Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
koda flashin zan kira mu dinga gaisawa, yana kai ƙarshen maganar Arman na isowa, cikin takunsa mai ɗaukar hankali, shi kuma saurayin yana barin gurin, "waye wancan?" Arman yai maganar cikin yanayi na ɓaci rai, cikin siririyar muryarta tace "oho nima ban sanshi ba" ta ɓoye takardar da ya bata, koda ta kalli yanayin fuskarsa sai da gabanta ya bada rass, amma sai ta basar tare da kallon agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunta, shi haushi ma ta bashi, ko shan ice cream ɗin ma basuje ba yace ta shiga mota, babu inda ta iya, dole ta shiga motar suka wuce, again dai wani gurin shaƙatawar suka nufa, wanda ya doke wannan a kyau da tsari, dakaga gurin kasan na zuwan ƴa ƴan manya ne, koda suka fito a mota, ba samari ba, har ƴan mata hankalinsu na gurin Talatu, wata anan sukayi faɗa da saurayinta ta tashi ta barshi, kujeru ne iri iri masu kyau gunin ban sha'awa, yayi mata nuni da ta zauna a wata wacce babu kowa, kuma tana can nesa da mutane, kamar inda ya umarceta hakan ko tayi, ta zauna anan tana ta ƙarewa ko ina kallo, wasu harufan ta haɗa ta karanta wasu kuma sun gagareta ta ƙyalesu, yana can shi dai yaje sama musu abin sha, ita kuma tana zaune tayi shiru kamar mai nazarin wani abu, "Aslmu alaikum Beautiful girl dafatan na sameki lafiya?" tuno nasihar da anty Tasneem tayi mata tayi, na cewar karta yarda ta wulakanta mutane, sbda ɗan Adam daraja ce dashi, sai tayi amfani hakan, ta amsa masa sallama, hakan ya bashi damar zama ya fara gabatar masa da kansa, "da farko dai sunana Ibrahim keda?" yai maganar yana jifanta da ƙayataccen murmishi, "Aysha" ta faɗa ba tare da ta kalli inda yake zaune ba, Sosai furta kalmar Aysha ya birgesa, domin kuwa ji yayi muryarta tayi kamar ana busa sarewa tsabar daɗi, kai tsaye yace "ko zan iya samun lambar wayarki?" Karaf a kunnen Arman dake dawowa hannunsa riƙe da wata takarda, wani mutumi ma'sikacin gurin yana biye dashi da wani kyakkyawan faranti an jere kayan ƙwalama a ciki, sam bata ma nunar da tasan da zaman Ibrahim a kusa da ita ba, sai ta wani sha ƙamshi tana sake gyara ɗaurin ɗankwalinta, ajiyar zuciya ya sauke, wace na kusa dashi yana iya tabbatar da hakan, rai a ɓace yace "malam kasan dai haramunne, yin magana da matar da ba muharramarka ba ko?" jiki babu power Ibrahim ya miƙa tare da kama bakinsa da hannu, kafin yace "dan Allah a gafarceni abokina, ya bar gurin, itako shi take kallo, saboda a inda yai maganar sai ka rantse ita ɗin matarsa ce, Tunda yaga kallo ya koma kanta, ya tattara kayan yaje ya karɓo leda, yace ta tashi su wuce, haka dai ta tashi ba tare da tayi masa musu ba, Koda ya fara driving, sai satar kallonta yakeyi, magana ya farayi a cikin zuciyarsa, "bai kamata in sanarwa da yarinyar nan ina sonta ba, saboda wallahi zata yimin wata fahimta da ban, zan bari idan ta ƙara girma sai in sanar mata, Yes hakan ma shine dai-dai" Ya ƙare maganar yana murmishi yana shafa sajensa, har suka iso gida bai ce mata ba, itama bata ce masa ba, koda suka iso parking space, ta fara shirin buɗe murfin mota Arman ya hanata, yana son ya yaudarar da ita suyi hira, yace "Aysha dan Allah ki tsaya kiyi karatu ki mori lokacinki karki fara soyayya yanzu Please and please na roƙeki, idan kika duba shekarunki kwata-kwata bazasu wuce 14yrs ba, kinga kinada sauran lokaci....! Kaina bisa wuyana, insha Allah daga yanzu da izinin Ubangiji zaku dinga samun update koda yaushe. Mom Islam 08141799224 *NA KASA JUREWA*        🪻🪻🪻          Mom Islam Page 35-36 Sunkuyar da kanta tayi, kana ta janyo zaren mayafinta tana wasa dashi, gaskiyarsa ne, sai dai bata ma kai shekaru goma sha huɗun da ya ambata ma, Har ya gama yi mata nasiha ƙala bata ce masa ba, sai dai jinjina kai da takeyi, Daga ƙarshe dai suka fito a motar suka wuce ciki, gurin anty Tasneem,  a parlor suka sameta tana zaune tana waya, sai dariya takeyi,  "Aysha kinji ana ta kiraye-kirayen sallahar magriba Please kafin in dawo ki ajiye min abinci" To kawai ta ce masa ta miƙe, ko da ta shiga kitchen ɗin  tunani iri-iri ta farayi, sosai ta san da cewar ta shigo sabuwar rayuwa, sannan ta ga sauyi sosai a tare da ita, bayan ta gama zuba masa abincin ta kawo parlor ta ajiye a saman table ɗin dake a tsakiyar ɗakin, kafin ta wuce domin ta kabbara sallah, sbda anty Tasneem ma lokacin da ta dawo daga kitchen bata parlor, Sai da akayi sallahar isha'i sannan Arman ya dawo, time ɗin dukkansu suna zaune a parlor, Tasneem ta kalli Talatu kafin tace "Aysha ina tsarabar mu?" murmishi kawai tayi, kana kuma tace "yana can mota" Anty Tasneem ta sake jefo mata tambaya, "to wa kuka barwa?" Shiru tayi bata ƙara cewa komai ba, sai ga sallamar Arman, fuskarsa ɗauke da murmishi yake cewa "anty wai yarinyar nan taki bata magana ne?" Anty Tasneem ta kalli Talatu kafin tace "Arman me ka gani?", Sai da ya sake kallon Talatu kafin ya sake cewa "walhi anty shiru-shiru kamar ma yin magana yana wahalar da ita" a yanayin inda yake maganar sai ya bawa anty Tasneem dariya, itako Talatu tashi tayi a gurin sbda da gasken ita kanta tana jin kamar an sauya mata ƙwaƙwalwa da ma komai na jikinta, babu wata magana da anty Tasneem zata gaya mata ko faɗa bata riƙe shi a ƙwaƙwalwarta ba, a duniya tana mugun girmama anty Tasneem ko mai yasa oho, ta sauya ɗin kamar inda Arman ya faɗa, domin kuwa ada idan ka ji wacce ba'a ɗagawa ɗan yatsa sai ta karyeshi to ita ce, a yanzu kuma ko hannu ka sa mata a baki bazata ciza ba, ko meye dalili oho, Bayan tafiyar Talatu bedroom ɗinta, Arman ya matso kusa da anty Tasneem kasancewar tana saman couch mai zaman mutum biyu, "Anty gaskiya inada shawarar da zan baki, inhar wannan yarinyar zata daɗe a gurinki, kinsan me?" Anty Tasneem tace "a'a, ƙanina sai ka faɗa ina sauraronka" Arman yace "anty dan Allah karki bari yarinyar nan ta san menene so, sannan tasan abubuwan da suka shafi soyayya, dalilina na sanar dake, shine, ya kamata ta mori ƙuruciyarta da lokacinta da tunaninta, tayi karatu mai kyau, kinga da farko dai babu wani namijin da zai kalli Aysha ya ji bata shiga ransa ba sai dai in ƙarya yakeyi, saboda Ubangiji yayi mata baiwa ta ɓangarori da dama". Ya kai ƙarshen maganar yana cewa "anty Please ki fahimceni" Anty Tasneem tace "wallahi Arman duk wannan maganar da ka faɗa gaskiya ce, sannan insha Allah zanyi ƙoƙarin ganin na inganta mata komai nata wanda zata yi alfahari dashi a nan gaba, bana son rabuwa da Aysha, kasancewarta yarinya mai shiga rai, ga jin magana, tunda tafiyar da zamuyi next week mai zuwa Junaid yace sai end of the year zamuyi, kaga zan sake nusar da ita abubuwan da suka dace, wlhi Arman Aysha nima ta shiga raina ba sai an kai ga maza ba, yanzu dai abinda nake so, a nemo min makaranta mai kyau sannan mai tsada wacce ake karatu sosai, Sallama yayi mata kana ya wuce, da niyar zai bincika makarantar da za'a sakata, Washe gari, tunda Aysha tayi sallah bata koma barci ba, tunda ta fara azkar har sai da gari yayi haske sosai, ta fito taje bedroom ta gaishe da anty Tasneem da masu aikin gidan kana taje kitchen ta ɗora ruwa, can anjima ta shiga wanka. Ƙarfe 12:pm lokacin suna lesson a parlo, sbda har da Islamic duk yana koyarda ita, Arman ne yai sallama, suka amsa a tare, sam beji daɗin ganin wannan mai koyar da ita karatun ba, sabda sai wani kallonta yakeyi kallon ma mai ɗauke da fassara iri,  iri, bayan sun gaisa da malamin kai tsaye ya wuce ciki gurin anty Tasneem, daga corridor yake ƙwala mata kira, ta fito da sauri tana cewa "Arman wannan kira haka walhi ka tsoratani, murmishi yayi kafin yace "anty an samu makarantar, St Thomas, kuntau science Academy. Anty Tasneem tace "wow kenan yau zaku tafi ko sai gobe, amma kuɗina yayi ƙasa abinda ke account ɗina bai wuce 100k ba, nasan ba zai isa ba" Arman yace "karki damu ba sai kin bada kuɗi ba, amma ta shirya mu wuce, ina sauri zan wuce office daga nan" Har anty Tasneem ta fara tafiya, sai ta dawo da baya, kana tace "dama inason in ce maka, a aji nawa za'a saka ta, kaga tayi girma fa?" Nazari yayi kafin yace "gaskiya zan ce a sata a pr 3 yayi ko?" Badan ranta ya so ba tace yayi sai ɗan babu inda zata iya, a hakan ma adu'arta ɗaya idan aka zo yi mata intabiyu ta basu haɗin kai, Kai tsaye parlorn ya wuce ta samu Malamin tace masa, zasu je makaranta tunda dama shi ya bada shawara sannan yace idan ta dawo gida sai ya dinga zuwa yana sake tuna mata karatun, sosai ya ji daɗi yace "inada tabbacin insha Allah zatayi ƙoƙari sosai a makaranta, anty Tasneem ta faɗaɗa fara'arta kafin tace "Allah yasa" Talatu dake zaune gaban malamin tana rubutu, itama farinciki takeyi, dan ko a yanayin mood na fuskarta zaka tabbatar da haka, Cikin bin umarnin anty Tasneem ta miƙe ta sauya kaya zuwa riga da skirt English wear ta zura hijabi kana ta ɗauko wata ƙaramar jaka, wacce ma babu komai a cikinta sai lipstick, man baki. Ta fito, time ɗin Arman yana can kitchen dan ya kasa zaman parlor, sosai yake kishin duk wani wanda yake da burin yin taraiyya da Talatu, malamin yayi musu sallama ya fice, duk wannan abin da Arman yakeyi anty Tasneem bata sani ba. Sai da sukayi breakfast sannan suka wuce, ada Talatu farkon zuwanta bata jure yunwa, amma yanzu sai ta kai ƙarfe 1:pm bata ci komai ba, sabda haka rayuwar anty Tasneem take, bawai babu bane kawai ra'ayin ci ne bata da shi, amma bata hana wanda zai ci ya ci ba.    KEFFI Kwanci tashi asarar mai rai, Saudart har ta gama idda, tunda Dady yaga ta gama idda ya fara yi mata siyayya,kamar su kayan makeup har gurin gyaran jiki yake kaita, cikin ƙanƙakin lokaci Saudart tayi ƙiba ta murje gunin ban sha'awa, Wata ranar Asabar tana zaune a parlor tana danne-danne a wayarta, gefe kuma tirai ne na apple cikin shauƙin bin waƙar da ke tashi a wayar ta kai hannu zata ɗauki apple ɗin wayarta tayi ringing ga shi babu suna, sai da tayi ringing ta ƙatse ta sake yin ringing kafin ta ɗaga, "Aslmu alaikum da wa nake magana?" Saudert tai maganar sabda tana neman sani, "Dariya yayi, kai da kaji Muryar ma kasan ba ta saurayi bane, muryarsa ko daɗi babu, yace "yarinya nine Alhaji Alherin Allah, ina fatan dai kin sanni kuma zaki amshi soyayyata, saboda idan har kin amince bana son bikinmu ya wuce wata ɗaya dan nikam a shirye nake" Abinda ya bata mamaki bai wuce, tunanin da ta farayi ba, kamar tana yawan jin labarin Alhaji Alherin Allah a gurin dadynta, Daga can ɓangaren nasa yace "yarinya naji kinyi shiru?  Ko in baki lokaci ne?" "Eh" tace masa, sabda ko sautin muryarsa bata buƙatar ji, yana katse kiran ta miƙe zuciyarta na yi mata zafi wani dummm takeji a kwanyarta, cikin sauri ta wuce ɗakin momy, tana shiga ko sallama bata ma yi ba, dan ko lura da Dady dake kusa da momyn batayi ba, ta rushe da kuka mai tsuma zuciya, cikin muryar kuka take cewa "momy tsabar wulaƙanci da rainin wayo ko wane tarkace sai ya zo yace yana sona, walhi nidai na gaji momy zan bar garinnan Allah kuwa" Dady ya ɗan matsa a jikin momy kafin yai gyaran murya, kana yace "Saudart ki tsayar da hankalinki guri ɗaya, ba wani bane kike kira da tarkece face aminina Alhji alherin Allah, kuma nine na zaɓa miki shi a matsayin miji, Saudart ya kamata ki gane waɗannan samarin da suke ruɗarki,  basa wani iya riƙe aure ya kamata ki nutsufa, kuma kinga shi ba da wasa yakeyi ba" Saudart ta tashi zaune tana sake duban Dady wanda bata ma san yana ɗakin ba, Cikin ɓaci rai momy tace "hmm Alhji which tallahi zaka cutar da yarinyar nan, daga ƙarshe nadama ne zai biyo baya, saboda, yarinya da ƙuruciyarta ka ce zaka aurar da ita ga abokinka wanda a shekaru ma ya girme maka nesa ba kusa ba, tai maganar a hassale, Dady yayi murmishi, wanda daga ganin murmishin kasan ya tara ma'anoni da yawa, yace "wato Zainab har yanzu baki san me duniya take ciki ba, ya kamata ki nutsu ki san me kikeyi a duniya, kinsan Allah idan baki mori duniya ba, sai ki tashi jahili ma ya fiki muƙami, kinga kuwa Naira abar so ce ga kowanne halitta" yai maganar yana gimtse fuska, Nidai na gaya maka bazan amince ba, tun yanzu ayita ƙirga mata ɗakin aure, wancan auren tayi maka biyayya, wannan ai sai ka bari ta zaɓi wanda takeso ko?" Momy tai maganar tana bubbuga bayan Saudart, "Wato Umarni kenan kike bani?, to bari kiji ko ƴan uwana ne suka shiga cikin lamarin aurannan wallahi zan iya ɓata wa dasu, saboda akan kuɗi babu abinda bazan iya yi ba, sosai ta jinjina kai, sabda sarai tasan halinsa, farin sani ma kuwa. Shiru tayi bata ce dashi komai ba, har ya tashi ya fice, BAYAN SATI ƊAYA. Alhaji Alherin Allah bai sake kiranta ba har tsawon sati guda, kamar kullum idan ta ɗan taya momy aiyukan takan je ta kwanta barci, hakan ko tayi inda take ta mafarkai iri daban daban, guɗa takeji, tayi tunanin ma a farkin ne akeyi, sai tajiyo Muryar momy a kanta cikin condition na ɓaci rai tana ce mata, Saudart ki rungumi ƙaddara walhi mahaifinki har ya karɓi kuɗin aurenki miliyan huɗu, da sauri Saudart ta tashi zaune, tana jujuya hannaye ta kasa magana, sai wani irin yanayi takeyi, daga ƙarshe dai ta fashe da kuka, momy ta rungumeta tana cewa "bari inje kayan sa lalle suka kawo, wai bikin nan da two weeks," Saudart kam ta kasa magana, har momy ta fice, sai dai bin bayan momy da kallo da tayi, ganin maganar momyn takeyi kamar a mafarki, ta fara mutsike idanu domin tabbatarwa, "ba fa ƙarya bane tunda ga shi can anata surutu a parlo" tai maganar tana share hawaye, Acan parlor kuwa akwatuna ne guda goma cif cike suke da kaya na gani na faɗa, masu kawo kayan ma cewa suke yi saura akwatiin ɗaurin aure" ita dai momy bata um bare u um, ko da suka zo tafiya, lokacin Dady ya dawo ya basu 100k, sukayi masa godiya suka wuce, kai tsaye parlorn ya shigo, inda ya samu momy da Saudart a zaune sun tasa akwatuna a gaba kowanne yayi tagumi...! More comment more typing Mom Islam 08141799224 *NA KASA JUREWA*     🪻🪻🪻 Mom Islam 37-38 "Ku kuma mai ya faru kun wani yi tagumi kamar anyi muku rashi?" Dady yai maganar yana neman guri ya zauna, Har yanzu babu wanda ya bashi amsa sai ma kuka da suke yi ita da momy, Tsawa ya daka, musu tare da cewa "Saudart ki tabbatar da kin lallashi zuciyarki, domin kuwa aure babu fashi, sannan idan naji wata magana ta ɓullo ki kuka da kanki, yanzu ma dai duk ba wannan ba, zo nan" Ta taso jiki babu ƙwari, nuni yayi mata da inda yake zaune, tazo ta zauna kusa dashi, ya ciro wayarsa kana ya shiga jiji app, wasu haɗaddun kayan furniture's ya nuno mata, kai da ganinsu ma kasan ba a Nigeria aka yi su ba, sunyi kyau sosai, sai dai a idanuwanta ne kayan suka birgeta a zuciyarta kuwa sam basu bata sha'awa ba ko kaɗan, "ki zaɓi wanda kikeso," Dady yai maganar yana sake nuno mata wasu, "ko wanne ka zaɓamin Dady sunyi" Saudart tayi maganar  cikin rashin walwalah, Ganin kar suyita jayayya yasa ya kashe datansa ya koma kan momy, "Zainab kafin biki nake son mu tashi daga gidannan mu koma wanda na siya" itakam momy ma bata da masaniyar ya siyi wani gida, sbda ada ne yake shawara da ita ban da yanzu da ya kama gashin kansa, "Bata amsa masa ba, sai ma ce masa da tayi, "yaushe Anam zata dawo?" shiru yayi na ƴan wasu lokuta kafin yace "kwanan nan" Kwata-kwata yanzu ta kasa yarda da Dady, ta kasa jure wasi wasinta sannan tana tunanin kar fa, ya je ya aikata wani abun da ƴarta, hankali a tashe tace "Habiby ka kira min ita mu gaisa koda yaushe bana samun ta a waya WhatsApp ma ta daɗe bata hau online ba" "Haba Zainab da ba haka kike ba, yanzu kin sauya sosai, na ce miki tana nan lafiya ko? ki kwantar da hankalinki, ai basuyi hutu ba" Gudun kar suyita jayaiyya a gaban Saudart yasa tai shiru. Bayan kwana bakwai, biki ya rage saura sati biyu, babu abinda momy ta yiwa Saudart, sannan ko tattauna maganar bikin basayi, kowa harkar gabansa yakeyi, sai dai shi dadyn in ya shigo ya fara damunsu da maganar abubuwan da za'ayi shine suke ma tunawa da maganar wani buki, Waye Alhji alherin Allah?, Wani babban mutum ne, wanda ya gurmewa mahaifin Saudart ɗin nesa ba kusa ba, yana da dukiya ta ban mamaki, yanada mata ɗaya, da yara biyar a cikinsu huɗu sunyi aure uku mata ɗaya namiji yarinya ɗaya ce take gaban matarsa Hajiya Zaliha, Hajiya Zaliha ƴar asalin garin mai duguri ce, kirarin ta shine, bata zama da kishiya, wasu ma har sunayi mata kirari da wai shiga da alwalarka, Matan su uku biyu sunyi aure a ƙasar waje, ɗaya kuma tana nan a Keffi anan tayi aure, tsakaninta da gidan iyayenta beyi 200 ba, sunanta Salma, tunda taji mahaifinta zeyi aure, tasa aka yiwa Hajiya Zaliha sabon furniture's da odar magungunan mata, a cewarta ƙarya ne amarta ta nuna mata wani abu, itama Hajiya Zalihan tana nan tana faɗi tashi gurin bokaye da ƴan bori, sabda taga an fasa auren, sai dai kash duk inda taje, sai suce mata wannan auren duk wanda yai shishigi a lamarin auren yana iya rasa rayuwarsa, ɗibarsu tayi ta watsar sbda ta dangana komai ga kanta, ita zata ji da komai, dama koda yaushe cikin ado da tsafta take, ya kasance ta ƙara a nada, duk da ta fara manyanta har gyaran jiki akeyi mata, ga gyaran gashi da ake turarashi da turaren mai duguri, tun kafin bikin kullum basa zama a gida ita da yarinyarta Salma, Salman bata taɓa aihuwa ba, sunyi neman magani har sun gaji, koda mijin yayi niyyar ƙaro aure, Salma na jin labari zasuje gurin boka a rufe masa baki, sai maganar ta shiririce. Kwanci tashi asarar mai rai, yau ta kasance Friday wato ranar sa lalle, momy kam bata gayyaci kowa ba, ta ɓangaren dady, kam yayi gaiyyata harda su gaiyyar soɗi, an cika gida sosai, 200k Dady ya mikawa Saudart, bayan kaya wanda zata sa daga yau har zuwa gobe ɗaurin Aure da yayi mata, dan ko na akwatin ma ba'a taɓa ba, har yanzu a cikin gasgata maganar auren takeyi, sbda ko kaɗan bata jinsa a ranta, ƙarfe 5:pm wayarta tayi ringing, lokacin suna zaune da Dady a ɗakinsa ita da momy, tai banza da kiran, wayar ta sake ringing, Dady ya lura da yanayinta, yace "amma kamar kiranki akeyi ko?" "Eh...eh" Saudart ta amsa masa bakinta na rawa, Wayarta ta sake yin ringing a karo na uku, dole ta ɗauka ba tare da ɓata lokaci ba, "Assalamu alaikum" ta faɗa tana cin ɗaci a ranta, daga can ɓangaren ya amsa da wa'alaikumussalam masoyiyata" gabaki ɗaya muryarsa bata yi mata daɗin sauraro, babu inda ta iya, dole ta ci gaba da jin me zai ce, "gani a ƙofar gidanku ki fito ina jiranki, Momy dai ta mayar da hankalinta a kan wayar da ke hannunta, bata ma san me Saudart ɗin take ciki ba, sai Dady da yake sa mata idanu, ɗagowa tayi ta kalli Dady wayar na ƙare a kunnenta, sai kuma ta juya ta kalli Momy da take ta murmishi ga dukkan alamu bata ma san wainar da ake toyawa ba, "Idan wata matsala ta biyo baya walhi ki kuka da kanki" Dady yai maganar cikin ɓacin rai, miƙewa tayi ba tare da ta sake magana a wayar ba, ta fice, kasancewar dama da hijabi a jikinta, bayan ta buɗe get ta hango motarsa a gefe, jiki a sanyaye ta ci gaba da takowa har zuwa gurinsa, tsayawa tayi cak, tare da rungume hannuwanta a ƙirji, yana daga cikin mota yana ƙare mata kallo, sai wani lashe baki yake kai kace maye, "innalillahi walhi zan more, kai kai dole in dinga bawa