ba".
"My luv yau kuma Auntyn tawa ake xagi a gabana"Kamal ya fada.
"fin zagima My luv,komai zan iya yi a kanta,tunda bata da tausayi bata da kuma mai fada mata ta ji,a kullun ina takaici da bakin cikin kasancewarta wani bangare a cikin rayuwarka,da ina da yarda zanyi to tabbas zan kankare hakan na raba duk wani alaka a tsakaninku tunda kaima bana da tabbas din ba taudararka zata yi ba,kai nifa ko menene nawa na gane yana da alaka da wannan butulalliyar matar da tayi silar tarwatsewar ahalina wallahi wallahi bazanyi jinkiri wurin rabuwa da shi ba,any way na manta ban fada maka cewar a yanzu Nihla matar Yaya Zafar bace".
Dam dam haka zuciyar kamal ta bada sauti,tuni gumi ya gama rifeshi ga wani irin sanyi dake ratsa jikinsa yace"My luv me nake ji hakan yana fitowa daga bakinki❓wanne irin aure kuma tsakanin Zafar da Nihla❓a yaushe aka yi shi❓kina nufin ko nine nake da alaka da Aunty zaki iya rabuwa da ni❓"kamal ya jerowa Miemie da wadan nan tambayoyin a lokaci daya ya kuma tsareta da idanuwansa da tuni suka gama fita a hayyacinsu,kunnuwansa suka kara tsayi da budewa suna neman ansa kota halin yaya.
Murmushi Miemie tayi tare da cewa"aure da kasan anayi mana,to shine a tsakanin su,da Allah ya rabata da Irfan sai ya bata Namiji adali wanda yasan ciwanta wato Yaya Zafar.Kuma da kake hada kanka da ita dan Allah kama daina,kai ba maciyi amana bane,ba kuma zaka taba kasancewa irinta ba karma ka batamun rai".
Jiki kam na Kamal tuni ya gama sanyi da daskarewa kwakwaran motsima da kyar yake iya aikata shi lallai allura zata tono garma kenan! akwai daukar dala ba gammo kenan sai dai ko da a wasa bazai iya daukar rashin Miemie a tare da shi ba,dan itace rayuwarsa kuma bugun numfashinsa rayuwarsa ma fansa ce ga tata.
Tafa hannu Miemie tayi akan fuskar Kamal tace "ya ya dai❓".
"babu komai,kije gida zan kiraki"be jira ansarta ba ya tashi yabar gidan,a guje yaja motarsa kamar wanda zai tashi sama .Da kallo Miemie ta bishi kafin ta wuce cikin gida tana jin yau jin kanta take kamar wata sarauniya.
Ko daidaita parking Kamal beyi ba ya fito yabar motar a kofar gida da key a jiki ya shiga gidan su Nihla garin sauri har hadawa yake da gudu gudu.Tsakiyar parlon ya yi wa kansa masauki.
A tsorace Aunty da Irfan suka tashi tare da hada baki wurin tambayar ko lafiya.Ruwan sanyi Kamal ya dauka tare da shararawa kansa daga tsaye kafin yace"lallai akwai tashin hankali da matukar damuwa,ina mai bakin cikin sanar da ke cewa Zafar ya Auri Nihla".
Dib haka jin Irfan ya dauke kamar wani gaula haka ya soma bin Kamal da kallo a matukar tsawace yace"karya kake,hakan bazai taba yiwuwa ba,wannan wacce irin zance ne marar kan gado,yarinyar dake asibiti kwance❓".
Ragab haka Aunty ta fada akan kujera tana cewa"Kamal anya ba wani abu kasha ba❓".
"tunda kike da ni kin taba ganin nasha wani abun maye❓maganar gaskiya nake gaya maki Zafar ya auri Nihla".
Wata irin dariya Aunty ya saki tare da mikewa a hassale tace"lallai dole Zafar zai mutu ko da lokacin mutuwarsa beyiba,tabbas idan hakan ta kasance aikin da nayi tsawon shekaru zai iya ruguza shi a yan kwanaki,tabbas shi zai mutu kai idan ya kama har Nihlan ma ta mutu,dole ka kashe su Kamal".
Wani irin zabura Irfan ya yi kamar wanda ciwan hauka ya taba yace"nevee babu jaddawalin kisa a tsarin nan,kina nufin zaki iya kashe Nihla❓".
