idan sun zauna lafiya shine farincikinta, da haka dai Saudart take daurewa, badan tana jin zata iya samun rayuwar farincikin a gurin wannan dattijon ba,
Tun gyaran jikin da akayi mata bayan fitowar ta daga gidan Ma'aruf shine, kuma har yanzu da haskenta, a jiya ƙawayen momy suka zo, har danginta sai jiya ta sanar musu, ada ta yanke shawarar babu wanda zata gayawa, kasancewar sunada hannu da shuni (dukiya) yasa ba ayi mata wani faɗa ba, da asubha wasu suka hallara, aiko an ɗurawa Saudart magungunan mata sosai, sannan a daren aka dinga turarata da turaruka masu zama jiki, Masha Allah tayi kyau, ranar bikin tasa kaya sunkai kala goma sha biyar, kuma ko wanne haura dubu ɗari uku, wasu suna cece kauce wasu kuma sunata farincikin,
A ranar da yamma aka wuce da ita gidanta dake Badiko gidane na gani na faɗa amma yana tsakiyar gidan talakawa, gidan ya mamaye anguwar, sannan ita kaɗai ce a ciki, a cewarsa ta ɗan zauna na wani lokaci kafin subar ƙasar, ko meye dalili oho,
Duk wanda ya zo kawo amarya sai ya tafi da maganar gidannan a baki, saboda kyawun gidan da yanayin tsarin gidan da ya mamaye anguwa guda, gidan sama ne mai hawa ɗaya, ƙofar shiga ma kana danna lamba zata buɗe ta gilashi ce mai ɗaukar ido, zallar parlorn ya ishi mai surutu ya je yayita zabgawa, bare a kai ga shiga asalin cikin gidan, get biyu ne a gidan, dana baya dana gaba, har da gurin shakatawa, gashi komai akwai a gidan furniture's duk Alhjin ya hana Dady ya siya komai, ya zamo nashi kawai idanu da fatan Alheri,
Zuwa dare kowa ya watse daga ita sai ƙawayenta guda biyu, wanda suka zo da amincewar momy ragowar duk ta hanasu zuwa, "daga can parlor ake ta ƙwala musu kira, suka miƙe ɗayar tace "Saudart kekam kin samu aljannar duniya saura ta lahira, nasan babu abinda zaki nema ki rasa wallahi, dan Allah kiyiwa mijinki biyayya kina gani dai gamu daga masu mashin sai masu Aron mota suzo zance gurinmu, ɗayar tace "hm Saudart Wlhi tallahi kin gama hutawa irin wannan aljannar duniya haka, ni Wlhi ko gidan da bai kai wannan ba na samu nasan zan huta bare ke kalli TV a ko ina har toilet, taɓɓ gaskiya kin zo duniya da hannun dama, daga nan suka wuce bayan sunyi mata sallama, tabbas bata taɓa mafarkin shiga irin wannan gidan ba, dadynta yanada mahaukatan kuɗaɗe duk iya yawonsu basu taɓa zuwa irin wannan gidan ba, sosai take mamakin wai yau itace a wannan duniyar?, dan wannan gidan ya wuce a kirashi da gida sai dai duniya, tunanin inda zata koyawa zuciyarta son Alhjin takeyi, saboda ta faranta wa iyayenta rai, duk da yin hakan a gurinta abu ne mai matukar wahala amma zata daure ta danne zuciyarta ta kwatanta hakan, sallamarsa taji sai da gabanta ya bada rass, lokaci ɗaya hankalinta ya tashi...!
Idan har naga comments zaku samu fiye da haka.
