Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
aurece. Taji tsoro iya tsoro amma ta daure ta bashi amsa ta kalleshi idonta cikin nasa tace, au auren akan mace kadai yake kenan kaima ai kanada auren nawa kaje gurin nan ko kaman ta kanada aurenane akanka? Idan kuma akwai banbanci tsakanin mu let me know. Yanda idan ka'aikata badaidaiba za'a maka hukunci haka nima za'amini so miye banbanci?? Wani baqin cikin kishi ya turnuqeshi. Muryansa na rawa yace iffaat tell me the Truth mi kikajeyi a gurin nan ? Ya bata tausayi yanda ya sassauto, nace abinda kajeyi shi najeyi. Sakinta yayi ya fuskanceta dakyau iffaat mi kakajeyi a gurinnan Har kika ganni? Tace abinci naje siya, Ya manna mata arniyar harara, daga yau na soke baki ba fita sayen abinci idan dai ba makaranta zakijeba baki ba fita, abincin kuma ki shiga ki girka da kanki!! Tsaki tayi ta wuce shi, Farhaan ya tsargu matuqa yauda ta kamashi da wata ai bai isa ya shigo gidannan ba.. [7:50AM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..?? 68 Na Hauwa M. Jabo Gari ya waye ma amaren farhaan yana jiran amai breakfast amma shiru har 12 yunwa ta isheshi ya duba ko ina ba alamar girki sai hayaniyar mutane, Yakama hanya ya fita abinsha bai dawoba sai guraren daya na dare bata damuba cox yan ganin amarya da qawayenta sunanan sunyi girki sun debe mata kewa, bayan sun tafi sannan ta fara tunanin ina yaje!? Daya na dare ya dawo daya shigo tamai kallon tuhuma tana Palo bai kula da itaba ya wuce dakinta, Koda ta shiga ya shiga wanka ta zauna bakin gado har ya fito ta kalleshi yana goge kai alamar wankan xxxxxx yayi. Ta fuskanceshi da kyau, tace ina kaje yau? Gurin abokaina ya bata amsa yana chire doguwar rigar dake jikinsa dagashi sai towel bata taba ganinsa hakaba sai yau tsoro yakamata ta tashi ta koma palo, ranar dai batayi bacciba zuciyarta cike da tuhume tuhume, sai guraren asuba bacci yayi awon gaba da ita bata farkaba sai guraren 12 Subhanallahi yau tayi lettin lecture dole taje ta nemo abinci ta tashi ta fita direvan bayanan an ma fita da motar da ake kaita skull da ita tayi tsaki tafito ta taka sosai sannan ta sami mai adaidaita sahu ya dauketa koda taje Al nasiha restaurant abincinda takeso ya qare aka mata kwatancen wani guri inda zata sami abincin ta qara tsayawa chan saiga mai adaidata sahu ta tsayar dashi suka tafi sun isa gurin tace ya jirata ta fito tana zaune tana jiran a hada mata abincin taji ance farhaan, wani rass taji mace ce ta kira Sunansa ta juyo ta kalleta ga dukkan alamu tasan ta amma ta manta ina tasanta Dan kamar ta qara fari yanxu, ta kashe kunne taji tace Tana xuwa yanxu. Iffaat tace ina xataje oho? Tana fita tabi bayanta Tana kallo ta tsallaka titi sai taga ta shiga wata villa a gun, tayi tsaki, ta dawo abinta ta karbi abinchinta ta shiga adaidata sunxo daidai villa taga motar da ake kaita makaranta.... Jiki na rawa ta tsayarda mai adaidaitan tace Tana xuwa qirjinta kamar ya fito Dan tsananin tashin hankali wata zuciya tana kije wata na fadin kada kije, haka ta shiga gurin taje gun Masu coffee ta nuna musu hoton farhaan mutumin ya gaya mata dakin da yake zama kullum, taje dakin da qarfin guiwa za'ayi kashin kai wallahi! Ta bubbuga farhaan ya taso ya bude