"Ko kadan banso hakan ba,amma ya zanyi tunda kaddara ta tunzura ni❓"Aunty ta fada.
Kamar wani sakarai haka Kamal kebin Aunty da kallo,tsab kalaman Miemie ke masa yawo da ansa kuwwa a kai,glass cup din hannunsa ya yi wurgi dashi tare da sakin wata kara yace"....
*Allah ka gafartawa iyayen mu kayi mana kyakyawan karshe*
Jorderh✍🏻
[3/3, 21:53] Maryam Jordan: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*FARAUTAR FARIN CIKI*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇
```By``` ```Maryam``` ```ismail``` ````Majidadi```
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*MARUBUCIYAR*
*SANADIN GATA*
*YAUDARA KO BUTULCI*
*DALILIN SO*
*SO DAYA*
*ASALINA*
*ADDININA*
*SHI NE AJALINA*
*RUHIN FANSA 1&3*
*HANAN* paid book
*ABU BILAL* Paid book
*FARAUTAR FARIN CIKI* ✍🏻🤸🏻♀️
84
"kina tunanin zan iya sadaukar da soyayyata dan biyan bukatanki ne❓,meyasa zan kashe Yayan wacce nake so❓ni da ke da kowa kuma munsan yarda take son shi❓sam hakan bazai taba yiwuwa ba Nafisa kidai canza abunyi".Kamal ya fada.
"kamal me yake damunka ne❓har yaushe zaka zabi soyayya akan rayuwarka❓tunda ka riga ka shiga lamarin ya zamar maka dole kamun biyayya kamun kuma abunda nake so ,idan kuma har kayi wasa a kan hakan har ita Miemien da kake takama da ita ina mai tabbatar maka ba zata tsira ba".
Tas tas haka kike jin Kamal ya dauke Aunty da tagwayen maruka har biyu,da sauri Irfan ya shiga tsakiyarsu tare da cewa"dan Allah ku daina wannan fadan,ta hakan ku gaya mun ta ina zaku samu mafita❓rabuwar kai bazai taba kawo masalaha ba".
"ka mare ni❓wallahi ina mai tabbatar maka sai kayi dana sanin marin nan da kayi,tabbas marin nan shine silar rabuwarka d wannan yarinyar da aka haifa a tafin hannuna amma ka wulakanta ni saboda ita"Aunty ta fada.
Hade fuska Kamal ya yi tare da cewa"muddun sunan Miemie bai fita a bakinki ba to ina mai tabbatar maki ke zaki fara yin dana sa ni a rayuwarki,wanda nasan sai kinyi din ma,ki sa ni duk wani iya shege da iskanci da kike nema gidan shi ki ka zo,bazanyi jinkiri ko daukar lokaci ba wurin yin maganinki ki tuna wannan"be jira cewarsu ba ya yi gaba abunsa.
Daura hannu a ka Aunty ta yi tare da koma sharab akan chair ta fada tana fadin"innalillahi tabbas rabuwa da Kamal kamar wani tonan asiri ne na rayuwata".
"kin aikata wa ni abun ne da baki so kowa ya sa ni❓"Irfan ya tambaya tare da zuba mata idanuwansa wanda tuni sun gama canza kala dauriya ce kawai yake yi.
"a'um dama ba ga dukiyar dana kwasa ba nan na baka,shi ne nake gudun tonuwar hakan".Aunty ta fada a daburburce.
Gyada kai kawai Irfan ya yi kafin ya fita daga parlon.Tafiya yake amma kamar wanda bashi da lakka ,kwata-kwata be ga ne gabas bare yamma ko kadan be san wacce duniya yake ba,kamar wani zautacce haka yake tafiya,hannunsa ya daura a kan kumatunsa tuni yaji damshin hawaye ,gyada kai kawi ya yi yana tunanin iya tsawon shekarun daya dauka beyi kuka ba,lallai dara taci gida,yau wani aikin ya juye da farin cikin rayuwarsa,tabbas ya dauki tsawon lokaci ya na farautar farin cikinsa amma yau rana daya kab komai ya rushe duk danadin da ya yi akan hakan amma ya tashi a tutar ba bu,lallai Al-amarin Allah sai kallo,innalillahi wa'inna ilaihir raju'un sune kalaman dake fitowa daga bakinsa,hakan ya yi daidai da faduwa akan gwaiwowinsa da ya yi ya fashe da wa ni irin matsanan cin kuka mai matukar cin rai da kunci.
