na rasa wacce iriyar amaryace wannan ace gyaran jikinka ma gudunsa kake?' Kyaje gidan ne mijin ya koroki astagfiroullah Allah na tuba. Wllh tsaya kiji wannan bikin da naje Ikaja. Bayan kai amaryar da kwana biyu mijin nan ga daho kaza a dafe rigijff tasha kayan miyarta sharr. Ai wllh nake baki labari yakai gidan su amaryar nan bayan uwarta taci taji salam babu komi tace wannnan ai kunyi mantuwa babu komi a ciki na kayan hadi. Kinsan me yace ce musu yayi yanda sukaji kazar nan haka yaji yar su, to yanzu dan Allah me amfanin hakan? Wllh babban gata nake miki yar nan"
Wani murmushin da baikai zuci ba meerah ta saki tana sunkuyar da kanta kasa. Acen kasar zuciyarta tana furta
(Ni wllh da yamin daidai kuwa amma fa ni bama yarda zanyi wannan me kama da birin ya taba niba, bare ya hada jiki dani nevermine wllh)
Fitowar Anne shine ya katse meerah daga duniyar tunanin data fada. Kallo daya Anne ta mata ta dauke kai tana karasawa inda hajiya umma ke zaune. Gaisawa sukai nan suka fada wata maganar daban ba wacce hajiya umman keta kokarin ganin ta kawota ba.
Jakar kayan Anne ta turama meerah tana fadin taje tayi amfani dasu kafin ta shigo dakin itama. Hayaniyar data kaure a cikin gidan ne ya sanya su umma fita.
Wata matashiyar mata ce wacce taci wani ubansun ado jikin farin leshin daya sha doguwar riga half bubu, sai farar siririyar yarinyar dake gefenta cin mutumci take zuwaba a cikin gidan tana fadin sai an nuna mata uwar data haifi amaryar da ake shirin likama dansu, dan son zuciya da bakar zalama anga gidan arziki shine za'a likema dansu...
Kallo daya Anne ta watsama matar ta dauke kanta tana komawa inda ta fito, shunenta maman affan ta mata ai kuwa ta tafi zata fusgo Anne.
Wani irin juyowa Anne tayi tare da watsa mata wani mugun kallon daya sanya maman sury jan burki daga shirin fusgar da taso yima Annen.
Tsananin kwarjinin da idanuwan annen suka mata ne ya sanya ta hadiye sauran maganganunta, tana kama kanta cikin muryan da baya daukar wargi ko wanne ta furta.
"Idan har kun isa da danku kuje gida ki hana a daure aurensa da DIDI!, jinina yafi karfin a wulakanta shi haka jinin Ayshatul humaira ba daskararren jini bane jinin dake gudana a jikinta tafarfasa yake ya tafashensa yake. Tafi karfin ta hada zuriya da gurbat.....
Maganar ce ta yanke mata sakamakon rufe bakinta da hajiya umna tayi. Ita kuwa sury tuni ta makale jikin mummynta haka nan ta tsinci kanta da shakkun matar ba karamin kwarji ta mata ba.
Daya bayan daya matan gidan suka fara zamewa domin su kansu ba karamin gwarjini Annen ke musu ba barin ma idan halinta najin kai ya tashi.
Su kansu yayanta wani bin sai su wuni ba tare da kalma daya ta shiga tsakaninsu ba, wannan halin nata kuma ba karamin tayarma da malam abdullahi hankali yake ba.
Jan hannunta umma tayi suna komawa parlournta. Nan ta shiga bata baki amma samm taki tanka mata ita kanta tasan wannan gwamutsen hadin auren ba son shi take ba, to amma ya ta iya.
Ta kasance matar da bata jayayya da hukincin ubanhiji in banda haka ko ita da tuni ta farke wannan auren da take ganinsa kamar ba tabbatacce ba har waye war garin yau din. Har yamma hajiya umma na gidan....
Bangaren meerah kuwa haka tayi wunin sukuku gashi ba damar fita bare ta dan fita ko ta samu full energy nata ya dawo. Ta hanyar shakar iskar wage, abincin da tun dazu Anne ta tura mata take ta faman jagwalgwalawa, ita bata ci ita bata dena jujjuya shiba. Har saida hajiya umma ta fasu ta furta.
"ya abincin gabanki tun dazun kinki ci sai famar jagwalgwalashi kike?. Meye haka kike yi da abincin nan meerah?" dago kanta tayi ta kalleta Itama Anne sai ta maida attention dinta kan meerah din. Wani dan murmushi ta saki irin me ciwon nan kafin a hankali tace.
