Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
4 / 9
duk inda zamu je dole sai munje tare dakai? Kuma ai nazata bacci kakeyi shiyasa na hana Ailat taje ta faɗo maka, yanzu dai ka tashi kaje kayi arwala kayi Sallah, kuma Dady ya ce a faɗa maka ka kyauta da bai ganeka ba har yanzu". Ammie ta ƙare zancen tare da miƙewa ta shige ɗalibta, shafa kansa ya yi haɗe da miƙewa shima yabar wajen yana murmushi tuno daddaɗan mafarkin daya yi na Madiyam ɗin sa, dama tun ɗazu yake son tashin amma kunyar kar Ammie ta fahimci wani abu ya hanasa, don kuwa ya gama jiƙe gaban wandonsa da daddaɗan mafarkin da yayi, don ma ALLAH yasa jalabiya ce akai da baisan ya zaiyi ba idan Ammie ta gani, da sauri ya haye sama haɗe da cire kayan ya faɗa toilet ya yi wanka tare da tsarkake jikinsa sannan ya fito yana jn wani irin nishaɗi da farinciki aransa, tare da addu'a ALLAH ya nuna masa ranar da za ace wannan mafarkin nasa ya zamo gaskiya ya mallaki Madiyam a matsayin matarsa, da ranar sai yafi kowa farinciki a duniya. A ɓangaren Madiyam kuwa Hisham na ɗauke wayarsa ta turo baki haɗe da cewa, "ALLAH yaba kowa tashi" sannan ta koma ta haye gadon taci gaba da baccinta hankali kwance cike da mafarkai kala kala. Bata farka ba sai bayan sallar azahar da Mahmah ta tada ita tayi Sallah, jin ƙafarta tayi ta saki sosai lokacin data sauko kan gadon tare dayin dariya ta ce, "Mahmah ƙafata ta warke" "Alhamdulillah, kai agaida Hisham ALLAH ya yi masa albarka." "Kai Mahmah, shifa mugunta kawai yake yimun amma kiyita faman saka mashi albarka" "Kema ALLAH ya yimaki albarka Madiyam, amma ai yanda kika da aturin kan nan ba don shi ba da yanzu nasan ƙafar ta yimaki tsami, shiyasa na saka masa albarka don ko ɗazu nasan da ni ce zan shafa maki maganin nan duka maƙwafta sai anjimu, amma da yake shine ai kinga kin tsaya ko?" Turo baki ta yi haɗe da wucewa ta fara watso ruwa sannan tayi arwala ta yi Sallah, tana gamawa Mahmah ta zubo mata abinci taci sannan ta ɗauki maganin ta sake shafa mata tana faɗin, "Ai ALLAH ya taimake ki kina da jiki mai kyau, badon haka ba ai sai kin gane kurenki." "Haddai ga ya dodo, ALLAH na gode maka." Ta faɗa haɗe da miƙewa ta saka kayanta na islamiya, kallonta Mahmah ta yi haɗe da cewa, "kinwa kanki ƙiyamul laili, a dawo lafiya". "Kai Mahmah idan wani ya ji fa sai ace bana son karatu?" "Ba haka nake nufi ba, ai nazata zaki laƙe ne saboda ciwon dake ƙafarki kice baza kije ba shiyasa". "To ai naji sauƙi, kuma bana so Nawwrah ta wuce ni". "ALLAH to ya bada ilimi mai albarka." "Amin" ta faɗa tana shafa powder da jan baki a fuskarta, tana gamawa ta ɗauki jikkar littafanta haɗe da ficewa tana faɗin, "Mahmah na tafi" "A dawo lafiya". Tana kawowa bakin ƙofar gida tayi tuntuɓe da wani dutse da aka tangale ƙofar gidan ta faɗowo Ashfaq abokin Hisham da suke ƙoƙarin shigowa tare, da yake kanta ƙasa yake tana dudduba wani abu cikin cikkarta ta islamiya, yanda ta faɗa ajikin Ashfaq ɗin yasa hannu biyu ya riƙeta shi ya bala'in ɓatawa Hisham rai, ya fizgota haɗe da ɗauke ta mari yana faɗin, "Wai ba