hali ne, yana iya yi mata abinda yafi haka"
Hamdala tayi sai ma taji yunwar da takeji ya ragu, tunani ta farayi to wa zata aika ya siyo mata abinci?"
Yanzu ba kamar ɗazu ba ta ɗanji daɗin jikinta, ta fito parlo sanye da ƙaton hijabi, ta murɗa handle na ƙofar taji a kulle, a fili ta furta "kodai Ma'aruf yana son kasheni ne?"
Tun jiya da yabar gidansu bai koma ba, sannan ya juya sim ɗinsa dan karsu kirashi, yana zaune a office sanye shadda mai ruwan ƙasa, tayi masa kyau sosai, idanunsa na nanne cikin baƙin gilashi, sai juyi yake a kan kujera,
Idanunsa a lumshe suke, duk da tulin file ɗin dake gabansa bai hanashi jin fargaba ko wani abu ba, nocking akayi yanaji yayi burus becewa me ƙwanƙwasawar ya shigo ba, sai da akayi sau uku kafin yace "Yes come in"
Tunda ya buɗe ƙofa ya hango mutumin nasa yasan yau yanajin rashin mutunci, sbda ba lallai su kwashe ta daɗi ba...!
More comment more typing
08141799224 WhatsApp only
Share fisabilillah inci arziƙin Manzon 👏
Mom Islam ce....
[7/12, 2:33 PM] Mom Islam: *NAKASA JUREWA*
🪻🪻🪻
Mom Islam
Domin samun more pages kuyi following ɗina a Arewabook danna blue link👇
https://arewabooks.com/u/momislam11
Ga wanda basa Arewabook ga link na Wattpad hilis ayi following ɗina 👇
https://www.wattpad.com/user/Momislam2021?utm_source=android&utm_medium=link&utm_campaign=invitefriends
Page 5-6
"Kai abokina kana cin duniya fa, kaga inda ka sake yin fresh kayi kyau, gaskiya amaryarmu ta iya kula da miji Masha Allah, ai da naso ma in..."
Muhammad ya faɗa yana dafa kafar Ma'aruf.
"Kai dalla kauce ka bani guri, uban me ya kawo ka office ɗina?"
"Nazo inji ya aka kashe boss ne a daren jiya"
"Mtsw tashi ka fitar min wallahi zan ci ubanka"
Dariya Muhammad yakeyi son ransa, dan ya lura abokin nasa yau a up yake,
Ganin baya son wasan ya nemi guri ya zauna har yanzu fuskar Ma'aruf ɗin a murtuke take, yace "abokina Hajiya ce ta aikoni wai idan ka tashi a office tana nemanka",
"Naji"
Ma'aruf ya faɗa a taƙaice.
Koda Muhammad ya gama zamansa ya miƙe tare da yi masa sallama, bai samu albarkacin amsa wa ba ya fice, tunda ya isar da saƙon da mahaifiyarsa ta bashi.
Wani ƙululun bakin ciki yaji ya turnuƙe shi, kasancewar shiɗin ɗan duniya ne ya basar tare da duba time 5:20pm ya rufe takardun da ya buɗe dan yau be taɓuka komai ba, ya rasa nutsuwarsa, kai tsaye hanyar gidansu ya nufa, sai da ya biya gurin mai siyarda banƙararriyar kaza ya siyo guda huɗu, na Hajiya ɗaya na Anty Jamila ɗaya, sai nashi ɗaya ɗayar kuma 🤔ina tunanin na Saudart ne uhm.
Horn yayi aka buɗe masa get, ya kutsa hancin motarsa ciki a parking space ya ajiye motar tare da fito da ledojin, kana ya shiga ciki,
Da sallama ya shiga babban parlon nasu tare da ƙwalawa Hajiya kira saboda bata parlo, babu kowa sai ƙarar TV,
Daga bedroom ɗinta ta jiyo muryarsa, da sauri ta fito tana washe haƙora, tana cewa "ɗan albarka, inata cigiyarka, naso in shigo gidan naku sai nayi baƙi"
"Hajiya ai dama inada niyar shigowa, sai ga Muhammad ya biyoni har office"
Ma'aruf ya faɗa yana ajiye wa Hajiya mama leda biyu,
Cikin farinciki ta ɗauko ledar tana cewa "amma dai Saudart na nan lafiya ko?"
