ya tsaru sosai tabude wadrop taga kaya dayawa nata, ga kan mirrow kayan shafa ne kala kala, an narka dukiya adakin bazan iya baku bayani ba, indai kunsan dakin KAJOL TO HAKA YAKE๐tafada toilet tayi wanka tare dayin alwala tafito tashirya cikin riga da wando na parkistan , ta dubi kanta amadubi, taga tarame kuma tayi duhu, tace azuciyar ta bazan taba mantawa dakai ba saheebina.
Yau gani agidan ku wajan mahaifiyarka, ta sauko palo wajan mami suka zauna suna hira suna cin abinci, abba shima yasauko yazauna kusa dasu,, ana hiran dashi yace Ni'ima awani kasa zakiyi karatunki abba ni INDIA nakeso nayi karatuna sai da gaban mami yafadi, donjin ta ambato India, to shikenan bari result dinku ya fito to abba,, ta tashi tahaye sama tana hawaye,, sbd garin da masoyinta yaje yarasune,, haka kawi ta tsince kanta da son zuwa india karatu.
TAKU UMMU RUMAN( NUSNIM) KUBIYONI AGABA, LOT A KISSESS NI'IMAH, MUJSE APAKI YADATI APTI HAI
[10:48AM, 1/24/2017] โช+234 806 448 1931โฌ: ๐๐๐LABARIN NI'IMAH๐๐๐1โฃ5โฃ
Zaman Ni'ima agidan su Ahmad ya mata dadi kullum cikin kulaww da ita akeyi kamar kwai, haskenta ya kara fitowa amma haryanzu bata kara kiba ba, sbda yawan tunanin masoyinta, kullum mami ta dinga mata mita kenan amma harta gaji tabari, abune wanda baza ta taba mantawa ba.
yau watanta daya a minna kuma tana so taje taga ummanta da abbanta da kawarta baraka mami tashirya musu tafiyar, sun isa fantagori lfy yayin da mami tawuce gidan goggonta ita kuma mama tawuce gidansu, inanan shigowa mama, to mami,tana isowa gda da gudu tafada sassan su umma umma, muryan waye wannan kamar ta mamana tana fitowa suka ci karo da mama.
Oyoyo ummana nayi kewarki dayawa saukan yaushe mama yanxun nan, sannu dazuwa ina mamin take ko kekadai kikazo a"a tashiga gidan goggo tace tana zuwa ,umma abba nanan baya nan yafita, hala mama haryanzu kina wannan tunanin naki ne, mekika gani umma gashi kin kara haske kinyi kyau amma bakiba sai rama. umma lokaci ne xanyi, to allah ya nuna mana ameen umma,tashi kije kigaida su umman aliyu da umman umar, to tana shiga tacikaro da salis hmm mutanan minna anmanta damu, anxama wasu bare. to ina ruwanka sa ido kawai, kai dai ha zaka kare wlh salis.
Ko ai kedama gaskiyar ce bakiso uhmm su umma su nanan eh, yaya ali yadawo fa to ni ina ruwana,, ina ruwanki.kikace, yanxu tunda ba ahmad mai zai hana ayi da yaya ali allah ya kyauta, ni nan da kake ganina yanxu bana shawa'ar soyayya mutum daya tak nayi mawa shi kuma yanzu bayara ye,, hakama soyayya axuciyata bata raye, sbd haka kabani waje nasha iska karka sake damuna dawani maganan su yaya ali.
Duk naganan dasukeyi akunnan ali din da ummarshi saiji suka ana cewa to yanzu dai kajiwa kunnanka aliyu yarinyar nan ba sonka takeyi ba saboda ta ganka baka da kudi kamar saurayin ta da yarasu, saiga umman su umar itama tafito banda abunka ali,, me zakayi da wannan yarinyar da tagama tallar kanta awajan masu kudi, mu da taki ya'ya yanmu saboda bamu da kudi,, yanma ankaita wajan masu kudin don tazauna acan tasami miji mai kudi.
Kamar ko kinsani mama sai zubar da hawaye takeyi tarasa ma meza tace duk umma ta najin abunda suke fada amma takasa taje ta janyo yar tata saboda hakuri yayi mata yawa dai dai nan mami tashigo ta tsinci maganan ana ta zagin mama, aliyu wanda ranshi yayi mugun baci yace shegiyar yarinya kawai juyuwa tayi ta kalleshi taji baza ta iya daukan zagin da yayi mata ba. tace mai ni ba shegiya bace sai dai kaine shege, yataho afusace zai mareta yadaga hannu kenan sai ga mami ta rike hannushi,, kai kana haukane zaka mari mace.
Are you mad sai yakasa cewa mami komai duk randa kayi kokarin taba mama wlh sai nayi shari'ah dakai, tace bata sonka dole zakubi kusa yarinya agaba meta muku ko ana soyayya dole ne, sai ga umma tazo tana bawa mami hakuri , kyaleni tunda ke kinki daukan mataki sai sun la'anta miki yarinya sannan zakiyi magana, to nikam vazan dauka ba. bari abban ta yadawo, suna jin an ambato uban dawaki kowaccen su tafara kame kame. saboda sun san uban dawaki baya wasa da mutane kuma zasu gane kuran su, taja mama dake kuka sukabar sassan nasu, tana lallashinta.
Umma tana bawa mami hakurin karta gayawa uban dawaki ita koma tace wlh sai tafa don idan akayi shiru ba asan me zasu yi nangaba ba, har suna cemata tabada kanta awajan masu kudi, kenan suna nufi ita yar iska ce bazai yuba wlh, mama tashige dakinta tarufe tana kuka, tana kiran sunan Ahmad dinta kaga cin mutuncin da ake min har ana la'antani da yar iska, ahmad kaikadai sonka ke zuciyata bazan iya son waninka ba har inkai da auranshi, inama inama kana raye, ta tashi tayi alwala tazo tayi salla tana rokon allah yashige mata gaba. tayiwa kuma masoyinta addu'ah.
Aikuwa uban dawaki yana dawowa yasamu labari wanda hakan bai mai dadi ba yata kannan nashi da matayaen da yaran nasu yayi musu fada, ya nuna musu bacin ransa yayi aliyu fada sosai, yau idan mama tace tana sonka zanbaka ita amma tace bata sonka,, sanin kankune nibanawa yara auran dole, shine har kana neman marinta saboda allah, to kar inkuma ji don zansabawa mutum, aliyu yace kayi hakuri abba baza akuma ba duk suka bada hakari, kowa yawatse.
Dagashi sai mama aka bari yace zonan mamanah kiyi hakuri ko bakomai abba, ya wuce, abban Ahmad yace min zaki fara makaranta a india kuma nan kike so kikace eh abba nafi son nan, meyasa bazaki yi anan kasarmu ba, abba ni nafison can to shikenan allah yasa shine mafi alkhairi.
Ameen abba banaso kitafi ke kadai ne ko zaki tafi da yar wajan innarku baraka tunda tare kuka gama ga mahaifinta ba hali kuma, ni sai indauki nauyin karatunta, eh abba wlh xanso hakan sosai tana murna, to shikenan sai ahadaku kubiyun ko, kira min ummanki, yasanarwa da umman nata itama tayi murna sosai batasan dame zata sakawa mijin nata ba.yafadawa mami da abba yadda yatsar abban Ahmad yace kabarmin komai a hannu na ni nadauki nayin Ni'ima da Baraka insha allahu.
Uban dawaki yanata ta godiya sosai, mami ko kamar ansata a aljanna kasancewar yan'mata biyu agabanta, mama tashirya da zuman taje gidansu baraka ta labarta mata, umma tace uwar zumudi to ba inda zaki, sai tayi kamar zatayi kuka haba umma zanje gaida inna mairo ne kawai fa, bawani ni zakije dai kilabartawa kawarki,, mami ta ashe maganan tana dariya.
shirya kije ko baby na rabu da umma, sai ta rungume mami, mamina nagode allah ya barmin ko ameen tayiwa ummants gwalo keba zanka maki, umma kina dai kishi danine sbd nafiki kyau , dalla awajan wa kika samu kyan inba wajena ba, suka kwashe da dariya. Ni'ima tana tafiya tana murnarta, taxu daidai inda suka fara haduwa da Ahmad dinta sai da ta zubda hawaye na tuno masoyinta, allah sarki saheebina, allah ya jikanka ta isa gidan da sallamarta sai ga baraka oyoyi kawalli suka rungume juna suna murna. ta gaida inna, sanna tafara bawa baraka labrin abunda ya faru, baraka harda kukan dadi kice zamu zama likitoci kenan inama Doctor Ahmad na raye dayafi kowa jin dadi, allah yabiya iyayenshi don bamu da abun da zamu biyasu, kuma har kasan india fa, amna wannan abu yayi min dadi,, umma zatazo tafadawa inna ai harda abba ma to shi kenan.
result din su mama yafuto kuma tasamu abunda take bukata hakama baraka,, anyiwa iyayenta bayani kuma sun ameence sai fatan alkhairi, wannan komawar da zasuyi da baraka suka koma bayan sunyi sallama dakowa kuma anmusu nasiha akan sukula da mutuncinsu, kuma suyi abunda yakai su karatu, kuma surike iyayen Ahmad sosai , don mutanan kirkine.
Abdulrahman ne yakaisu minna tare da mami, suna ta hira a mota mami tana jin dadin su,, yauwa abdulrahman inaso zaka koyamu musu mota, mami mota fa kikace, gaskiya zaki sha gwabasu daya ina ruwanka bayarana bane, inban shagwabasu ba wazan shagwaba cikin raha yace gani mami, a haba kai kagirma sosai, mama ta mishi gwalo, sun isa gida lfy masu aiki suka tarbesu mami ta nunawa Abdulrahman dakin Ahmad, mama kuma tace ita da baraka daki daya ya ishesu don suyi ta hira, kowa yaje yayi wanka anfito kan daining cin abinci, gobe nefa nake son afara koya musu. so that ina so sutafi indi sun iya mota, kaga basai sundinga hawan motan haya wajan zuwa lectures ba, ok mami allah y kaimu.
TAKU UMM RUMAN ( NUSNIM) KUBIYO NI AGABA DON.MUJI๐บ๐miss u NI'IMAH
[10:48AM, 1/24/2017] โช+234 806 448 1931โฌ: ๐๐๐LABARIN NI'IMAH๐๐๐1โฃ6โฃ
Yau suntashibda zumar abdulrahman zai koya musu mota bare ma Ni'ima tafi kowa zumudi, baraka ko tsabagen kunya ne, yacika ta koma amotar ahmad abdul ke koya musu, wanda hakan sai da hankalin mama yatashi tana ganin kamar ahmad dinta ne. sannu ahankali suna koya, akwana atashi bawuya su mama an iya mota.
Har sai da sukayi kwarya kwaryan waliman koyan mota inda mami da abba suka mika musu gift na keyn mota, kowacce ansiya mata, tare da murna suka rungume mami suna mata godiya sukaje wajan abba ma suka mishi godiya tare da addu'a mai kyau, abba allah ya kara bude yasa albarka aciki koma ya jikan iyaye, tare da Ahmad sai ga hawaye a idon su duk. ameen nagode allah ya muku albarka y baku abunda kuke so duniya da laheera ameen.
kushirya gobe da safe in allah ya kaimu zamuje muyi siyayyan kayanku donnan da 1 week zaku tafi, to mami, abdulrahman yace lallai yaran mami, nikam abdul wai yaushe ne zaka fitar da mata kayi aure ya sosa keya abba yace inkudi ne akwai su sai kafada amaka, Lah abba wlh ba haka bane, to menene bani da budurwa ne mami tayi salati kamarka ace baka da budurwa mama ta anshe maganan wlh mami yana da shi,bayaso yayi auren ne yanxu, wai sai dani bai san nikuma bani damiji ba, to aikema inkin samuzakiyi, tab niko bazanta ba yin aure ba don bazanci amanar Ahmad dinaba, sai ga hawaye ta tashi tabar wajan.
Baraka ta bita daki mama sai kuka takeyi haba mama zaki bi duk kitada mana da hankali wanda ya mutu ya mutu bazai dawo ba,, har kice baza kiyi aure ba yau wata shida da rasuwan doctor fa yaci ace kindaina damuwa, kin rike iyayenshi da hannu bibbiyu, basa jin dadi idan suka ganki cikin damuwa fa, saboda haka pls kidaina kinji kawata kuma kanwar mijina, tayi sauri tadaga kai takalle baraka.
Baraka tayi mata murmushi what did you mean. kina nufin kece budurwan yaya abdulrahman , YES IS TRUE, mama tayi wani irin tsalle tafada jikin baraka tana murna, nikam kar ki karyani,, allah ya amsa addu'ata wlh, amma yaushe kuka fara soyayya bai wani dade ba, kafin dai muxo minna, amma inna tasani, bata sani ba, to wlh sai nafada don allah rufamin asiri kar kifa, allah sai nafadawa mami, tafita da gudu taje palon. tana mami mami baraka ma tabiyo ta aguje, duk suna zaune harda yayan nata da abba tafado kan mami tana haki, lafiya mama shima yayan da abba suna lfy sai ga baraka. mama ta tuntsire da dariya, baraka tace abba mami duk abunda mama zata ce muku karya ne, wlh abba gaskiya ne to fada muji shiko abdulrahmanyakosa yaji menene.
Mami kunyi siriki fa ke don allah aina yake ina abdulrahman, hmm ingaya maka yaya baraka tayi wani saurayi hadadde ga kyau kuma tana matukar sonshi, dakyar yake hada miyau yace aina yake , dan nan minnan ne, yazaro ido baraka kuma takara duban mama dake son hada mata bom agaban abdulrahma, taciga ba dacewa yauma yace zai zo ayi magana zai turo abdulrahman yace what yakalli baraka wanda idonshi ya canja kama, wlh karya takeyi dama kina dawani saurayin shine baki fada min ba zaki yaudareni, wlh karya take min. mama ko sai dariya takeyi tana durkusa kasa.
Mami da abba sunkasa fahimtar abunda ke faruwa, mama tace abba mami kaga asirinsu yatono ko yaya abdul ne saurayin baraka nikuma nashirya haka don inga ya yaya zai yi mami tayi dariya amma allah ya shiryeki baby, yayana yanxu nagane kana son baraka ya harareta, abba yace ashe yar gida za'ayi, ai da tuntuni kafada mana, amma kuna soyayya bayan idon mu to zansanar da uban dawaki. yauwa abba hakan za ayi ta.
Gobe zamuje kusuyo jaka, jirgin ku zai tashi karfe biyar sai kushirya komai naku, to abba, to kutashi mutafi , mami tayi musu siyayyan komai. abba yasa abokinshi dake can india yagama musu komai na makarantar, har dakuna anka ma musu, tare da siya mosu mota daya.