kida hankali ne ke.." kasa iyarwa ya yi ganin yanda ta cika fuskarta da kwalliya, abunda ya tsana kenan aduniya yaga tayi musamman idan zata fita, fizgar kafaɗarta ya yi ya koma cikin gida da ita haɗe da jawo wani towel dake saman igiya da Mahmah ke goge goge dashi ya sa ya darje mata fuska tas har sai da kwalliyar ta fita, lokaci ɗaya fuskar Madiyam ta yi jajir da yake farace tas irin farin nan da zakaga kamar an surka da madara madara, haka ma tana da cikar gashin gira da zarazaran gashin ido, ɗan bakinta ƙarami ne sosai dake ɗauke da laɓɓa madaidaita masu matuƙar kyau da ɗaukar hankali da idan ka gani zaka ɗauka ta shafa janbaki ne, amma azahiri haka laɓan suke, ko bata yi kwalliya ba idan ka kalleta sai ta burge ka duk da kuwa ƙanƙantar ta balle kuma idan ta yi, hakan yasa Hisham ke tsananin jin haushinta idan yaga ko mai ta sakawa bakinta, "Wuce kafin na hamɓaraki a wajen ya faɗa cike dajin haushinta zuciyarsa na yimasa zafi". Ba tare data ce uffan ba ta wuce abunta tana jin wata irin tsanarsa a ranta, ta rasa meyasa Hisham ya tsaneta yake takura mata hakan sai kace ba ɗan uwanta ba, shiyasa sam bata son sa ta tsanesa har cikin zuciyarta, murmushi Ashfaq ya saki yana kallonsa bayan ta fice haɗe da cewa, "Gaskiya ka rage wannan zafin kan naka akan yarinyar nan, duka duka Madiyam nawa take da zaka riƙa takurata haka? Kabarta mana ta mori ƙuruciyarta in yaso idan ta girma sai ka saka mata sharuɗɗan da kake so tabi, amma haka tsanarka zaka saka mata a zuciya gaskiya." "Shin zaka shigo ku gaisa da Mahmah ɗinne ko kuwa wucewa za kayi?" Hisham ya faɗa shaye da toka ba tare daya kula da maganar da Ashfaq ɗin keyi masa ba.... *FIL HUB (Acikin so), littafin kuɗi ne, ki biya ₦500 kacal don ki mallaki naki, ƴar uwa ki gujewa cin haƙƙin ƴar uwarki dake neman ci da guminta domin faranta maku👏 ga masu buƙatar wannan littafi zaku tura kuɗinku ne ta wannan account no, 0434776437 gt bank Balkisu sani kaura ko kuma katin waya na mtn da shedar biya duka ta wannan lambar, 07040402435* mungode. *ALLAH KA JIƘAN IYAYENMU 👏😭* Free page 6 *FIL-HUB*♥️ (Acikin so💘) Paid Book: N500 Written by Billy s fari💎 ______________________________ Kallo Dady ya bi Najlah dashi haɗe da ajiye jaridar hannunsa, ba tun yau ba ya san irin son da Najlah ke yiwa Haisam, haka shima Haisam ɗin yana nuna mata kulawa da soyayya sosai, abunda kawai bai sani ba, shin soyayyar aure yake yiwa Najlah ko kuwa?, Ƴar ajiyar zuciya ya sauke yana mai addu'ar ALLAH yasa Haisam ya so ta kamar yanda itama take son sa, a zahiri kuma kallonsa ya yi haɗe da cewa, "My son ka faɗa mun gaskiya? Anya kai kace ta shirya zaka kaita wajen shopping ɗin ko kuma ita ta matsa maka? Saboda a yanda naga ka ɗan tsorata dajin zancen kamar takuraka ta yi, idan hakane kawai ka ƙyaleta in yaso anjima sai na kaita ita dasu hajiya". "A'a Dady ni nace ta shirya zan kaita". "To shikenan ngd, ka shiga ciki ka faɗawa Hajiya Zeenat saƙon dana bata ta ajiye maka ta baka". "To Dady, ina godiya" Haisam ya faɗa tare da nufar cikin gidan, yana shiga