A hankali take taka kafarta tana bin bayan Zafar tsab ta warke ras sai dai rashin kwarin jiki a haka har suka shiga mota suka bar harabar asibitin dan kishin gidawa ta yi tare da lumshe idonta,tsayawar da motar ta yi yasa ta dago lumsassun dara-daran idanuwanta ta zuba su a cikin in da suke,wani irin zabura ta yi ta mike sosai a motar tana rau rau da ido kamar zata fasa ihu cikin rawan murya tace"Ya..ya..yaya meyasa ka..ka..kawo ni nan❓ka mayar da..da ni gida".
Ko kallonta be yi ba yace"nan ne gidanku da ga yanzu dan haka ki fito bana son shirme".
Kara rudewa ta yi jin ya ambaci nan ne gidan su,a tsorace ta saka kafarta da sauri ta fito ta kama rigarshi daga baya ta rike kamar wanda ya yi mata sata,kyafta ido kawai take daka ganta kamar an tsoma kaza a ruwan zafi.
"ki sa ke ni mana".Saurin girgiza kai ta yi ta kara boyewa a bayansa tace"Dan Allah ka mayar da ni gida,wurin Aunty zan je".
Kamar wanda aka safkarwa da mutuwa haka ya hade fuska yace"idan kika karw kira mun wannan sunan a gidan nan sai na sassaba maki,oya wuce muje".
Make kafada ta yi a dole ya yi gaba ta bisa baya tana rike da shi har cikin parlon.Kuuuuu haka cikinta ya bada sauti kamar zata saki zawo a wurin jin muryar Hajiya Kaka a parlon afkawa ta yi bayan Zafar ta rungumesa da karfi tuni kyarma ta kace mata ko kadan ta kasa lekowa ta kalli parlon,cak Zafar ya tsaya jin an cukuikuye shi,dariya Ammi ta yi tace"a'a Malan Muhammad a karaso mana".
Shafa kai ya yi kafin yace"taya zan karaso bayan ta mun daurin goro?"
Nokews suka yi kowa a dariya,kamar daga sama haka Muryar kaka ta karade parlon tana fadin"Maryama zo nan kinji".
Raba ido Nihla ta fara yi,janye jikinsa Zafar ya yi kafin ya juyo yaja hannunta,suna tafiya a hankali tana tsaitsayawa a baya,gaban Kaka Zafar ya tura Nihla,kamar wacce tawa sarki karya haka ta dukar da kai tare da kama jikinta jira take a ce ar ta saka gudu.
Kallon yarda take yi ne yasa Miemie da Ramadan sakin dariya ,hararar da Zafar ya jefa masu ne yasa sukayi shiru ba shiri.
Kamar da ga sama ba zato ba tsammata sai dai aka ga Nihla a jikin Kaka ta rungumeta,fuskarta fal farin ciki ga hawaye na bin gefan idonta.
Sosai kowa ya cika da mamakin hakan,dan ko da wasa babu wanda ya taba kawo wa ransa hakan zata faru ko Kaka zata karbi Nihla ta sauki haka .
Basu gama karewa da Mamaki ba sai da kaka ta dago Nihla ta tarbi fuskarta da hannu bibbiyu ta fara magana"ban taba tunanin kara sake dawowarki a gidan nan ba,sai gashi da kika tashi dawo wa ba kin dawo a matsayin jika ba kawai kin dawo harda matsayin da nake da buri a kanshi,lallai kina da sa'a daya kasance kin kama zuciyar jika mafi soyuwa a gare ni,duk wani farin cikin mu yana tattare da nashi,barka da zuwa Maryama Zafar Al-ameen sirikar gidan nan ta farko".
