Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
magrib, jin ana bude get yasa su fitowa tarbar uncle din Sosai murmushi shin sa, yakaru ganin sabha" ah harkin iso?yaushe kika karaso"laaa uncle tun wajen 2pm nazo, Masha Allah karasowa falon sukai nan akabaje anata hira, harasuka gama cin abinci... ************ Kiran sallah ne yatadashi, toilet yaje yay wanka, jallabiya yasa purple me hula, sosai taimai kyau kamar don shi akayita sannan yatafi masjid Se wurin 7am yafito daga masjid din, sashen ammi yaje yagaidata, sannan yaje yagaida, abbu dan hira sukai akan tafiyar tashi tareda, samai albarka daki yaje yadau duk abunda yasan zebukata, lokacin wurin 10am, fitowa yai cikin bakaken suit wanda sukai das ajikinahi kamar kasacewhi... Zuwa yai yaima su ammi sallama lokacin abbu yananan yana breakfast. Baki yasaki ganin Abbas zaune yanacin chips, kai yaushe kazo??anan nakwana ai! Au bakasaniba tab Kai dalla banson iskanci, ammi ce tace to kaji,duk dry sukai hannu sukai yna tambayarahi yasu mama?wlh alhamdulillah sunce inmak Allah ya kiyaye ameen, ahima zamayai yafaraci bawani da yawa yaciba, yace Abbas tashi muje Kai nifa bankoshiba, karka koshidin, ammi,abbu zantafi yafada yana tsugunnawa gabansu, fatan alkhairi sukamai dukansu Sannan suka fito, shida Abbas motar Abbas suka shiga, sabida shi zekaishi airport din, suna hanya suna hira har suka karaso lokacin 11am takusa kuma, 11 din zasu tashi, bawani bata lokaci yashiga jirgin Abbas nacewa Allah yasa kadawo kaga, an maka aure, sedai kai, yafada yana karasa ahigewa, hannu suke dagama juma, sunajin zasuyi missing sabida sunyi sabo sosai Gida Abbas yakoma yashirya yawuce hospital don yanzu aiki zemai yawa tunda dr sao'od benan Sun sauka lpy, alhamdulillah harya fara abinda yakaishi, donshi beson Westing time, infact ma beson yakai 3weeks din, don wlh shikanshi jiyake yadamu da maganar Abbas akan cewa Allah yasa ai mishi aure kan yadawo, yarasa meyasa meyasa, aikin gabanshi yaci gaba dayi. Yakira Abbas sukai fira sannan yakwanta Kusan satinshi 2 amma tuni yasan abinda yay don Sosai yadage, gefe daya kuma yana famada ciwon mara, maganin yakesha Amma bb wani sauki. Sosai aiki yaima Abbas yawa, sabida kusan shiyake kula da rabin aikin asibitin. ********* Kusan satin sabha 2 yanzu, duk tagaji dazama sabida babu inda take zuwa, yauda wani irin ciwo mara ttashi tana tunanin period dinta ne zezo, gashi batado da pad ba, kuma aunty ciki gareta Balallai tanada shiba, toilet taje tai tsarki, don har pant dinta ya dan baci, zuwatai tace aunty bakida pad pls!eyya wlh babu, sabida yanzu bana amfani dashi shiyasa. Amma Miko min wannan jakar tawa, inbaki kudi, kije driver yakaiki shopping dama akwai abubuwan danakeson siyo wa, Kinga seki siyo pad din ko??to aunty bari in canza kaya Goguwar riga tasa na atamfa, metsada ce atamfar sosai ko kalarta kagani kasan, daga gidan masu kudi sabha tafito, veil tayafa madai daici, wanda yarufe mata jiki, sosai tayi kyau kamar sarauniya, gashi rigar tayi mata das ajiki tafito da shape din uban hips dinta dasuka cika rigar daga kugu Komawatai gun aunty ta amsa kudi, aunty nata tsokanarta