kanki idan kana tsammanin ni ba masoyiyarka bace Fadil to to hakika kayi kuskure sonka ma yanzu nafara badura ta amsa min na sami kaina a kafadar badura tana jana ina tangadi saboda jinin daya zuba ajikina yanada matukar yawa idona a rufe badura ke jana. Zan saka acikin but din motata badura tace dani saboda duk yansandan garin nan an basu kamanninka ashirye kuma suke su kama ka acikin harda kwararrun yandan ciki daga durba hotel kaduna ban samu damar ce mata komai ba saboda duk jikina ciwo yake ahaka na lallaba da taimakon badura na fada cikin but din motarta ta mayar ta rufe dani banida wani zabi sai abinda badura tayi dani ahalin yanzu duk da yake kuwa har yanzu zuciyata bata amince da duk abinda tace ba ahaka na kwanta cikin but din motar kamar matacce amsa kuwwar muryar Amina shi yaketa kai komo cikin kwakwalwata FADIL FADIL FADIL Bansan iya lokacin danayi akwance ba kafara ta kage saboda rashin isashshen sukuni acikin but din motar bani kumada tabbacin shin bacci nayi ko suma nayi nidai kawai na farka naji badura tana ta tafka musu da wadansu wadanda daga karshe na gane yansada ne. . Muna son muga bayan motarki daya daga cikin yansandan yace da ita nace ma babu komai amma kaki ka yarda badura tace inason naga babu komai din domin an bamu damar bincikar duk wanda ya biyo tanan don haka dole ki bude bayan motar ciwon dake damuna shi ya hanani fargaba ko kadan bandamu ba ko su bude koma su bari saboda idan ma sun barni babu mamaki mutuwa zanyi saboda jinin daya zuba ajikina. . Bazaku bude ba to badura tace dasu cikin tsiwa kai kirawo yallabai wannan yarinyar batada gaskiya daya dansandan yace bayan wani dan lokaci naji takun sawun wani dansandan agidan but din motar ke yarinya munason ki bude mana but din motar nan idan kuma bahaka ba zamu balla da karfi Baka isa ba badura tace tas naji karar mari ya daki dodon kunnena badura ta kwalla kara mai tsanani ku kamata kusata a mota dan sandan yace to yallabai saura suka amsa kai kuma dauko guduma dansan ya sake bada umarni na lumshe idanuna ina sauraron a bude bayan but din da nake dan lokaci sainaji an fara dukan but din motar dukan but din motar da ake daidai yake da bugun zuciyata. . . KASHI NA UKU 12 Aka cigaba da dukan but din motar kamar za'a ragargazata ba dukan motar ne ya dameni ba abinda yafi damuna shine jijjiga jikin motar da sukeyi duk lokacin da jikin motar yayi rawa sai naji hannuna kamar ba'a jikina yake ba haryanzu jini na zuba agurin da aka harbeni na gane hakanne ta hanyar jin danshi danshi ko ina a hannun rigata Ku buga da kyau mana babban yansandan yabada umarni nan da nan suka bude wuta suna dukan but din motar duk karfinsu. Sannan ne kuma naji shiru an daina dukan bayan motar irin shirun da zakajine a duk lokacin da aka dauke ruwan sama kamar da bakin kwarya sannan kuma aka dauke lokaci guda babu mamaki shirun danaji tafi haka kakaraf naji karar bugun takalma a kasa ga dukkan alamu wani yansandan suke sarawa sannan ne to naji abinda ya sake sani fitar da rai daga rayuwa duk da yake hankalina bajikina yake ba hakan bai hanani gane muryar sojan nan daya yiwa Amina tambayoyi ba. Bakuga wata yarinya ba ta wuce tanan gurin? Sojan ya tambaya gata can yallabai acikin motarmu daman ita muke bincike mun dauka batada gaskiya don hakane ma kaga muna balle bayan motar bayan motar wa? Sojan ya bugawa dan sandan tsawa sannan yaci gaba da cewa shin kasan ko motar wacece kuke lalatawa? Ranka ya dade wallahi bansani ba na tuna dansan yace jikinsa na rawa ai kana da sauran tuba sojan yace saimakaji ko yar gidan wacece na tuba yallabai dansan ya sake tuba mu tafi gurin Kanal Muktar ka tuna