Dib haka jin Nihla ya dauke ko kadan tama kasa fahimtar menene kalmar sirika ke nufi❓kamar wata doluwa haka take bin Hajiya Kaka da kallo,ganin yananyin da take yasa Ammi zuwa ta kamata tare da cewa"muje kiyi wanka ki huta kinsan yanzu kika dawo da ga asibiti".Bin Ammi kawai take duk abunda take tana daga mata kai ne kawai amma sam bata ko fahimta kwatakwata ta kasa gane tareyen da Hajiya kaka tayi mata,a haka ta samu tayi wanka tea kawai tasha kasa kara saka wani abun a bakinta ta yi gaba daya zuciyarta a cushe take bata gane ma duniyar da take,kamar daga sama a jikin window din da take ta hango Irfan na shigowa cikin gidan taku yake yi irin na cikkakun maza,ganin yana doso kasan window d take yasa ta dukar da kanta dan taga shin wai da gaske nan yake tahowa❓lallai kam Zafar ta ga ni tsaye ya zuba hannuwansa cikin aljihun wandonsa a hankali yake taunar lips dinsa tare da tsotsa kamar zai huda.Baya tayi zata fadi sai tayi saurin dafa bangon da take ji,ganin sunyi musaba yasa ta saurara dan jin abunda suke fada.
"kamar ko yaushe Zafar da nake gaya maka bana da niyar futar da Nihla,Nihla ita ce rayuwata,itace farin cikina,zan iya sadaukar da rayuwata dominta,amma yau naji wani batu wai Nihla ta kasance mata a gareka,tabbas bazance nayi bakin ciki ba sai dai zance nayi farin ciki da hakan dan tabbas nasan Nihla zata samu kula,zata samu kuma wanda zai iya sadaukar da komai nasa a kanta wanan shine burina tun asali ko ni idan zan gagara kula da nihla zanyi fata allah ya turo mata da jagora wanda zan jibanci maraicinta alhmdllh addu'ata kuma ta ansu".
Hannu Zafar ya daga tare da tsayar da Irfan yace"duk menene na wannan maganganun❓kana son farin cikinta kuma ka zabi cutar da ita❓kaine jigon bakin ciki da kuncin rayuwar Nihla a yanzu bata da matsalan daya wuce kai Irfan ya kamata ka gane haka,dama dan ka gaya mun wannan maganganun akan Matata yasa kazo nan❓,to thank u find a way just leave".
Wasu hawayen bakin ciki ne suka zubowa Irfan yace"komai zaka gaya mun bazan taba jin haushi ko kunci a kai ba,nasan duk kallon da kowa kemun kenan,amma ina so na fada maka har gobe har jibi ba za'a tabayin namijin da zaiwa Nihla soyayyar da nake mata ba,sai dai na yarda Allah bai halicce mu dan mu kasance tare ba,ni ban zabi na kuntatawa Nihla ba sai dai rayuwa ce ta zo da haka,nayi hakan ne na sadaukar da soyayyata dan na ceto Nihla daga tarkon da take niyar fadawa na kishiyar uwa,na sadaukar da farin cikinmu ne dan na samawa Nihla rayuwa mai kyau a gaba,nayi duk wannan ne dan gujewa rudin zuciyar Nafisa da take kokarin mallakar dukiyar Nihla kota halin yaya,na anshi soyayyar Nafisa ne badan ina sonta ba sai dai amfanin masoyiyata wanda nasan da naki hakan tabbas wani labari ake yi ba wannan ba"jikka ce Irfan ya mikawa Zafar yaci gaba da cewa"ka ansa wannan duk wani dukiyar Nihla ne da Nafisa ta bani akan na adana mu yudu da shi,ni kuma bazan iya cin hakkin wani bawa a duniyar nan ba,tabbas hakan ya yi mun amfani ko da zan kasance cikin bakin ciki amma nasan Nihla zata rayu cikin farin ciki,and shawara daya ka yi kokari ko ta halin Ya ya ka kubutar da Miemie daga soyayya da Kamal"yana gama fadan haka ya juya zai tafi,hannunsa Zafar ya rike tare da cewa"kana nufin kayi duk wannan ne dan kubutar da nihla❓"
Murmushi kawai Irfan ya yi tare da gyada kai yace"ni zan wuce".
"hakika baki da duk wani abu da zan malllaka maka yayi kankanta wajen gode maka ,kai namijin kirki ne,wanda irinku ko wacce mace zata bukata ta samu,tabbas kowa ya kalleka da mumunar fuska sai dai hakan bai gushe ba face sai da alkhairanka suka bayyana gare mu,kayi hakuri da nesanta ka da farin cikinka da na yi,Abba ya daura aurena da Nihla ne a ranar da zai bar duniya badan haka ba babu abunda zai hanani sadaukar maka da soyayyata dana raina na jima ina jinta tun kallon farko dana dauki Nihla a ranar da aka haifeta,na rayu ne akan soyayyarta kuma soyayyarta ita ke bani kwarin gwaiwa da jarumta da kara son kasancewa tare da ita".