cikin corridor ɗin da zai sada shi da ƙaton falon dake gidan ya ji anyi tafi ta bayansa juyowar da zai yi yaga Najlah tsaye ajikin ginin tayi folding hannayenta a ƙirji tana kallonsa kafin can ta tintsire da dariya haɗe da cewa, "Matsoraci!" Gyara tsayuwarsa ya yi yana nunata da makullin motar dake hannunsa haɗe da cewa "look Najlah, karki sake yimun irin wannan wasar, yaushe nace zan kaiki kiyo shopping?" "Ok, idan baka ce ba inje in faɗawa Dady abunda mukayi da safe kenan, ko ka manta in tuna maka?" Ta ƙare zancen tana wasa da gefen mayafin dake jikinta, haɗe da jifarsa da wani irin kallo mai matuƙar rikirkitawa, dafe goshi ya yi haɗe da girgiza kai sannan ya bar wajen yana faɗin, "Silly girl". Murmushi ta saki haɗe dabinsa da kallo har ya shige falon sannan ta biyo bayansa itama ta nufi kitchen, zaune ya isko Hajiya Zeenat ita da Hajiya Raheema suna kallo, cikin girmamawa ya duƙa ya gaishesu kansa sunkuye a ƙasa, wata irin kunyar yake ji don gani yakeyi duk abunda ya faru ɗazu Makka ta sanar masu tunda ba kunya ne da ita ba, kujera Hajiya Zeenat ta nuna masa tana murmushi ta ce, " Tashi ka zauna akan kujera Hisham, wai dai ko ƴar gida za a yi tsakaninka da Najlah naga sai faman sussunkuyar dakai kake yi? Ko ka manta nan ma gida ne bai kamata kayi haka ba? Ko ba haka bane Hajiya Raheema?" "Nima shi na gani, ko ƴar gida za a yi ai nan kam gidansu ne bai kamata ya riƙa jin kunyar mu haka ba". "Ah to, anzo gaida Dady ko?". "Eh" ya faɗa ba tare daya sake cewa komai ba, so yake yi ya faɗa mata saƙon Dady amma ya kasa saboda nauyin haka yake ji, hakan yasa Hajiya Mariya da dama sunyi maganar da Dady cewa idan Haisam ya shigo ko baya nan ta bashi saƙon ta miƙe ta shiga ciki ta ɗauko wat leda ta kawo masa tana faɗin, "Ga saƙonku kai da Hisham inji Dadynku". "To Hajiya, mun gode Hajiya, ALLAH ya saka da alkhairi" ya faɗa tare da karɓar ledar ya miƙe ya bar falon yana yimasu sai anjima, Godiya ya sake yiwa Dady daya zo fita sannan ya wuce gida, yana shiga cikin falo message ɗin Najlah na shigowa a wayarsa, ciro wayar ya yi yana cilla ledar akan kujera haɗe da cewa, "Ammi ga tsarabarmu nan ni da Hisham inji Dady" ya ƙare zancen yana karanta saƙon da Najlah ta turo masa, _"Dear my feature husband! yaushe zamu tafi wajen shopping ɗin?"_ Ɗan tsaki ya ja haɗe da maida wayar a aljihu yana kallon kayan dake cikin ledar da Ailat ke zazzagewa tana dubawa, kwalaye ne guda biyu fararen jallabiyo masu kyau aciki, sai wasu ƙwanƙuna guda biyu suma, ɗaya ta ɗauka ta buɗe tana faɗin, "Wow take a look of this ya Haisam, ya yi kyau sosai" ta nuna masa agogon dake ciki mai shegen kyau ƙirar italy back colour". sosai agogon ya yi masa kyau ya amsa ya gwada a hannunsa, dariya Ailat ta kwashe da ita haɗe da cewa, "Bai yi maka kyau ba gaskiya, da ya Hisham ne sai yafi yi masa kyau sosai". "Ahhhh...Ailat banda son kai gaskiya, shima ya yi masa kyau sosai." Ammie ta faɗa tana dariya, murmushi ya yi shima haɗe da cewa, "ƙyaleta Ammie jealous ne take yi, ni na san indai zai yiwa Hisham kyau to tabbas