agabansa sojan yace dashi sannan ya buga masa tsawa ku fito da ita to yallabai dansan yace nayi shiru ina sauraro numfashina sama sama saboda jini mai yawan gaske ya zuba daga jikina da kyar nake bude idanuna na kuma godewa Allah lokacin da aka harbeni ta fito nemana Gata yallabai dansandan yace aka danyi shiru sannan sojan yace a fusace ai ba wannan muke nema ba banda ita bakuga wata ba? Yallabai wallahi ba muga kowa ba sai wannan Alamar jin dadin da yafita daga bala'i a bayyane take acikin kalamin dayayi. Banga amfanin zamanku anan ba tunda har kuka bari yar gidan oga ta bace kuma tanan ta biyo yallabai wallahi batanan ta.... Ku saki wannan yarinyar sojan ya buga musu tsawa inason ku shiga motarku ku zagayawa zaku gano mana ita mu kuma zamubi ta bayan titinan ko zamu ganta kun gane ko? Yes sir yansandan suka amsa baki daya ga yadda na fahimta sojan yanada dan mukami saboda irin yadda naji yansandan na bin umarninsa sau da kafa basu gardama karar cin tayar motocin yansandan dana sojojine ya tabbatar min da sun tafi ba'a dade ba sainaji badura na kokarin bude but din motar da kyar ta samu ta bude saboda yansandan sun mommogada bayan motar na kumayi mamakin yansandan saboda ganin basu karbi dan makullin but din ba daga hannun badura da sun karbi dan makullin motar da tuni ina hannunsu nayi mamaki matuka da dabarar hakan bata fado musu ba idanunsu ya rufe wannan wani abune daga ubangiji nace cikin zuciyata. . Fadil badura tayi kirana Na'am na amsa da kyar tayi ajiyar zuciya sannan ta kamo hannuna marar ciwon da niyyar fitar dani daga cikin motar matsanancin ciwo ya saokeni nayi yar kara badura ta rike numfashinta sannu Fadil tace dani na yunkura da kyar jikina babu laka ko kadan da kyar badura ta fito dani daga bayan motar tana fitod ani na yanke jiki na fadi numfashina sama sama da kyar nake shakar iska badura ta sake dagoni sama ta hanyar sake kama daya hannun da haka tajani ranga ranga har jikin motar muna zuwa saita bude ta turani ciki ahankali sannan ta rufe ta zagayo gaban motar ta shiga ta tashi motar sannan ta tuka ta tafi dani inda bansan ko inane ba koda yake dai alokacin banida zabi amma kuma haryanzu bansaki jiki da Badura ba badon harbin da akayimin ba to da yanzu mun rabu ciwon ya sake sukata naji kaina yayi dum ba'a jima ba bakaken taurari suka bayyana a idona daga bayane na fahimci ashe suma nayi. ** Sassanyar ruwan sanyin da aka yayyafa min a fuska shi ya taimaka wajen farkowata daga suman danayi badura na zaune a kusa dani kofin ruwan sanyi a hannunta na hagun hawaye na kwarara akan kumatuna abin yaban mamaki idan na tuna da cewa wai yau ga badura tana kuka da hawayenta saboda wani mummunan hali dana shiga na dubeta nayi murmushin karfin hali.. Wai yau ga badura tana kuka da hawayenta saboda wani mummunan hali dana shiga. Na dubeta nayi murmushin kafin hali. . Sai bayan data dawo min da murmushina ne na lura da inda aka harbeni a daure yake da wani farin kyalle. Menene kuma abin kuka Badura? Na tambayeta ba abinda kukeso kenan ba ku ganni cikin bala'i bada hakkina ba? Ai abinda ya kamata kiyi shine farin ciki da dariya ba kuka ba kina jin zan sake yarda dake ko kuwa.... Jiwa ta daukeni naji kamar zan sake suma numfashina sama sama nayi luuu zan fadi baduta ta tareni tana kuka bayan dan tsawon lokaci sai hankalina ya dan dawo jikina na bude ido badura na kallona. Daman nasan bazaka sake yarda dani ba Fadil badura tace dani muryarta na rawa mahaifiyata ta riga ta lalata rayuwata tunda tayi sanadiyyar daka tsaneni ka kuma tsani yar uwata Amira na fada maka ba laifina bane Fadil amma kaki yarda tace dani cikin karaji da sheshshekar kuka. Tausayinta ya kamani duk da yake kuwa ban yarda da ita ba saura kadan na amince da ita kuma sauran kalamanta. Karka yarda da ita wata zuciyar tace dani shashasha ka manta abinda tace dakai a durba hotel kaduna? Daga baya kuma ta butulce maka? Kaine mutum na farko dana fara jin sonsa azuciyata lallai kam na tuna bazan amince da ita tunda kalamin data fada abaya bai hana mata cutata ba da kuma sanadiyyar jefani awani mawuyacin hali . Kana jin zaka kashe zainab a banza ne? Bani na kashe taba. Maganganun badura da suka faru a kwanakin bayane suke dawowa zuciyata zaman kuma da nake yanzu agaban badura wacce hawaye ke kwarara daga fararen idanunta ina iya jin siririyar muryarta garai garai kamar a faifain rediyo inda take cewa DAURE SHI DA KYAU DON KA SAN KAKKAFAR NE... . Badura na kira sunanta bata amsa ba banajin akwai wani sauran kalami daga bakinki da zai iya sawa na amince dake tuni kin fada min ire iren kalamai masu sanyaya zuciya masu kuma karyar da zuciya su kuma yaudari duk wanda ya amince da mai muryar don haka duk wani dadin baki da zakiyi yanzu kamar maimaicine ga abinda kika fada min kwanakin baya kuma kika yaudareni bari na tambayeki Badura nace da ita kanta a sunkuye tana zubar da hawaye haryanzu kofin ruwan sanyin na hannunta tayi far da fararen idanuwanta wadanda ada sukan sa gabana faduwa saboda so da kauna amma yanzu bazan iya fayyace tsakanin mu da ita ina ganin sanin abinda ke tsakaninmu da badura sai ko ubangijin daya halicci kaddara damu kuma baki daya. Me kake son tambaya? Tace dani cikin sheshshekar kuka na dubta sannan naci gaba da cewa ke a ganinki Badura da kece amatsayina nikuma a matsayinki na badura kina ganin zaki sake amincewa dani? Tayi shiru bata amsa ba sannan naci gaba dacewa To ashe kuwa in dai hakane bai kamata ma kifara ganin laifina don naki amincewa dake ke bari ma ta wannan shin halin da nake ciki ayanzu kina ganin zan samu damar tsira kituna fa duk wani dansanda dake garin nan nemana ruwa ajallo yake ina amfanin badi babu rai badura? Ina ganin zancen na amince dake baima taso ba domin kuwa damar tsirata kadance nasan koba dade ko bajima zasu kamani bazai kuma yiwu ace kullum inata guje guje ba cikin tashin hankali. Na kalleta sannan nayi murmushin karfi lokaci kuma na cije lebena saboda ciwon dake hannuna ya takura min. Mukayi shiru na dan lokaci babu wanda yasake magana sai bayan mintuna uku sannan badura ta dago kai ta dubeni. Zan nuna ma cewa kayi kuskuren fahimtata tace dani saikuma na nuna maka cewa nafi Amina kaunarka tunanin raina zai baci shiyasa badura tayi sauri tace dani Fadil karka dauka wai ina kushetane agabanka sam sam bahaka bane abin dai kawai da nake so ka gane shine nima masoyiyarka ce wacce kuma ke begenka fiyeda Amina nayi shiru bance da ita kmai ba haryanzu kuma bansan a ninda muke ba abin kawai dana sani shine muna gefen titi motoci ne saboda lokaci lokaci motoci sukan wuce ta kusa damu duk da yake talatanin darene kuma daren damuna daga inda nake zaune ina iya ganin walkiya ta cikin gilas din tagar motar badura wanda duk suke a kulle kofar motar dayace a bude wacce badura ke bangarenta a zaune agogon dake gaban motar shi ya sanar dani cewa yanzu karfe uku da mituna ashirin na dare hakan shi ya nuna sa'o'ina uku kenan da barin gidan da Amina ta boyeni Badura ta dubeni taci gaba da cewa kar fa kayi tsammanin duk taimakon da amina tayi maka daga kaduna zuwa nan bansani ba ko kusa ba haka bane idan kayi tunanin haka ma to ka zolayi kanka Salman ya sanar dani duk yadda abu ya faru kuma ya sanar dani duk yadda ya kwace ku ahannun dansandan daya ritsaka acikin gero ta danyi shiru tana