Aunty ta shammaci kowa da soyayyarta ta karya,ta kwashi dukiya mai tsananin kauri da yawa wanda ita kanta bata san iyakarta ba ta hanyar Abokin ta'addancinta data hadu dashi wato Kamal shine yabi mata duk wata hanya ya bata kwarin gwaiwar da nema mata wanda suka iba kudin ta hanyar office din Abba,wanda sosai companyn nasu ya raunana har masu hannun jari a ciki duka suka janye.Wannan dalilin ya kawo babban sabani ga ahalin guda biyu da rikici yaki cinyewa Hajiya kaka ta kira Abba a matsayin mayaudati maciyi amana ta kuma yanke duk wata alaka dake tsakanin su dashi,sai a lokacin Aunty ta samu sukuni ganin ta samu galabar rarraba ahalin.Ba karamin wuya Abba yasha ba kafin Allah ya tado masa da dukiyarsa ta hanyar wasu da yake bi kudade sukaita maido masa nan Allah yasawa kudin albarka suka bunkasa ya tsaya da kansa tsayuwar da ko shi kansa besan iya abunda ya tara ba.
Lokacin da Zafar ya dawo,yayi bakin ciki itace rana ta farko daya fadi akan kafafunsa hawaye masu tsananin zafi suka zubo masa,jujuya kai yakeyi cikin tsananin bacin rai ya dago idanuwan sa da suka gama sauya kala ya kalli Hajiya kaka tare da cewa"Dan da kika raina a hannun ki,shin ke kin yarda zai iya aikata haka? a duk gidan nan akwai mai riko da gaskiyarsa da kuma amanarsa?,Ammi kema kin yarda? Daddy kaima?" a rikice yake gaba daya.Cikin tsananin tashin hankali yace"to idan kin raba shi da saura ni bazaki taba yanke alakata dashi ba kada ki manta Amanata tana hannunsa,kuma duk kiransa da nake muna waya da ita bai taba shaida mun cewar bakwa tare ba".
"kayi mun shiru Zafar,babu abunda ke damunka daya wuce yarinta,duka shekaranka nawa,to ina so ka sani baka ba wannan amanar".Hajiya Kaka ta fada.
Buga kansa yayi da karfi tare da cewa"a hannun dana karba bata raye bare na mayar mata da nauyin dana dauka,ina so na gaya maki babu kuma yarda za'ayi na janye jikina daga cika alkawarin dana dauka duk runtsi kuwa".Yana fadin haka ya fice daga gidan da sauri.Kiran Abba yayi kafin ya samu ya gane bayan gidan su suka koma,a lokacin Nihla na da shekara hudu ,ko da ya shiga gidan ba karamin tashin hankali ya shiga ba ganin Nihla ba lafiya anata fama a kuma lokacin ne Abba ke sanar masa Nihla sikila ce,Zafar yayi tashin hankali kunci damuwa akan ciwan Nihla,hakan ne yasa ya sauya ra'ayinsa daga zama Soja ya juya mafarkin sa zuwa karantar Likitanci dan ya kula da amanar.
Ci gaban labari.
*Allah ka gafartawa iyayen mu kayi mana kyakyawan karshe*
Jorderh✍🏻
[3/3, 21:53] Maryam Jordan: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*FARAUTAR FARIN CIKI*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇
```By``` ```Maryam``` ```ismail``` ````Majidadi```
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
78
A hankali ta soma bude idanuwanta da suka mata nauyi alamun baccin bai gama isarta ba,sam baya mata dadi yasa ta farka,akan tuskar Zafar idanuwanta suka sauka wanda ya kureta da ido fuskarsa a sake,kokarin tashi yake yasa ya karaso gabanta tare da taimaka mata ta tashi zaune,ji yayi jikinta zafi sosai alamun zazzabi na neman rufeta yasa yace"ki daina wannan koke koken,kinga zaki janyowa kanki ciwo".
Rau rau tayi da ido tare da fadin"Yaya Irfan ne".
Hannu yasa tare da dalle mata baki yace"kada na sake ji kin ambata mun sunan nan,in ba haka ba ranki zai baci"
Kasa tayi da kanta ta soma wasa da yatsun hannunta ganin duk ta takura kiris take jira ta saka kuka yasa yace"kiyi hakuri kinji Mamana,bana son damuwar nan taki ne,ko dan lafiyarki ya kamata a ce kiyi hakuri,Mamana kika rasa Mahaifiya kika rasa Mahaifi sai saurayi ne zaki kasa hakura da shi? saurayin ma irin Irfan ?"