"Wannan bazai taba zama da matsala ba Dr,tabbas na cika da farin ciki da kai ka auri Nihla nasan ko bayan raina kai Garkuwanta ne"Irfan ya fada fuskarsa cike da fara'a Juyawar da zaiyi idanuwansa suka sarke a cikin na Aunty wacce take tsaye bayan Irfan ta kuma gama jin duk wani batu da suka tattauna,wani irin kuka ne ya kubce mata ta yi waje a guje .Share guntun hawayen da suka zubo masa ya yi kafin ya yiwa Zafar sallama ya fice faga gidan shima.
Kamar watq statue haka take sulalewa zuwa kasa,ko kadan bata iya banbance tanayin da take ciki,wani irin kuka mai cin rai ta saki tare da kwala kiran sunan Irfan da iya karfinta,a guje ta mike zata yi waje ,Daddy ne ya yi saurin tare kofar da take niyar fita,ko ina a jikinta kyarma ya ke bakinta rawa take ta kasa furta komai face nuna hanya da take yi.A haka Zafar ya shigo dakin yana karewa Daddy da Nihla kallo.
*Allah ka gafartawa iyayenmu kayi mana kyakyawan karshe*
Jorderh✍🏻
[3/3, 21:53] Maryam Jordan: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*FARAUTAR FARIN CIKI*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇
```By``` ```Maryam``` ```ismail``` ````Majidadi```
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*MARUBUCIYAR*
*SANADIN GATA*
*YAUDARA KO BUTULCI*
*DALILIN SO*
*SO DAYA*
*ASALINA*
*ADDININA*
*SHI NE AJALINA*
*RUHIN FANSA 1&3*
*HANAN* paid book
*ABU BILAL* Paid book
*TABON 'DA NAMIJI*
*FARAUTAR FARIN CIKI* ✍🏻🤸🏻♀️
END END END
Ido cike da hawaye Nihla ke kallon Zafar kamar idanuwanta zasu fado,kai ya gyada mata da karfi ta fada kirjinsa tana fashewa da kuka tare da cewa"Yaya dan Allah ina so na gan shi,ina so nayi magana da Yaya Irfan".Kuka ne yaci karfinta bubbuga bayanta yake yi tare da alamar lallashi.Kamota Daddy ya yi tare da zaunar da ita,kallonta ya yi "Nihla kiyi hakuri babu wanda yasan da hakan,shiyasa Abbanki ya bawa Zafar aurenki yana kuma ganin babu wanda zai iya kula da ke sama yarda Zafar zai iya kula da ke,kiyi hakuri ki yi biyayya akan kaddarar data sameki."Daddy ya kare maganar yana kallonta.
Kasa tayi da kanta shiru tayi hawaye na zuba a fuskarta cikin karfin hali tace"Daddy i'm not complaining,Allah yasa haka shine alkhairi a rayuwata,ni hakw tawa kaddarar tazo amma Daddy dan Allah ka ce masa ya barni nayi magana da Yaya Irfan ko sau daya ne".
Cike da tausayinta Daddy yace"Maryama ki daina wannan kukan zakiyi magana da Irfan insha Allah,bana so ciwanki ya kuma tashi saboda wannan wahalan da ki ke yi,har gida Irfan zai zo ya sameki nayi maki alkawari".
Kasa da kai Zafar ya yi kafin ya kalli Ramadan da shigowarsa kenan yace"ka dauki kuje da Nihla dakin Ammi,zamuyi magana ne".
Da kallo kawai Nihla ke binsa rashin gane wacce magana za'ayi yasa ta mike tana yin gaba Ramadan na bin bayanta.
Daddy,Ammi,Kaka kowa hankalinsa ya mayar ga maganar da Zafar keyi.
Sake da baki haka Daddy ke bin Zafar da kallo gaba daya he's spechless wani irin rudu da tashin hankali ne suka tarar masa gaba daya,cikin son tabbatarawa da kansa abunda yaji yace"kana nufin Kamal ya bawa Nafisa gubar da Alhaji Umar yaci❓".
