Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
jarumtaka tanbuwal ya sheƙe da wata mahaukaciyar dariya kafin ya dakata. Cikin Wata irin dangerous voice ya furta. "Ai baka cika cikakken NAMIJI ba tunda Saida ka hada hannu da mace kafin kawoni i zuwa gare ka,karkaga ina karkashin ikon ka ka zata zaka iya min wani abu. duk da cewar zaki shine sarki a dokar daji amma karka manta damisa itace gwana wajen iya farauta" Wani irin lalataccen kallo Æk ya wurgama tanbuwal tare da Crossing ƙafafunsa yana kora kwalbar wine ɗinsa. Cikin wani irin hosky voice ya ce. "Ko wanne mafarauci garzone har sai sanda ya fuskanci ingarman zaki. Wannan haushin ƙaramin kuykuyon kare kake! Ka sani haushin ɗan ƙaramin kuykuyon kare kuwa ba gurnanin damisa bace! Ammah Ka jira hasalin yadda gurnanin ta yake. Ka sani ABDOUL-MALEEK ba kamar sauran sharar daka saba takewa bane, wannan Asalin Cikakken fusataccen damisar daya fito domin farauta ne a gabanka" Ya fadi tare da rotsa kwalbar wine ɗinsa kwalbar tai ratsatsa ta baje a wurin. Zuwa loƙacin babu komi a tare da Ak sai asalin fusatarsa kawai ake iya hangowa. Armstrong dake tsaye ne ya tunkari inda tanbuwar ɗin yake tare da soka masa allura a gefen yuwansa Yana bin bayan Ak ɗin shima. Bai tarar dashi a main sequence parloun gidan ba, wayarsa ya fidda tare da tambayar su Boss ya fito ne?, Tabbacin be fito ba suka bashi hakan ya sanya shi sauke wayar tare da bin ko wanne entrance door da kallo. Wani irin zafaffen numfashi ya fesar tare da tsananin tausayin uban gidan nasa. Kabar ƙasar ka kabar gidanku kabar danginka kazo ƙasar daba taka ba kana musu aiki da dukkanin zuciyarka da rai da ruhinka. Ko dan wannan abin ma bai ci ace gurɓatattun cikin ƙasar Nigeria'n sun sauya ba da kunya ma ace an rasa gwarzo zakwakurin da yake tsaye akan ƙasar sa. Kodan sun riga sun sanya tsoro ne a zukatan al'ummar OHO? Duk wani namijin da yake jin kansa da zafin kansa ta kawo akan ƙasar to kuwa Insha Allah sai an san yadda akayi aka kawar da wannan mutumin. Shin me masu kuɗin duniya da masu mulkarta suke son zama ne???. A kullum shine tambayar dake bisne cikin zuciyar Armstrong. Shi kikakken ɗan Nijeriya ne amma baya alfari da hakan saboda gurɓatattun cikin ta da ɓata garinta suka kewaye ko ina na cikin ta. Kasar data zamo koma baya ko lissafinta ba'ayi a cikin duniya. A cikin gidanku ma babu adalci bare akai ga wani wuri me nisa, a gaban idonsa dangin mahaifinsa da suke ƴan uba suka sanya wuƙa suka yanke makogwaron mahaifinsa sa!, Akan dukiyar da guminsa ne shima ya bashi ba sata yayba ba kuma haram yabi wajen tara taba. To taya muke tunanin duniyar mu zata gyaru a cikin gidajenmu babu adalci? Sai tsananin azaba yakai tsanani mu dinga ƙiran Allah gyara. Tofa baya gyara ba dole muma sai mun gyaro ɓarnar dake cikin gidajenmu. Bawai Ƙasarce a ɓace ba mu al'ummar cikin ta mune a ɓacen mune ɓatattun dole kuma dama gyara ta cikin gidajenmu yake farawa. Idan muka gyara halayenmu sai Allah ya gyaramu Amma muma muna da kaso mafi girma akan tarin abubuwan dake faruwa da kasarmu uwarmu...... Wani irin zafaffen numfashi ya furzar tuno yadda ƙanwarsa ƴar shekaru uku a loƙacin take kuka tana dukan ƙirjinsa tana ƙiran mommy na daddy na. Gaba ɗaya jininsu ya ɓata jikinta. Wasu hawaye Masu zafin gaske ne suka zuba masa a lokacin daya tuna sadda mahaifinsa ke faɗin. "Ka gudu! Ka gudu kai da ƙanwarka ka tabbatar kun rayu ABDOUL-MAJEED, ka reni zuciyarta akan gaskiya da gaskiya ka tabbatar