Mom Islam ce taku ta gargajiya ga numberta ga duk wani mai son magana dani 08141799234
*NA KASA JUREWA*
💋💋💋
💋💋
💋
_Mom Islam_
45-46
Cikin sauri ta fara ƙoƙarin gyara zaman mayafin da aka lulluɓe mata fuska dashi, kafin ta ji sautin muryarsa ɗazu tayi wa zuciyarta alƙawarin zama dashi, lokaci ɗaya zuciyarta ta raunata, cikin sanyin murya ta amsa da "wa'alaikumussalam"
Kallo ɗaya tayi masa ta cikin mayafin, kasancewar ba mai duhu bane, ta kawar da kai, tare da ƙoƙarin danne zuciyarta, "Masha Allah" ya ambata lokacin da yake kutsowa cikin ɗakin hannunsa riƙe da ledoji guda biyu manya, "sannu da zuwa" Saudart ce masa tana goge hawayen da ya fara zarya a kumatunta, tabbas shikam fuskarsa wasai take, kai kace wanda aka yiwa bushara da gidan aljanna, sai wani washe haƙora yakeyi, bayan ya ajiye ledojin a saman wani haɗaɗɗen table na glass mai ruwan golden color anyi masa ado da flowers masu kyau da ban sha'awa, ya tako a hankali zuwa inda take bayan ya amsa mata, "amarya bakya lefi, Barka da shigowa gidana, yarinya ki kwantar da hankalinki zan baki farinciki fiye da yadda kike tsammani, ina fatan zaki farantamin?" Yai maganar yana ƙoƙarin yaye mata mayafi, bata da zaɓin da ya wuce ta amsa masa, murya a hankali tace "insha Allah" sannu a hankali yake matsawa kusa da ita, har ya zo daf da ita, yana murmishi yace "tashi ki ɗauko plate a kitchen kinji, kokuma muje in rakaki tunda baki san ko ina na cikin gidan ba" ya ƙare maganar yana miƙewa tsaye, a hankali ta zuro ƙafafuwan ta da suka sha zanen lalle baƙi, kana ta gyara zaman mayafinta a kafaɗa, ya lura da kuka tayi, sbda idanunta sun ɗan kumbura, a maimakon yayi gaba ita ta dinga bin sa, kawai sai ya wani tsaya a baya yana yi mata kwatancen inda kitchen ɗin yake, dalilinsa ko na tsayawa a baya, ya kasa haƙura da maitar son ya kalleta, sai bin ta yakeyi da wani irin fitinannen kallo yana lashe baki, koda suka iso kitchen ta buɗe ta shiga, kanta kusan juyewa yayi, lokaci ɗaya ta fara tunanin shima kitchen ɗin yana cikin wata duniyar kenan, "wai wannan mutumin wane irin dukiya yake dashi, irin wannan kitchen ɗin ai ya ninka parlon gidan Ma'aruf a kyau, ya lura da tunanin da takeyi, "ɗauko mana Habibty" yai maganar cikin Muryar lallashi, "wow wannan sunan yayi mata daɗi, inama ace wanda takeso ne matashi ya aureta ba wannan tsohon ba, da ta ji daɗi wlhi,
Wani haɗadden plate ta ɗauko, wanda samun irinsu a Nigeria yana iya yin wuya, tunda kaf kayan ko cokali ma daga ƙasar waje aka kawo su, koda ta ɗauko plate ɗin zata juyo ya rungumeta, tare da cewa "muje kici abinci"
Tofa🤣
Lokaci ɗaya ta mance da wa take tare, domin idan baku mance ba, bazawara ce...
Da sauri ta dawo haiyyacinta ta turo baki tare da cewa za "meye haka?"
Alhaji yace "kam yayi da uwar ƙaton ciki yace "shauƙin ƙaunarki"
A hankali ta zame tare da wucewa ta gefensa tunda taga hanya, a saman table ɗin ta ajiye plate ɗin, kana ta koma saman gado ta zauna,
Mamaki ta bashi, sai ya nemi guri saman couch ya zauna mai zaman mutum biyu, kafin ya ɗauko ɗaya daga cikin ledojin ya buɗe guda ɗaya, soyayyen naman ɗawisu ne, a cikin wani bowl mai masifar kyau ɗan ƙarami, sai wasu kayan ciye-ciyen wanda nima ban sansu ba, "Habibty taso kici"
"Naƙoshi "
Saudart ta faɗa tana gyara kwanciyart, ita dama ba ci zatayi ba, kawai ta bishi ta ɗauko ne gudun kar ya ga kamar ta fara yi masa wulaƙanci tun yanzu,
Yoghurt ya ɗauko tare da glass cup wanda ya ɗauko acan kitchen, ya tsiyaya a cup ɗin, wanda ya ke haɗe da kwakwa da dabino da madara kai nama rasa sunan ragowar🤔, sai da ya cire babbar rigarsa kafin ya ɗauki yoghurt ɗin kana ya isa gareta, cikin sigar lallashi yace "haba Habibty ya kamata ko wani abun kisa a bakinki" itakam ta riga da tayi barci bata ma san yanayi ba, badan yaso faruwar hakan ba, ya dawo ya ajiye cup ɗin tare da zama gefen bed ya fara ƙoƙarin cire agogon hannunsa, kana ya cire rigar ciki, innalillahi lilahi wa inna ilahir raji'un, ba mutuwa akayi ba, shirgegen ƙaton cikin Alhaji na hango.