"Yaya ba barina da yayi yake mun ciwo ba,amma sai ace ya rasa wacce zai so sai Auntyna,wacce nake dauka a matsayin mahaifiyat..."bata karasa magana ba Zafar ya daura yatsan shi akan bakinta tare da cewa"ba ta haife ki ba,ba kuma zata taba zama mahaifiyarki ba"tashi yayi ya hado mata drugs dinta ya bata ta sha,Hijab ya bata ta saka yace"tashi muje".
Bata musa ba ta mike tare da saka platshoe dake gabanta ta bi bayansa,babu kowa a parlon haka suka fice,yana gaba tana binsa har suka zagaya bayan gidan su.Saurin cin burki tayi ko kwakwaran motsi ta kasa.Dama yasan za'ayi haka kallonta yayi fuska a daure tare da cewa"wuce muje mana".
Girgixa masa kai tayi,tana kokarin yin baya,hannunsa yasa tare da riko nata ya soma tafiya cikin muryar tsoro take fadin"dan Allah ka barni bazan shiga ba,ni gida zan koma".Wata uwar harara daya aika mata da ita yasa ta yi saurin hadiye sauran maganar cikin hade fuska yace"Billah na kuma jin bakinki sai na mammare ki".
Gate din gidan ya tura tare da shiga,lumshe idanuwanta tayi,hawayen dake makale suka sauko akan fuskarta,abubuwa da yawa suke dawo mata a kai,ta zo gidan yafi a kirga lokacin yarintar ta amma Hajiya kaka na korata,hakan yasa tun tana naci harta hakura ta saba da rashin zama a gidan,ganin ya nufi main entarance na gidan yasa ta danji sanyi sanyi,kanta a kasa take binsa.Dam dam dam haka kirjinta ya bada sauti lokacin data dago idanuwanta ta ganta a tsakiyar parlon gidan ga Hajiya Kaka hakince a kan kujera tana aika mata da sakon nin harara.a take kyarma ta kwace mata tana niyar rantamawa da gudu.Murza hannunta Zafar yayi tare da kuma rikesa a nasa hannun.A hankali ya soma taku zuwa benen da zai sada shi da part din sa.
"Zafar!" shi ne abunda Hajiya kaka ta fada cikin tsananin bacin rai,kai tsaye gabansa ta dawo ta tsaya tare da nuna Nihal da hannu tace"menene jinin Umar yake yi a gidan nan?".
"tazo gaishe da yan uwanta ne ta kuma ga Amminta wacce take matsayin uwa a gareta"Zafar ya bata ansa.
"karya kake ! wacce alaka ce a tsakaninta da yan gidan nan❓,balle harda raina ina cikin gidan nan ka shigo mun da ita a gida"Kaka ta fada a hassale.
Murmushi yayi tare da cewa"Hajiya kaka,alaka da yawa mana,to tazo gaishe da Kakarta ne"ya fada tare da turo nata Nihal a gabanta.
Da matukar karfi Nihal ta juyo tare da afkawa a kirjin Zafar ta rungumesa da karfi ko ina a jikinta kyarma yake ,tuni hawaye sun fara zarya a kan kuma tunta,wani irin tsoron Hajiya Kaka ya taso mata lokaci daya.
Saurin kawar da kai Hajiya kaka tayi tare da cewa"ka ce mun kuma rashin tarbiyar har ya kai a gabana kake rungume mace?,kaji kunya yarinyar da aka haifa akan idonka? ka fitar da ita daga gidan nan yanzu kafin nayi abunda raina yake raya mun".
kallonta Zafar yayi tare da cewa"shiyasa zan kaita part dina ba naki ba nace,tsabar gulma ce ta kawo ki nan din ai".
Wani uban rankwashi ta kai masa a kai,ashh ya fada tare da rike mata hannu yace"wallahi kika kara dukana nasan mi zan maki,naga in da aka taba hana Mata shiga dakin Mijinta"yana fadin haka ya suri Nihal da gudu ya wuce ta gefan kaka.