maida numfashi ko dan jinin daya zuba ajikina inda ma nayi sa' shine alburushin bindigar bai sami kashi ba naman hannun ya dan goga ya wuce rashin samun kashin hannuna da harsashin yayi shi ya bani damar kaiwa haryanzu a raye ya kuma bani damar sauraron badura amma daya sameni to da yanzu labari yasha bam ban. . Amina ta tserar da rayuwarka daga hannun mafarautanku sassanyar muryar badura ce ta sake kwarara zuwa dodon kunnena sai dai kuma ba gaba daya ta tserar dakai ba Fadil tace dani cikin sassanyar murya amma kai aganinka tayima wani babban taimako wanda na tabbata hakan ne yasa kaso amina tayi shiru sannan ta kura min ido nima na kalleta mukayi ido hudu bayan yan dakiku na fara kawar da idanuna Fadil nayima tambaya mana kamar yadda ka tambayeni dazun. Tambayi mana nace da ita a sanyaye maganar data fara yanzu ta fara tasiri akaina nasan har yanzu ban amince da ita ba to amma kuma nasan abinda take fada gaskiyane tabbas tserar dani da amina tayi shi ya sani kaunarta Fadil badura ta kira sunana a sanyaye sunana ya zama kamar wakace a bakin badura tana son idan zata yi min magana ta kira sunana. Zaka amsa min tambayar idan nayi maka? Zan iya amsawa mana idan tanada amsa Ada can to Fadil kana kaunar Amina kuwa kamar yadda take sonka? Nayi shiru ban amsa ba saboda bansan abina zance da ita, Nifa fadil kwanakin baya kana sona kuwa? Nayi shiru ban amsa ba yakamata ka amsa min tunda kayi alkawarin zaka amsa min indai tambayar nada amsa. Na sakeyin shiru na dan lokaci sannan nace da ita. Bangane abinda kike son tambaya ba nace da ita na fadi hakane domin na baiwa kaina damar tunani haba fadil kasan amsar mana kaidai kawai kace tayi ma nauyi sannan danyi murmushi tsigar jikina tayi yarr murmushinta shi ya tuno min haduwarmu ta farko a durba hotel kaduna lokacin ina cikin mayen begenta amma yanzu fa? Na yiwa kaina tambayar fam miliyan guda. . Idan amsar tayi maka nauyi fadil bari ni na amsa ma da farko dai tunda can nasan baka son amina itace dai take kaunarka ana cikin haka ne muka hadu na sani fadil tace dani cikin daga murya kana mutuwar sona a kwanaki kadan din da suka wuce amma sakamakon abinda mahaifiyarmu ta kulla sai duk ka tsaneni ka kuma fara begen amina saboda taimakon da tayima to nima zanyi ma taimakon da yafi na amina domin ni zan tserar dakaine gaba daya cikin tashin hankalin daka fada Tayaya? Na tambeyata cikin mamaki murmushinta mai sa gabana faduwa ya sake bayyana a kyakkyawar fuskarta duk da yake babu cikakken haske acikin motar babu kuma farin wata a sararin samaniya hakan bai hana min ganin fararen hakoranta ba. Yanzu kayi tambaya abin kaunata tace dani zan iya tserar dakai ta hanyoyi da dama sanin kankane cewa duk abinda mahaifiyata ta kulla maka da masaniyata kuma dani aka kulla komai duk da yake kuwa bana so kamar yadda na sanar dakai tun farko tayi shiru tana duban bangaren da nake zaune ta cikin gilas din motar sannan ta juyo taci gaba da cewa Zan iya saida rayuwata don ganin na bada shaidar da zata tserar da rayuwarka agaban alkali domin wannan itace hanyar da kawai zan gamsar dakai cewa nafi Amina kaunarka tayi ajiyar zuciya sannan muka yi ido hudu da ita dan duhun dake cikin motar bai hanani ganin hawayen daya fara sartu a idontaba. Nasan Fadil ba zasu kyaleni hakaba tace dani tana sheshshekar kuka indai Alkali yaji duk labarin dolene ya dau mataki akaina dakuma yar uwata Amira akalla ko ba komai za a iya yanke mana hukuncin shekaru biyar koma fiyeda haka agidan yari kaga kuwa babu rayuwa mafi kaskanci irin ace yarinya kamata agidan maza to amma hakan shi yafi soyuwa agareni tunda kaidai rayuwarka zata tsira kuma ko ba komai