wai Allah yasa tasamo musu miji, susha biki, murmushi kawai tayi, Layla da husna ne suka fito (yaran aunty) cikin shirin fita suke suma, aunty sabha zamu rakaki To kuzo muje, Allah ya tsare cewar aunty ameen duk suka amsa sannan suka fita, gurin drivern sukaje, Sabha tace supermarket zekaisu zasuyi siyayya To yafada yana dauko keyn motar, shiga sukayi suka cilla hancin motar, sosai sabha take kalleΒ², don tun randa taxo bata Kara fitaba, sosai take kallon yanda garin yakeda kyau dukda bawanna ne zuwanta na farko ba amma garin yakara mata kyau sosai..........✍️ *#Zarahh* πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€ *βœ“DR SA'OOD* πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€ written by zarahh AA πŸ…ΏοΈ9&10 """"""""""Ammi zaune tana tambayar abbu, tanason fita yanzu zata dawo,"don Allah"dan ahiru yay sannan yace mezaki siyo dakanki??Anya yafada cikeda tunani Kaga wa'innan makotan namu kusan gida uku, akai haihuwa babu abinda muka basu, zansiyo kayan yara Ga turaren wutar mu, ya kusa karewa!kinsan dai bakida lpy ko??kuma bada driver zakiba kk ce? inshallah zanje indawo lpy". Allah yasa Allah ya tsare"ammadai don turare dakinyi waya za'a kawo Miki,dondai kinason fitane".aidole inso fitama gidannan se inyi kusan shekara, sedai makota suma seda dalili Dry yay yace, sekindawo yana mika mata kudi masu yawan gsk, godiya tay, shikuma yafice, donzeje gun baban abbas tunda shi jiya bezoba". Kusan tare suka fita!kowa yai hanyarsa tana drive ahankali cikeda nitsuwa harta karasa. ******** Sabha ko tuni sukazo, kasancewar itada su Layla ne yasa basu tafiba, don se dauakr kayan wasa suke, suje can suke can"sunata sata yawo harta gaji!cewatai pls kozo mutafi haka,to aunty ai mungama, "oya let's go''kudi sukaje suka biya sannan suka fito, baba driver yana cikin motar ya kunna radio Kayan yafito yadauka yasaka a boot, su husna suka shiga baga, tazo shiga shiga kenan taji kara kamr mutum yafadi Da sauri ta juyo, sosai kirjinta ya buga, ganin wata mace akwance babu alamun numfashi, da gudu takarasa gurinta tahau jijjiga ta, baba driver ne yafito a tsorace yake cewa hjy karama kitashi,bakisan irin mutanen vane basuda imani yanzu haka tana jinki, bamajinshi takeba A rude take cewa, mama don Allah kitashi sosai hawaye kefita a idonta, dama Sabha badai tausayi ba, babu wanda yay kokarin temakon matar Ganin haka yasa tafara kokarin daukarta, da kyar ta cibota dangefenta ta kalla, motar datake kusa dasu ta tabbatar motar matar ce, to yazatayi Kawai cewatai baba driver mujeda ita gudanmu ko??Dan zare ido yay yace, kinga ki ajeta kizo mutafi Banza tai mishi tadora hannun matar a kafadarta, ahankali take tafiya harta sata cikin motar Bangaren matar kuwa tanajin komai amma bazata iya ko bude idontaba,baba driver yace yanzu idan alh yay fda fa??kindauko mata bakisantaba itako hryanzu kuka take "Duk su Layla sun damu don matar tabasu tausayi, suma kukan suke harsuka isa gida, fitowa tai still tana sakale da hannun matar, harsuka karasa katon falon, Aunty dake zaune, tataso dasauri tanacewa lpy?" wacece wannan??duk arude take wannan maganar, Aunty bansantaba pls