Tamkar saukar aradu haka Kaka taji maganar Zafar na ansa kuwwa a cikin kunnuwanta,tuni kyarma na niyar kwace mata ,bata tsaya sauya shawara ba ta rufawa Zafar baya,sai da yaga tazo dab da kofar tasa ya mata gwalo tare da dannawa kofar key yana murmushi da tunanin fitinar daya taro a gidan nan yau.
A kan chair ya ajiye Nihal tare da cewa"matsoraciya ni sake ni,sai kace wacce na sato".
A hankali ta soma dago kanta daga jikin shi zubawa fuskarsa ido tayi ,uwar harara ya watsa mata da sauri tayi kasa da kai tana turo baki,tureta yayi daga jikin sa ya gyara zama tare da jawo table din gabansa ya fara dube-dube a laptop.Hannuwansa biyu yasa tare da toshe kunnuwansa yace"wallahi Hajiya Jamila idan zaki kwana nan bazan bude maki kofar nan ba,in yaso ki karya ki shigo".
Kuka Hajiya kaka ta fashe da shi tare da cewa"walllahi haihuwarka annoba ce Zafar,shege debabban albarka,wallahi ba zaka samun hawan jini ba sai dai ka kashe uwarka Maryam,labcecen banza,dana sani tun a ciki nasa an zubar da cikinka,kuma wallahi baka isa ba ka fiddo wannan yarinyar ka mayar da ita gidan ubanta,jinina yafi karfin jinin barayi".
"kibar cika mun kunne,ke kika koya masa satar tunda ke kika raine sa ae,kuma ke kika gayyato barauniyar a gidan,wallahi ki fita harkata a gidan nan kafin na maki rashin mutunci".
Hannu kaka ta daura a kai tayi dakin Ammi da gudu tana rurin ihu,a tsakiyar parlon Ammi ta fadi tana kuka wiwi kamar wacce ake fitarwa rai.
Dariya sosai Ramadan ya saki suka tafa tare da Miemie kafin yace"maganin ki kenan,tsab zai mana maganinki tunda shi kadai ke iya maki"
Dariya kamar zai kashe Miemie kafin tace"amma dai kasan duk yau bamu ba kwanciyar hankali ".
Da gudu Ammi ta fito daga bedroom har tana tuntube gaban kaka ta fadi tana salati "Mama lafiya ❓"shi ne abunda ta ke fada.
Gefan zani kaka tasha tare da share kwalla tace"Maryam kin haifo mani bala'i,amma ina so ki sani ajalinki kika haifa ba dai ni ba,wallahi ba'ayi dan da zai kashe ni ba,ni Zafar ke kika barauniya,kuma zai wulakanta ni"wani kukan ta kuma saki taci gaba da cewa"ki kira mani Aminu yau sai ya zaba ni ko Zafar a gidan nan,kuma yazo ya fitar mun da karuwar daya kawo a gaban idona ya dauketa ya haura sama".
"Hajiya dan Allah kiyi hakuri,wallahi bansan yayi haka ba,dan Allah kibar kuka,yanzun nan zan maki maganinsa,dan Allah kaka ki share hawayenki"Ammi ta fada.
A hassale kaka tace"to uban waye yace kuka nake❓,bakin ciki ne yamun yawa da bansan ruwa ya fara fita a idona ba,wallahi wallahi nan da sati mai zuwa sai an daurawa yaron can aure,zamu gani ni da shi waye a gaba,idan bazaiyi aure ba sai dai yabar gidan nan,dan bazai janyo mana abun kunya ba,Duk laifi ai naki ne,ko tarbiya ta gagare ki❓wallahi kin ban kunya Maryam"bata jira cewar Ammi ba ta fice daga dakin tana kwalawa Ramadan kira.
Da sauri Ammi ta mike ta nufi hanyar dakin Zafar ,tana zuwa ta soma buga kofar tana fadin"Muhammad ka bude kofar nan yanzu".
Jin muryar Ammi yasa ya yunkura,saurin rikosa Nihal tayi tana gada masa kai cikin muryar kuka take fadin"Kaka zata kashe ni idan ka bude,ni sai ka mayar da ni gida".
Shafa kanta yayi tare da cewa"babu abunda zai sameki".Cire hannunsa tayi daga rikon data masa yazo ya bude kofar.
Carab Ammi tayi da kunnansa tare da murdawa tace"kai kullun burinka ka janyo mun fitina kaji dadi ko Muhammad"
"ahhhh,ashhh Ammi kunnena zai cire,ki daina biyewa rikitacciyar tsohuwar can wallahi".