nima zaiyi mun kyau, ƴar iya yi kawai". "Ba wani jealous, ai nima ya siyo mun nawa ko Ammie?, hadda ma zoben azurfa da takalma". "Ai kowa ma ya siyowa indai Dady ne, ALLAH ya saka masa da alkhairi kuma yabar tare". "Amin ya rabbi, Ammie ki ajiyesu hannunki, gobe zanje Giwa dubo Madiyam da jiki sai in wuce wa Hisham da nasa". "To ai shikenan, nima akwai saƙon da zan baka ka kaiwa Mahmah, Ailat ɗauka kikai ɗaki". Ta ƙare zance tana miƙawa Ailat ledar. "Ya Hisham nima zan je". "Bazan je dake ba, kin manta gobe monday, indai kina da saƙo ki bayar na wuce maki dashi". Cike da jin haushi tunawa da eh haka ne gobe fa monday ta wuce ta kai kayan a ɗaki, bayan ta dawo ya sa ta zubo masa abinci ya zauna kan dining yana ci suna taɓa fira da Ammie sai ga Najlah ta shigo, abincinsa ya cigaba da ci ba tare daya ya kalli ko inda take tsaye suna gaisawa da Ammie ba, "Zo ki zauna mana". Ammie ta faɗa tana murmushi haɗe da kallon Haisam da itama Najlah ɗin ke kallo, ganin abinci yake ci ya sa bata ce dashi uffan ba ta cigaba da kallon wani African series film dasu Ammie ke kallo, gaisheta Ailat ta yi haɗe da cewa, "Aunty Najlah ko ya Haisam kike nema?" Sai data aika mata da harara ta ƙasan idanuwa sannan ta ɗan yi yaƙe haɗe da cewa, "Eh, amma ai naga abinci yake ci". Tana rufe baki Haisam na miƙewa haɗe da wucewa yana faɗin, "Muje in kin tashi." "Ya Haisam ina zaku je?" Ailat ta faɗa tare da miƙewa zaune, kamar bazai yi magana ba tunowa da abunda ya faru ya sashi saurin juyowa yana kallon Ailat ya ce, "Shopping zan kaita ko zaki je kema?" "Eh zanje wlh." Ailat ta faɗa haɗe da miƙewa da sauri har tana ƙoƙarin faɗuwa ta nufi ɗakinta ta ɗauko mayafinta, shi kuma ya fice Najlah ta bishi a baya tana yiwa Ammie sai anjima, suna fita ta ɓata fuska haɗe da cewa, "Me yasa sai da ita zamu tafi? Gaskiya ni bazan je tare da ita ba sai dai ka bari gobe ka kaita." "Haka nake sha'awa, idan kuma baza ki ba, sai ki koma gida abunki kin hutar dani". Har ta buɗe baki zata sake yin magana sai ga Ailat ta ƙaraso wajen, juyawa ta yi ta kalleta tare da balla mata harara, kauda kanta ta yi ta ƙarasa wajen Haisam tare da riƙe hannunsa tana faɗin, "muje ya Haisam" ta yi hakan don ta hasala Najlah dake faman aika mata da harara, har suka kai bakin mota ya shiga ya tayar Ailat ta buɗe baya ta shige abinta Najlah na nan inda take tsaye ko motsawa bata yi ba, riverse yayi tare da juya motar zai fita sannan ya sauke glass haɗe dayi mata horn yana faɗin, "kefa muke jira" har ga Allah tana son fitar tare dashi shiyasa baza ta iyayin zuciya ba da ta fasa fitar gaba ɗaya, amma ba komai zata koyawa Ailat hankali, ta faɗa cikin zuciyarta tare dayin kwafa sannan ta nufi wajen motar ta buɗe gaba ta shige. Sai da suka hau kan titi dai-dai sannan ya juyo ya kalli yanda ta tsuke fuska, murmushi ya saki kafin yace, "Ya akayi?" "Ban sani ba". Ta bashi amsar a hasale, hakan ya bashi dariya sosai haɗe da dukan sitari sannan ya sake kallonta ya ce, "ALLAH yasa hanyar da kika sani ta ɓace maki". "Amin". Ailat da bata san zancen