Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
3 / 10
Abdul yanzu wannan shine zumuncin da iyayenmu suka hada muyi kenan Hakeem yayi wani uban tsaki kafin yajuya ya kwanta abinshi Can tace ai idan kai baka bukatata ni ina bukatarka Bai kamata kahanani hakkina da Allah yarataya a wuyarka ba """"' Tabbas yasan hakane kuma mummynshi ma ta mashi tuni akan haka Koba komai gwamma yafita a hakkinta Yajuya yace mata damuwarki kenan yasa aka miki aure ko Kafin tayi magana ya bajadda ita akan bed din Yacire sleeping dress din nata yayi wurgi da shi bako romance Sai dai adduar da akeyi lokacin da miji zai sadu da iyalinsa ai kuwa dai Laila tafada musu Tagane shayi ruwane Yanagama abin da zaiyi ya tureta ya kwanta abinshi Ita kuwa Laila tana cikin farin ciki Dan ita yadda taji din ne kuma bazata iya hakuriba """"" Kullum zata kawo kan nata indai zai biya mata bukatarta kafin ta shekashi lahira taci dukiya Nan itama ta kwanta bacci ya dauketa cike da farincikin kasancewarsu da Hakeem a Daren nan . Washagari Hakeem kota kanta baiyiba yana gama shirinsa cikin wata yadi mai tsadar gaske iri daya ma sukayi da Ahmad Yadin ash colour ne sai yasa bakin takalmi da hula Wanda akekira da senator Duk Wanda yakalli Hakeem sai yasake kallonsa Dan ya hadu iya haduwa Yana fitowa Laila ta tareshi tace abdul ga break fast dinka fa mai aiki tagama , Wani matsiyacin kallo yamata yace kinga nayi miki kama da mai cin abincin masu aiki """ Ban guri nawuce ni Tabishi da kallo tace aikuwa sai dai idan bazaka ci abinci agidan nan ba Dan ko kwai ban iya soyawa tayi dadi batare da ya kone ba """ Hakeem suna break fast daddy yace mishi Shi Ahmad din yashirya kuwa Dan naga kaman kai ka matsa kutafi Hakeem yayi dariya yace bahaka bane dad kasan fa I want to be come professor like you kaga yakamata indage ko dad Daddyn Hakeem yace hakane but please son take care of your self sosai kaji ko banda harka da mutanen banza """ Mummy tayi murmushi tace kai daddyn Hakeem duk komawarshi school saikayi mishi wannan nasihar yanzu fa babban mutum ne tunda ya ajiye iyali Daddy yayi murmushi yace wai haka son Shidai Hakeem baice komaiba Daddy yace nifa wallhi ina mantawa yarinyar nan tana cikin gidan nan Ya bara kace tazo akarya da itaba . Hakeem yace daddy ai tana da mai aikinta har tagama komai sunci abincinsu Daddy yace duk da hakadai ai itama yar gida ce Mummy tace kasan alamarin yara sai a hankali Kawai kabarsu nan dai mummy ta canja magana Tace jirgin safe zakubi ko Abdul Hakeem yace da asuba makuwa mummy tace aikuwa kaman nasani nagama hada ma komai Mummy Allah yasa kinmin wanna cake din naki medadi Tace ai duk abinda kasan ina maka ba abin da na rage Cikin jin dadi Hakeem yace that's my mom Allah yabar minku iyayena Daddy da mummy sukace ameen Allah yamaka albarka Yauma da daddare sai da Laila takai kanta gurin Hakeem Tun karfe uku yatashi yagama shirinsa tsaf bai Dade da gamawa ba Ahmad ya kira yace man kataho tafa nigani a air port ma Hakeem yace OK gani nan Yadauki cheque ya rubuta dubu Dari biyar yasama Laila akan bed Da kuma short note Yafita daddy da mummy shi kawai suke jira suka rakashi Next page Your comment is needed fan's =???=???=؋?=???=???=??? [30/04, 5:49 PM] UMMU AFAN

Chapter 3 of 10