*Allah ka gafartawa iyayenmu kayi mana kyakyawan karshe*
*Dan Allah duk wanda ya karanta ya taya ni da addu'a ina da bukata a wurin Allah,fatana Allah ya cika mana burukan mu gaba daya*
Jorderh✍🏻
[3/3, 21:53] Maryam Jordan: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*FARAUTAR FARIN CIKI*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇
```By``` ```Maryam``` ```ismail``` ````Majidadi```
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
79
"Kakance kake kira da haka❓neman maganarka yayi yawa ko Muhammad"cewar Ammi ta kare maganar tana duban in da Nihla take duk ta takure alamar a tsorace take.Sakin kunnan nasa tayi tare da sakin kayataccen murmushi lokaci daya ta furta" 'yata".
Jujuyawa Nihla tayi ta hango ko ba kowa a tare da Ammi,ganin ba kowanne yasa ta kara so da sauri tare da tafiya zata duka a gabanta.Saurin riko kafadunta tayi tare da rungumeta a jikinta tana sakin ajiyar zuciya kafin ta zaunar da ita a chair suka koma suna fuskantar juna.Sunkuyar da kai Nihla tayi tare da cewa"Ammi ina ina wuni"
"lafiya qlau alhmdllh,ya hakuri da rayuwa❓"Ammi ta bata ansa.
"Alhmdllh"shi ne abunda ta samu damar furtawa kawai.
"ki saki jikinki Nihal ,ko kin manta a nan din gida kika dawo❓,ki daina tsoron Hajiya nasan duk abun nan da take yi ba zata iya cutar da ke ba.Hajiya tana da kirki sosai misalinta kamar kwakwa ne,a waje tana da matukar tauri da wuyar fahimta amma a ciki tana da tsananin taushi da tausayi sosai".Ammi ta fad'a.
Kwanto da Kai Zafar yayi akan kafadun Ammi tare da cewa"ke dai dan tana sirikarki shi yasa ko yaushe kike a bayanta".
Wani irin dundu da aka saukewa Zafar a baya yasa shi saurin dagowa yana so yaga wanne isashen ne,wa idon sa zai gane masa in ba Hajiya kaka ba❓.Fuskarta a matukar daure babu alamun annuri a tattare da ita.
"nayi maki wani abunne da zaki mun dukan nan❓"Zafar ya tambaya.
Ko kadan Kaka batayi ta kansa ba illa kallonta data mayar ga Nihla tare da cewa"ke maza ki bace mun da gani,ki kama gabanki wannan ya zama takunki na karshe a cikin gidan nan".
Da sauri Nihla ta mike tana niyar antayawa da gudu,ko ina a jikinta banda tsananin kyarma babu abunda yake yi,rike hannunta Zafar ya yi ya juyo yana kallon Hajiya kaka tare da cewa"shiyasa na kawota dakina,kuma bangarena ba naki ba,ban kuma san lokacin da kika fara kirgawa yan gida mutanan da kike so su shigo ba".
Nu na shi tayi da yatsa tana cewa"ba da kai nake ba,ka bari nayi magana da wacce zatayi ta kanta a gidan nan".
Saurin mikewa Ammi tayi tana fadin"Hajiya dan Allah kiyi hakuri,kai kuma Muhammad kada na sake jin bakinka a wurin nan".
Sallamar Daddy ce ta katse masu maganar su,da sauri Nihla ta janye hannunta daga rikon da Zafar ya yi mata ta karasa gaban Daddy da sauri,wani irin kauna bege da kuma tsananin tausayin kanta ya taso mata ganin Daddy ya kuma tunzura ta tana ganin kamar zata ga Abba a bayansa,wasu zafafan hawaye ne suka kawo a idanuwanta.Tsaye ta tsaya cak ta kasa motsa tare da zuba idanuwanta akan fuskar Daddy.
Murmushi ya sakar mata tare da bude hannuwansa yace"shikenan tunda ba Abba Umar bane kin rasa damar zuwa ga mahaifinki❓ ba za ki sake jin dumin Mahaifi ba❓ "
Wani irin kuka ne ya kubce mata da matukar sauri ta fada jikin Daddy tana shashekar kuka.bubbuga bayanta Daddy ya shiga yi tare da fara lallashinta.
