ya nufi wajen wadrobe ɗin kayansa ya fiddo kayan da zaisa haɗe da shafa mai, cikin mintuna kaɗan ya gama shirinsa cikin wani rantsattsen boyel fari tas ɗaya matuƙar karɓar jikinsa, kai tsaye ɗakin Mahmah ya nufa ya tadda Abbu yana karyawa,
"Abbu ina kwana" ya faɗa yana Sadda kai ƙasa saboda abunda ya faru jiya, murmushi Abbu dake kallonsa ya yi haɗe da cewa,
"Lafiya klw Malam Hisham, anfito?"
"Eh Abbu". ya faɗa yana warar idanuwa, dariya Mahmah ta yi haɗe da cewa,
"A haf! Tana ciki tana aikin, ka ganshi nan shi yace na ƙyaleta sai zuwa anjima".
"Me yasa Abbu?"
"Hisham ko bakwai naga bata yi ba, kuma ga alama baccin bai isheta ba shiyasa"
"To amma Abbu idan bata tashi dawuri ta shirya ba, taya kake tunanin zata isa makaranta cikin lokaci? Sannan idan yaro ya yi lattin zuwa makaranta hakan na nufin ya rasa darasi na farko da akeyi, wanda hakan ba ƙaramin cutar da yara yakeyi ba".
"Kamar ya Hisham?"
"To Abbu da safe koda yaro zai tashi ƙwaƙwalwarsa fresh take, duk abunda aka karanta ko aka faɗa masa zai ɗauke, haka kuma akwai msimaicin darasin jiya da akeyi wanda idan ɗalibi bai fahimta ba yau idan anyi zai fahimta, ka ga rasa wannan a wajen ɗalibi abune da zai cutar dashi sosai".
"Haka ne gaskiya, to ai bansan haka abun yake ba, shiga ki tafi da ita" Abbu ya faɗa yana nuna ƙofar,
Kusan mintuna biyar Mahmah ta kwashe tana fama da Madiyam ta tashi amma taƙi hakan ya sa Abbu zuwa da kansa shima ya yi yayi taƙi tashi, da an ɗaga ta sai ta koma luuuu.ta sake yin kwanciyarta tana faman ƙwakume tedinta, hakan ya sa Mahmah fitowa cike da takaici ta ce,
"Je ka tadota da kanka shima ya yi yayi taƙi tashi".
Dama kamar jira Hisham keyi ya shiga cikin ɗakin tana kwance saman gado ta naɗe cikin tedin, wani irin takaici ne ya rufesa ganin Madiyam fa ba ƴar shekara bakwai bace ko goma, shekaru kusan sha huɗu cikin ta sha biyar take dasu amma ace sai abubuwan yara takeyi tsabar shagwaɓawr da kayi mata, tedin ya fara fizgowa da ƙarfi aikuwa Madiyam tayi wani zallo ta riƙe tedin tare dayin kwance ajikinsa tana faɗin, "wayyo Abbu kabrmun babyna" tana sake gyara kwanciyarta akan ƙirjinsa, runtse idanuwa yayi jin wani irin abu kamar anyi masa shocking a jiki tare dasa hannu ya fizgota da ƙarfi daga jikin nasa ya dire ƙasa yana faɗin.
"A gidan uwar wa wannan abun ta zama babynki? Zaki buɗe idanuwa ne ko sai na ɗaukeki mari tare da ƙona wannan abar". Ya faɗa yana wurgota falo haɗe da taso ƙeyar Madiyam a gba yn mangarar mata kai, karaf tedin ta faɗa a hannun Haisam daya shigo falon yanzu, cike da ɓacin rai ya nufo kan Hisham ya ɗaukesa mari tare da riƙo hannun Madiyam ya maida a gefensa haɗe da miƙa mata tedin yana watsawa Hisham wani irin mugun kallo haɗe da cewa, "Kai wane irin mugune marar tausayi Hisham, wane irin zalinci ne haka kake yiwa yarinyar nan fisabilillahi, ka kuwa san irin matsayi da soyayyar da nake yi mata azuciya ta?, Kasan irin ɓacin ran da kake saka ni aduk lokacin daka musguna mata? Look daga yau ina so ka fidda hannunka a lamarin Madiyam kafin mu samu matsala dakai domin Madiyam rayuwata ce" ya ƙare zancen haɗe dasa hannu ya rungumota a jikinsa sannan ya ci gaba da cewa "saboda haka ka ƙyaleta tayi rayuwarta yanda take so ni ina sonta a duk yanda take kuma aduk yanda zata tashi, shagwaɓa, sakalci da duk wani rashin jin maganarta basu dameni ba kuma a haka nake sonta, don haka babu ruwanka da lamarinta na faɗa maka". Ya ida zancen yana nuna sa da yatsa.