aunty ruwa dasuri tanufa kitchen tadauko ruwan har ta kwantar da'ita, Aunty tadago kan baiwar Allah'r tafara bata ruwan ahankali Tana gama sha kuwa bacci yai gabada ita, se'a sannan aunty tace sabha ina kika samota haryanzu Hawaye ne a face dinta, nan ta kwashe komai tagayawa aunty dan jinjina kai tai tace to, bari akira dadyn Layla mufada mihi ko?eh aunty...baba driver ne yashigo da kayan dasuka siyo Ita harta manta, da kayan wlh amsatai tanamai gdy, aunty kuma ta kira uncle Usman tagayamishi,babu damuwa kantatashi zan dawo semuji ina take, amaida itako? to shikenan sukai Sallama Sosai take bacci tana sauke numfashi ahankali, Aunty ta hau sama tabar sabha tana cemata bari indan watsa ruwa, kikula da ita," to"zama tai tana karewa matar kallo kekkyawa ce ajin karshe amma tadan girma ba lefi Aranta take, cewa ko in wannan tafito gidan arzikine, karar wayan matar NE yadawo, da Ita duniyar tunanin data tafi, jakar matar ta duba nantaga wayar harya tsinke Jin ankara kira yasa, batareda ta dubaba ta kra akunne! sallama taji wanda jin murya dabatasan wayeba, seda kirjinta yce Damm! Haka kawai tatsinci kanta da bugun zuciya jin ankara sallama Yakara sa kirjinta duka, sallamar tayi itama, wanda seda shima mekiran yatsinci kanshi da, bugun zuciya batareda yasan daliliba Bame wayar!yafada zuciyatshi na duka;am...am.seta kasa magana, wata uwar tsawa yabuga mata wanda seda tayarda wayan akan carpet Daidai nan aunty tafito, tana cewa lpy??dama..dama wanine yakira, yawwa bani wayar akunnenta tasa tana sallama, amsawa yay, cikeda girmamawa yace;am. Don Allah ammi fa, dan Jim tay setace ni sunana Amina...nan tafada mishi komi, tareda karawa dacewa kanwatace ta kawota. sosai hankalinshi yatashi, yace don Allah kidan turamin address dinku yanzu, cikin rudewa yake mgnr ok bada muwa, tawayar matar tatura address din ******** Cikim dimuwa yace Abbas, juya motar nan kabi wannan location din;yafada yana mikama mishi wayar hannun shi, lpy? abbas muje mana, kawai juyawa yay don yasan halin sao'od beson musu. Ahankali yakebin location din hrsuka karaso, munzo inji Abbas"to kayi horm mana yafada cikeda kosawa"horm ya Danna cikin sauri megadin yabude, dai dai nan kuma wata motar ta kunno kai. Kusan tare suka shigo.. Acikin gidan kuwa, ahankali tafara bude idonta wa'inda sukadanyi jaa kadan, dasauri aunty ta matso manacewa sannu, kintashi?? murmushi tay tace ina 'yata?ganin aunty bata gane metake nufiba Yasa tace wacce takawoni gidannan, murmushi Aunty tay tace oh, kinga mama yanzu kibari kisha ruwa se inkira miki ita. To amma ruwan zafi zansha kinji yata, murmushi tay tace ba komai, kitchen taje tahada mata black tea, me dadin gsk; fitowa tay tace gashi mm cikeda girmamawa Amsa tay aranta tana mamakin karamci irinna yan gidannan basu santaba amma ji yadda suke girmama ta? Ahankali tafara sha, takara cewa don Allah kikawomin yata inganta. Wlh inaji sanda, wani yake camata ta kyaleni amma tau banza dashi harkuka fa tay, dry kadan anty tay tace, haba wannan sarkin tausayi kenan Allah sarki wlh nakosa inganta. Ahankali take tako steps din, kanta babu dankwali kayam dazune ajikinta, ganin