da akeyi ba ta dai ji an ambaci sunan ALLAH ta faɗa tana ci gaba da latsar wayarta don tun ɗazu hankalinta na akan wayar tana charting da wata ƙawarta, juyowa Najlah ta yi haɗe da cewa, "wa yasaka bakinki ke kuma, ALLAH Ailat kifita idanuwa na". "Ha'ah, jimun aunty Najlah, addu'a fa ya Haisam ya yi nace amin, to meye laifina kuma?" "Babu, amma don ALLAH kici gaba kar ki dena, bakinki zai faɗa maki don sai na fasa maki shi wata rana". "Too.. ALLAH ya baki haƙuri". "Ki amshe idan ya bani." "Enough Najlah, ya isa haka mana, Ailat fa ƙanwarki ce me yasa zaki riƙa biye mata?" "Ai shiyasa banso muzo da ita ba saboda ta rena ni". "Ailat kidena ba kyau, kin san idan Ammie ta ji sai kin rena kanki ko?". Shiru Ailat ta yi bata koma cewa komai ba sai da ta ji ya ce, "ina zan kai ku?" "Arewa mall, jifatau" suka faɗa a tare, "to ina zamu je?, Ke kince Arewa mall, ita kuma ta ce jifatau." Ya tambaya yana kallon Najlah. "Oho, duk inda ya yi maka, amma dai ka tuna fitar tawa ce ba tata ba". "Amma ai kema baki tambayeni ba, kawai zancen tafiyar na ji a sama". "Shikenan kayi yanda kake so". Ta yi maganar tare da folding hannayenta tana juyar dakai gefe, wannan irin takaici dame ya yi kama, yarinya sai kace kishiyarta? A zuciyarta tana faɗin ai kuwa wlh akwai aiki tsakanina da yarinyar nan duk mukayi aure, don ni bazan yi toloreting wannan iskancin ba ko kaɗan, da haka suka isa Arewa mall ya yi parking yana faɗin "ku shiga ku siyo abunda zaku siyo ina jiranku anan". Haɗe da miƙa wa Najlah ATM ɗin sa. Ganin Najlah bata fita ba ya sa itama Ailat taƙi fita ta yi zaune ta tana cigaba da latsar wayarta, juyowa ta yi fuska a ɗaure haɗe da cewa, "ya kuma kika zauna? kije ki zaɓi abunda kike so mana gani nan zuwa". Ba musu Ailat ta buɗe ƙofar ta fita, Najlah ta sauke ajiyar zuciya haɗe da kallonsa ta ce, "wai yanzu ya Haisam don ɗai na ce ina sonka kake yimun wuɗan nan abubuwan, can i deserve it from you?" "No Najlah, Amma.." "Wait! Banyi maka bane? Ban cancanci ka so ni bane ko kuma ni ba mace bace kamar sauran mata?" "Ke mace ce Najlah fiye ma da wasu sauran matan, kuma kin cancanci a soki, amma maganar gaskiya bana so na yaudareki, zuciya ta akwai wacce take so kuma take mafarkin kasancewa tare da ita". Wani irin faɗuwar gaba Najlah ta ji haɗe da dafe saiti zuciyarta tana kallonsa kafin hawaye su fara sauko mata a fuska, "wacece wannan dake neman tarwatsa mani rayuwata? wacece ke nema ta rusa ganin dake tsakanin ni da kai tun muna yara? Ya akayi ban santa ba kuma duk zamanmu baka taɓa faɗa mun komai akanta ba?" Ta faɗa cikin tashin hankali da karyewar murya. "Kin santa Najlah, kawai dai baki san ita bace saboda na ɓoye sirrin azuciyata". "Idan kuwa haka ne tabbas baka yi mani adalci ba, domin irin shaƙuwar dake tsakanina dakai da kulawar da muke yiwa juna babu wanda zai ce ba *A cikin so* bane, faɗa mun ko wacece naji me tafini da zuciyarka zata zaɓe ta akaina" "Madiyam ce, ƴar gidan Baffa Auwal, wato ƴar uwata." Wata irin dariya Najlah ta kwashe da ita tana goge hawayen dake kan