yarinyar nan kulawa ta musamman, da zarar ta shigo gidana zan nuna mata so da ƙauna" har ya kai ƙarshen zancen zuci da yake yi bata ƙara so ba, tana tsaye ta sunkuyar da kanta ƙasa, Allah sarki Saudart yarinya mai biyayya. Rage gilashin motar yayi, kana yace "haba my wife ki ƙara so mana" cikin suɓutar baki tace "waye wife ɗin?" Cikin samun ƙwarin gwaiwa yace "ga ki tauraruwata" yai maganar yana nunota, "hmm" kawai tace, ya buɗe mata ɓangarensa yace ta shigo, "a'a" nan ma yayi, ta faɗa tana gyara tsayuwarta, "motsin buɗe get da taji ne ya sa ta yi saurin matsawa, ta fara ƙoƙarin shiga motar, murmishi yayi sabda hakan yayi masa daidai, koda ta shiga sai wani irin kallo yakeyi mata, kai kace yau ce rana ta farko da ya taɓa sanya mace a idonsa, ya ɗan matso kana yace "shekaran jiya nayi miki text message akan ki gayamin abubuwan da kike buƙata sannan kamar nawa ne zai isheki yin siyayya?" "Bana buƙatar komai, saboda inada komai" Tai maganar tana matsawa, saboda a inda ya matso suna iya jiyo numfashin juna, "A matsayina na mijinki ya kamata ace mun fahimci juna kafin ki shigo gidana, amma naga kamar bakya wani mararin kasancewata a tare dake" kamar jira takeyi ya gama magana caraf ta karɓe da cewa "eh mana auren dole Dady zai yimin, kaima son ranka kabi, baka tunanin ya rayuwa zata kasance, ko kana tunanin auren da akayi shi ɗaya bayaso ana samun farinciki?, washe baki yayi, kafin yace "haba (SaudatatulBash) sunan da nayi miki laƙabi dashi kenan, ai duk wannan ba damuwa bane, zan sa ki soni sosai da sosai, sannan nayi miki alƙawari idan munyi aure da sati ɗaya zamu tafi yawon shakatawa acan zaki fi sakewa, sai ƙasar da kikeso nan zamuje" ita dai jinsa take, abu ɗaya wanda ta ƙudurewa zuciyarta shine, idan ma ta tayar da hankalinta ba fasa auren za'ayi ba, tasan halin Dady sarai idan har ya sawa zuciyarsa zai yi abu to babu makawa sai ya aiwatar yake jin daɗi, shi yasa ta ƙudurewa zuciyarta Tata ƙaddarar kenan babu inda zata yi, dole ta rungumi ƙaddara, koda ta gaji da surutansa, ta ce masa, "zan koma gida inada aiyyuka da yawa" Washe haƙora yayi kana yace "eh lallai kam nasan kinada aiyuka sabda gobe I War haka kina gidana" wani ƙululun baƙin ciki ne ya tokareta, ta fito ba tare da ta jira maganar da zai ƙara yi ba, "Lokacin da ta ji alamun buɗe get tayi tunanin Dady ne yake shirin fitowa, sai taga babu kowa, Da sauri ta buɗe get ta shige, koda ta shiga masu aikace-aikace dangin Dady sai guɗa suke yi mata, sam baya mata daɗi sai takejin inama Allah zai ɗauki rayuwarta ta huta tsabar takaici, ko da ta dawo kai tsaye ɗakinta ta wuce, acan ta sami Momy tana ta kuka, duk a tunaninta ita kaɗai ce wannan auren be yiwa daɗi ba, ashe har da mahaifiyarta, cikin raunin zuciya tace "Momy kwata-kwata bana ganin Anam ko a WhatsApp ne fa, Anam ɗin da ko kwana ɗaya bamayi bamuyi magana ba, cikin suɓutar baki Momy tace "shikenan na rasa ki Anam, shikenan Anam" tai maganar tana sake rushewa da kuka mai tsuma zuciya, da sauri Saudart ta riƙe hannun Momy, itama ta fara kuka, cikin muryar kuka tace "Momy me kike nufi? mutuwa tayi ko me?" Momy ta toshe bakinta da hannunta sabda

Chapter 8 of 22