ka kulamin da RIYYERNERTOU, ka zama gatan ta,haskenta, ita kaɗai ce danginka ƴar uwa ɗan uwa ku tafi ka tafi wata duniyar kaje zaka rayu tare da tsarkakkiyar zuciyar da zata reni taku zuciyar da irin tashi zuciyar da ɗabi'arsa.kamin alƙawarin zaka zamo mutum na farko da ƙasar sa zatayi alfahari da shi... Wadannan sune kalaina na karshe da suka tsaya masa cakkkk acikin tsakiyar ƙirjinsa. Mahaifiyarsu kuwa ta mutu ne ba tare data iya furta masa komi ba sai idonta dake kan Riyya. "Ka gudu karsu dawo su sameku domin a zatonsu kuna makaranta ne, yanzu haka sun tafi ne da niyar su dauko ku kuma su kashe ku. Wannan kuma shine babban zunubi mafi girma da zasu aikata idan har suka taɓa lafiyar koda ɗaya daga cikin kun!........... Be ƙarasa maganar da yake shirin faɗar ma rai yayi halinsa haka ya ɗauki RIYYERNERTOU akan shoulder nashi ya gudu da ita. Sun sha matuƙar walahar gaske har tsawon shekaru uku a lokacin yana shekara na goma sha biyar ita kuma riyya tana da shekaru bakwai. A haka wani baƙin dare ya riski rayuwarsu shida ƙanwarsa. Daga nan babin sabuwar rayuwarsu ta fara shida ƙanwarsa ta hanyar keta mata mutuncinta ta hanyar mata fyaiɗe Anyi Raping ɗin. Masu iya magana sunce ko wacce ƙaddara tana da nara madubin,sudai nasu madubin Ak ne domin a lokacin da yake tsaka me wuya cikin mugun yanayin makauniyar ƙaddarar data riski ƙanwarsa. A daidai lokacin Allah ya kawo masa Ak shine ya shige masa gaba akan komi! Shine yake amsa sunan UWA UBA a gare su shida ƙanwarsa har kwanan gobe da safe. Ya basu tarbiyya ya inganta rayuwar da tarin ilimin addini da na boko. Ya shige musu gaba wajen ganin sun zama wani abu A koda yaushe Har abada abadan abada ABDOUL-MALEEK KUWAIT shine kashin bayansu. Hawayen tausayin gwagwarmayar rayuwarsu da suka fuskanta ya share ya nufi entrance door ɗin da yake da tabbacin anan Ak ɗin yake. Shima ɗaya daga cikin room din ya fada yana kokarin ganin ya kawar da tunanin dake kokarin zeroying maid nashi. Duk kokarinsa nason ganin ya kawar da tunanin dake neman addabarsa abin yaci tura, kansa ya jingina da jikin kofar tare da lumshe Idonsa. Numfashi yake fitarwa Ahankali yayinda yake furta kalmar. " Innalillahi wa'inna ilair raji'un,² Ya hayyu ya qayyum" daga cikin zuciyarsa domin kuwa tsabbb komai din da yake gudun ya faru ya rigada ya farun. A take kwakwalwar kansa ta nemi juyewa amma ambaton sunan Allah da yake hakan ya sanya. Ahankali nutsuwa ke saukar masa acikin zuciyarsa yayinda yaji tarin damuwarsa na gushewa.sosea yaji sanyi da cikakkiyar nutsuwa da salama acikin zuciyarsa. Gaban fridge bottle water ya nufa kai tsaye tare da ɗauko bottle water ya ɓalle murfin, ya kafa bakinsa Saida ya tabbatar ya shanye ruwan dake ciki tsabbb kana yayi wurgi da gorar. Wata iriyar ajiyar zuciya yake saukewa tare da sanya hannu ya ya dafe kansa. duk yanda zuciyarshi taso sanya shi dogon nazari yaki aminta da hakan haka kuma yaki bama brain nashi daman yin tunani kamar yanda ya saba a wasu lokutan. Ya jima a tsayen da yake kafin ya nufi bathroom, ya sakarma kansa ruwa Ya ɗebi mintoci kafin ya fito jikinsa na faman ɗigar da ruwa, mini towel ɗin dake rike a dayan hannunsa na aikin tsanewa. Wani farin trouser ya zira da t-shirt ita ma farar directly ƙroom din daya tabbatar da ak din na ciki ya nufa, tare da danna door belt din bedroom din yana jiran a bashi umarnin shiga. ★★ÆK★★ Yana shiga bedroom din kayan jikinsa kadai ya cire tare da daura fari tass din towel wanda ya