"Eh Hajiya, tace ma a gaishe ki, da zamu shigo tare, sai kuma na shigo kafin in shiga gida"
A wannan karon hankalin Hajiya mama ya kwanta sosai, dan a iya tunaninta Ma'aruf ya sauka kama inda zuciyarta ta labarta mata,
Nan sukaci gaba da fira kamar babu wata damuwar da ta gifta a tsakaninsu,
Anan gidan hajiyar yai magriba yai isha'i, a takaice ma anan yaci abincin dare.
Ƙarfe 9:pm ya miƙe yana danna wayarsa, "Hajiya banga Anty Jamila ba ina ta shiga ne?"
"Ai ba kwanan gidannan ba yau kam, taje ƙauye"
"Ƙauye??"
Ya maimaita, "eh mana, nasan kai baka son zumunci shiyasa kake ƙyamatarsu, duk ɗan halak baya ƙin asalinsa, komai daren daɗewa dole kaje ka dubosu"
Kawar da kai yayi, tare da cewa "Hajiya sai da safe"
"Allah ya bamu alheri"
Hajiya ta faɗa, ta yago jinyar kaza, tare da binsa da murmishi.
"Allah ya tsallakar dani wannan case ɗin"
Ma'aruf ya faɗa time ɗin da yake ƙoƙarin shiga mota.
Kai tsaye ya wuce gidansa,
Bayan an buɗe masa get yayi parking motarsa,
Ya fito da ledojin tare da jakar aikinsa kana ya wuce ciki,
A parlo ya sameta tana zaune saman Capet hannunta rike da gorar hollandia yoghurt, gefe kuma tsire ne ta baje tana ci,
Sosai yayi mamakin, ya akayi ta samu arzikin cin waɗannan kayayyakin, koda yake bai kamata yayiwa kansa wannan tambayar ba,
"Amma waye ya siyo mata?"
Shine tambayar da yake yiwa kansa,
Niko nace horo da yunwa?
A zahiri taji shigowarsa, sbda ko sallama beyi ba, a matsayinsa na cikakken musulmi, ƙin ɗago kanta tayi bare ta nuna masa tasan da shigowarsa, dogon tsaki yaja "mtswww" tare da take mata ƙafa, har sai da ta ƙwalara ƴar ƙara, cikin jin tsananin azaba tace "sai Allah ya sakamin"
Har ya wuce ya dawo da baya, kana ya bige mata baki ya wuce.
Hannu ta ɗora a saman lips ɗinta cikin jin zafi ta runtse idanunta.
*****
ƘAUYEN ƊAN ƁAURE
Tuntsurewa tayi da dariya lokacin da take gwaguyar goruba, kafin ta kalli ƙawarta Gudidi tace "yasin raken Iliya kamar an zambaɗa madara da suga, wai kinhya kinji kuwa?"
"A'a Talatu ɗan hammin mana"
"Alƙur'an se kinyi min alƙawari"
Talatu ta faɗa tana ƙwalalo idanu.
Talatu ta sake cewa "kasuwa yau bana son Inna ta sani, idan na hammiki rakena kina faɗa wa Inna ga inda naje, wallahi tallahi sai nayi ƙulikulin kubura dake"
Talatu ta ƙarashe maganar tana murguɗa baki,
"Zaro ido waje Gudidi tayi, kafin ta haɗiyi wani miyau maƙwat, kana tace "yo ni hauka nakeyi Talatu? wallahi ko haurawa ta katanga kikayi bakina ƙanin ƙafata, amma dai hammin raken sbda miyau ɗina ya tsinke"
Talatu ta washe haƙora gami da cewa "ahe dai kina sona"
Gudidi tace "sosai ma"
Kafin ta gutsiro mata raken sai da ta gama wanke shi da miyau kafin ta miƙa mata, Gudidi na ƙarɓa ta ruga da gudu tana cewa "wallahi sena faɗa me warin baki kawai, da hakori kamar na kaza"
Sosai Talatu ta tunzura domin tabi Gudidi da uban gudu, cewa takeyi "tsohuwar munafuka zoki biyani raken da na baki, yau ko zaki hige cikin Ramma sai na ƙwaƙuloki"
Karaf sai a kunnen Ramma, mahaifiyar Gudidi, "ke Talatu uwa naji kamar zagina kikeyi?"
Ramma tai maganar tana yiwa Talatu daƙuwa,
Murguɗa mata baki Talatu tayi kafin tace "ki gayawa Gudidi ta biyani rakena"
"Dalla can tafi kiba mutane guri, lokacin da kika bata raken kin nuna min?"
Talatu ta wani murtuke fuska tare da riƙe ƙugu tace "kunci bahi, daga ke har ƴar taki"
Ta faɗa tana ficewa daga gidan.
Tunda Gudidi ta tabbatar da Talatu ta shigo gidansu take ta leƙe ta windo ga wata uwar zufa dake ta tsatsa tsafo mata,
"Ramma wallahi kibi Talatu a hankali ko kin mance wacece ita?"
Ramma ta wani mulmulo uwar ashar ta yiwa Gudidi gami da cewa "idan na sake ganinki tare da wannan yarinyar wallahi sai na lahira ya fiki jin daɗi"
"Toh" kawai Gudidi tace tana cino baki.
Tunda Talatu ta fice daga gidansu ta wuce can gonar baban Gudidi, mijin Ramma kenan,
Daga nesa ta hango shi, ya haɗa zufa sosai yasha aiki, sai da tayi nazarin kalaman da zata gaya masa, kafin ta ƙarasa gurinsa, har ƙasa ta durƙusa tace "ina kwana baba" lafiya lau ƴar albarka ya Innar taki?"
"Tana lafiya lau baba"
Gudidi ta faɗa tana sunkuyar da kai.
"Baba dama nazo in sanar dakai wani abu, amma kayi haƙuri baba"
Talatu ta faɗa tana wasa da sanda wace ta tsinta a inda take tsugune,
"Ina jinki ƴata gayamin koma menene, domin na yaba da hankalinki"
Talatu tace "baba dama kullum idan zamuje kai niƙan tuwo injin me Kano, kullum sai Gudidi ta tafi da leda ta rage gari, da na tambayeta sai tace wai Ramma ce tace mata ta dinga yin haka, tunda wai kana barinsu da yunwa sai kaje can waje kaci abincinka me rai da lafiya"
Koda takai ƙarshen maganar ta miƙe tsaye tare da cewa "amma dan Allah karka ce nice na faɗa maka, saboda gudidi ma taso gaya maka Ramma ta kamata tayi mata duka"
Jikin baba na rawa yace "yarinya Nagode, badan kinzo kin gayamin ba wlhi babu inda za'ayi in sani, ungo wannan kyasha alewa"
Ta durƙusa ta karɓi kuɗin tanayi masa godiya.
Har tayi nisa da hanyar gonar, bata duba ko nawa ya bata ba, sai da ta kusa da ƙofar zuwa gidansu kafin ta duba kuɗin, nera Hamsin ce,
Sosai tayi murna, tana ta taka rawa, tana cewa "idan rabonka ya rantse, kai kai kai idan rabonka ya rantse, ɗin ɗirin ɗin"
Ta ƙulle hamsin ɗin a hannun zani kana ta shige gidansu da gudu.
A tsakar gida ta samu Inna ta raba dambu, kasancewar shi suka girka, "wayo daɗi kaheni wuya barni" Talatu ta faɗa tana cigaba da taka rawa,
Kasancewar tsakar gidan nasu yanada tsaki, ita kuma Talatu tana can nesa, Inna tace "Talatu ina kikaje nasa a dubomin ke kizo ki ɗauki allo ki wuce islamiyya ba'a ganki ba"
Tofa.
Daga can inda take ta buga tsalle ta faɗi tik a ƙasa, ko gezau tunda dama ta riga ta saba, kurma ihu tayi tana cewa "wayyo na mutu na lalace wayyo na balaga ayimin aure wayyo Inna bata sona"
Inna na zuba yaji bata san lokacin da taketa zubawa a ƙasa ba, dan a iya tunaninta a abinci take zubawa,
Mamaki suruntun Talatu ya bata ko da yake ma, ai ba yau ne farau ba, inda sabo ma ai yaci ace ta saba,
Da gudu ta bita tana cewa "wallahi sai kinje makaranta, idan kika zauna a gida me zaki tsinana banda yawo a gari?"
A zauren gidan ta laɓe tanajin maganar da Inna takeyi, tana murguɗa baki.
Tana ganin Inna ta gama rabon damu ta wuce ɗauki, ta siɗaɗo a hankali taje ta ɗauki nata, ta nemi guri ta raɓe ta fara ci, duk wanda ya shigo ya ganta ze ce marai niya ce.