matar tatshi yasa ta karasowa dagudu tn cewa alhamdulillah, mama kintashi?inake miki ciwo kamo hannunta tai tace, babu inda yake min ciwo yata Numfashi tasauke ahankali tace, Masha Allah bari inkawo miki abinci, kamota tai tace"am ok kinji nasha tea yanxu, kusada ita tazaunarda sabha tce Allah yamiki albarka, Aunty tan kitchen don hada musu abincin dare, yanzu 4pm ta wuce. Yasu nanki yata, cikin dukarda kai tce *SABHA* wow nice name, smiling sabha tai, how old are ur tasakejin ammi na tambayar ta?17 but next month November zankai 18, tafada tana smiling Wow my daughter ashe kin girma, dan smiling tai"dai dai nan su uncle Usman suka shigo"dan waro ido ammi tai ganin sao'od, dan murza idon ta tai don tabbatar wa tabbas shitake gani harda abbas to yaushe yadawo tadai san bayanan. To waya gaya musu tananan?? dan karasowa sukai ganin fuskarta yay kalan mmki". durkusa wa yai gabanta, yace amminah.. yaushe kadawo shine tambayar datai mushi ammi dama inason surprising dinki nefa, shine nace zandawo baki saniba, ynzu daga airport muka wuto. Murmushi tai, tace ka kyauta Abbas da Usman ne suka gaisheta tarefa yimata yajiki, alhamdulillah ta amsa cikin fra'a, yata kigaida yayanki kinji, kunya taji Sosai, setake ganin bata kyauta dabata gaidasu tuniba Dan dago da idonta tai don gaidasu, karaf idonsu yafada cikin na juna, wanda shiya dagone donjin ammi tace mata yata, dammmmm kirjinsu ybuga atare Wanda basusn dalilin hakanba......✍️ *To su sao'od wannan bugun kirjin na miye, baridai inyi shiru🀐* *_Comment and share_* *#zarahh* πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€ *βœ“DR SAO'OD* πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€ Written by zarahh AA πŸ…ΏοΈ11&12 """"""""""""""Itace tai kokarin cire nata idanun, ganin ya kfeta da kaifaffun idanun ahi, tuni ya gano itace tadaga mai waya"ina wunin ku tafada ahankali Abbas ne ya amsa yana murmushi"dan dagowa tai don kanta akasa yake, ganitai yana aika mata wata uwar Harara donshi Gani yake girman Kai gareta, dan tsaki yaja ahankali wanda itace kawai taji, dabida akusa dashi take "Dan dagowa tai, haka kawai tasamu kanta da murguda mai baki, karaf a idonshi kallon zan maganinki yai mata, dan kara murgud a mai bakin tayi, wannan karon nuna kanshi yai alamar Niko??daga kai tai, ashe duk akan idon ammi ake wannan dramar" Murmushi tai kawai, Aunty tafito hannunta dauke da kayan motsa abinci Diresu tai kan sofa, Usman nne yace Bismillah abokaina, murmushi Abbas yai yace kai alham...tunkan yakarasa ammi tace,Oya kumuje muci dry Usman yai kadan yace yawwa,"ammi"sabida yaji haka su Abbas din suke cemata Cikin ranshi ko yana jinjina, miskilanci irinna sa'ood wanda tun gaisuwar dasukai a waje Duk tasowa sukai harshi uban gayyar, tankwashe kafa yai, Aunty ce ta kalli sabha data dan takure waje daya,"tace taso kiyi saving nasu"itako bakomai bane yasata natsuwa sedan batada ko Dankwali, gakuma uban kallon da waccen sarkin Miskilancin ke jifarta dashi, ahankali tatshi Dan karasowa tai ta tsugunna, tafara zubama wako, seda tazo kanshi, dan dagowa tai don itafa wlh batasan mezata samai ba, dama duk seda ta