Kamar wata statue haka Hajiya kaka ta daskare,ido suka hada da Zafar ya yi mata kwalo,saurin kawar da kai tayi tare da fadin"Al-ameen".
Ansa kiran Daddy ya yi tare da karasowa gabanta.Cike da isa da gadara tace"ina so yarinyar nan ta bar gidan nan.Bana kuma fatan sake ganin kafarta a gidan nan,ina kuma umurtarka da cewa nan da sati daya ka daura auren Zafar da Aisha".
"to" shi ne abunda Daddy ya fada sannan yaci gaba da cewa"bawai naki ta taki bane Hajiya,sai dai yau gani a gabanki a matsin Umar ina rokonki da kuma baki hakuri,Umar yana gabar mutuwarsa amma ke yake ambata da kuma tabbatar mun da cewa shi bai aikata abunda kike zarginsa da shi ba,yana kuma umurtata da in nema masa yafiyarki,in kuma rike masa Maryama amana,Maryama marainiya ce Hajiya bata da kowa kuma kinsan ita din dawainiyar Zafar ce tun daga ranar data diro duniya,haka zalika Mahaifinta ya kuma damka masa amanarta ,kuma Zafar bai gajiya ba ya ansa ya kuma yi alkawarin riketa kamar yarda yawa mahaifiyarta,shin Hajiya zaki so jininki jikanki mafi soyuwa a kama shi da laifin cin amana❓da kuma kasa rike alkawarin daya dauka❓ wannan karan amanar daya kuma dauka tana da matukar girma fiye da wacce kika sani"
Hannu ta daga masa alamar ya isa kafin tace"idan bashi ya yi ba wa ya yi❓ shi kuma jikan nawa a haka zai kare da rikon amanar mai lalura❓duk wani abunda ya tara sai ya kare a kanta❓"
Murmushi kawai Daddy ya yi kafin yace"Ummana idan lokaci ya yi zaki sani,dan Allah ki yafewa Umar ki kuma bari Zafar ya sauke nauyin daya dauka akan Maryama,ka da ki hukuntata da laifin da aka aikata tun tana zanin goyo".
Kasa furta komai Hajiya kaka tayi ta raba ta gefan Daddy ta wuce da sauri shi da Ammi suka bi bayanta.
Saurin mikewa Nihla tayi bakinta na rawa take fadin"Yaya zan tafi gida,dan Allah kada ka hanani".Kafin Zafar ya yi wata magana tuni ta runtuma a guje .Murmushi kawai yabi bayanta da shi,sosai murmushin ya haskaka fuskarsa ya yi matukar yi masa kyau ya kuma fito da ainahin zallar kyawu na fuskarsa.
Ko kadan Nihla bata tsaya ba sai da ta shigo cikin tsakiyar parlon su,a nan ta tsaya tana mayar da numfashi.A hankali ta soma bude idanuwanta ta kuma bude su tar akan fuskaf Irfan dake fuskantar ta amma idanuwansa a kasa ya kasa kallonta.
"lafiya kuwa❓waya biyo ki Nihla❓Aunty ta fada.
Kafin Nihla ta bada ansa Miemie dake shigowa tace"babu wanda ya biyota tsabar farin ciki ne kawai"
Sosai Aunty ta sake fuska tare da fadin"to Alhmdllh,Nihla ki kawo wa bakona ruwa,su lami basa nan".
Gyada kai Nihla tayi alamar to ta juya tare da nufar hanyar kitchen tana kokarin mayar da hawayen da suke kokarin zubo mata,ruwa da kuma lemu da cup ta daura a plate ta dauko ta dawo parlon a saman table na tsakiyar dakin ta ajiye tare da juyawa zata wuce dakinta,yayin da zuciyarta ke dukan ukku ukku a yanzu kam bata da iko ko karfin zuciyar tsayar da ruwan dake kwaranyowa daga cikin idanuwanta zuwa akan fuskarta.Tsaki Miemie taja tare da fadin "amma dai Irfan kaji kunya wallahi".
Murmushi kayace a fuskarsa yace"anya dai Miemie yau kinyi gaskiya kuwa❓miye abun jin kunya a tattare da soyayya❓lamarine na zuciya ka kuma mikata a in da ya dace in da kuma kasan zaka samu kwanciyar hankali da tsantsar kulawa".