mata, tsaye yayi yana mamakin mi tazo yi anan gurin ya kalleta mi kikeyi anan ta watsa mai harara abinda kakeyi shi nakeyi ta shiga dakin ta duba ko ina ba mace, tazo ta kalleshi karuwar taka bata Iso bane?? Keeee waike bakida hankaline?? Mutum bai isa ya fito shaqatawa ba sai ace yaje gun karuwai wall....... Sheeee ta katseshi da Dora hannu a lebenta... da kunnena naji kana waya da karuwarka kana taxo ka iso tazo kuyi iskancin da kuka sabako?? Ya daga hannu zai wanka Mata mari tuni ta riqe hannunsa,... [7:50AM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..??71 Na Hauwa M. Jabo Ta sadaqar kawai har zata danna power Off ta kulle wayar sai ta tsaya tayi clear din duk abinda ta bude tabar wayanda ta gani ta danna power off ta bude bayin, Tana jiran ya fara masifa akan me zata Taba mai waya amma taga ya shiga bayin baima kalleta ba tana ganin haka tayi sauri ta ijiye masa kayan sa tana ijiye wa ko hannu bata daukeba alarm ya fara bugawa na sallar asuba. Allah yasota da ya buga Tana bayi ai da asirinta ya gama tonuwa, tayi murmushi yana fitowa itama ta shiga tayi alwula tayi sallah...... ********** Aiki ya sami iffatu duk yinin ranar Tana biye dashi a latitude duk inda yaje Tana biye dashi haka tayita saka mai ido har kwana uku ta gano gurin da yake xuwa kullum ta gano gunda yake yawon dare, hatta gurinda yake parking din motarsa ta gane so zata fara aiwatarda aikinta akansa. Farkon abinda ta farayi ta Riga ta gano gunda yake parking kuma tasan lokacinda yake xuwa gurin, saida ta tabbatarda yana office ta kira driver tace yakai motarta gurin ya ijiye tamai kwatance ya kuwa je ya ijiye farhaan an qare aiki akazo gantali tashin hankali abinda ya fada kenan lokacinda ya hango motar ta, ko miya kawo wannan yarinyar anan gurin?? Ya fara tunanin ko tazo nemansane ya tafi akan tazo nemansa ne kawai, bai tsaya bata lokacinsanaa jikinsa na rawa yabar gurin bayan ta duba taga yaje sai kuma taga ya bar gurin ya nufi hanyar nasiha restaurant Tana ganin haka Tama driver dinsu magana akan yaje da sauri ya dauko motar bayan ya ijiye motar a gida dama tayi kwalliya kamar wata amarya, yana dawowa ya ganta kuma, ya kalleta kwalliyan ta ya sakashi zargi,! To Ina taje miye na kwalliya ma! Cox bata taba masa irin wannnan kwalliyar ba, Yanason Ya mata magana amma yana tsoro, yasan zatace shima mi yajeyi a chan? Ko kuma tace ina ya ganta? Tinda bai gantaba gara ya bari har y kamata da kanshi, haka ya zauna yana tafarfasa har yayi bacci Dan baqin ciki ranar ko fitar dare baiyiba.. Goben ranar sai baije gurin ba daga office ya dawo gida kuma idan ya dawo saiya ganta gida zaune ba inda tajee har kwana uku ranar na hudu yaje gurin tana ganin haka ta tura driver yaje yayi parking din motarta daga kan hanya hanya ta yanda dole dole yaga motar tazo tayi kwalliya abinta ta kame bayan ya fito hotel din yaga motarta, mamaki ya kamashi, tana kallon duk wani moving dinsa a latitude yana yawo hakan ya tabbatar mata da nemanta yakeyi a gurin tayi murmushi ya fito wajen gurin yayin parking yana jiran ta fito kusan awa daya yana jiran ta tafito amma bata ba labari, ya gaji. ya riqa ya tabbatar da cewa nan gurin tazo yaja mota Kamar wani mahaukaci..... [7:50AM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..?? 72 Na Hauwa M. Jabo Tana ganin yabar gurin dama driver yana gurin tamai waya tace yayi sauri ya dawo da mota gida yayi gudu sosai farhaan kam traffic ya tsare shi a hanya ga uban go slow ya biyo ta PZ shi kuwa driver ta by pass yabi kamin farhaan ya kawo tudun wada tuni an dawo da motar gida yana shigowa gida yaga motar, yana huci Kamar kasa tana zaune a Palo ta saka fura gaba tanasha yana xuwa yasa qafa yayi ball da furar gaba daya ya finciko gashin kanta ya wurgata saman kujera, yazo Dai dai da ita zai kasheta da mari ta wani riqe hannunsa da qarfi, tayi tsaye saman kujerar wallahi idan ka mareni ba mijina bane ko waye kai sai na rama... A fusace yace ke Dan ubanki ubanwa kike yiwa kwalliya kina kina fita? Ta watsa mai harara tace ubanda ya chanchanchi na yiwa kwalliya shi nake yiwa.! Ya daki iska ya juya yana huci iffaat ni kike yiwa rashin kunya?? mi kike zuwayi a Zaria hotel? Mi kikiye achan?? tsaki ta masa ta diro daga kujerar ta kama hanyar dakinta ya biyo ta kinsan Allah wallahi idan bakiyi magana zan iya kashe ki iffaat wallahi xan sallantar da ruwuyarki..!! tashin hankali lallai farhaan yafi iffaat kishi hadda zancen kisa ta bala'en jin tsoro ta juyo ta kalleshi taga yanda yayi wani iri dashi, tayi sauri tabi gefensa ta fita bata tsaya ko inaba sai Gidan su farhaan tana zuwa ta fada jikin umma tana kuka... Akayita tambaya amma ba amsa umma ta kira farhaan tace maxa yaxo tana Neman sa ya kuwa zo, umma ta fara tambayar sa mi ya mata haka duk ta firgice shiru yayi ya kasa magana umma ta dakamai tsawa ya mata bayanin komai tsaki tayi, rudadden banxa wai kai mi yake damunka ne? Ko kunya bakajiba Dan Allah kace ka ga mota amma baka gantaba kuma ka dawo ka tarar da ita gida, haba wane irin shirme ne wannan umma wallahi har kwalliya fa takeyi.! Umma tace to mace a Gidan mijinta batayi kwalliya idan batayi kwalliya ba mi kake son tayi kaji shiriritar banxa, kai waya gaya maka haka ake kishi da hauka, ka bari sai ka tabbatar sannan ka yanke hukuncin waima kai uban me kakeyi a Zaria hotel? Da har kaje kayita ganinta? Ya Sosa kai iffaat data narke jikin umma ta dago ido ta saci kallonsa ya duqar dakai, yace umma baqi nake saukewa a gurin. Tayi tsaki wallahi ka shiga taitayinka. kada ka qara daga mata hankali da haukarka kaji na gaya maka sannan duk abinda kakeyi ka bari sai ka tabbatar sannan ka yanke hukunci farhaan kam ya rasa bakin magana umma ba fahimtar sa zatayiba tonon asiri ne ma zai yiwa kansa idan yace zaiyi ma umma bayani har ta gamsu,!! akace ta tashi ta bishi ta sa kuka ita bazatajeba dole umma tace ya tafi gobe ya dawo ya tafi da ita, Na gaya muku iffaat fa taji tsoro matuqa taji zai kaita lakhira... Dole ta chanxa wata hanya... Muje zuwa muji hanyar da zata komawa. [9:32PM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..??73 Na Hauwa M. Jabo Farhaan kuwa zaune ya kwana yana ta tunane tunane, kamar ya hade rai ya mutu Dan baqin ciki... Ya janyo wayarsa ta bude hotunan ta yana kallo tabbas yasan yana son iffaat babban abinda yake damunsa idan ya tuna WACE CE ITA.. Yar aikinsace fa wannan gani da yake mata har kullum shi yakesa baya darajata, amma yasan yanasonta babban dalilin da yasa ya qara aminta da auren Suhaila Dan sunyi kama da iffaat ne, hakadai yayita mulmula saman gado kamar an xuba lemu a paranti sai zagayawa yakeyi yana juyi wata zuciya tace idan ma Yar aikinkace ai matarkace yanxu yakamata ka bata haqqinta na matarka, ko ka sami sauqi, chaiiiiii. qarshe ya tafi akan iffaat bazata taba aikata hakanba amma xaiyi magana da driver dinta yaji gaskiyar magana,. Hmmmm nidai jabo Bantaba tunanin farhaan yana son iffaat hakaba ba sai yau Ashe shima ya kamu bamuda story, Haka gadon ya masa fadi yasaba da kwanciya tare da ita koda ba abinda sukeyi amma yana jin qamshin jikinta, yanajin dadi amma yau babu... Tunda qarfe 8 yaje daukota umma tace sai ya dawo office sannan yazo ya dauketa.. Yinin Ranar dai bai gane komaiba gashinan sai a hankali, har ya taso ya dawo office yazo umma tamusu fada musamman shi, sannan suka tafi, iffaat dai taji tsoro fa yanda ya mata ya firgitata ba kadanba, amma bata nuna masaba So ta yanke shawarar bazata qara kai motar ta gurinba...!! Iffat Kura ga tsoro ga ban tsoro.!! ****** Farhaan ma haka bai qara xuwa Zaria hotel ba. Bayan yayi bincike ya gano shirinta dariya kawai yayi, lallai wannan yarinya akwai rigima.. Yanxu ta saka masa ido sosai a latitude tana yawan ganin yana zuwa wani guri so abinda ta farayi shine ta sami mai adaidata sahu ta biyashi tace kawai ya bishi na kwana biyu yaga mi yakeyi a gurin ai kuwa an kawo mata labari wata yarinya yake dauka gurin tasa aka duba mata gidansu yarinyar da komai nata, ta riqa ta shirya abinda zata mata ta kiyaye lokacinda yake sauketa ya wuce. ta sami almajirai su biyar tace aiki zasu mata farhaan na sauketa ta riqa ta tare hanyar tasa yaran suka tareta har ta fara xaginsu iffaat taxo ta wanketa da mari tace wayannan almajiran sun fiki daraja Yar iska yarinyar.! mamaki ya cikata hakadai iffaat tace ta shiga wani kongon gida zasuyi aiki, ta turje sai tasa almajiran nan suka durata cikin kongon gidan taso tayi taurin kai sai taga batada mafita illa miqa wuya, bayan sun shiga iffaat ta zauna saman wani bulo tabata almakashi tace ta yanke gashin kanka ta fara gaddama iffaat ta qara waske banxa da mari saida bakinta ya fashe da jini ba shiri yarinyar ta karba ta aske iya yanda zata aiya iffaat tace bai mataba haka tasa reza ta mata tall kobo almajiran sai dariya suke nima jabo dai na dara cox mace ba gashi batayiba!! bayan ta mata gwandal tace saura Abu biyu kuma, matar ta fara kuka tana tataimaketa iffat tace ta rufawa kanta asiri ta bari suyi aikinsu idan ba hakaba zata qara mata wani punishment,mata kuwa sai kuka take tana roqon iffaat tayi haquri amma iffaat ko kallonta batayiba tasa almajiranta suka danne mata ita ta mata bille guda biyu a fuska sannan ta fito da bulalarta ta zaneta saida ita kanta ta gaji da dukan nata sannan ta barta tace idan an tambayeki wa ya miki haka kice iffaat ce ko kice Mrs PURHUUN..... ta fita tabarta nan tana kuka..... [9:38PM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..?? 