ma wani irin lago lagon dauri kafun ya wuce bathroom. Kai tsaye cikin bathtube ya shige wanda ya hada ruwa me dumi da fresh out din wankan daya zuba. Aqalla sai da ya shafe mintuna masu dama kafin ya fito,tamkar wanda yake sauya fatar jikinsa. Fatar nan sai uban daukar ido da walainiya take ta kota Ina Ak namiji ne tsayayye da babu abinda yake masa shamaki da cikar zatinsa. Lafiyayyar fatarsa dake daukan idonsa ya kalla ganin wato shi Hutu da jika cikin arziki da nutsuwa Wani abu ne na daban da idan Allah yayika cikinsu basa taba boyuwa ko yayana. kauda idanunsa da suka dan canza launi sakamakon shigar ruwa cikinsu ya mayar ga madubi yana qoqarin tsane sumarsa data jiqe da ruwa,abu guda daya tak da zai fara gaya maka AK din ba asalin bahaushe bane, kodan yadda farar fatar jikinsa take da kuma tulin gashin kansa da yake amsar kudade masu gwabi wajen gyaranta. Tamkar babu wanda yake jiransa haka ya kammala shirinsa a nutse cikin wasu Ash din riga da wando Armless marasa kama jiki.wasu tausassan flip flops ya zura dogayen qafafunsa wadanda kamar basa taka qasa dan tsabar laushi da kuma taushinsu. kana ya kwashi wayoyinsa tare da daukar rimot ya danna kofar bedroom din ya bude. Waya ya fito yana yi cikin yanayin sakewa kadan. Gaidasa Arms yayi tare da fada masa an shirya dining. Bai ajiye wayar ba ya dan dago ya dan kalle shi kadan tare da amsa shi da kai, bai kuma janye wayan ba har zuwa lokacin. Cikin ishashshen takunsa ya nufi dining din har kuma lokacin yana manne da woyarsa, Ba wasu abinci masu nauyi bane junk food ne kasancewar babu restuarent a kusa ga kuma a wannan gidan babu kuku's. Idan ka dauke sikuriti babu kowa dake rayuwa a gidan. Wannan kamar gidan horo yake. A nutse ya jagali food din bame yawa ba yaci ya tashi har lokacin kuma woyarsa yake hankalinsa kwance. Kai tsaye coumpaund na gidan ya nufa da jikin railer ya jingina yayi crossing kafafunsa. Rigar nan da bata kama shima iska sai dade kwantar da ita a jikinsa take kan babu yar gadon fcarp. ★★★ ★★★ A dab plat din me napep ya sauke ta kamar kullum yauma sanye take cikin dogon shijjab har kasa, yau ba nikap ta sanya ba nose mark kadai ta sanya sai idonta data rufe da bakin glass. Rolex din skmee 2/1 din dake daure a hannunta ta sake dubawa da kyau don tabbar da nan din ne inda na'urar biyayar ta kawo ta. Tun daga kan uban tight security'n dake zagaye da get din ta tsorata. Amma kasancewarta mutum bame nuna sarewarta a fili bane ya sanya ta nufar katon get din. Cikin rashin tsoro ta tunkari get din baki daya kawunansu a sama yake hakan ya sanya ta yin sadab sadab taje a sukwane zata shige suka farga da ita. Ko kafin su dago kuwa wata farar kwalbar dake rike a hannunta ta musu fesar turare da ita ji kake "fessssss" yuf tayi ta fada gidan. Sadalaf, satalaf haka ta shiga kutsa kanta cikin gidan dayafi kama dana barayine ma zatace kome, gadai yadda hantar cikinta take kadawa a zahiri amma kuma ta danne tsoronta haka ma a yanayinta baka isa fuskantar a wanne yanayi take a ciki ba. Kasancewar duhun magrib na dab da kawo karasowane ya sanya ta ringa bin jikin manyan flower's din coumpound na gidan. A haka har takai ga jikin katuwar railer din dake coumpound na wurin,Kamshin da bazata taba mancewa dashi bane taji sun kawoma kofofin hancinta ziyara. Kanta ta dago daga kokarin tafiyar da take shirin ci gaba dayi,Ido biyu sukai daidai Yana kammala wayar shi. Wani irin mugun tsoron kai tsayene yanzu kammm taji ya ziyarceta, Hannuwanta da suka shiga mazarine ya sanya ta dire Robar dake hannunta ahankali gudun kada ya subuce mata, wani shegen kallo ya jefeta dashi a kuma daidai ta sake dago kanta aikuwa yaja kyawawan fararen idonta masu kama dana mashaya a cikin nasa ta hanyar sarketa da nashi catizeen eyes dinsa. Yau kam ta gama tabbatarma kanta tata kuma ta kare tunda ta kawo kanta da kanta gidan wannan me satar mutanen. Muryarta na yankewan tsoro da mamakinsa cikin qaramin sautin ta furta "pah pa pls don Allah........ Wani shegen kallon daya jefa mata ne ya sanyata kimtse bakinta tayi shiru. Gashi kuma daf da juna suke sosai Kai tsaye hancinta babu Abinda yake shakar mata bayan mayen kamshinsa. Wani numfashi taja ahankali tareda dauke idanuwanta daga kallansa gabaki daya saboda tsoransa da taji yana nema Kamata. Jikinta ne ya fara mazari na tsatsanin tsoronsa ganin yana sake matsota, ja baya ta shiga yana sake binta yana ci gaba da jefa mata wannan dan iskan kallon nasa. Kankame jikinta tayi wuri guda tare da toshe kunnuwanta ta fasa wata uwar kururuwar data sanya duka mutanen dake cikin gidan yowa wurin a guje. Wani irin fusgarta yayi a fusace yana yin wata boyayyar hanya da ita. A daidai lokacin kuma harsu arms dake cikin gida sun kawo wurin, wulgawarsa kawai suka kalla ba tare da sun lura da Meerah ba. Suna kaiwa wani wuri ya danna wata na'ura me kamar botton kai tsaye sai gasu a cikin wani fitinannen hadadde tsararren cumputer room. Gaba daya shiga dakin na'ura ta dauki shelar shigowarsa dakin tare da ambatar cikakken sunan meerah kai tsaye. Hakan ne ya sanyata kwatar hannunta daga kyakykyawan rikon daya mata tana bude idonta da niyar mata masa wasu maganganu masu irin myankar zuciyar nan. Ai kuwa bata sauka idonta a ko ina ba sai kan grey 11/in/21 rose glasses out din da kai tsaye hoton mutum yake irin rarrabewa nan, idonta bai sauka akan ko ina ba saikan hotonta daya rarrabe kusa ashirin da wani abin. Sai nashi daya juya baya iyaka lafiyayyar farar fatar jikinsa kawai take iya gani!, Ai bata san sanda ta tafi da wani irin mugun gudu ta fada jikinsa ba tare da kankamesa tana sakin wata gigitacciyar karar daya sanya baki daya nu'urorin dakin daukar karar itama. Wani irin kulle idanunsa yayi tare da sakar mata wata razananniyar tsawar da kai tsaye ya idasa tafiya da numfashinta, domin dama tana dab da somewar na a lokacinma numfashinta ma seezing yake sai tsawar ta idasa tafiya dashi kai tsaye. "Ochhhhhh!" Ya furta yana ma rasa yadda zaiyi da ita saiya saketa daga tsayen da yake, muguwar buguwan da kanta yayi ne ya sanya numfashinta dawowa. Ahankali ta shiga kokarin wara idanuwanta, Dashi dake zaune kan wata kafurar luzury caution ta sake bude idonta. A take komau daya faru da ita yanzu ya sake dawo mata da rarrafe cikin muryan kuka ta isa gabansa. "Don Allah ka taimakeni! Na rantse batar hanya nayi ne Anne nace ta aikeni gidan gwaggonta" "Really?" Ya fada da alamar tambaya yana fiddo da wata yar karamar aba daga cikin aljihun dogon wandon dake jikinsa tare da fadin. "Kodai kin biyo wannan abar ba ohhh" Wani irin zaro idonta tayi tare da fara jijjaga kanta zara fara magana yayi saurin katseta cikin dakilalliyar muryan san nan na no nonsense ya furta. "Shiiiiiiii" Da alamar zeeping na bakinta sai kuma yace. "Ki sani gidan nan da kika samu damar shigowa duk a cikin target nawa ne, don hatta napep in da kika shigo duk cikin tarko nane domin ni kaina na'ura ne. Motocin na kaiwa inda nake