Cikin ɓacin rai shima ya yo kansa ya ce, "Baka isa ba wlh, kai meka sani akan so da har zaka furta cewa kana son Madiyam, wai a tunaninka duk abubuwan da nake yi mata saboda bana sonta ne? To kayi kuskure ya Haisam domin wannan abun da nake yimata shine so, shi ake kira da ƙauna kuma duka ina yimata su ne *A cikin so*, me ma kace? Madiyam rayuwarka ce? To tabbas zaka mutu domin baza ta taɓa zama mallakinka ba, ni ne nan na dace dana kira Madiyam rayuwata domin duka tawa rayuwar mallakinta ce ita kaɗai, sannan zanci gaba da gina rayuwarta izuwa yanda nake so don ta tabbata cewa ni ɗin da ita mallakin juna ne ta hanyar cuɗanya a cikin halaye ɗaya". Shaƙo wuyan rigarsa Haisam ya yi haɗe da cewa.
"Karya kake Hisham kai ba masoyinta bane, dubeka a haka kake kiran kanka masoyi kana neman muzguna mata akoda yaushe, da wuɗan nan munanan halayen naka da kake nuna mata kake sa ran zaka iya zama masoyinta? You Are just playing Hisham, idana kana tunanin wuɗannan abubuwan da kakeyi duka *A cikin so* ne, You fail Hisham, domin tuni suka maida kai zero behind a decimal point (0.00) a zuciyarta, idan kuma baka gane ba to ina nufin fanko kake a zuciyar Madiyam.." kafin ya rufe baki Hisham da idanuwansa suka kaɗa suka yi jajir saboda tsananin ɓacin rai da ɗacin maganganun da Haisam ya faɗa masa ya shaƙo wuyan sa tare da haɗewa ga ginar ɗakin yana faɗin,
"Waye fanko a zuciyar Madiyam? Kana tunanin zamowarka yayana zai sa ka faɗi irin wuɗannan kalaman akaina kuma in ƙyaleka? Bazai yuyu ba don idan har ban mallaki Madiyam ba kaima baza ka taɓa mallakar ta ba" kafin ya rufe baki Abbu dake tsaye sake da baki yana kallon ikon ALLAH ya ɗaukesa wani irin Zazzafan mari ganin yanda Haisam ke kokuwa da lumfashinsa yana neman taimako, don ba ƙaramar shaƙa Hisham ya yi masa ba da kaɗan ya rage ya leƙa barzahu ya dawo, cikin ɓacin rai Abbu ke magana haɗe da cewa.
"Kana son Madiyam ko ba ka sonta, kai ne ke sonta ko shi ke sonta duka ba damuwata bane, Madiyam ƴata ce kamar yanda kuma kuke ƴaƴana, saboda haka haƙƙin zaɓa mata miji na akaina sai wanda naga dama kuma ya kwanta mani arai na kuma aminta da irin soyayya da kulawar da yake yimata sannan zan aura masa ita". Ya ƙare zancen tare da karɓar wayarsa dake hannun Mahmah ya fice daga gidan.....
_Hmmm tirƙashi!, Ko ya wannan wasar zata kaya tsakani Haisam da kuma ɗan uwansa Hisham? Ina labarin Najlah da kwanaki kaɗan suka rage a tsaida maganar aurenta da Haisam? Shin Haisam zai amince ko kuwa? Tsakanin Hisham da Haisam wa Abbu zai zaɓawa Madiyam a matsayin miji, shin ya Madiyam zata karɓi kalaman Hisham da suka yimata dirar mikiya acikin kunnuwa cewa duka abubuwan da yake yimata *A cikin so* ne, shin zata yarda da hakan ko kuwa? Idan kina son jin yadda labarin zai kaya to maza ki hanzarta biyan kuɗinki domin ayi wannan kyakkyawar tafiyar mai cike da kyakkyawan salo da kuma kyakkyawan tsari a tare dake.💃💃💃💃_
*FIL HUB (Acikin so), littafin kuɗi ne, ki biya ₦500 kacal don ki mallaki naki, ƴar uwa ki gujewa cin haƙƙin ƴar uwarki dake neman ci da guminta domin faranta maku👏 ga masu buƙatar wannan littafi zaku tura kuɗinku ne ta wannan account no, 0434776437 gt bank Balkisu sani kaura ko kuma katin waya na mtn da shedar biya duka ta wannan lambar, 07040402435* mungode
An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels