Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 10
maitsoka nasan zamu huta sosai Yace ameen yar kanwata jeki karkiyi latti Tafita abinta tana murmushi Umma ta sauke ajiyar zuciya tace wa yaya shamsu Kasan wani Abu kuwa shamsu deen yaya shamsu yace a a umma saikin fada Tace wato akullum na kalleku kaida kanwar ka ina wa Allah godiya daya mallakamin 'ya'ya nagari Dan ba abinda zance wa Allah sai godiya kawai amma duk inda ake neman 'ya'ya nagari nasamu Abba dayake shirin fitowa daga dakinsa yace munsamu dai zakice zainaba Tunda Allah yasa shamsu yakawo kwari fa shiyake dawainiyya damu agidan Shine komai na kanwarsa shine namu aiba abinda zamuce sai muce shima Allah yabashi mai mishi Umma tace Ameen malam Malam sulaima yace babban damuwata shine inga kasamu aiki kayi aure Dan shine cikar mutuncin mutum Umma tace hakane ai baki yayi tunda yana da wacce yakeso khadija yarinyar kirki taki kowa saishi take jira Ko a yanzu aka tura za ayi komai tunda iyayen ma sun komai Malam sule yaja numfashi yace hakane kam to Allah yabamu yadda zamuyi Ya kalli shamsu da tunda suka fara zancen auranshi yashiga duniyar tunani Dan yana matukar son budurwarshi khadijat wacce akekira da kubra kitama tana son yaya shamsu sosai Dan Shekarar ta daya kenan dagama secondary school Manema sunzo Neman aurenta taki ita sai shamsu Haka iyayen suka hakura suke zaman jiran shamsu yakawo sadaki a daura aure Malam sule yakalli shamsu yace karka damu akwai Allah Shamsu yace barinje Abba sai na dawo ya ma umma ma sallama ya wuce zuwa Neman abinda zasuci YAYA SHAMSU daga secondary bai kara gaba ba saboda rashin kudi daya musu katutu shida mahaifansa Dan haka kawai ya hakura yake Dan buga bugansa dahaka kuma har Allah yasa aka haifi kanwarsa husna saiya yaci burin Husna zatayi karatu tunda shi Allah baisa zaiyi mezurfiba Sai kuma gashi Allah yafara cikawa shamsu burinsa inda husnah taci scholarship ** Husnah tana isa school tasamu anfara assembly Ta tsaya daga bayan 'yan mate dinsu suna sauraron jawabi daga bakin principal dinsu Can sai vice principal yace yace zamufara kiran new prefect dinmu daya bayan daya Principal tace a fara da head girl ko Sai copper bash yace am sorry ma Gwamma afara da sauran kafin head girl Zaifi Jan ra ayin su Principal tace OK afara kira kawai Nan akafara kiransu ana samusu hula da kuma belt Dansu prefect din hula suke sawa green gabadayansu na head girl ce kawai ya banbanta Dan nata read cap take sawa Can taji ance social prefect AMINA HAKEEM ABUBBAKAR Nan aka dau tafi raf raf raf ana murna Can sai vice principal yayi gyaran murya yace yanzu zamu Kira me gayya me aiki wato our head girl Nan aka kira sunan ASMAU SULAIMAN SHAMSU cikin gigicewa Husnah tadago kanta aikuwa tana dogowa sukayi ido hudu da Copper bashir Ya kashe mata ido daya Cikin tashin hankali Husnah ta daga kafa dakyar tana zuwa ta hau kan stage Principal ta rungume Husnah tare da Da samata hulan head girl dinta read cap Ta daura mata belt dinta read shima aikuwa daga students har malaman dake wajen aka dautafi Dan sunburge kowa ga read cap din yawa Husnah kyau sosai kaman Dan ita akayi hulan Nan dai aka rantsar dasu Husnah a matsayin new prefect *** Copper Bash ya tsare Husnah alokacin dazata wuce gida itada meenat Copper bash yace asmau Ya naga kina ta shan kamshi ne Yau Meenat tafashe da dariya Tace uncle ai Husnah fa batasan za abata prefect ba ballantana Head girl Copper bash yayi murmushi yace ai kuwa ta yaudari kanta To inba a bata ba waza aba wa Meenat tace aifa dai kam Husnah dai tana jin su batace komaiba Nan driver din meenat yazo daukarta Husnah kuma dama da kafa take zuwa take komawa Meenat tace Dan Allah Husnah kizo musaukeki a gidan kinga sai naga gidanku ko Husnah tayi murmushi dimple dinta suka lotsa Copper bash ya tsaya kawai yana kallon Husnah komai nata cikin aji takeyinsa da nutsuwa shiyasa takeda farinjini a school din Husnah tace wallahi meenat idan ya shamsu ya ganni a mota zai min fada sosai . Meenat tace kedai kawai bakyason kibimu sai kiyi tayiwa yaya shamsu sharri Copper bash yace kinga kuyi sauri kutafi gida kar anemeku kuntsaya surutu Meenat tace to shikenan sai mun hadu goben idan munzo ko Husnah tace to meenat Allah yakaimu kigaida gidan Nan sukayi sallama Copper bash yace wa Husnah muje nakaiki gida da kaina Tunda kinki kawarki takaiki Husnah tace Dan Allah uncle kayi hakuri wallahi yayana yaganni da kai zaimin fada Copper bash yace mezaisa yamiki fada baki kai a rakakin bane ko yaya Husnah tayi shiru tace kayi hakuri Dan Allah Yace wato har yanzu Husnah kinkasa yarda da sonda nake miki ko Kibani dama nasan gidanku da iyayenki wallahi dagaske nake auranki zanyi Asmau Husnah tace Dan Allah malam kayi hakuri kar yaya yasan da wannan maganar Dan ya hanani kula koda kawace ballantana Maganar soyayya tun yanzu Da kyar yabani dama kawance da ?mina Hakeem ma Copper bash yace OK na fahinceki Ba wai nidinne bakyaso ba umarnin yayanki kikebi ko Husnah ta rufe ido tana murmushi tayi hanyar fita daga gate din school din Copper bash yayi murmushi tunda ya gano yafara shiga zuciyar Husnah Zaisan hanyar da zaibi Dan yasan iyayenta da yayanta shamsu Bashir Dan wani hamshakin maikudi ne sosai acikin garin kano Bautar kasa wato NYSC yakaishi school dinsu Husnah Tunda yadora idonshi kan Husna yaji yakamu da son ta amma takibashi daman hakan Next page [05/05, 11:05 AM] UMMU AFAN

Chapter 4 of 10