Saurin juyowa Nihla tayi tana kare masa kallo,tana kuma jin maganganunsa kamar saukar aradu a kanta,cike da karfin hali ta tako zuwa gabansa,da sauri ya dauke kansa tare da juyawa idonsa daga kallonta."sau daya dai Irfan ka kalle ni ka kuma fuskance ni,wanne irin mutun ne kai❓ haka shi ne tukuicin soyayya❓ kana tunanin yin hakan da kayi zai haifar maka da nasara ne a rayuwarka❓ barina da kayi bai taba mun ciwo ba Irfan,amma ka rasa wacce xaka so sai Matar mahaifina❓"
"Nihla wannan ba tarbiyar dana baki ba ne,ki tsare manya kina masu tambayoyin da kika ga dama,kamar yarda ya fada lamarine na zuciya kuma ita take da hukunci akan wanda zata so ko kuma wanda zata ki,shin laifi ne dan Irfan ya nuna ni yake so❓ ta ina hakan ya zama kuntatawa❓ Irfan ina so yau ka bayyana zabinka a cikin mu biyun,Shin ni ce ko kuwa Nihla❓ina ga hakan shi xai kawo karshen duk wannan".
"ka daga kanka Irfan ka kalli cikin idanuwan Nihla ka gaya mata baka santa "Miemie ta fada.
Kallonsa ya mayar ga Miemie tare da cewa"Haba Miemie nasan kinsan furta kalmar kiyayya bata da dadi ko a wurin makiyinka balle kuma ni da Nihla take so,bazan iya kallon idonta ba dan hakan ya haramta a gare ni"kallonsa ya mayar ga Aunty fuska cike da fara'a yace"Auntyna a soyayyah bana ganin kowa sama da ke,kece cikon rayuwa da farin cikin Irfan,rasa shi tamkar wata illace ce ko tawaya a rayuwata,ke ce zabina kuma mafarkina a ko yaushe".
Wani irin kuka ne ya kubcewa Nihla tayi part dinta da gudu cike da tsananin tashin hankali da rashin sanin madafa.
Fuska cike da hawaye Miemie ta kallesu tare da cewa"shi fa sharri kare ne duk in da ka aikasa zai dawo maka,da yardar ubangiji yarda Nihla tayi kuka dukanku sai kun koka,yarda kuka tozarta rayuwarta sai taku ta tozarta,yarda kuka ci amana sai amanar Allah ta ci ku,ko Nihla ta fada ko karta fada Allah yana kallonku kuma zai mata sakayya".Kuka ne yaci karfinta ta masa ci gaba da magana ta juya zata wuce taci karo da Kamal dake tsaye ya daure hannuwansa a kirji yana kallonta.Karasowa yayi tare da jan hannun yana nuna mata alamar tabar kuka.....
*Allah ka gafartawa iyayenmu kayi mana kyakyawan karshe*
Jorderh✍🏻
[3/3, 21:53] Maryam Jordan: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*FARAUTAR FARIN CIKI*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇
```By``` ```Maryam``` ```ismail``` ````Majidadi```
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
80
Rike hannun Kamal tayi da karfi cikin nata,hawaye kuma na zarya akan fuskarta.Janta yayi zuwa dakin Nihla yana kuma lallashinta,tsaye tayi gaban bed din da Nihla ta fada tana kuka kamar ranta zai fita.Rungume juna sukayi da kyar Kamal ya samu ya shawo kansu tare da basu baki,rike kafadun Nihla Miemie tayi suna fuskantar juna cikin sanyin murya ta fara magana"Nihla meye a tattare da Aunty da har baki iya daukar fansa a kanta❓kina zaune kina kallo garin ta Farauto farin cikinta ke tana salwantar da naki Farin cikin❓ me ake da mata irin wannan".