"Umma kinsan dazu da yamma na ci
Wannan abin sam bana wani jin cin abincinne kawai na ji yanzu bana jin yunwar ma"
"Toh idan baza ki ci ba ki rufe anjima kyaci" tashi tayi sai kuma jiri ya dibeta ba tare da kowa ya lura da hakan ba Kawai sai faduwarta suka ji. Da sauri Anne ta nufeta tana jijjigata, dakatawa tayi sai kuma ta juyoo da kallonta zuwa ga hajiya umma tare da furta "Bata numfashi"
"Subhallah dama ba jiri bane ya dibeta?". Hajiya umma ta fadi tana yin kan meerah din " Maza kira malam ki sanar dashi Ayshatu" hajiya umma ta fadi cikin kidima domin ba karamin tashi hankalita yayi ba.
Cikin kankanin lokaci saiga malam tare da Ibrahim babban dansa. Fito da ita sukai suka sanya a mota suna nufar hospital drektly....
A hankali take bude idanunta da sukaimara masifar nauyi, dan motsa idanunta tai tare da dan cije leɓe kadan.
kafin ta samu nasarar bude ido da ƙkyau. "Asibiti kuma?" Ta ambata a hankali tana dan waige-waige da kallon dakin data bude ido ta ganta cikin bazata.
Nan komai ya shiga dawo mata sai kawai ta koma tana jingina da jikin gadon, lokacin wajen goman dare.
"Meerah ashe kin tashi ma?"
Hajiya umma ta fadi tana komawa don yin magana da dactor. Tunda Anne tana gida babu jimawa hajiya umman tace taje. Ba don taso ba ta tafi tana tunanin damuwar da ake taima didinya yawa da kuma yawan tunani.
Sai gasu ita da nurse ta dawo sake aunata nurse din tayi nan tace ma da umman babu wata damuwa insha allah zuwa safe ma zasu basu sallama. "Zanyi sallah ummah"
Meerah ta fadi cikin muryan da yayi low sosae.
Da taimakon Umma ta sakko a gadon sai yanzune ta kuma fahimtar a daki na musamman take, kuma ita kadaice a ciki hakan ya sanyata kallon umman da alamun tambaha.
"Bamusan wanda ya sanar masa ba muma kawai ganinsa mukayi yazo ya sanya an sanja miki daki" dan lumshe ido tayi tana jin ma sam.. Bata son ci gaba da zaman hospital din. Sallan magrib da isha'i ta kawo tana koma ta jin gina kanta da karfen gadon.
Sallamar salman din itane ta katse mata rufe idon da take niyar yi. Hannuwansa rike da manyan ledojin shopping ya shigo. Gaida umma yayi ts amsa tana tsokanarsa da angon kwana biyu. Dan murmushi yayi yana shafar sumar kansa yana jin wani irin madararn dadi na lullebeshi. Don ji yake tamkar ya jawo wannan kwanan biyun su dawo yau, kamar ya janwo nesa kusa haka yake ji da yana da damar hakan da tuni ya dawo da nesansa kusan sa. Kodan muradin wannan lafiyayyan jikin da yake ya kwadaitu sosae da sosae da tsarin halitta da kuma surar jikinta.
Kallo daya ta masa ta dauke kanta shine ya gaida ta tare da mata ya jiki ciki² ta amsa. Nan ya shiga yar firarsa da umma domin gwanar tamu taki ko saurarensa.
Kiran wayar sa friend's nashi suka yine akan sun sauka lafiya suna airport yazo ya dauke su, shine ya san yashi masu sallama yana cema umman abokanan sane suka zo domin tun gobe juma'a zasu fara shagwalgulan bikin. Yama so ace tun laraba suka fara amma malam da kanshi ya dakatar da hakan. Domin ya kawoma meerah katunan shagulgulan ne d nufin ta rabama friendies nata, wannan shine dalilin dakile maganar da malam abdullahi yay, ba tare daya sani ba kuwa haka salman da manyan abokanansa suka kama manya manyan hotels dake garin lagos dim suke abinda suka ga dama.
Ta hilton hotel yabi ya taho da wasu domin debo manyan friends dinsa. Ajeborters na waje sa sauran garuruwa, a lokacin dayay ido biyu da dolly ba karamin baci ransa yayi ba domin idan ya tsani abu ya tsane shi kenan. Haka idan yaso tofa ya so shi kenan da dukkan zuciya da ruhinsa. Cikin kaushin murya ya kalli moussa yana fadin.
"Kaine kazo da wannan abin ko?"
Ya fadi yana masa nuni da dolly wani kafurin murmushi dolly ta saki tana " hey beb baka happy da zowa na ba kenan?"
Tana shirin rungume shi ya ture ta a jikinsa yana fadawa motarsa yana fadin.
"Le's go guys ku muje ko?"
Sauran motocin suka shishshiga suna barin airport din tare da kama hanyar hilton hotel dasu..
Tun da suka shigo harabar hotel din suka soma jiyo tashin sautin Wakar da aka sanya din. Irinta shegen nan wanda suka rike a harkar tantiranci.
Tab katon harabar inda suke yake da wayayyun matasa da yan mata 'yan bana bakwai,wadanda rayuwa da kuma duniya ke musu dadi suke cashewarsu cikin kwarewa, wasu babu kayan arziki a jikinsu mafi yawan mazan kuma gajerun wanduna ne a jikinsu.
Hannuwansu dauke da manyan kwalaben giya wasu cigarette's ce a hannunsu suna busa hayaki. Wasu kuwa pep na shisha ne a ganansu suna zuka su fesar da hayakin cikin wani dan iskan salo.
Tun kamin motarsu ta gama parking dolly dake sanye cikin wasu shegun outfit riga da wanda na baxon ta balle murfin motar fa fito. Akan inda giya, shisha, cigarette's coc suke ta fara nufa kai tsaye. Shishar ta dauka ta mata wata kafurar zuka tana baza hayakinta daya hada hoton love. Zaune takai akan almurun kujera. Tana zare wawakeken shade din daya kusan cinye rabin fuskarta.
Mafi hankalunan yayan ajebor din dake zagaye da wurin ne ya dawo kanta, Nanfa suka mata caaa aka har wasun su na kakarin kama hannuta donsu shakata tare da ita. Kai tsaye club dancing din ta shige ya soma wata kalar rawar daya sanya manyan yaran daukar ihuuuuuuu suna sowa.
Nan fa kowa ga fara kokarin isa ga dolly saidai taki ba kowa damar hakan. Har suka karaci shedancinsu suka tashi wajajen karfe biyun dare.
★★KANO★★
Idan muka koma kano kuwa sosae rayuwar kamal da mariya ke gudana cikin kanciyar hankali, akwai girmama juna a tsakanunsu sosae suna zamansu lafiya yau kimanin kwanakj tara kenan da aurensu. Amma babu abinda ya taba shiga tsakaninsu. Hasalima kowa daki daban yake kwana abinsa. Sammm daga shi har ita babu abinda ya dame su kowa ya harkan gabansa. A kullum zata shiga dakinsa ta gyaro masa ta kuma wanke masa ƙananan kayansa a washing machine. Kamar kullum yanzu ma aikin gyaran ɗakin take hankalinta kwance, ɗomin dama sauya fita take shigowa ta gama masa Aiyukansa ta tafiyarta. Riga da wando ne a jikinta na palazzo ride vizzon ruwan kasa inda rigar ta kasance baka irin me kamar robar nan. Kanta babu ɗan kwali sai fakin gashinta da tayi a ƙasan ƙeyarta. Bluetooth ne a kunne ya tanaji latest waƙar Hamisu Breaker me taken mu daina TSORO. Wanda wakar yake ratsa zuciyanta kai tsaye, domin tabbas talakan kasa shine a wahale babu tsoron Allah a zuciyoyin shuagabannin mu. Kana babu tsoron Allah a wajen wasu jami'an kasar.
Tun ɗazu yake tsaye yana kallonta a ƙalla ya mata sallama sama da sau uku amma shiru bama ta jishi ba. Wani kakan shagaltar yayi a kallonta yadda take motsa ƙananun laɓɓanta shi yafi komai tafiya da imaninsa, aikinta take cikin nishadi da nutsuwa harta kammala ta juyo da biyar tafiya, Nan sukayi hudu dashi saurin ja baya tayi tana sunkuyar da kanta kasa tare da faɗin.
"Kayi mantuwa ne yaya?"
Ta tambaye shi,shiru ya mata yana sake kureta da mayen kallonsa. Jikinta ne ya ɗan soma rawa kaɗan Idanunta na cikowa da kwalla. Gudun ko ganinta a dakin sane ya ɓata ransa, "Don Allah kayi hakuri!" Ta fadi muryanta na karyewar sansomin kuka. Komai baice mata ba haka ta raba gefensa ta wuce....