na tabbatar da akwai wannan cctv footage nan" Ya karasa da jefa mata abarta yana mikewa tare sai kuma yadan juyo kadan yana sake fadin "Ohhhh Ashe bayan arhar da kike da harda jarum ma kin iya na jinjina miki dama nasan ko waye me ita dole yazo weldone ashe ba silly girl ce" Daga haka ya juya da nufin tafiya ta gudu ta biyo bayansa tana "Niban fadama kowa ba don allah ka fitar dani na Kar hankalin Anne na ya tashii bata san na fito ba da mij....... Wani wulakantaccen kallon daya watsa mata ne ya sanya ta shanye sauean maganarta. Cikin tafiyansa na kamar koda yaushe ya fice ai kuwa tayi wuff ra wawuri hannunsa ta kankame a kirji suka fito tare a dakin. Da wani kyakykyawan lafiyayyan mari ya sauki kyakykyawar fuskanta me kama da atafa don tsananin laushi da haskenta. Ba karamin gigitata marin yayi ba amma ta gwammaci ta juro ta shanye daya dai barta a wannan killed house ne ma ko die house zatace mane oho. Zuwa lokacin kuma har an fara shiga sallan magrib hannunsa ta samu ta yankama wani azabben cijon da saida ta fasa mar fatar hannu, amma kota kanta be biba saima wurin daya bari cikin sauri don masallacin da za'ashiga. Ai kuwa kamar yadda ta shigo yanzun ma tanan tayi nasarar fita kasancewar duk security'n sun riga da sun wuce masjid ne, amma duk da wani gudun bala'i tabar gidan tana faman sauke ijiyar zuciya, Kai tsaye ta sami napep ta fada tare da fada masa sunan anguwar data nufa dab da zata shiga suka hada ido ya mata wannan shegiyar alamar tashi, baki ta murguda masa da yimay alamar yanka wuya tana cewa me napeo din suje..... A lokacin da suka kawo anguwarsu har ana dab da fitowa a masallacin baffanta, da gudu ta fada zauren gidan saida da tsaya ta daidaita numfashinta kana ta shige cikin gidan. Sa'arta daya babu kowa domin duk rashin mutumcin mutan gidan basu wasa da sallarsu, da sauri sauri tayi alwular itama tana fadawa dakinsu a sukwane....... *By Ammey laylerh* *🦅 MIKIYA 🦅* *~We want an end to oppression💪~* https://chat.whatsapp.com/GiLzmY90dz17bRbw5yMYBg ____________________ *MARYAM NASEER* ~AMMEY LAYLERH ✍️~ ✯ *~🌠 JAJIRTATTU WRITER'S ASS.... 💫~* Page 41&42 # ROMANCE # BLACK MONEY # DEEP # Hope # courage # Survival # Humanity # Inspiration 🤍🔥✅ _______________________ Koda Anne ta idar da sallah tambaya daya ta mata shine "daga ina kike? Sai after magrib kike dawo bayan kuma tun sanyin la'asari kika fita?" Dake ita sammm bata iya karya ba inma tayi karyar nan take ake gane tane ya sanya soma inda indar fadar inda taje din. Uban tsawar da Anne ta daka mata ne ya sanya ta fadin. "Gi gidan su su di sha naje Anne" Ta fadi mafanar a rarrabe ga rawan da muryanta yake. Wani irin kallon baki da hankali annen ta cilla mata tare da fadin. "Saidai kuma kinyi kuskure domin dishan tazo nemanki itama tama jima anan din, don haka ina kikaje DIDI!?" Anne ta sake jeho mata wata tambayar. "Zamu fita wani aiki ne dama shine da bata zo na tafi" "Kuma ita karyar ta miye da kai tsaye kika gaza fadamin?" Wasu hawaye ta share amma kuma sake zubowa suke yadda annen ta tsareta da ido ma shi kadai firgitata yake. Haka dama anne take zakayi wasa da ita amma kuma bata karbar no nonsense,sai kuma annen ta sake dubanta a nutse cikin tsantsar kulawa domin ba ta lura ba iyaka tsoron tuhamar da tay mata take gani dangane da Didinta ba. "Ki dauke tamkar babbar aminiyarki, yayarki kan uwarki kana ki dube ni a matsayin mahaifiyar da baki da kamarta, ki fadamin meke damunki?, domin na lura tunda wancan