74 Na Hauwa M.Jabo Yarinyar taji jiki matuqa sai kuka takeyi, babban baqin cikinta billen data mata cox gashi zai fito nan gaba amma bille bazai baceba har abada ta fara tunanin WACE CE ITA?? Mrs PURHUUN kuma?? waima da wane dalili ta mata haka?? Ta gaji ta rarrafa taje gidansu tana kuka..! Ran iffat yayi sanyi farhaan na dawowa ta kalleshi ta kwashe da dariya ya juyo ya kalleta yace lafiya? Ta wani daga ido alamar dawa kake? Yace hmmm yasan tabbas akwai abinda takema dariya, sai daibai bazai kulataba. Iffaat haka ta riqa bin farhaan a latitude saida tama yan matanshi shida aski hadda su ramcy ko ina hafsa take ohoo taso ta aske hafsa ta mata bille.... ******* Ranar sun fito lecture ta hadu da wata tsohuwar qawarta Aisha armiya'u mada. Sun Dan yi skull tare da ita tanason iffat sosai bayan sun gaisa take bata labarin tayi aure tanata tayata murna hardai tace zataje gidanta bayan lecture sunje gida akan hanya ta siya mata abinci Dan iffaat har yau bata iya girkiba hasalima bata taba girkiba saidai dafa tea, hatta kunna gas har yau bata iyaba.... Bayan sun qare chin abinci suna tadi saiga farhaan ya shigo, armiya'u ta gaidashi ya amsa iffat kam ko motsi tadai kalleshi kawai, bayan ya wuce ta kalleta tace iffaat wannan ne mijinki? Tace eh kinsan shine? Tace Eh nasanshi, iffaat aranta tace wallahi zan miki bille kuwa. Ina kika sanshi? No tunda dadewa sunyi soyayyah da wata cousin dina but Allah bai qaddari aurensuba, iffaat tace eyyah aure nufin Allah ne.! Eh hakane har an bar zancen amma iffaat sarkin kishi abin yana cinta. Chan tace ya sunan cousin din taki? Tace hafsa, amma sun rabu yanda tace min wai yasa house girl dinsa ta mata wulaqanci abin dai ba dadin ji wallahi... Nidai nace ko baka son mace ai ba haka ya dace kayi Dan ka rabu da itaba.... Ka gaya mata bazaka auretaba sai a zauna lafiya iffaat tayi murmushi wato abinda ta mata ya rabasu da farhaan lallai aikinta yayi kyau.. A munafunce tace Allah sarki kinsan mazan yanxu sai a hankali , tanason ta sami information a gurinta, Kuma ai farhaan ya damu da ita har ya bani labarinta, armiya'u najin an fadi haka sai ta saki jiki dama tana tsoron tayi siririn baha ya zamana batasan da zancen ba..... [9:45PM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..?? 75 Na Hauwa M.jabo Armiya'u tace Wallahi kuwa hafsa taso farhaan kamar rayuwarta ta bashi kanta sabida tana gannin kamar zai aureta, kai ai hafsa tayi jinyar rabuwa da farhaan, iffaat ta gyara zama tace ai yace min tanada jarumta sosai, armiya'u tace uhum Ashe dai kinsan komai kena,? nama daina jin tsoron fada, iffaat tace eh duk ya fadamin yace har matarsa ta farko tananan yana tare da ita yace har gida yake kawota.! armiya'u ta gyara zama za'ayi gulma ai iffaat in gaya miki yanda hafsa ta bani labari mijinki akwai tsananin buqata kuma yanason jarumta matuqa gurin harka, idan kika kiyaye haka wallahi zaki sameshi a hannu shiyasa ma hafsa ta daga tuta duk cikin yan matanshi yafi ji da ita, idan kika kiyaye sai yanda kikayi dashi.! Iffaat dai duk da qunan da zuciyanta keyi bai hanata saurareba, wai har wata tasan asirin mijinta Allah wadaran halin farhaan, Kinga mijin ki Dan gayu ne, so wallahi sai kin kasa kin tsare yanda yan mata sukayi yawa idan ma Allah ya tsareki bai miki kishiyaba to zai nemi mata a waje amma idan kika gyara kanki kin gama komai Dan maganin matannan kinasha kwalliya duk ki riqayi kissa da kisinsina