"kwarai kuwa Daddy,mutuwar Abba ba hakanan tazo kai tsaye ba,hakan ya faru ne ta dalilin kashe sa da akayi,ina da rahoto na asibiti,sannan kuma Abba da kansa ya fada mun muguntar da Aunty ta ke shirin yi akan dukiyar Nihla,ya gane hakan ne bayan wata rana daya dawo daukar wasu files a nan ya sameta tana waya da Kamal sai ya wayance kamar beji komai ba wannan dalilin ne yasa ya daura aurena da Nihla"kallonsa ya mayar ga Hajiya kaka yace"kinata zargin Abba akan satar hakudan kudade ga takardu ki duba Kamal da Nafisa sune wanda suka saci kudin a office din Abba,wanda dukanku kusan yarda Kamal yake amintacce a wurin Abba".
innalillahi wa'inna ilaihir raju'un shi ne abunda Kaka ke maimaita ta kuma fashe da kuka hannu ta daura a kai cikin muryar kuka tace"yau naga abunda ya ishe ni,ni da kaina na auro wa 'Dana bala'in daya tarwatsa mun kan zuri'a Allah bazai bar Nafisa ba,ga Umar harya mutu banje na ganshi na roki gafarar shi ba,innalillahi wa'ina ilaihir raju'un."kuka rurus haka Kaka ta saka kamar zata shide.
Riketa Ammi ta yi duk da ita ma bata da bakin magana kuka kawai take yi,Daddy kam hularsa ya cire yana yin fita da ita,tuni zufa ta gama rufe shi ta ko ina,bai taba tunanin rashin Imanin Nafisa ya kai haka ba duk da dama yasan rashin kirkinta da kuma irin satar da takeyiwa Abba.
Kamar wacce aka ingizo haka Miemie ta shigo dakin,fuskarta caba caba da hawaye kamar wata zautacciya haka yake binsu da kallo ya yin da hawaye ya kasa tsayawa a idanuwanta.Wani irin zaro ido Zafar ya yi cikin dakewa yace"ke me ki ke yi a nan❓."
Cikin muryar kuka take magana"shin Yaya bai kamata na san halin da Kamal ke ciki ba ne❓,Kamal shine rayuwata shine farin cikina kowa cikin ku yasan haka,na rayi da son shi na bude idona da son shi dan mi yasa zaku zabi boyemun hakan❓."
Kasa karasa magana ta yi tuni kyarma ta kwace mata juyawa tayi tabar dakin tana gudu ,kamar wacce aka jefa haka ta harde steps tayi kasa kafin ta karasa kasa taji ta fada jikin mutun ,duk da idanuwanta na rufe hancinta da bugawar zuciyarta basu yi kasa a gwaiwa ba wajen sanar mata da zabin zuciyarta ne wa to kamal,a hankali ta soma bude idanuwanta da suka soma sauya launi,da duk iya karfinta daya rage mata tasa wurin ture Kamal ta mike da sauri,a tsawace take fadin" meya kawo ka wurina❓ko akwai wani daya rage zaka cutar a nan❓ni ko iyayena❓yayyena ko kuwa Nihla❓,nayi dana sanin saninka a rayuwata kamal,na kasa yarda ni ce naso makashi ,mayaudari,maciyi amana,innalillahi wa'inna ilaihir raju'un"karar kukan Miemie yasa kowa fitowa,dib haka jin Nihla ya dauke na wani lokaci janye dogon riganta dake jan kasa tayi tare da soma safkowa daga stairs a guje ko ganin kirki bata yi,sai da ta iso tsakiyar parlon ta tsaya tana haki kamar wata zautacciya haka take bin Miemie da kallo tana bakinta na rawa take fadin"Mie..Mie Kamal da A...aunty suka kashe ...Ab...Abba❓".
"Kwarai da gaske,Kamal shi ne wanda ya bada gubar da aka ciyar da Abba naji hakan da kunnena,nayi danasanin rayuwata Nihla,a kullun rayuwarki nake tausayi ban sa ni ba ashe tawa ma abun tausayi ce,wanda na bawa yarda da duk soyayyata shi ne wanda ya zama sanadiyar tarwatsewar ahalina"Miemie ke fada cikin kuka.