abun ya faru mood naki ya sanja sosae. Idan har bakiji tausayina a matsayina na mahaifiyarki kin fada min damuwarki ba wanne hali kike tunanin nizan shiga? Karkiji tsoron komai ki fadamin komai din da yake faruwa da rayuwarki MARYAMA" Kife kanta tayi akan kafafun annen domin ta yarda kafff duniya bata da ya mahaifiyarta. Komai na labarinta da Ak bata boye mata har dauketan da yayi da irin yadda take ganinsa ya kwamushe mutane. Har zuwa yau data sake cin karo dashi wanda ita ko a ranta bata taba kawoma ranta cewar shi ne ba.... Kuri Anne tayi da ido tana kallon didin nata kawai tama rasa ta yadda ya kamata ta fara, cannn taja wani numfashi kadan tare da duban meerah din ta fara jeho mata tambayoyi tana bata amsa ita kuma. Haka harta ta bata shawarwarin dasuka kamata duk da ma ita nata ya kusan xuwa karshe domin suna cikin satin biki ne tsulum tsulum. Dama kuma daga yau din Anne'n tayi niyar hana abarta fita domin killace ta bata gatan da ake bama ko wacce ya idan za'ai aurenta. Duk wasu hidinduminta suna a gidan hajiya ummah na a gidan kuwa yadda Kasan ba biki za'aiba haka gidan yake domin ko tada zancen ba'ayi. Ba danma wannan rikitacciyar tsohuwar kakar tasu tazo ba da itama kanta har mantawa take da wani zancen aurernta. Amma itama da biyu tazo yau kwanaki uku kenan domin bata kaunar Annenta sammmm acikin duka matan baffanta ita kadai tafi takura mata sa'ar annen ma daya da take da tsare gida bata daukar wargi ko wanne iri ne kuwa daga wurin ko wanne mutum. Shi yasa sau da yawa matan gidan ke shakkarta yadda kasan irin jinjn saurartar nanne ke yawo a jikinta haka take. Ita kanta meerah din wani sa'in kawai kallon annen nata take. Nan anne ta bata shawarwari sosea kuma taji dadinsu tare dajin nutsuwa ta musamman. Don duk wannan tsoron saita nemasa ta rasa Lallai sai yanzu ta yarda da wannan karin maganar ta bature Na *_A problem shared is a problem solved*_ Sai gashi tun ba'aje ko inaba komi yazo mata da sauki. "ALHAMDULILLAH!" Meerah ta fadi incheerfully. ★★KANO★★ Yau kwanakin su baffafofin kamal hudu a kuma yaune suke shirin komawa. Amma sai baban mariya yazo da batun kawai su tsaya a daura Auren dansu a gabansu, da sunso kin tsayawar saida kamal din yayi magana kana suka yarda zasu tsaya a daura auren. Bayan sun sake kiran dangi sun sanar musu wohoho zokaga yadda ake bidiri a dangi nan fa mata da maza suka ringa yowa tururuwa suna dannowa kano gidan kamal. Sunce shima sai sunyi may auren gata irin na ko wanne da, Wasu a gidan kamal din suke wasu kuma a gidan baban mariya aka sauke su. Da yamma kamar yadda baban mariya ya bukata aka daura auren KAMAAL SURAJ RANO da amaryarsa MARIYA USMAN SHEKA akan sadaki dubu dari da hamsin. Akwatuna kuma daga baya zaiyi kwasam saiga abinda ya kusan gigita duniyar kamal domin ga sanarma Ak a kurarren lokacine don besha ma zaiga sakon shiba. Amma sai gashi ya niko gari tun daga lagos zuwa kano dake dama ya taba zuwa sau daya bayan Shi kamal din ak din ya kirashi abujan nan da yaje.. Shi da kansa ya amsawa kamal auren mariyan ya kuma hada musu party dinner a wani katon holll. Ya kuma turama kamal din zunzurutun kudi har million biyu. A daren yabi girjin dare ya koma wajen sha daya da wani abu yabar kano shida arms, Washe gari aka sake sabon biki kana mazan suka tafi sauran maran kuma sai an gama shagulgulan bikim kafin su tafi. A wata sabuwar anguwa kamal yasai gida yabar wannan baban mariya ya aika a gano gidan don su

Chapter 14 of 18