Ashe har tafiyar da takeyi a hankali da zuwanta ɗaukar abinci duk Inna ta gani, sai da ta bari tayi nisa sosai kafin ta leƙo, hannunta rike da bulalar inji ta riƙeta gam, tare da haɗe mata hannaye, cikin kururuwa take cewa "Inna kiwa Allah da ma'aikinsa ki yi hakuri Inna ki duba darajar Musa me jaki da tantabaru, Inna ki duba darajar Hama me tuyar ƙosai, kasaƙe Inna tayi tana jinta, abin ya matuƙar bata mamaki, sai haɗata da sana'ar iyayenta da basa raye take yi,
"Na duba darajarsu, amma ki tahi ki wuce makarantar Allo"
"Inna nifa malamin ne sai ya dinga ɗagamin gira, ɗan iska ne yasin"
Talatu ta faɗa tana buga ƙafa.
"La hula wala ƙuwwata illa billah ni Zainabu naga abinda ya isheni"
Inna ta faɗa tana riƙe haɓa,
"To tashi in rakaki yanzu"
Babu inda ya iya dole ta tashi ta ɗauko hijabinta, sbda basa wani rayuwa da hijabi, idan aika yayi nisa haka suke tafiya, koda yaushe rayuwarsu ta sanya riga da ban zani da ban ne.
Suna isowa makarantar, Talatu ta zame hannunta a na Inna, a hankali tace "Inna duk maganar da na gaya miki akan malaminnan ƙarya ne wallahi, dan Allah ki koma tun daga nan karki kaini gurin hi, gardawa zesa su ɗagani ya zaneni.
"To naji, amma tsan tsaya anan har sai naga higarki"
Inna ta faɗa tana yi mata nuni da yatsa,
"Wace ni Inna zan higa fa dan Allah ki koma kar malam yace "nayi taurin kai ne kikai min raki ya"
Sam bata son a daki Talatu, hakan yasa ta juya tana murmishi.
A gindin bishiyar mangoro suke yin karatu, inda suke shimfiɗa tampol a gurin, maza na can gefe mata ma suna gefe,
Kusa da gudidi taje ta zauna, cikin ƙasa da murya tace "idan kere na yawo zabo na yawo wata rana za'a gamu, wa na kama?"
Gudidi tayi wulli wulli da idanu, cikin marairaice murya gudidi tace "dan Allah dan Annabi Talatu kiyi haƙuri bazan sake ba, daga yau zan dinga ce miki abinnan da ƴan binni suke gayawa yayunsu, Antu yake ko meye ma? "In kinso kice gwaggo babu abinda yai tsalle ya wankan mari, kizo kawai mu cire raini, ta cukuikuyo mata wuyan hijabi, ƙara Gudidi ta tsanda wanda yaja hankalin malam dake biyawa ɗaya daga cikin ɗaliban karatu, da sauri ya tashi tsaye da zafgegiyar dorina yace...!
Page 7-8
"Wai ke wace irin sheɗaniyar yarinya ce?, a islamiyya ma bazaki rabu da wannan yarinyar da kika sa a gaba ba? kullum sai an rabaku faɗa kenan"
Haba ai tunda Gudidi taji malam yana yiwa Talatu gargaɗi, ta saki baki ta fara bashi labarin rashin jin Talatu, a take a gun ya tsula mata bulala har uku, sam batayi kuka ba, sai dai tayi ƙwafa, irin "zamu haɗu ɗinnan"
••••••••
SINGAPORE
Bulan Island
Wani haɗaɗɗen gida na hango wanda komai nasa da remote yake amfani, hatta get ɗin ya haɗu ya gama haɗuwa, kutsa kaina nayi ciki yayinda nake ta ƙoƙarin kwaso muku jawabi, ƙarewa farfajiyar gidan kallo nayi, wanda yai matuƙar ƙayatar dani, "Masha Allah" na faɗa a cikin zuciyata, gidane na gani na faɗa, gidane wanda idan ka shige shi zaka rantse waɗannan mamallakansa basu da labarin talauci a duniya, sosai yanayin tsarin shuke-shuken zai birge me karatu, hmm yo gini ne na turawa,
Wata matashiyar budurwa ce ta fito daga wata ƙofa, wacce na tabbatar da ta danna wasu lambobi ne yasa ƙofar buɗewa, a ƙalla budurwar zatayi 23yrs cikin shiga ta nuna tsaraici, daga ganinta kasan babu musulunci a tare da ita, riga ce a jikinta ƴar yaloluwa milk color, ko Cibiyar ta bata rufe ba, sai ɗan mini skirt ɗin dake jikinta pink color iya cinya, kayan sun matseta sosai, ƙafarta kuwa takalmi ne mai bala'in tsini, duk igiyoyi ne a jikinsa, hannunta riƙe da handbag, gashin kanta har gadon baya, fara ce tass kunsan dai fari irin na turawa, ita ɗin baturiya ce..