Har yakai hannu zai buɗe toilet, yaji ana nocking da ƙarfi kamar za'a ɓalle door ɗin, ɗaga kansa yayi sama, kana ya kalli makeken agogon dake manne jikin bango lokacin ƙarfe 11:pm na dare, kawar da tunanin zuwa buɗe kofar yayi ta hanyar murɗa handle na ƙofar ya shiga toilet ɗin, wow ya Subhanallah, banɗaki har TV ni mom Islam, uhm wasu na'urori ne suke sarrafa kowane kayan amfani na banɗakin, ruwan zafi ruwan sanyi da sauran abubuwa, kai harda jaridu wato drowarsu a banɗakin, nidai a tunanina idan kashi zakayi sai ka ɗauka ko?🤣hhh,
Sai da ya cire kayan jikinsa, kana ya tara ruwan wanka ya shiga ciki, lumshe idanu yayi tare da hango inama ace shi da Saudart ne a cikin wannan ruwan suke yin wanka, sai kuma ya sake jin nocking ɗin kamar ba na mai hankali ba, a gurguje ya yi wanka ya ɗauki ɗaya daga cikin towel ɗin da aka rataye su, ya goge jikinsa kafin ya fito, tare da ɗaura wani towel ɗin a ƙuginsa, fitowa yayi zuwa ɗakinsa har yanzu ana nocking, ya ɗauki jallabiya ya zura, har ya iso parlo wata zuciyar ta bashi Shawara akan ya kira mai gadi ya ji ko su waye,
Hakan ko yayi, koda ya kira mai gadi yace "masa wasu mata ne guda biyu Wlhi bai gane fuskarsu ba, thinking ya fara yi shin waɗanne mata ne zasu zo masa gida a dai-dai wannan lokacin?" Bashi da amsar tambayarsa hakan yasa shi, jingina da jikin bango tabbas ya fara tunanin anya ba Hajiya Zaliha bace?" Itama wannan tambayar da yayiwa kansa bashi da amsarta, ya yanke shawarar ya koma ciki, sam bazai bari kowa ya shigo masa gida ba, kai tsaye ya koma bedroom ɗin Saudart ya bi lafiyar gado, tare da matsawa kusa da ita, kana yayi hugging ɗinta yana sa wayarsa airplane mode.
Acan bakin ƙofa kuwa, Hajiya Zaliha ce ita da babbar ƙawarta, cike da masifa suke tsaye a gurin zuciyarta sai turiri takeyi, rai a ɓace tace "wato wannan ɗan rainin hankalin ni zai nunawa yayi aure ko?" Ƙawar Tata tace "Zaliha kawai kizo mu koma gida in ya so gobe da sassafe sai mu yi sammako mu zo" "Hadiza Wlhi tallahi bakisan irin tuƙuƙin da zuciyata takeyi yi ba, abin kunya abin takaici kamar Alhaji ya auri ƴar cikinsa, haba, sannan tunda nake dashi bai taɓa raɓar wata mace ba bayan ni, inafa zan iya barci ai kwanan zaune zanyi, ina nan anan billahillazi"
Hajiya Zaliha takai ƙarshen maganar cike da ɓaci rai da takaicin abinda Alhjin yayi, dole Hadiza ta biye mata, nan fa suka fara tunanin inda ya kamata su kwana, Hadiza tace "ai baza'a rasa ɗakin baƙi ba, barin tambayi mai gadi, Hajiya Zaliha ta dakatar da ita, tare da cewa "ni zanje dawo" fuu ta tafi gurin mai gadi tana zuwa ta riƙe ƙugu kana tace "akwai wani emtin ɗakin kwanan baƙi ne anan?" tunda ya ga yanayinsu yasha jinin jikinsa da cewar akwai wata a ƙasa, tabbas waɗannan matan akwai abinda ya kawosu, cikin daka tsawa ta sake cewa "magana nakeyi baka ce min komai ba?" "Bab...bab...bu.." yai bata amsa muryarsa na rawa, Hajiya Zaliha ta yaye mayafin dake yafe a kafaɗarta tare da yafashi a gefe ta turo ɗaurin ɗankwali gaba, kafin tace "kai sa idonka a nawa, na rantse da Allah idan baka bamu gurin kwana ba sai nayi maka tijarar da har ka koma ga Allah baka mance ba, kasan ko Ni wacece?" Ya girgiza kai alamar "a'a"
Ta kwashe da dariya, kana tace "ni matar mai gidan ce, dama nayi tafiya ne yau na dawo, nayi kiran duniya yaƙi buɗemin kuma kayana suna ciki, tunda na jima da tarewa a gidan, da yaji tsoro yanzu kam ya washe haƙora kana yace "ahh Hajiya ai kin firgitani, ai bai kamata a baki ɗakin baƙi ba, barin buɗe miki ɗakin manyan baƙi, amma ko kin kira Alhjin a waya?" Hajiya Zaliha tace "eh amma inaga yayi barci ne"
Tai maganar cikin siyasa, saboda taga yin masifar ba zai kai ta ga nasara ba.
Kai tsaye ya wuce dasu ɗakin da Alhjin yake sauƙar manyan baƙinsa, haɗaɗɗen ɗaki ne, wanda ya amsa sunansa ɗaki, ga shi an yalwatashi da kayan alatu na zamani da ƙyale ƙyalen turawa, kasancewar sun gaji gado suka haye, Hajiya Zaliha ta buɗe hand bag ɗinta ta sa car key ɗinta kana ta kwanta, koda barcin ya ɗauke su ita a wani hali ta kasance, saboda mugayen mafarkai da ta dingayi akan Alhajin da matar da ya aura, bata ƙaunar ta ji wannan lamari ya faru ko kaɗan, sam bata so, bata son Alhaji yayi taraiyya da Saudart, saboda Alhaji nata ne ita kaɗai, ƙarfe 2:am na dare ta farka cike da tarin baƙinciki da takaici mai cike da tsantsar nadamar saken da tayi har wannan lamari ya faru, miƙewa tsaye tayi tana mutsike idanunta masifar kishi na cinta, tace "wayo Allah, ta dafe dai dai saitin da zuciyarta ke bugawa,
Itako Hadiza barci takeyi harda munshari, Hajiya Zaliha ta fara zagaye ɗakin tana neman mafita,
Bazata iya bari gari ya waye ba, bata ɗauki mataki ba, tayi tunani iri iri, daga ƙarshe dai ta buɗe ƙofa ta fito harabar gidan tana sake ƙare masa kallo, gingina kai takeyi tana taɓe baki gami da yin tsaki mtswww, takai kusan 30mints barci ya ƙauracewa idonta tsabar zafin kishi.
Har yanzu dai ta kasa haƙura gari ya waye ta sake zuwa gurin ƙofar ta bubbuga kamar zata ɓalle door ɗin, a firgice Saudart ta buɗe ido, ta fara ƙoƙarin tashi zaune, kallon hannun Alhjin da ya rungumeta sosai tayi, a hankali ta zame daga jikinta tare da saukowa daga saman bed ɗin ta tsaya cak a tsakiyar ɗaki, zuciyarta ta rabu gida biyu, shin taje ta buɗe ƙofar taga waye yake nocking kokuma ta tashi alhaji?, "Ina!!" Ta faɗa a fili a hankali ta juya key ɗin ƙofar dan batayi tunanin komai ba, kofar ta buɗe....
SINGAPORE
Buland island
Tun tafiyar Anam da sukayi da Dady, aka juyar mata da hankali, ta koma sai inda akayi da ita, duk da sanin Dady, wannan abin ya faru.
A estate ɗin su, A ranar da aka kawo Anam aka sauya mata suna zuwa Neria, ita kuma Hussaina sunanta Misha, ikon Allah kenan, lokaci ɗaya jininsu ya haɗu, sosai Misha ta ja Anam a jiki kasancewar ta shiga ranta, gata yarinya ƙarama a shekaru bata wuce 16yrs ba, duk da ƙarancin shekarunta sai da suka san inda suka sa ta fara tarbiyya da maza Christian ƴan uwanta, tunda yanzu ta fita a musulunci, tun tana jin kunya tana ɓoyewa har ya zamo ta zamo ƴar gari, amma sai dai duk wanda zasuyi taraiya dashi sai anyi taste an tabbatar da lafiyarsa kana kuma ya sauke maƙudan kuɗaɗe, yau ma kamar koda yaushe, suna zaune a ɗakinsu, kasancewar Misha tace Anan ɗin ta kwaso kayanta, ta dawo ɗakinta, bayan sun gama tsara kwalliya aka fara koyar da ita sanya kaya matsatstsu kuma iya cinya, da yawo babu ɗankwali, dole takeyi dan bata iya yin musu sai dai wani abun a ƙasa ranta tana jin zafinsa amma bazata iya furtawa ba,
A yau ne oga ya shirya babban taro wanda ya kasance jimami ga dukkan ƴan matan dake cikin estate ɗina, abinda ke faruwa shine, haka kawai aka ga uwar ɗakin nasu ta faɗi ta mutu babu wanda yasan abinda ya faru da ita, a ranar ansha giya kamar ba gobe, wasu alamomin sukanyi nuni da kamar ogan yanada masaniya akan mutuwarta.
Bayan sati ɗaya da mutuwarta ya shirya babban taro a hall ɗinsa dake nan Buland island, babban Hall ne, wanda ya amsa sunansa, ko wacce budurwa an jere mata drinks da snacks da giya da sauran kayan shaye-shaye, bayan ya buɗe taro da yaba musu da yayi kana ya fara gabatar da dalilinsa na haɗa wannan taro,
"Mun samu canji sosai, bazance mutuwar uwar ɗakinku alheri bace a gareni, haƙiƙa naji mutuwarta, kuyi hakuri zaku sameni mai baku duk abinda kukeso a faɗin duniya, Abu na farko da nakeson sanar daku shine, akwai wani cigaba da na hango mana, wanda kuma zaku sake samun canji duk da nasan a cikinku babu wacce zata ce ta buƙaci wani abu bata samu ba, na farko dai shine..
"Inason ko wacce budurwa a cikinku idan ƙarshen wata yayi kokuma in ce lokacin da ta fara period ta kawomin pad ɗinta na adadin kwanakin da takeyi, akwai wani magani da za'ayi na rigakafi" ya kai ƙarshen maganar yana tuntsurewa da dariya, ragowar abokan aikin nasa ma dariyar sukeyi, yayinda suma ƴan matan suke dariya gami da yin tafi,
Sosai taron yayi masa daɗi, hakan ya sake tabbatar masa da cewer, aikin bokansa yana tafiya inda ya kamata,
Bayan nan yace "yau a club ɗinsa akwai shagali na musamman"
Suka sake yin tafi raf...raff..,
Daga nan ya rufe taro da yi musu faɗa akan duk wani abu da suka rasa su gaya masa,
Duka suka cewa "toh"
Daga nan taro ya watse kowa ya nufi sashensa,
Bayan Oga ya dawo gida, ya tuntsure da dariya, babban dalilin da yasa ya kashe uwar ɗakin nasu shine, sam bata goya masa baya a wasu abubuwan nasa, to meye amfanin zamanta a duniya tunda har bazata bari su haɗa kai su yi kuɗi na ban mamaki ba.
Washe gari.
Akwai wani babban kamfani da yake dashi wanda suke safarar haramtattun magunguna wanda suke ƙirƙira sannan suyi rubutu da sunan wata ƙungiya, sau biyu ana yi masa worning amma yaƙi fahimta, cikin basaja mutanensa suke kai magunguna tare da nuna shaidar amincewar gwamnati, hakan yasa masu asibitin basu da tabbacin banbance marar kyau da mai kyau,
Safiyar yau Monday an tsananta bincike game da masu aikata laifin,
Oga Reed na zaune saman tsafaffiyar kujerarsa, ɗaya daga cikin securities ɗinsa yayi masa magana, da cewar yayi baƙo da alama akwai alƙairi game da zuwan bakon, Cikin amincewar Reed aka shigo da baƙon, fari ne tass Balarabe ɗan ƙasar Saudiyya, abinda ya bawa Reed mamaki bai wuce, ya akayi wannan Balaraben ya san da zamansa har ya kawo masa ziyara?" ba yanzu zai buƙaci wannan amsar ba,
Tabbas idan har mutumin bai zo da wata ƙullalliya ba, zai yi musu amfani, idan kuma ya kasance mai kishin musulunci ne yazo leƙen asiri ne,
Reed yayiwa baƙon nasa umarni yace "inayi maka maraba, da Yaren su, kasancewar Balaraben yana ji, ya amsa da yauwa tare da miƙawa Reed hannu cikin muryarsa mai daɗin amo yace "sunana Thabit ina fatan zamu zamo abokai"
Reed ma ya miƙa masa hannu kana ya kasa ɓoye mamakinsa yace "amma mai ya baka sha'awar siyarda ranka har kazo inda nake kai tsaye ba tare da kayiwa zuciyarka shawarar ka ci gaba da rayuwa a duniya ba?" Thabit yai ɗan gajeren murmishi, kafin yace "wato Reed idan har mutum yana neman hanyar da zai zamo wani abin kwatance a duniya ba sai ya tsaya jin tsoro ko makamancin haka ba, kawai kai tsaye zai miƙo buƙatunsa idan anyi na'am dasu to, idan kuma rai yayi halinsa duk ɗaya"
Sosai maganar Thabit ta shigi zuciyar Reed lokaci ɗaya yaji ya fara amincewa dashi, sai dai ya yi umarni da a kawo masa wata kujera Thabit ya zauna a kai, kujerar itama tsafaffiya ce sosai, wadda take auna abinda ke zuciyar mutum na alkairi ko na sharri, koda aka Thabit ya zauna a wannan kujera sam bata bada wata matsala ba, hasali ma tayi nuni da gyara tare da ci gaba zai kawowa Foundation ɗinsu" dama Reed ya daɗe yana jiran wannan rana, ranar da zai samu mutumin da zuciyarsu zatazo iri ɗaya, tabbas ranar yau ta zamo ranar shagali a gareshi, ranar yau ta zame masa haske, ya mikawa Thabit hannu suka tafa tare da rungume juna,
Tun a daren suka fara gabatar da aiki gadan gadan babu wasa...
ƘAUYE
A ranar da gudidi ta koma ta dinga ihu tana birgima a ƙasa, sam bata ƙaunar sake rayuwa a cikin ƙauyen, koda mahaifiyarta Ramma tayi mata tsawa, itama tsawar ta daga mata tare da cewa "yasin wannan baƙinciki ne, ina cikin ni'imar Ubangiji kin wani dawo dani nan, a aljanna ta ɗaya muke, ramma tace "kiyi hakuri Gudidi gonar rogo na siya nasa aka haƙomin kaɗan daga ciki nakeson in fara siyarwa ko Allah zai taimake mu, Gudidi ta kwaɓe fuska kafin tace "yasin hedai ki nemi wanda zeyi miki talla naje binni nahya ruwan garɗi kuma yanzu kice wani talla yasin bazanyi ba, bari ma kiga in samu kuɗi Wlhi binni zan koma zaman ƙauye ai sai wanda yayi niyya, tunda ba anan aka binne cibiyar mutum ba, tai maganar tana taɓe baki.
Ramma ta zaro idanu tana dafe ƙirji kafin tace "Wlhi idan hakane zaman binni bai tsinana miki komai ba, kwata-kwata kwanan ki ɗaya kika dawo, amma duk kinbi kin fetsare, to Wlhi tallar rogo babu fahi sai kinyi kinji na gaya miji" Ramma tai maganar tana nunata da yatsanta, kuka sosai takeyi tana ta shure-shure,
Washe gari, samarin ƙauyen suka dinga shigo da rogo a buhu, bayan sun gama kawowa, Ramma ta haɗa wutar kara ta dafa rogo ta saka a farar ledar buhun suga, ta zuba ƙuliƙuli dakakke wanda aka zabga masa farin maggi da gishiri,
"Gudidi kizo ki higa wanka ni na kammala nawa aikin ke nake jira, abin mamaki ko musu batayi ba, ta tashi ta shiga wanka, tana fitowa ta tsantsara kwalliyar hauka, janbaki har a saman gira, harda wani wai hawayen masoyi, ta zabga farin janbaki abin dai sai wanda ya gani.
Wasu daga cikin kayan da Hajiya mama ta bata, ta ɗauki atamfa ɗinkin buba ta saka, Wow Masha Allah tayi kyau sosai, Masha Allah,
Bayan ta gama sanya kayan ta ɗauko wani baƙin mayafi duk ya tattare ta ɗaureshi a ƙugu, kana ta ɗauki tiren tana cewa "na tafi" Ramma dake ɗakin girki ta fito da gudu tana cewa "Gudidi bakici komai ba" Gudidi tace "na nawa zanci?" Ramma tace "na Ahirin" babu musu Gudidi ta wuce, mamanta nayi mata Allah ya tsare...!
Idan kinason shiga group wanda nake posting kimin magana ta WhatsApp 08141799224
*NA KASA JUREWA*
💋💋💋
💋💋
💋
Mom Islam
Page 47-48
Tun a hanya ta fara ciniki, kafin takai ga gurin da take zama har rogon ya ƙare, sai dai anyi ba ayi ba, wai matar bakanike ta haifi sifana,
Da sallama ta shiga gidan murya a sanyaye tace "Ramma na dawo, jin Muryar Gudidi yasa Ramma fitowa da sauri daga ɗakinta, fuskarta ɗauke da murmushi tace "hannu da dawowa Gudidi mai kasuwa da sunan Allah, ajiye tiran ki higa ɗaki ki ɗauko fura da nono ɗazu yaro ya kawo talla na siya miki.."
Duk da tsananin fargabar da take ciki bai hanata zuwa ɗakin Ramma ba, taje ta iske fura da nono mai sanyi, sai da ta cika cikinta kana ta fito tana goge baki,
Bayan ta dawo gurin Ramma ta kunce ɗamarar da tayi, kana ta durƙusa har ƙasa, idanunta cike da hawaye tace "dan Allah dan Annabi Ramma ki dubi sallahar iyayenki ki yafemin"
Ramma ta tsorata sosai dan ita bata san dalilin neman yafiyar ba, "tashi ki zauna kiyimin bayani inda zan fahimta"
Ramma tayi maganar tana kallon Gudidi, da har yanzu kuka takeyi,
Sosai sautin kukan gudidin ya cika mata kunne, ta daka mata tsawa saboda haushin da ta bata, kafin tace "wallashi ko kiyi magana ko in zaneki da tsumagiya, jin haka yasa Gudidi share hawaye tare da zuƙo majina ta shanye🤣 kafin tace "Ramma Wlhi na yi ciniki sosai, na kamo hanyar dawowa gida, na nemi kuɗin na rasa"
Da sauri Ramma ta tashi tsaye tana dafe ƙirji kana tace "Na higa uku Gudidi kin cuceni, Wlhi da ki yimin wannan ɓarnar ai gara ki gaura min mari"
Ramma ta wani rarumo ƙatuwar sanda tare da cewa "gara in karyaki Hegiya kawai, kuma wallashi kije duk inda kuɗi yake ki nemo min kuɗina dan wallhi bazan ɗauki asara ba, saboda suma masu rogon ba yafemin zasuyi ba" ta ƙare maganar tana bin gudidi da gudu ko mayafi babu a jikinta, cikin ɗaga murya Gudidi take cewa "dan Allah Ramma kiyi hakuri Wlhi tallahi ban gansu ba, ni ban ci miki kuɗi ba"
Har yanzu dai surfa mata masifa takeyi, na,,, taje duk inda kuɗi yake ta kawo mata idan ko bata samu ba, sai ta kusa sumar da ita,
Tana tafe tana share hawaye, ta hango ƙulin baƙar leda irin wanda ta ƙulle kuɗin rogon a ciki, tana ci gaba da kukan ta sunkuya ta ɗauki ledar kana ta kunce, "alhmdulilah ta ambata tana kuka tana dariya" ta waiga taga babu kowa, ta ruga da gudu, tayi nisa sosai da gidansu, sai da ta isa gindin bishiyar mangoro kana ta nemi guri ta zauna, ta ciro kuɗin a leda kana fara ƙirgawa, dubu biyar ne cif, ta washe haƙora, kome ta tuna oho sai kuma ta turɓune fuska kamar zatayi kuka, kalmomi biyu da mahaifiyarta tayi mata ne yasa ta sauya yanayi, na farko, Taje duk inda zataje ta nemo mata kuɗinta, na biyu, kar ta
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 11 Chapter of 22