na nuna ma kauna fiyeda Amina wacce ta kasa hanawa sojojin gidansu su harbeka. Na kalleta cikin mamaki me kike nufi na tambayeta abinda nake nufi shine ta kasa kare lafiyarka bayan kuma tana ikirarin wai ita masoyiyarka ce idan soyayyar gaskiyace me yasa bata boyeka ba? Na kasa amsa wannan tambayar akaro na biyu kenan na dubi Badura itama ta kalleni idanunta cike da kwalla ko kusa wannan batayi kama da badurar dana sani ba a kwanakin baya badurar dana sani a kaduna dakakkiyace wacce bata kuka bata kuma tsoron komai amma sai gashi wannan badurar tana kuka da hawayenta agabana tana kuma kokarin na amince da ita wai har zata saidai rayuwarta akaina abinda mamaki kodayake.... . Bansamu damar karasa tunanina ba indai har ba idanuna ne sukayi min karya ba to naga motsin wani abu ta cikin gilas din motar mu tsigar jikina tayi yarr alokaci guda kuma badura ta fahimci hakan muka dubi dubi gurin gaba daya mutumin ya nufo gurin ahankali hannayensa cikin bakar rigar ruwa bansan ko wanene ba Badura takai hannunta zata hanye gilas din motar domin mu sami damar ganinsa nayi sauri na gargadeta kada ki bude nace da ita cikin rada mutumin yaci gaba da nufi inda muke babu cikakken hasken da zan iya ganinsa gaba daya sakamakon bakin hadarin da ya zagaye sararin samaniyar mahaliccin komai amma hakan bai hana farin fentin da akayi rubutun saman hularsa tona asirinsa ba POLICE a rubuce a saman hular kwanon dake kansa yana matsowa ina kara ganinsa sosai numfashina kuma yana dada yin sama sama tuni jikina yayi nauyi ba kamar da ba lokacin da sauran jini ajikina na lumshe idona ina kokarin maida numfashi sannan na sake budewa dansan ya matso sosai tsakaninsa da motar. Dansandan ya matso kusa sosai tsakaninsa da motar bai wuce taku shida ba zungureriyar bindigar harbi ka rufa a rataye a kafadarsa yanata muzurai kamar kowane lokaci zai iya bude wuta duk da yake kuwa babu tabbacin harsashin dake cikin bindigar yakai Uku. . Dansan ya kwankwasa gilas din motar bangaren da nake daga baya kuma ya ya dallaro cocilarsa mai hasken gaske ta cikin gilas din motar cikin sa'a dansandan bai kula da bangaren badura ba wacce kofar ta ke bude ahankali sai badura ta janyo kofar ta rufe lokaci guda kuma ta sunkuyo tace dani lumshe idona na yarda ta ita wajen yaudara don haka sai na lumshe idanuna sannan ne ta janye gilas din motar hasken fitilar dansandan ya kara haskake cikin motar idanuna ba a rufe suke gaba daya ba don haka ina iya ganin gashin bakin dansan wanda ke tsaye yana hasko mu karan sigari a bakinsa hannunsa agogo mai lamba lamba ne a daure 3:35 abinda ya nuna kenan. . Kuna shirin kwana nan ne? Katuwar muryar dansandan ta daki dodon kunnena saidai kuma tsawar da yayi bataui tasiri ba a sakamakon tsawar asali da kararta ya keta sararin samaniya hade da walkiya mai hasken gaske alokaci guda kuma aka fara yayyafar ruwa. Ko bakuji ba ya sake daka mana tsawa ku bude kofar motar yace damu badura tayi sauri ta bude kasancewar hannun da aka harbeni bangarenta yake a boye me kuke anan? Ya sake tambayarta. Kaga yallabai daman wallahi neman wanda zai taimaka min nakai shi gida nake motar taki tashi kuma gashi tatul yake da ruwan BAGAJA. Me kike nufi? Ya tambaye tayi murmushi ina nufin ruwan yan birni ko sai nayi ma gwari gwari GIYA to. Tace dashi adaidai lokacin ne dansan ya dallara hasken fitilar a fuskata sannan naji ya sunkuya ya dan daki kafadata sannan yace tashi abokina yaudarar karya kake shin kana tsammanin duk yandan garin nan basuda hotonka Haba Fadil tuni har bindigarsa ta fado hannunsa. . 