Batsha kenan yarinyar mai ji da kyau.
Ci gaba da tafiya tayi, inda ta iso parking space securities suna take mata baya, ɗaya daga cikin scuritin shine drivernta, bayan ta shiga back side shikuma ya shiga mazaunin driver, "Madam ina zamuje?"
Yai maganar cike da girmamawa,
Am sorry to say da yare suke maganar, mukuma zamu ci gaba da yarenmu na Hausa, lolx.
"Kaini Ariana hotel"
Okay scuritin ya faɗa cike da girmamawa,
Tunda suka iso Hotel ɗin na gama tsinkewa, saboda kai da kaga kyau da tsarin gini kamar ba da bulo akayi ginin ba, ga wasu flawoyi da walwali da gurin yakeyi, bayan an buɗe musu get ya kutsa motar ciki, a inda ake parking ya ajiye motar kana ya fito ya buɗe mata ƙofa, takai kamar 10mins bata fito ba, can sai gashi ta zuro kyawawan ƙafafunta wanda suka sha adon jan farce mai kwalliya, buɗe hand bag ɗinta tayi kana ta ciro wayarta ƙirar 💕 ta kara a kunnenta, "Hello Vijay ka gayamin number"
Daga can ɓangaren wanda ta kira da Vijay ɗin yace "144" ta katse kiran tana yiwa scuritin alama da ya tafi, girgiza kai yayi kana ya shiga mota ya wuce.
A hankali take takawa kai kace tana tsoron taka ƙasa, har ta isa cikin Hotel ɗin, my fans Ina baku labari wani sassanyar sanyi naji ya ratsa kowacce gaɓɓa ta jikina, tunda nikam ba saba zuwa nayi ba, amma anam zan barta,
Bayan tayi musu bayani, ba tare da ɓata lokaci ba kai tsaye ta wuce room ɗin, yana zaune saman bed ta sameshi daga shi sai boxer ƙirjinsa a cike da gashi,
Yana ganinta ya miƙe tare da hugging ɗinta ya manna mata kiss a kumatu yana cewa "i miss You pretty"
Wani farr da idanu tayi masa wanda ya daɗa sace zuciyarsa, ya wani rungume ta ya sinsinar wuyanta, my pretty wane irin turare kike using kowane time sai inajin shauƙi idan muna tare" rufe masa baki tayi da nata, kana ta kashe masa one eye tace "uhhh muyi selfie mana, two days bamu haɗu ba"
Kamar koda yaushe idan sun haɗu sai sunyi hoto, yau ma hakan ta kasance, tana rungume a ƙirjinsa shikuma babu riga ga shi ƙirjin nasa duk gashi yayi masa luff, ta wani kwantar da kanta a saman ƙirjinsa, sunyi kyau sosai, kamar koda yaushe idan sukayi hoton suna ɗorawa a media, haka yau ma ta kasance, duk wasu kafafe da suke yi sai da suka ɗora shi.
ABUJA NIGERIA
"Saudart!! Saudart!! Saudart!!" firgit ta tashi daga barcin da takeyi, jiki na karkarwa sbda wannan kiran da yakeyi mata cikin ƙaraji yakeyi,
"Na am" tace, murya a sanyaye, tana takowa har inda yake,
"Saboda yawon dare da kike zuwa ne yasa baki tashi da wuri ko?"
"Yaya ban fahimci abinda kake cewa ba?"
Sai da Ma'aruf ya ƙare mata kallo up and down kafin yace "oky kinaso in baki labarin fitarki ta jiya ne?"
"Jiya kuma zuwa ina?"
"Zuwa gidan ubanki"
Ma'aruf ya faɗa ransa a ɓace, "are you nonsense?, me kike nema a duniya, Saudart na tsaneki na tsaneki har abada bazan sake sonki ba wallahi ki ficemin a gida, ya sanya hannu cikin aljihun wandonsa ya ciro bandir na ƴan dubu-dubu, guda biyu ya watsa mata tana durƙushe a gurin tana rusa kuka, hannunta na karkarwa da wayarsa a hannunta, ya fizge tare da shureta da ƙafafuwansa, har ya fara tafiya, sai kuma ya dawo da baya, ba tare da ya juyo ba, cikin kakkausar murya yace "zan shiga wanka, idan har na fito da ga wanka baki bar min gida ba sai kinyi nadama"
Ya ƙare maganar yana cigaba da tafiya.
Rushewa tayi da kuka mai tsuma zuciya, a fili ta dinga maimaita innalillahi wa inna ilahir raji'un, zafafan hawaye ne suke ta zarya a kumatunta,
Jiki babu ƙwari ta miƙe, a fili ta sake furta "na gaji da wulaƙanci da cin mutunci, cikin ƙarawa kanta ƙwarin gwaiwa tace "ko me za'ayi yau sai ya sakeni, idan ya sakeni shikenan, Dady bazai sake matsamin akan komawa gidansa ba"
Tayi maganar tana share hawaye,
Yaushe rabonta da ta shiga sashen sa, har ta manta,
Cike da ƙwarin gwaiwa ta ci gaba da tafiya har ta iso ƙofar ɗakinsa, inda kasan ƙwai ya fashe mata a ciki haka tayi, ƙirjinta sai dukan uku-uku yakeyi, da sauri ta sake ƙoƙarin kawar da tsoro, ta yi nocking da ƙarfi, sam beyi tunanin ita ba ce, sbda tunda waɗannan abubuwan suke faruwa ko inda yake bata zuwa, buɗe ƙofa yayi fuska a tamke, daga shi sai gajeren wando da farar singileti ya waro ido, sai kuma yaci magani yace "wa ya baki izinin zuwa bakin ƙofa ta?"
"Babu wanda ya bani izini tunda ba gidan ubana bane"
Sosai yayi mamakin zafafan kalaman da Saudart ta gaya masa,
Ya ɗaga hannu zai kai mata mari ta riƙe hannun cikin ƙarfin hali tace "a wannan karon na kasa jure wulaƙanci da tozarcinka, haba Ma'aruf, ko a bola ka tsintoni ai na ci darajar ɗan adam, bare a gidan iyayena ka auroni, ko dan kaga iyayena basu goyamin baya ba? to ka sani wallahi tallahi yau sai ka sakeni nagaji na gaji, NA KASA JUREWA wulaƙancinka, ta ƙarisa maganar hawaye na sake wanke mata fuska....!
Please kuyi manege.
Mom Islam ce
Ayi following ɗina fisabilillah
*NA KASA JUREWA*
🪻🪻🪻
Mom Islam
Page 9-10
Cikin isa da jiji da kai ya furzar da isa mai huci kana yace "me kike nufi?, ba dan an takura min ba me zan ci dake?, kinga ni sauƙi ma kika nema min kije na sakeki saki uku"
Kafar a kunnen Hajiya mama dake ta kwaɗa sallama tun daga parlo bataji motsin kowa ba, a take a gurin ta faɗi sumammiya, cikin azama Saudart ta taho da gudu zata taimaka mata, yai saurin dakatar da ita gami da cewa "idan har kika taɓa ta wallahi sai na illata ki"
Ko da jin haka ta miƙe zuciyarta fess dan har ta fara jin tausayin Hajiya, tunda ya gaya mata magana tayi ta kanta, cikin farinciki da samun ƙwarin gwaiwa ta harhaɗa komai nata, kuɗin da Anam ta turo mata ta sake dubawa, a fili ta tace "hmm wallahi bazan sanarwa kowa maganar sakin nan ba, amma fa dole in nemo sheda kodan kar Dady yace min ƙarya nakeyi.
Biro da takarda ta ɗauka zuciyarta fess ta wuce ɗakinsa, a bakin ƙofa ta sameshi yana yayyafawa, Hajiya ruwan sanyi, tace "yaya nazo ka rubuta min shedar saki"
Babu musu ya karɓa saboda har ga Allah ta zame masa tamkar gobara, duk da tashin hankalin da yake ciki na suman Hajiya be hanashi rubuta mata saki ba, ya miƙa mata tare da cewa "kafin inje asibiti in dawo kar in sameki anan"
"Ai bazaka sameni ba, yanzu kam meye haɗinka dani, Allah yabi bayan me gaskiya" ta faɗa tana wucewa abin ta,
Ko saurar ta beyi ba ya kin kimi Hajiya zuwa parking space yana ƙwalawa Idi mai gadi kira, da gudu Idi ya taho yana cewa "lafiya kuwa alhjaji?"