ki zama first class gaki da gashi kiyi yanda kikasan mijinki zai ji dadi, Dan girkinnan duk ki xama kece kan gaba, wallahi nasan yan matan da suke son mijinki ba adadi kuma duk sun fiki girma da wayo, ko wacce tasan yanda zata sace zuciyar namiji so ki zama very careful iffaat kam ta sassauto da kishi tana sauraren jawabin qawarta Aysha armiya'u mada lallai ita tasan inda duniya ta Nufa kuma itace qawa ta gari.... Armiya'u tace ki duba yanxu ina kallo mijinki ya shigo baki gaisheshiba kuma ko ruwa baki kaimasaba bare abinci, iffaat tayi murmushi batace komai ba Armiya'u dai ta baiwa iffaat darasi kuma ya shigeta matsalar batasan yanda zata fara bane, bayan sunyi sallama ta tafi saiga farhaan ya fito a daki dama jiran tafiyarta yake yaxo yayi tsaye yana kallonta wannan yarinya akwai kwarjini sau da yawa idan ta masa Abu ya tunkareta sai ya kasa..yaga idan ma masifa zai mata aikin banxa zaiyi don ba jin masifar takeyiba so gara ya mata magana cikin ruwan sanyi.... Ya kira sunan ta tana kwance ta dago ta kalleshi, ki tashi zaune batace komaiba ta miqe zaune yace ki ijiye waya, zamuyi magana kafada inajinka kawai. Ya kira sunanta, Iffaat tace na'am ki ijiye waya, sai ya bata tausayi ta ijiye waya ta fuskanceshi dakyau yace iffaat abinda kikayi kina ganin kin kyauta? Ta xaro ido mi nayi kuma? Kin fini sani, aah Malam kada amin sharri ina zaune lafiya mi nayi?? mi kika yiwa yaran mutane? Ta bone kuwa wayanni yara kuma ?? Yace abokan aikina! Uhum yy kenan abokan aikinka kuma? Ya za'ayi nasan abokan aikinka? Iffaat wannan serious issue ne, miyasa kika aikata hakan?? Nifa yaya ban gane mi kake fadaba kamin dalla dalla kawai, yaga zagaye zagaye ba nashi bane yace yaran da kika yiwa aski da bille Kuma kika dakesu....!! [9:59PM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..??76 Na Hauwa M. Jabo Au kace min karuwanka koda yake suma abokan aikine tunda dasu ake iskancin no no no na manta wayewace, ko ba wayewa bace?! ranshi ya baci, sai ya share yaci gaba da magana kinsan kuwa kan haka wata har qara ta shigar kotu dagayar na rufe case dinnan,? iffaat tayi dariya hadda kwalla, wallahi da ka bari an tafi dani kawai kaga sai kaji dadin kawo su har cikin gida kamar yanda ka saba,! shiru yayi aransa yace wannan duk abinda aka fada tanada amsa, shikam gara kawai ya nemi shiri gunta koya sami sassauci dama laifin sane dabai nuna mata shi wayeba da yanxu rawar ta chanxa amma soon zata shigo hannu.. chan yace iffaat kinsan kuwa ina tsananin sonki? Kinsan tun yaushe nake fama da sonki cikin rayuwata? Please iffaat kidaina wahala min da zuciya... Wani sanyi taji a ranta inaga tinda tazo duniya bata taba jin kalma mai dadi kamar wannan ba, amma bata nunaba Sam, iffaat ki tausayawa rayuwa wallahi wasu abubuwan duk rashin ki yake sa ina aikatasu...¡! Ta kalleshi ta watsa mai harara Malam Dan kawai yan matanka sun gudu shine zaka lallabo gurina ka min wayo ko? To kayi letti bazakasamu hakanba, No iffaat ni ba sai na sami komai a wajenkiba just kawai ki amince dani maisonkine, mudaina rigima nagaji. wallahi ina axabtuwa da rashinki, guntun tsaki taja, ta koma ta kwanta ta dauki wayanta ta danna recoding duk abinda yake fada tana dauka har ya qare batace dashi komaiba, ya qare yazo kusa da ita tayi sauri ta kashe ya dafa kafadarta ta watsomai ido miye haka wai? Ta bani dariya miji ya taba mata tana miye haka!? Yace ba komai yakai hannunsa akan gashinta ya shafa yace kizo na gyara miki gashin ki! Kallonsa kawai tayi yanda ya chanza ya bata tsoro ta yinqura zata tashi ya danneta ta koma kwance ta kalleshi wai mi kakesone Malam? Ya kawo bakinsa daidai da kunnenta ya mata rada saida tsikar jikinta ta tashi yace ke nakeso iffaat, tace Banganeba! ina nufi matata nakeso! Tofa yau akeyinta gata kwance duk ya dabai bayeta, yana zauna qasa hmmm kawai tace bata ce komaiba tana jinsa yana Dan mata wai waye a qirji alamar yanason ya aika hannunsa ciki, Yya farhaan ina zuwa bari nayi fitsari. Ya gane guduwa takeson tayi sai yace muje na rakaki,! Burinta dai ta tashi zaune ya daga mata ta tashi zaune muje mana. Ta harareshi nama fasa xuwa. Murmushi yayi yace idan kina tsiwa kinfi kyau.! aransa yace sai kin shigo hannunna yarinya ya miqe ya shiga daki, Iffaat kam dadine yake Neman ya hallakata dama Ashe yanasonta? Da tasani ta tambayeshi tun yaushe yakesonta tayi murmushi ta shafa gashinta, ta tuna shine mutum na farko daya fara gyara mata gashinta! Ta qara murmusawa ta tashi tayi sallah... Goben ranar farhaan ya ya fitowa office wata budurwarsa ta kirashi tace su hadu wani guri kamar bazai jeba sai kawai ya wuce gurin iffaat kuma tana sukul bayan ta fito lecture sai ta duba latitude dinta taga farhan yananan kusa da skull dinsu, har ta qara shiga lecture ta fito bai motsa daga gunba tayi refreshing still yana gun tayi zooming sosai taga gurin a qafa ta tattaka koda taje ta qara refreshing taga itama tana gurin nisansu Kadan ne, koda ta daga kai sai ga motarsa da wata mota,! Tayi tsaye ta rasa yanda zatayi, ta duba ba kowa a gurin, sai mai gadi, tanuna ma mai gadin gurin hotonsa tace yaga wannan yace eh yana ciki.! tayi shiru ya zata shiga gurin aka nuna mata dakin tana kallon dakin amma ta kasa qarasawa sai ta fito Dan tasan baqin ciki kawai zata gani idan ma taje din tana hanyar dawowa sai taga police station tayi murmushi wallahi yau farhaan sai ka kwana a Gidan yayan sanda direct gurin su taje........ Muje zuwaa [10:07PM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..?? 77 Na Hauwa M. Jabo Ta je gurin yansanda ta sami babban su tace tanason yan sanda hudu ya tambayeta dalili batasan abinda xataceba tace wanine yake bata mata qanwa kuma ta rabasu sunqi rabuwa shine takeson akama- matasu duka biyu taga kamar baxasu bataba tana dubawa sai taga gun cirar kudi anyi Sa'a ATM yana cikin jaka ta chiro kudi tazo ta miqewa Dan sandan jiki na rawa ya karba ya bata kwalawa hudu tace kuma kada abada belinsu karma a bari suyi magana taje tanuna musu gun tayi sauri ta dawo skull, policawa kuwa sun cika aikinsu suka kama farhaan da budurwarsa dama iffaat tace kada a sakeshi kuma kada a sauraresu dukansu sai taxo gobe zata karbesu kuma kada a bari yayi magana da kowa!! farhaan kam Dan baqin ciki har kuka yakeyi mi yake faruwa dashine tunda yake ba'ataba kamasahiba sai yau an wulaqantashi ba kadanba.. tsanar bariki ta shige mai zuciya yayi nadama, yayi yayi abari yayi magana amma ina sunqi kulashi