Taku ɗaya tayi a na biyu taji lallausan hannunsa cikin tafin hannunta, cak ta tsaya zuciyanta na bugawa domin duk tsawon zamansu ko yatsarta be taɓa kwatankwacin kamawaba.
Juyowa tayi Idanunta na zube da hawayen da take ta kokarin ganin boyewa. Ta buɗe baki kenan da biyar sake bashi hakuri ya taryi nata numfashin ta faɗin.
★I LOVE YOU★
Wani irin yankar kirjinta taji yayi numfashin na kokarin barin gangar jikinta. Dagowa tayi a tsorace hakan ne ya bashi daman tallafar fuskanta yana jefa idanunsa cikin tsakiyar nata idanun. Wani kalan mamular baki tayi Idanunta na far far. ★And I really love you 2 appreciate my love★
Kalamansa suka dade mata dirar MIKIYA a tsakar kanta. "I lOBE YHU MARRIYERTOU" ya sake faɗi yana janyo ta zuwa cikin jikinsa. Xuwa lokacin kuwa ƙafafun kariya sun soma rawa tana dab da kaiwa kasa ya rigata yana dorata a kan ƙafafunsa.
Ji da ganinta ne suka dauke na wuccin gadi, {KAMAAL?} Ta tambayi zuciyarta ta hanyar furta sunan sa a cikin zuciyar. Hannuwansa dake cikin nata har loƙacin ta damke da karfin daya sanya kamal ɗago kansa yana me sake dubanta kaɗan. (KAMAAL!) ba tare data sake fargaba zuciyanta ya ƙara ambatar sunan. "Yeah KAMAAL SURAJ RANO na tsananin ƙaunar MARRIYERTOU fiye da duk yadda zaki zata"
"Kasan kuwa da wace kake tare?. Tare kake da Mariya Mariyan da sau uku anasa bikinta ana fasawa, wannan mara sa'ar! Wannan wacce ba kowa bace ita fa ce wacce ta tashi cikin tsananin rayuwa? Sammm Ni banyi zubi da kalan matar auren kaba yaya KAMAAL, A nawa tunanin ka aure nine domin cire mahaifina daga cikin damuwa. Ka aure ni domin kana tausayinmu wacce zaka iya sak........
Bata karasa ba ya rufe bakinta da nashi tsawon minti uku. Sai kuma ya ɗago idanunsa na tara ruwa.
"Na aurekine don ina sonki MARRIYERTOU! Na aureki bisa jagorancin zuciyata domin tun baki kai haka ba nake jinki har cikin raina!, Yanayin nutsuwarki, kamalarki haɗi da kyawawan halayenki ban bayyana miki bane gudun kada na ɓata alaƙarki da tsofaffin samarinki. Amma sai gashi Allah ya bani ke ta inda banyi zata ko tsammata ba!. Sai da nayi azumin kwana uku na nuna godiyata ga Allah daya bani ke a matsayin matar aure na, Alfarmar dazan nema daga gareki shine kawai ki SONI!, Ki SONI kada kwatankwacin yadda nake muku ne inason mu rayu cikin aminci bisa jagorancin tsabtatacciyar soyayyar da zamu gudanar a cikin rayuwar zaman aurenmu!"
Sosae ta sake ƙanƙameshi tare da sake shigewa cikin jikinsa tana sakin wani irin kukan da batasan dana me zata ƙirashi ba, kukan farin ciki ko akasin haka?....
"Nasha tazarar dake tsakanin mu irin tazarar sama da kasa ne yaya KAMAAL! Na zata SO be yimin adalci bane dana kamu da son wanda nasan bazan taɓa samu ba har gaban abada a matsayin mijin aurena. Nima INASON KA YAYA KAMAAL! Inaga tun kamin ka kamu da soyayya nina kamu da taka soyayyar yaya KAMAAL. A zatona kamin zarra kafi karfina tako ina Shi yasa na bisne hakan a cikin cannn karshen zuciyata! I LOVE YOU FOR EVERYTHING my Ayh"
Kanta ya dora akan kirjinsa tana jin yadda zuciyarsa ke bugu fat fat. "Da gaske kike? Da gaske kina sona Mrs Ayh?"
Ya fadi kuma yana jefa idonsa cikin tsakiyar idonta, kanta ta gyada mishi tana sake lafewa a jikinsa.....
Bakinsa ya haɗe da nata daga zaunen yana mata wani irin lafiyayyan Romance. Daukarta yayi cilak yana shigewa bedroom nashi, a ƙalla sun ɗauki good 30 minutes kana suka fito hannunsa riƙe da files ɗin daya dawo ɗauka......
Wurin aikinsa ya koma kai tsaye domin kota halin yayane so yake saiya cafke me lefin nan, haka zai ci gaba da zakulo manyan masu laifukan da suke ɓuya ta karkashin kasa. Kai tsaye Lafiyayyen office nashi ya wuce Saida yayi wasu ƴan rubuce rubuce akan file ɗin kafin ya janyo laptop dinsa copying komai yayi ta ciki.
Wayansa da yay ƙara ne ya fidda woyace me muhimmanci dole ya amsa, bayan sun gama ya kunna data da niyar turo sako ta Whatsapp sai abubuwa suka yi ta faɗowa saman screen ɗin woyan musamman ta peonies.
Da niyar share sakonnin Ni yaje amma saiya dakata ganin hoton kamilallar fuskan da bazai taɓa mantawa da ita bane akayi wasu rubutuka akai. Kai tsaye ya gane pisc ɗin na ranar dazai bar kasar ne.
★WANTED?★
Ya sake maimaitawa wani guntun murmushi na kufce masa kaɗan.
"Ya baku baya kuyi duk iya yinku har zuwa makura maza kuyi ta Aman wutarku, don shi idan ya tashi wanka da wutar yake bi ma'ana wankan wuta fire 🔥🔥🔥"
Manna woyar yayi da fuskansa yana sakin ijiyan zuciya bayan yayi wani short rubutu akan fuskan AK ɗin daya juya.
*BY AMMEY LAYLERH*
*🦅 MIKIYA 🦅*
*~We want an end to oppression💪~*
https://chat.whatsapp.com/GiLzmY90dz17bRbw5yMYBg
____________________
*MARYAM NASEER*
~AMMEY LAYLERH ✍️~
✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~*
Page 49&50
# ROMANCE
# BLACK MONEY
# DEEP
# Hope
# courage
# Survival
# Humanity
# Inspiration
The Beginning of the Beginning
🤍🔥✅✅✔
⭐⭐⭐⭐
Akace salati baya hana ɗaukar rai kowani rayuwar ɗan Adam akwai salon ƙaddarori masu tarin yawa, akowacce duniya akuma koda yaushe kaddara tana tafiya ne daidai da rayuwa, haka kuma tana rayuwa da mune cikin farinciki ko akasin haka.
Sannan kuma babu wani bawa wanda ka iya gujema tarin ƙaddarorinsa lallai ƙaddararmu tana gudana ajikinmu ne kamar jini, akowace rana abubuwa mabanbanta suna faruwa to haka itama ƙaddara takan iya sanjama bawa ako da yaushe, haka kuma babu bawan da yake iya sanja tarin ƙalubalen yadda ƙaddararsa tazo mai ayau gani a daren juma'a wanda wayewar garin azabar itace zata zamo ranar da ALƘALAMIN ✍️ ƘADDARATA zai ci gaba daga ranar daurin aurena. Ko wacce ƙaddara tana zuwarma ko wanne Muminine feji bayan feji haka ko wanne feji yana dauke ne da nashi salon rubutun.
♡✩❤♡♡ ✩
♡NIGHT IN THE MORNING♡
Du inda ka gimla ta cikin shilton hotel ɗin sautin Night music ne ke tashi. Wata iriyar badakalar rawa ake gudanarwa a cikin hotel ɗin. Duk wasu ƴaƴan manya kuwa wanda basu samu halartar sauran shagulan dasu Salman suka shirya ba to ayau kammm sun sami isowa, domin na daren yau din shine shakundum.
Wadan da manyan yara suka shirya ma Salman ɗin ♡BACHELOR's NIGHT✩ duk wasu ƴan gang bang nasu masu ji da fatu da tsantsar wayewa suna cike a wurin. Kallo ɗaya zaka ma wurin ka gane Are not my kind of people domin bana kowa da kowa bane.
Kowa ka kallo yana tare ne da Ben ɗinsa suna kwalɓewa a tare wasu kuma Romance na junansu suke. Kamar yadda uban gayyar da yake tare da dolly ɗinsa da suka shirya tun daren jiya, yanzu ma rungume suke da juna daga shi se wata shegiyar fit out ɗin riga da wani guntun wando, gaba ɗaya gaban rigar a bude yake sai sake shigar da kanta da babu ko wula take. Kwalbar wine ce a hannunta idan tasha saita bashi.