tambayi saura me za'a samusu?? Ganin haka yasa ammi cewa, zonan kizauna autata, dadi taji cikin sauri takoma kusada ammi ta zauna tana satar kallonshi"yana kallonta dan cije lebenshi yai"ya kwabe fuska ammi ni kumafa?duk kallonshi suke suna jinjina shagwabar shi, kato dashi, itako sakin baki tai tana kallonshi, ammi ce tace, karka ci kaji!abinci kowa yafara ci... Usman ne yace,oh my friend zomuci tare, hala shine autan ammi ko??yatambayi Abbas dry yai yace tab kannen shi uku biyu sunyi aure, dan waro ido sukayi har aunty Ita kanta sahba tai tunanin yanada aure wlh" amma dai shine autan maza still inji Abbas harara ya ballama Abbas yana hade rai tamau"don yaga abbas yana shirin sa waccen mara kunyar ta rainashiπŸ˜‚" Taredai yaci abinci da Usman, harsuka kammala nan, ammi takara fada musu yanda akayi, har sabha ta dauko ta; dan kallon sabha yai yaga bama shitake kallo ba, mtss yaja tsaki!lpy?cewar abbas, banza yamai Sundan yi fira sannan suka tashi zasu tafi, exchanging number sukayi, ammi da aunty;har harabar gidan suka rakosu. Ammi tace yata, zantafi laaa!kinga daughter ban amsa numbern kiba, murmushi tai tace bakin manta daniba, tafada tana zumbura baki, dry ammi tai tace"eyya sorry my daughter"sakamin numbern ki amsa tai tasa mata Sabida uncle yase mata waya, me shegen tsada zuwanta, kallon Usman tai tace dana yashe daughter zata zomin?? murmushi yai yace ammi, takusa tafiya fa!dan waro ido ammi tai tace school zata??a'a hutu tazo mana, kai dama ba'a nan takeba?"murmushi yai yace takusa tafiya, a kd take Dan kallon sabha tai tace daughter kizo kafin kitafi kinji? nidama uncle zaka tambaya min mom dinta, tabani ita tafada cikeda tsokana.. Dan kasa da kai Sabha tai, kobazaki ba autata, shiru tai tana murmushi, sao'od yace ammi kizo muje, Hararar shi tai, tace bazaniba"dan hararar sahba yai, itama hararar shi tai Abbas ne yamikawa sao'od key nashi yace, kai driving din"nise inje indauko motan ammi"ok amsa yai yashiga ya zauna Ammi tace yata, kindauke amatsayin uwa, daga mata kai Tai"kinga kinzama autata ko?don ko Hafsat autar ammi ta girma sabha To tafada tana murmushi, to zamu tafi"mungode mungode sosai da karamcinku garemu"auta Allah yamiki albarka don Allah kizo before kitafi kinji, inshallah." Shima sao'od godiya yama Usman da aunty ko kallon sabha beyiba, donshi beson raini, shiko Abbas dama driver yaje kaishi wurin motar ammi. Mota tashiga tana daga musu, hannu"sosai sabha take jin tashaku da ammi daga haduwar su yau, ciki suka koma uncle kuma yafita masjid Don lokacin sallah yakusa, suna shiga aunty tace gsky matar Nan akwai kirki sosai, wlh kuwa aunty don sena kejin kamar karta tafi Wai ashe dama tanada wani ciwo, inyatashi se kawai tafadi"inji aunty, wlh haka naji wannan dan nata yana fadawa dadyn Layla, wayyo but seta dena fita, wlh sunce bata fita yauma tsautsayine, Allah ybata lpy, ameen dai Daki sabha tashiga zama tai donba sallah zatai ba Layla da husna ne suka shigo, aunty zomuyi sallah"ni nayi sallah"kuje kuyo alwala ina zaune inga kun iya sallah, to Aunty, alwalar sukayo suna tada sallar harsuka idar" Kuma sun iya sallah babu lefi, husna ce tace aunty wannan kekkyawan dandan wannan matar ne??wa ye?tafda kamar bata ganeba nanko tagano watake nufi sarkin girman kai Layla ce tai karaf tace, wlh aunty nima naganshi me kyau, tafada tana murmushi, umh kawai tace, don baxata iya shirmen suba!haka sukaita surutunsu sukai shiru.. ********* Suna tafiya ammi tace, abiey na'am ammi, kaga yarinyar nan me kirki sosai, ga uncle din nata da matarshi duk masu kirki, dan tabe baki yai yace, sudai sunada kirki amma wannan yarinyar ina taga kirki "Tawani zauna kai ko dan kwali se uban shagwaba takeyi kamar wata yarinya, gashi kekuma sewani biye mata kike, nifa bawani yimin yarinyar tai ba, yafada irin I don't care dinnan" Kallo shi tai, tana mamkin aina take shagwabar itadai bata ganiba, dan murmushin manya tai tace, to Masha Allah niko tamin komai, tunda ta nunamin kulawa sanda babu wanda yai tunanin temakona Cewa yai ammi nifa wasa, nake"um inma gsk kake sedai kayi, don kantatafi ma zatazo gaidani,wai ammi wani gari take?kaduna mezakai mata da garin nasu "Dan jan gemunshi yai, yace ammi daga tambaya nifa wlh yarinyar gani nake kamar tacika rawar kai, ni rufemin baki, abbas yakira yace mishi shi haryama dauko matar yana gida" Basu wani dadeba suma suka, karaso ciki suka ahiga dan zama ammi tai, shikuma yaje yadau kayanshi a bot yai ciki, sallah yai kawai sega abbas yashiga yana cewa My friend kaga wata fine babe agidannan?wlh yarinyar tayi kyau sosa....mtwss yaji sao'od yajamai tsaki sannan yace kaidai Bakaji dadiba wlh wannan yarinyar meye abin kyau ajikinta, yarinya kamar aljana,hhhh wlh bakada ido banza kasamu kai ciki da ita, dan ubanka abbas bar dakinnan wlh bazan fitava aiba gidanka bane bare kace infita ko?amma daki nane ko?wlh bazan fitaba. ammi ce takirata lokacin wajen 9pm, tana zaune tana tunanin umminta wayanta yai kara, dagawa tai tana sallama, amsawa tai auta ykk laaa!ammina ya kika koma alhamdulillah,ina Auntyn ki tana daki to ki gaisheta Inshallah zataji, fira sukasha sosai kamar uwa da ya sannan sukai Sallama, ammi jitake kamar tafada mata abinda keranta, amma tanajin tsoro karta ki amincewa Tafiso tafara magana da abbu, se iyaye su shiga lamarin, don bataso aja lokaci me tsayi, dakin abbu taje, yana zaune yarike tsarbi... Tariga tafadawa abbu duk abinda yafaru, dayanda suka dauketa kamr uwa duka gidan, harta fada mishi abinda ke ranta, yace mata karfa ta takura yarinyar...........................✍️ _fans meye a cikin ran ammi??_ _*comment and*_ _*share*_ *#zarahh*πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€ *βœ“DR SAO'OD* πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€πŸ₯€ Written by zarahh AA πŸ…ΏοΈ13&14 """"""""""""""""Inshallah babu komai naga yarinyar tanada hankali!ga tausayi wlh har kuka take sanda, nafadi kamar tasanni"to Masha Allah tunda naga da gaske kike"nizanje gurin uncle din nata se muyi musu magana, inyaso seya kaimu muhadu da mahaifinta; to shikenan Allah yazaba mana abinda yafi, alkhairi,ameen abbu yafada, nan suka fara fira akan yanda zasu bullowa abin, ammi ce tace gsky zanfi kowa farinciki idan hakan takasance. Yana dakinshi, yana duba ayyukan