fuskarta haɗe da cewa, "Shamless thing to you Haisam, wannan ƴar yarinyar ƴar ƙauye kake so? To dame tafini ne ko kuma me zata nuna mun, Yarinyar dako halittar ta ba'a gama haɗawa ba zaka zaɓa akaina? Wlh shammatar kanka kake yi don indai akanta ne bazan taɓa ja da baya ba har sai naga abunda ya turewa buzu naɗi tsakanin ni dakai" "Koma dai meye ita zuciyata ke so kuma itace zaɓina, ki yarda da hakan ko karki yarda ya rage naki Najlah, zan reni abita har zuwa lokacin da za a gama halittartar kamar yanda ki ke koma fiye dake sannan na aureta kuma na kawota cikin gidana a matsayin matata uwar ƴaƴana". "Wlh mafarki ne kake yi ya Haisam, wannan sunan in Sha ALLAH nice zan amsashi a gina ko kana so ko baka so, no wander tun zuwan yarinyar nan na ƙarshe naji bana sonta saboda rashin kunyarta tayi yawa, abunda kenan ya haifar da rashin jituwa ta da Ailat saboda yanda har ita ta koyawa rashin kunya da fitsara irin nasu na ƴan ƙauye, Ailat dake bani respect sai gashi ta renani rana ɗaya, ƙwanda ka sani tun wuri bazan taɓa son wannan yarinyar ba wlh balle har na iya sadaukar mata da kai". Ta ƙare zancen tare da ficewa cikin motar ta rufo masa ƙofar da ƙarfi saboda haushin da take ciki, hakan ya bala'in ɓata masa rai musamman maganganun data faɗa akan Madiyam ɗinsa, tada motar ya yi da ƙarfi ya ja ya bar wajen cike da jin haushinta shima, Koda ta shiga mall ɗin Ailat ta jidi kaya iya son ranta ta ajiye tana jiran shigowarsu, dama ba wata doguwar sayayya Najlah za tayi ba kawai dai son takeyi ta kasance tare dashi saboda suyi magana shiyasa ta tsiri fitar, bodyspray kaɗai ta ɗauka ta kawo aka faɗa mata price ta miƙa ATM card tace acire, cike da ƙarfin hali Ailat ta kalli mutumen haɗe da cewa, "ka cire kuɗin duka aciki". Sannan ta ɗauki kayanta da aka sa mata acikin leda ta yi gaba, Najlah bata ce komai ba tunda dama ATM ɗin na yayanta ne aka cire kuɗin aka miƙo mata haɗe da ledar da aka kaɗa mata bodyspray ɗinta aciki ta karɓa ta yi gaba itama, waje ta samu Ailat tsaye tana dube-dube ganin babu motar da suka zo da ita awajen, dariya ta yi haɗe da saƙalota tana faɗin, "to masu yaya sai ayi haƙuri aje a tari napep a hau, yayan naki ya yanki tiketin fushi ya yi gaba abunsa, Shan toka Ailat ta yi tana turo baki haɗe da cewa, "To meye na dariya kuma?". "Babu?" Najlah ta bata amsa tare da ciro ɗari biyar ta saka mata a hannu haɗe da jan chicks ɗin ta ta ce, "Maza a tari napep a tafi gida". sannan ta juya tabar wajen, duk da abun ya bata haushi itama sai ta ɓoye don kada Ailat taga damarta, amma a ranta abun ya bala'in ƙona mata zuciya, wato a dakeka a hanaka kuka, ta faɗa a fili tare da tare mai napep ta shige, Ailat kuwa wayar Ammie ta kira tare da fashe mata da kuka, "Ke lafiya?" Ammie dake kitchen ta faɗa bayan ta ɗaga wayar. "Ammie kinga wulaƙancin da ya Haisam ya yi mana ko?" "Ina zan gani tunda ba tare nake daku ba, me yafaru ne halan?". Cikin kuka ta labartawa Ammie abunda ke faruwa, dariya Ammie ta yi haɗe da cewa, "Ai maganinki kenan, waya aike ki binsu? Ina Najlah ɗin