Daga nan surar ta yayi suka faɗa wani bedroom wa'iya zubillah, babu ruwandu da jama'ar dake dakin wanda suke aikata masha'arsu. Suma wani wurin daban suka faɗa........
★RANA BATA ƘARYA
Masu iya magana suka ce wai Rana bata ƙarya sedai uwar ɗiya taji kunya.
Ni Meerah Ayau nafi kowa yarda da batun domin kuwa nima da kaina na yarda wannan rana tawace kam. Domin A yau gidanmu cike yake taff Yan uwa na kusa dana nesa duk sun gama hallara kansu. Ta ko ta ina hayaniyar ƴan bikice kawai ke tashi masu farin ciki nayi haka basu baƙin cikin ma duk nayi. Ga tarin abinci kala-kala da ake ta hidimar yi saidai kash! Babu dangin Anne'nmu ko ɗaya. Sai Hajiya umma kawai wanda za'a ƙira da dangin Anne'n sai kuma mutanen da ake mutunci dasu.
Zai wasu ƴan ƙananun gulmace gulmacen dake tashi wai babu abinda Anne tayi tanadi na biki. Tanaji tayi shiru ta share su domin ita sammm wannan ba matsalar ta bace, Ni kuwa Ina cannn kuryar ɗakin Anne'n zaune cikin shigar wani mayen leshi maroon color's.
Wanda yay masifar fitowa dani sai na tashi tamkar wata irin jinin larabawan nan ko kasashen ketare, ga gyaran da aka min ya sake tsatstsafo da zallar kyawuna na asali sosae dan ba ƙarya Anne tayi ƙoƙari ba lefi ita da Hajj umma. Acan ƙasan zuciyata kuwa jina nake duk wata iri kamar yanda aka san duk wata amarya da shiga irin wannan yanayin a irin ranar Ranan. gefe.Shigowar Disha da wasu kawayena suna rangada min guda aka shine ya sake sanyaya jikina sai kace ba wannan meerah'ɗinba ƴar zafin kai. "Allah yayi an daura amarya a gidan Salman, Ni zaki fara Bama wannnan kwallelen farin goran albishir ɗin"
Ban sake tsinkewa da lamarin ba Saida naji shigowar babban yayanmu yaya Ibrahim. hakan shiya sake tabbatar min cewar shikenan an ɗauro auren. gabana sai ya shiga wani irin luguden daka da sauri-sauri wani irin tsoro da fargaba na ratsa min cikin ɓargo da duk wata magudanar jini ta jikina. Shikiyancin da su disha sukaci gaba da min tare da guɗa a saman kai shine ya sake tattare duk wata nutsuwa data saura wa jikina. Sai na samu kaina da sakin hawaye masu zafin gaske da ban san dalilin yinsu ba, domin na gagara banbance komai a yanda ya dace na fahimcesa wanda kai tsaye Ni zan iya kiransa dana baƙin cikin zama mallakin Salman da nayi a wannan rana. Bugun da zuciyata taci gaba yine ya sanya ni lumshe idona a take wasu hawayen suka sake sakkomin. Shewa da dariya suka shiga min suna cewa duk hawayen farin cikin mallakar Salman ne ai hawayen. Ni kuwa ni kaɗai nasan kalan yanayin da nake ciki. Ya tabbata kenan ƙaddarar wani sabon fejin ta sake buɗe min? Ganin kuma yanayin sanyin nawa yayi yawane ya sanya su disha kyaleni, batare da sun fahimci kamar akwai abinda ke damuna ba don sun dauka ƴan izzar ne a kusa.
Daga can tsakar gida kuwa taro yay taro gida ya sake kacamewa da hayaniya irin ta biki, Wasu na hotuna wasu na kwalliya wasu na hirarsu haka ma masu aikin abinci nayi. Bayan daura Aure da kamar mintina ashirin baffanmu ya ƙira Anne, bata ɓata loƙaci sosae ba ta dawo fuskanta da ɗan sassauci ba kamar kwanakin bikin ba. Nan abokan zamanta suka shiga kus kus a tsakanin su bayan sun gama gulmar wanne irin sulun bikine da babu dangin mahaifiyar amarya, a loƙacin ma Saida Aunty labiba babbar ƴar Hajiya umma ta taka musu birki kana suka shiga nutsensu. Domin
All Chapters
Font Size
16px
Background
Progress
Chapter 17 Chapter of 18