"Dalla can buɗe min get, lafiya ne zan dinga yi maka wannan kiran?"
Jikin Idi na rawa yai azamar zuwa buɗe masa get sbda yasan halin uban gidan nasa.
A guje ya fice daga gidan kamar wanda zai tashi sama, cikin ransa ya dinga mai-maita innalillahi wa inna ilahir raji'un, har suka iso (Mai tama District Hospital)
Emergency room aka wuce da ita, inda aka bata taimakon gaggawa,
Duk wanda ya kalli fuskar Ma'aruf ko ba'a gaya masa ba yasan yana cikin matsanancin tashin hankali, adu'arsa bata wuce Allah yasa babu abinda ya sami hajiyarsa ba, idan kuma ta kamu da wani ciwon ta sanadinsa fa?"
Gaskiya bazai yafewa kansa ba.
Duk wani likita me shige da fice a ɗakin da aka kwantar da Hajiya, sai ya bishi yana cewa "likita dan Allah ya farfaɗo? likita tana magana?,
Inda kasan zautacce haka ya koma, wayarta dake hannunsa ya kalla, a sanadin faɗuwarta, duk ta farfashe, ya kawar da kallon wayar da yake sakamakon rurin da wayar ta farayi,
Sunan Anty Jamila ya gani yana yawo a fuskar wayar, sosai gabansa ya bada rass, lokaci ɗaya zufa ya fara karyo masa, be san amsar da ze bata ba, ƙarfin hali yayi ya ɗaga a ɗarare yace "As...asalamu a.."
"A'a Ma'aruf yakuke ina Hajiyar?"
Shiru yayi bai bata amsa ba, jin shirun yayi yawa, ta katse kiran ta sake kira, dolensa ya ɗaga, duk girman kansa da jan ajinsa baya yiwa mutum biyu, idan ka cire mahaifinsa da ya rasu, wato Hajiyarsa da Anty Jamila ƙanwarta kenan.
"Kayi magana mana, wai meke faruwa ne Ma'aruf?"
"Hajiya na hospital"
Kalmar da ya iya gaya mata kenan ya katse kiran.
Sosai hankalinta in yayi dubu ya tashi, ta fara harhaɗa kaya,
ƘAUYE
Ko da aka tashi daga islamiyya kowa ya watse amma Talatu bata matsa ko nan da can ba, sbda tun kafin a tashe su malamin ya fita, anyi masa kiran gaggawa, ɗaya daga cikin manyan ɗaliban ne ya yi musu addu'a kowa ya watse, har lungu Talatu taja wuyan hijabin Gudidi, mutane biyu ne a biye dasu, ɗaya sahura ce ƙawar Gudidi, ɗayar kuma Lantana sunanta ƙawar Talatu,
Rawa suke tiƙa sunayi musu waƙa suna cewa ...
"🎺A casu mata a casu, ku casu ba me rabaku araba ace anyi cuta, a zamanin nan na yanzu"
Sosai suke tiƙar rawa, kan kace me har Talatu tayiwa Gudidi lilis, babu mataimaki sai Allah, duk su biyun ƙawayen nasu basu isa suja da ƙarfin Talatu ba, sosai ta haɗawa Gudidi jini da majina, kafin faɗan ya ƙare, Gudidi na tafiya tana ɗingishi, tace "Hegiya maiyya jaka me ƙarfin Allatsine me kai kamar na duwatsun murhu"
Talatu ta biyota da gudu, itama gudun takeyi tana ɗingishi har ta ƙarisa gidansu,
Tana shiga ta samu Tabaiyye da malam sai uban musayar yawu suke yi, ita kuma ta shigo tana kuka babu wanda ya saurareta,
Wucewa tayi ɗakin Tabaiyyen ta kwanta a ƙasa ko zataji sassaucin mutsikar da tasha gurin Talatu.
Malam ya gyara zaman babbar rigarsa kana yace "Wallahi wannan hine gargaɗi na ƙarhe idan kika sake ragemin hatsi kowa ze kama gabansa"
Cikin masifa Tabaiyye tace "yo in kama gaban nawa mana, ka gayamin me na tsinana tunda na aureka, kaf kiwon da iyayena suka
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 2 Chapter of 22