"ya isa,ya isa haka"Kamal ya fada da karfi,cikin daga murya da tsananin fushi yaci gaba da cewa"nayi hakan ne duk dan saboda ke ne,nayi hakan ne dan na baki rayuwa mai kyau,bani da kowa sai ke soyayyarki itace ta mayar da ni mutun,idan da ban biyewa Nafisa ba taya zan sameki ❓bayan tana ikirarin idan na juya mata baya zata saka a koreni aiki,Aysha ta ina zan ganki har ki soni❓,na rokeki duk abunda zaki mun kimun amma karka gujeni dan Allah"ya kare maganar nasa tare da hada hannuwa wuri daya,for the first time da hawaye ya fara gangarowa akan fuskar Kamal.
Ragab haka suka ji karar faduwa Nihla ta fadi akan gwaiwowinta tana jujuya kai da sakin wani irin kuka mai kara,da sasasarfa Zafar ya yo kasa shima ya tsugunna akan kafarsa,janyo Nihla ya yi yana lallashinta,a jikinsa ta fada tana wani irin kuka mai cin rai da tsananin kuna,ji takeyi zuciyarta ta yi mata nauyi kamar zata fasa kirjinta ta fito,lallai wani kukan da hawaye salama ne,a wannan lokacin ne ta nemi ruwan hawaye ta rasa lallai ashe bayan duk kuncin da tayi a baya salama ne akan na yau da take jin kanta dama mutuwa tayi ta huta,lallai Aunty da kamal sun kasance wani jigo na turata ga kusantar bakin cikinta da kewarta.'Dago idonta tayi tana kallon Aunty dake shigowa parlon da iya karfin tana fadin"ina Nihlan da Irfan suke❓lallai tunda yaci amanata yau tashi tazo karshe".
Janye jiki Nihla tayi daga jikin Zafar ta mike,saurin riketa ya yi yana girgixa mata kai,alama ta yi masa daya saketa,cikin takun karfin hali ta isa gaban Aunty,kallan kallo sukeyi kafin Aunty tace"saboda ke,saboda ke yau na gagara cika burin da nake dauke da shi na tsawan shekaru,kinsa Irfan ya guje ni ya kuma yaudare ni,abunda wani bai taba yimun ba,naso har na gama abunda nake na tafi na barki ba tare dana taba lafiyar jikinki ba amma kinki bani damar hakan,kada ki zarge ni a duk abunda xai faru da ke Nihla,komai laifinki ne".
Cikin muryar kuka Nihla tace"yanzu duk abunda kika aikatamun yafi ace raina kika dauka da ki rabani d mahaifina,shin kinsan menene shi a gareni? shine duniyata,alfaharina da duk wani abu da zanyi takama dashi,na miki kallon Uwa ban taba jin daidai da rana tsaya zan iya saba maki ba duk da Irfan da kika dauke a wajena ,ashe kedin me fuska biyu ce,kedin rayuwata kike nema kin kuma ci nasarar rabani da duk wani farin cikina,sai dai ina mai farin cikin sanar da ke cewa babu wani da zai kaiki kotu ko wani wuri kara,hakkin ran salihin bawa kadai ya isa ya hanaki jin dadin duniya,Allah kadai xai iya maki sakayya akan abunda kika aikata,duk wata kotun duniya tayi kadan wajen daukar fansan ran mahaifina,dukiya kike so❓dukiya ta saka ki yin duk wannan❓ki dauki komai kije dashi ,da nasan wannan ne burinki wlh raina da duk wata dukiyar dake garemu fansa ce ga ran mahaifina"kuka ne mai tsananin karfi ya kwacewa Nihla,bata ankara ba taji an fizgeta da karfi gefe,feee haka garin maganin ya soma bin iska wanda ke hannun Aunty da taso zubawa Nihla.Kamar statue haka Aunty ta tsaya tana kallon Irfan daya zanje Nihla,kwararo ido tayi kamar mayya sabon kamu kafin ta fasa kara da karfi tace"ka kuwa san abunda kayi mun Irfan❓Malan ya gaya mani ma damar wannan maganin behau jikin Nihla ba to tabbas ni zan haukace ba ita ba"
Kowa kallon Aunty yake yana jinjina rashin imani irin nata,"bakin halinki da mugun abunki kab kanki zai kare badai kan jikata ba,baka mai bakar aniya wacce bata san abun arziki ba,tsintacciyar mage Allah wadaran halinki Nafisa ,Allah shi zai mana sakayya akan