13 Idan har ana sabo da bindiga to ya kamata ace na saba da ita wannan bashine karo na farko ba bakuma na biyu ne ko na uku ba da aka ritsani da bindiga tun sa'adda na fada tarkonsu badura mai kofa daya sai wasa da bindiga ya zama kamar wasan gargajiya agareni duk da yake kuwa ba dadinsa nakeji ba ko kusa ban zolayi kaina ba domin nasan ba' saboda da bindiga ko banza dai tafi maciji kwarjini domin duk lokacin da aka ritsaka da ita to kafarka daya alahira take daya kuma a duniya a wannan karonma zungureriyar bindigar dansandan a kirjina bakinta yake kasan kuwa ko banza zaiyi wuya na bayyana ma irin faduwar gaban da nakeyi awannan lokaci saidai zan iya baka misali da mutumin dake zaune akan sanda kuma agaban rijiya gaba dubu. . Fito da hannayenka waje dansan yace muryarsa na dan rawa kada kuma ka sake kayo kokarin yin wani abu ya gargadeni haryanzu badura na zaune acikin motar bata ko motsa ba yayyafin ruwan kuma da aka farayi bai hanani gumiba nayi kokarin fito da hannayena gaba daya amma hannun da aka harbeni yaki daguwa idan na daga hannun sainaji kamar an sokeni da kibiyar Ajali dansandan ya fahimci cewa banason fitowa da hannuna na dama don haka sai ya matsa kusa dani hancin bindigarsa manne akirjina dan yatsansa na hagun akan kunamar bindigar ta hakane yayi amfani da hannunsa na dama ya dago hannuna mai ciwon radadi ya sokeni na yi yar kara amma bai fito fili ba ka dago hannunka mana dansandan ya buga min tsawa kayi masa ahankali harbinsa akayi a hannun yana kuma da kyau ace ka maida bindigar kafadarka domin baka bukatar amfani da ita idan kabar shi ma bazai iya guduwa ba muryar badura ce ta ratsa shirun daran haryanzu ana yayyafar ruwan saman kuma bakin hadarin na nan anata walkiya saidai kuma hakan baisa an tsuge ruwan da karfi ba. Dansan ya dubi badura idonsa cike da shakka da kuma zargin abindatace sannan ne ya hasko cocilarsa kan hannuna alokacin to yaga jinin dake jikin kyallen shi ya tabbatar masa kumari da hakan. Ahankali cikin nutsuwa da kwanciyar hankali fuskarsa cike da annaurin yin nasarar kani sai dansan ya dauke bindigar daga kirjina sannan ya mayar da ita inda take rataye kafadarsa kenan a daidai lokacin to ankwa ta fado hannunsa kayi kuskure daka mayar da bindigar nace cikin zuciyata badura ta karanci abinda nake shirin aikatawa don haka sai tayi sauri ta gargadeni ta hanyar girgiza kanta bansan abinda take nufi ba amma sanin cewa ita kwararriyace gurin yaudara saina rabu da sandan ya matso kusa dani sannan yakama hannayena yabuga ankwa ga mimakina sainaga ko taka tsantsan bayayi saboda shi azatonsa karfina ya kare gaba daya sauran na naushi wuyansa amma dana tuna gargadin badura saina rabudashi ya buga ankwar ahannuna sannan ne abin yayimatukar girgiza ni ya faru kamar a wasan kwaikwayo sai bindigar dansan ta sake fadowa hannunsa a wannan karon hancin bindigar yana saitin kan badura shiga ki tuka motar dansan ya buga mata tsawa cikin muryarsa ta yan doka dumi ya lullubeni na kalli badura cikin takaicin hanani dukansa datayi ita kanta bata taba zaton dansandan ita zai ritsa tatuka motar ba ta kalleni na kalleta sannan ahankali saita Ta kalleni na kyalleta sannan ahankali saita fice daga kusanidani ta rufo kofar alokaci guda kuma shima dansandan ya rufe kofar dake bangarena na dama sannan ya daga bindigarsa yaci gaba da saitin badura bayan dan lokaci baduta ta shiga motar shima dansandan ya shiga kusa da ita ya zauna sannan badura ta tashi motar yanzu kam na tabbata na kamu banga yaudarar da badura zatayi ta tserar dani ba. . Ofishin yansandan cikin jiha zaki kaimu dansandan yace cikin kakkausar muryarsar wacce ke cike da amon samun nasara badura ta fizgi motar da gudu muka harba kan titin kamar

Chapter 7 of 9