take?" "Ta hau napep ta wuce". "Shikenan, ai kema saiki hawo napep ɗin ki dawo, gobe kya ƙara ganin zaya fita kice zaki bisa, ni Najlah ɗin ma nafi ji don hakan ba daɗi ko kaɗan". Ganin Ammie bata goya mata baya ba ya sa ta kwashi kayanta niƙi niƙi ta wuce ta tari napep ta yi gida tana sharar ƙwalla...... FIL HUB (Acikin so), littafin kuɗi ne, ki biya ₦500 kacal don ki mallaki naki, ƴar uwa ki gujewa cin haƙƙin ƴar uwarki dake neman ci da guminta domin faranta maku👏 ga masu buƙatar wannan littafi szaku tura kuɗinku ne ta wannan account no, 0434776437 gt bank Balkisu sani kaura ko kuma katin waya na mtn da shedar biya duka ta wannan lambar, 07040402435* mungode *ALLAH KA JIƘAN IYAYENMU👏😭* Free page 5 *FIL-HUB*♥️ (Acikin so💘) Paid Book: N500 Written by Billy s fari💎 ______________________________ Girgiza kai kaɗai Ashfaq ya yi don inda sabo ya saba da lamarin abakin nashi, hanyar cikin gidan ya nuna masa haɗe da cewa, "Muje" ya wuce gaba shi shi kuma yana biye dashi a baya, sake da fuska Mahmah ta tarbesa tare da kawo masa ruwa ya sha sannan ya ce, "Mahmah Barka da rana, anwuni lafiya?" "Lafiya klw Ashfaq, ya fama da ɗalibbai da can wajen mahaifiyarka?" "Duk lafiya klw Alhamdulillah Mahmah, ai na haɗu da Madiyam anyi makaranta". "Ka dai gani, idan islamiya ce babu wani gumu da nake sha da ita wajen shiryawarta ta tafi, amma wlh Ashfaq duk aka ce maka ranakun zuwa boko sun kama na dinga haushi da ita kenan duk maƙwabta ana ji na, na rasa meyasa bata son karatu ta wannan fannin, shiyasa kullum za kaga latti take zuwa nayi faɗa da ita har na gaji". "Ai Mahmah addu'a zaki dinga yi mata, wlh ni kaina bana son lattin da take zuwa, ayi ta dukanta ko haushi bata ji." "Ƙyaleta akayi Ashfaq shiyasa, kuma na san duka laifin Abbu ne, amma ALLAH yakai ranmu gobe lafiya". Hisham ya faɗa yana cije leɓensa na ƙasa, kallonsa Ashfaq ya yi haɗe da cewa, "To kai kuma waya sanko bakinka a wannan maganar fisabilillahi, wai ma me yasa dole sai makarantar su Madiyam za kaje volunteer? Ka je wata school ɗin mana". "Can nake sha'awa" ya bashi amsa a taƙaice tare da miƙewa ya bar ɗakin, da kallo Ashfaq ya bisa har ya fice daga ɗakin tare da maido kallon nasa ga Mahmah ya ce, "Laifinku ne Mahmah da kuka barshi zuwa koyarwa a makarantarsu Madiyam, yanda take tsoron nan nasa b lallaine ta tsaya tayi karatun yanda ake so ba, ƙara saka mata tsanar karatun kawai zai ƙarayi". "To aini ban ma san da wannan zancen ba Ashfaq, kasan halin mutumen naka miskilancin da rashin son magana ya yi masa yawa, amma na ji daɗi sosai da zai tafi makarantar tasu koyarwa, ko ba komai dole ta shiga taitayinta yanzu, ni ai hakan ya yimun daɗi sosai wlh ALLAH ya taimaka kuma ya yi jagora". "Amin ya rabbi Mahmah, na lura haddake kike ƙara ɗaurewa Hisham, sam indai akan Madiyam ne bakya taɓa ganin laifinsa". "To uban ƴan surutu, idan ka tashi tafiya sai ka tashi mutafi, ALLAH Mahmah laifinsa ne da Madiyam ba ta maida hankali wajen karatu, meye amfaninsa makarantar a matsayinsa na abokin yayanta? shikenan kawai

Chapter 4 of 9