Murmushi mai tsananin kyau Nihla ta saki har jerin fararen hakoranta suka bayyana,hannu tasa tare da share sauran hawayen daya rage akan fuskarta "Auntyna duniyata ce,Auntyna matsayin uwa take a gare ni,Auntyna taci kashina taci fitsarina duk da hakan ya kasance a fuska biyu ne,Auntyna tana da daraja a idona,tafi gaban wulakanci a gabana,ko ba komai zan kirata uwa wacce ta tsaya mun a lokacin farin ciki da akasinsa,ta jajirce a kaina kuma duk yarda take da fuska biyu hakan besa ta bani gurbatacciyar tarbiya ba,ta kula da ni tamkar yar data haifa a cikinta.Lokacin da Yayana Zafar ya yi tafiya itace mace data tsayawa maraicina ta kula dani ,haka zalika lokacin dana rasa mahaifi na kalleta a matsayin family tawa daya tak data rage mun a duniya wanda take da alaka da mahaifina,shin ki gaya mun duk wannan alkhairan data mun be isa na kauda kai akan abunda ta nuna tana so ba❓ba amfanin idan an cuce ka ka rama da cuta ilimun mu bazai mana amfani ba kenan,ina kuka ne badan abunda Aunty tamun ba ,a'a ina kuka ne ta dalilin wai Irfan ne zai maye gurbin da Mahaifina ya bari,ina kuma kuka ne akan na zama sakara dana mika yardata ga wanda besan darajata ba"Shiru Nihla tayi tana mayar da numfashi.
Girgiza kai Miemie tayi tare da janye jikinta daga rikon da Nihla tayi mata tare da cewa"ya ishe ni haka,na gaji dajin wannan maganganun naki da basa da hanyar kamawa balle dadin rikewa,yardarki da yawa shiya bawa waccan matar lasisin cutar da ke,ki gane mana Maryam karki kuma zama wata sakara akan wasu hujjojinki da bazan taba ansa ba,Nafisa ba zata taba zama uwa a gareki ba,garama kisan abunda kikeyi"jan mayafinta tayi tana niyar barin dakin,saurin rike gefen mayafin Nihla ,a fusace Miemie ta juyo tana zabgawa Nihla harara.Murmushi Nihla tayi tare da cewa"yau kuma zakiyi fushi da Aminiyar taki ne❓idan kika yi fushi da ni baki yi tunanin zafin dazai kuma shigata ba❓".
Can't control her tear's of happiness da matukar farin ciki tayo baya tare da rungumar Nihla a jikinta tare da cewa"Allah ya barmun ke,ya kuma kawo maki karshen duk matsalolinki" .Da ameen Kamal ya ansa tare da fadin"tunda an manta da ni a nan tsaye sai azo mu tafi ni na tuna da kaina".Bye bye Miemie tayiwa Nihla tabi bayan kamal suka tafi.
Sai lokacin wani radadi da rashin kwarin gwaiwa ya dirsar mata,kamar wata gunki haka ta daskare a wurin kwakwalwarta na tunasar da ita kalaman Irfan da suka kasance kara a zuba mata garwashi a kunnuwanta "shi ne wanda na fara so!a rayuwata irin son da bana hadasa da komai,irin son da zuciyata zata iya fashewa idan naga wani na rabarsa,son da wani irin zazzabi ke rufe ni idan har ban gansa ba! irin son da yake rufe ido wanda bana ganin kowa sai shi,irin son da a kansa na daina bacci sai dai naita juye-juye,akan sonsa na daina koshi wanda hakan ya haifar mun duk dadin abinci bana iya kaisa bakina balle harna iya gane dandanonsa! ,yanzu duk wannan son besa Irfan ya ji tausayina ba ya kuma tallabi maraicina😭❓ ta kare maganar wasu siraran hawaye na gangarowa akan fuskarta.A hankali ta zame hular dake rufe da yalwataccen gashin kanta,ta yi kokarin yiwa kanta masauki akan pillown dake bayanta ta kuma lulawa duniyar tunani.
Hannusa zube cikin aljihunsa yake taku tamkar kasa zata tsage saboda yacce take ansa takun nasa cike da izza,mulki da isa! hannunsa daya ya zaro daga aljihu tare da b'alle bottum din wuyansa na rigar suit din dake jikinsa.Bakinsa dauke da siririyar sallama ya saka kansa cikin parlon Hajiya kaka.Tsaye ya yi tare da dago kyawawan golding eye's ball's dinsa ya sauke su akan Hajiya kaka dake zaune tare da wata matashiyar budurwa.
Baki Hajiya kaka ta washe fuska dauke da yalwatacciyar fara'a ta mike tare da cewa"Aysha yau ga Zafar a gabanki,kuma mijinki nan da kwana shidda insha Allah".Budurwar da aka kira da Aysha ta dago kanta a hankali tana sauke idanuwanta akan Zafar Ma sha Allah shi ne abunda ta fada tana