da yai, da wanda yefara, in Allah yakaimu gobe;don gobe akwai babban aikin dazeyi, kuma yanada hadari sosai Don gobenne zefara aikin ahida abbas zasuyi, sabida aikin yatafi don kawai ya koyo, alhamdulillah kuma yanajin ze'iya babu wata matsala, tunda dama tun yanacan yake koyawa Abbas duk abinda ya koya shima Sosai ya dade yana kara, binciken aikin don beson asamu matsala ko kadan, abbas yakira yana kara, fahimtar dashi wasu abubuwan, har wajen 2am bacci yakeji, amma baze iya bacci ba yakai, wannan lokacin begaida Maha liccinshi ba. toilet yaje yai alwala, fitowa yai yasaka jallabiya, milk color me matukar kyau, sallaya yashim fida"yatada sallah sosai yake".jero salloli wanda yake fadawa Allah damuwar sa, a kowani sujjada dazeyi Sosai yake addu'a, har wajen 4am wanda, ankira sallar farko lokacin, dan kwanciya yai don yadan rintsa, baccine yai gaba dashi wanda, seda yakusa makara... masallaci yaje yai sallah, yadade a masallacin yana azkar da addu'oi, seda rana tadan fito Sannan yafito yanufa part din ammi, itama tana kan sallaya, hannunta rikeda tsarbi, fadada fara'arta tai tace".ah son"na'am"ina kwana yafada yana zama kusada ita suna shafa addu'ar tare, lpy qlw, ya gajiyar tafiya, alhamdulillah ammi, ya karfin jikin??ah naji sauki, nida bama fita nakeba, jiyanma rabon alkhairi ne yafitar dani; dan waro ido yai yace ammi, wani irin alkhairi? Alkhairi mana tunda nahadu da, wa'inda suke shirin kawo karshen damuwarmu, still mamakin ammi yake, yace ammi wata dumuwa Kuma??yafada cikeda mamaki me ammi take nufi, um kaga tashi katafi bakace yau da wuri zaka fitaba?eh aise wajen 8:30 haka,oh amma dai tashi kaje, bari inkira daughter na. Inji yatake, wacce daughter kuma ammi, bayan yanzu naga auta tana, breakfast zata school, bakasan nayi sabuwar auta ba kenan ko? Mhh nibansani ba, aizaka sani very soon karka damu, "um nikam ammi wlh yau duk magana a cukurkude kikeyinta" dry tai tana kissa wan abu aranta gameda dan nata. Mikon wayata, yana dauka ana kiran waya, daughter yaga ansa.....dan tabe baki yai shiko besan wace wannan ba, mikon mana ana kira, mika mata yai, tna ganin sabha ke kiranta, tai murmushi, karawa tai akunne Sallamar sabha, da'alama yanzu tatshi bacci, amsawa tai fuskarta na fitarda wani murmushi, cikeda girmamawa ta gaidata nan ammi tafara janta da fira har tadan sake itama. "Tashi yai don besan dawa ammi take wayaba"don wlh shi ya mantada wata sabha, jin ammi nacewa yaushe zakizo yasashi,tunani kodai wannan mara kunyar yarinyar ce?itakam sabha daurewa kawai take don bakadan mararta ke ciwoba, tun jiya amma jitai kawai tanason gaida ammi, dama tana tashi umminta ta kira, sallama takewa ammi amma setaji tana cewa, ga yayanki kugaisa." "Dam dam kirjinta ya buga", Allah yasa bawannan mara dariyar ammi take nufiba, take fada aranta, jin tayi shiru yasa ammi mikawa sao'od wayar shiko harga Allah, besan wayeba, amsa yai yana sallama, wani irin tsoron shi taji, yashigeta, ahankali tace ina...kwa...na tafada ararrabe. Mhhh yasauke numfashi wanda besan yayi hakanba, lpy waye yafada kamar begane, me magana ba?nanko tunda tai magana yagane itace, am...am..a.m