tunanin sa daya iffaat yanda zata kwana ita kadai..! Uhum, itakam hankalinta kwance tanajin dadi koba komai tamai rashin kunya da safe ta chaba ado na gani na fada ta saka kayanda ita kanta tasan tayi da saka glss dinta ta wuce skull bayan ta fito lecture taje gurin yansanda, tace yazo beline, aka fito da farhaan da matar tace a maida matar sai an qare case din farhaan aka maida matar wata jaka da ita sai jalkuna, yana ganinta ya rude ya ma rasa abinda zai fada kamar gaske tace ma yansanda Dan Allah a bata belin sa mijintane bazai sakeba ayi haquri.!! ya kalleta cike da mamaki iffaat waya gaya miki inanan? haka kawai ya samu damar ce mata..! tace naji a jikina kaje abinda ka saba an kamaka.! Ta kalleshi but so happy wallahi Allah ya qara maganin irinku kenan masu bata yayan mutane.. Sosa kai yayi, police din yace kai kanada wannan baby mixakayi da waccan ashawon kalleta haddadiya da ita kunya ta rufe shi da haushin dansanda ina ruwanshi da matarsa.. ta cika takardu aka saki farhaan sun fito ita dashi ta kalleshi ta nunashi da hannu, kalleka Dan Allah namiji har namiji amma ba halin kirki.! Tir da hali irin naka, idonta suka ciko da kwalla amma da yake ta saka glass sai baxai ganiba nayi nadamar kasan cewa tare dakai a matsayin matarka. Kullum cikin tunanin kana ina mi kakeyi!!? kallonta yake tamai kyau iffaat baby ce shima yasani kullum qara cika takeyi tana wani fresh murmushi yayi ya janyota jikinsa ya rungume yana bata haquri, tayi tayi ta kwace kanta amma ta kasa sai ta barwa Allah....... Dagyar Tasamu ya saketa hawaye ta gani a idonsa tausayi ya bata, ta bude mai mota ya shiga itama ta shiga taja suka tafi,mamaki yake ya akayi ta iya mota? Waya koya mata? waima waya gaya mata yana gurin baiso ta saniba Sam har suka Isa gida bata kalleshi ba tana tauna chewing gum a hankali suna Isa gida kuma sai yaga motarsa...... [10:14PM, 5/13/2015] .: WACE CE ITA..?? 78 Na Hauwa M. Jabo Ya kalleta chike da mamaki yaga batama kula da mamakinsaba sai shima ya basar.! sun shiga gida ta kawo mai abinci abinda bai taba samuba tunda ya aureta yasan ba ita ta girkaba amma duk da haka yaji dadi ya zauna yaci yana chi tace, nasan police station ba abincin kirki shi yasa na kawo maka wannam, lokaci daya har ya hargitse, tayi dariyarta ta mugunta ya dago ya kalleta tace kaima ka dandana kwana Gidan yan sanda ko? Ta qara yin dariya tace dadi ko?? Baice mata komaiba ina tambaya.! ya kalleta wai ya akayi kikasan ina chan ? Tayi murmushin mugunta tace sabida ni na saka a kamaka..! Ya zare ido Kamar ya? Tace Kamar haka.! Please kimin bayani ya akayi kikasan ina gurin? Wallahi Nina tura a kamamin kai, kuma yanxu na fara duk lokacinda na ganka da wata mace wallahi saina kulleka. Mamaki yakeyi dukda cewa yasan iffaat fiye da hakama zata iyayi amma ta bashi mamaki, miyasa duk motsinsa akan idonta,? Ya akayi kikasan gunda nake zuwa? Tace sabida ina iffaat, baice komaiba aransa yace Ko ta saka a riqa bibiyarshine? Kallonta kawai yayi Dan gaskiya tamai yawa,!! yana zaune wayanshi tayi qara ya daga abbanshine ya gaisheshi anan abba yake gayamai zai aikeshi Thailand, kuma ya tafi da matarsa, bayan ya qare waya ya mata bayani ido bude tace baxataba

Chapter 8 of 10