tana in ina takasa magana, dama ga mararta tana barazanar tarwa tsewa don ciwo, kawai seta samai kuka. Don wlh batasan mezata ce mishiba, "ya Salam" yafada yana cewa ammi,nifa bansan waye ke maganaba, mika mata wayar yayi, tanasawa akunne taji sheshshekar kukanta, rudewa ammi tai tana tambayar ta, lpy?? Dan shiru tai, Aunty ce tashigo tana cewa, Aunty sabha husna tace bakida lpy??kara fashewa tai da kuka tana cewa Aunty marana kaman ze fashe wlh cikin muryar kuka take maganar, eyya sorry bari muje hospital kinji?ammi dake rikeda waya tace ya Allah! daughter shine kike kuka, bama auntyn taki wayan mika mata tai, waye inji aunty? Jin sallamar ammi yasa Aunty yin murmushi tace, laaa ammi kece, takewa shagwaba haka?to ai batada lpy ne, kingane ki kaita hospital din sao'od kinji, seya dubata.. Wani uban waro ido tai, jin an ambaci sao'od ne ze dubata, tab yanda take kukan allura aise ya rainata, jin Aunty nacewa akwai doctor zezo yadubata, ammi ce tace pls kikawota kinji bari ingaya mishi, alama takewa Aunty da tace a'a, amma setaji tana cewa,ok gamunan zuwa, ammi ce tace, nima bari inje hospital din dama akwai wa'inda nakeson dubawa bansamu, najeba semu hadu kawai, tom shikenan cewar aunty, sallama sukai, kamar taita ihu haka takeji "Ita wlh ko tuna fuskarshi tai tsorone ke kamata", bare harya dubata kuma tasan dole yasan Period take, duk aranta take wannan tunanin tana turo baki, aunty tace sekije kiyi wanka kixo muje, aunty don Allah karmuje ninamaji sauki!hhh wlh kirata kifada mata bazaki zoba kinajin tsoron danta" "Dan waro ido tai, tace tsoron wa nakeji aunty, dan nata mana, Allah ya yauta wlh wannan miye abin tsoro ajikinshi, dry sosai aunty keyi, tace ke za'a tambaya keda kikejin tsoron shi ai, nifa bana jin tsoron shi aunty, tafada tana shigewa toilet din, murmushi kawai aunty tayi tajuya tafita." Itama daki daje tashirya, cikin wani danyen less me matukar kyau da tsada, dama takira uncle tafada mishi, yace suje tunda, su suka bukata, amma shi beson amai kallon meson abin duniya donta fada mishi yanda, ammi taita cewa suje din, shiyasa ya yarda. Dakin sabha takoma, taganta tana sa kaya, tana kunkuni ciki ciki, ita batason zuwa, um kinyi kingama wlh,"aunty menace kuma yanzu! dariya tayi tace ninace kince wani abu?"dan turo Karamin bakinta tai tace wlh, dazakiji aunty muje wani hospital din, um sekuma kiyi, tafada tana cewa inajiranki inkingama, to, sosai tai kyau cikin doguwar rigar datasa ta abaya, baka da veil, turaruka tabaza masu shegen kamshi. "Fitowa tayi taga aunty najiranta" wow Aunty sabha kinganki kuwa? Dama soda yawa Aunty take cewa sabha sabida su Layla haka suke cemata aunty sabha shiyasa itama tasaba,fitowa sukai suna rufe kofar." Drivern yaje kaisu Layla school, kuma da dan nisa shiyasa, bedawo ba.....aunty ce zatai driving din sabida ta iya mota, ahiga sukayi,"tace aunty kinsan hospital dinner?"lallai waye a abuja besan dr sao'od hospital ba?aiko sedai bako, bakinta taja tai shiru, suna tafiya babu me magana, ita duk damuwarta wannan dan iyayin mutumin ne batason gani wlh, Aunty tace Auntyn su, naga kinyi shiru

Chapter 2 of 13