Ana gobe za sutafi suka kara zuwa fanta gori yin sallama, haka ubandawaki yakara jankunnen su akan karatu, har gurin inna ma sun mata sallama tama tayi musu nasiha, sunkama hanya za su koma taga aliyu. mama ina son magana dake lafiya kuwa don sauri nake, mama wallahi ina sonki haryanzu ki amin ce min, kaga yaya ali don girman allah kayi hakuri karatu zantafi, ko ina zaki zanjiraki, bazan tabayin aure ba har sai naga kinyi. hmm ashe zaka mutu bakayi aure ba in har sai kajirani, kaga saduwar alkhairi ana jirana, tawuce yabita da kallo harda hawaye.
mami da abba da abdulrahman sunkawo su airport don hawa jirgi, mami ta tuna lokacin da suka rako Ahmad tafara hawaye ta rungume yan matan ta, mehaka kuma kinaso kisa su kuka ne alhaji kamanta hakama muka rako Ahmad dagabaya kuma muka rasashi, shima jikinshi yayi sanyi. mama da baraka sai kuka mami zamuyi missing dinki keda abba kuyi hakuri zamu dunga ziyaranku fatanmu kuyi karatu sosai insha allahu zamuyi, baraka taje sukayi sallama da masoyinta shima yana kwalla to baraka allah ya bada sa'a kuma arikemin amanata insha allahu yaya abdul zanyi, pls kisawa mama ido tom aka kira sunan su, sukawuce jirgi suna daga masu hannu, wajan zaman su daya, sun zauna sai taga wani mutum kamar tasanshi shima kallonta yake, ashe doctor adnan ne, yaxo wajan kamar nasan ki nima kamar nasanka, ๐๐ปNI'IMAH ko, kai kuma ๐๐ป DOCTOR ADNAN ko sai ga hawaye.
TAKU UMMU RUMAN( NUSNIM) KUBIYONI AGABA
HATUMSE PYARI HAI ALL MY FRNDS๐บ๐
[10:49AM, 1/24/2017] โช+234 806 448 1931โฌ: ๐๐๐LABARIN NI'IMA๐๐๐1โฃ7โฃ
Baraka tace kedai daga haduwa da mutum sai ki fara kuka, kin sanshi ne Eh abokin Ahmad ne tare suke aiki ayya sannu fa, yace Ni'ima ya hakuri mungodewa allah yakaji dajiki? jiki
alhamdulillah, naso zuwa gidan ku don inmiki gaisuwa amma ban samu zuwa ba, sai gidansu ahmad dana musu gaisuwa.
Ina zakuje haka tace karatu zamuje a india wani course kenan madicine, muke son karanta woow kice zaki gaje abokina kizama doctor, allah yataima, nima can zani don yin wani harkoki, ok! jirginsu yatashi lfy kuma sun isa INDIA MY BEST CONTRY, ( arjuhai pata hai mera dil hai) suna sauka taji wani sanyi azuciyarta, allah mungode maka da ka kawo mo lfy. tana sauko da kafarta daga jirgin taji wani iska ya hurata tare da wani kamshin turare mai dadi. tayi shiru da alamun tana tunanin wani abune, bayan sun sako sai ga medaukan su awajan yana jiransu, doctor adnan yayi musu sallama tare dafadin zamu hadu don ya karba numbern wayen ta.
Yace sannunku da isowa yauwa, kushiga muje to, bayan sunshiga sunata ta kallon garin mai kyau haddde kuma ya tsaru, suna ta tambayanshi nan inane yana fada masu. yakai su masaukin su yace gobe zai zo don su shiga makarantar, badamuwa mungode.
Dakin nasu ya hadu, kuma ma agyare yake da alama baifi jiya aka sake dakin ba, baraka tace kanshin turare mai dadi nakeji,, Ni'ima ma haka tace kamar nataba jin wannan kamshin, da alamu kamshin turaren wanda yabar dakin ne, suka shiga gaggyara kayansu cikin wadrop, suka kara gyara dakin bayan kowa yayi wanka suka shiga kicin suka hada tea da indomie, suna ci suna hira tare da murnan ganin su a india, baraka tace cikin zolaya ko zaki nemi mutumin ki SHARUKHAN, ta harare ta, gobe fa xamu fara zuwa school allah yabamu ikon cika ma iyayen mu alkhawari ameen amma fa nayi missing din gida, tun ba akwana ba har kinyi missing din su mama.
Ni kam mama mutumin da yayi miki magana a jirgi kice abokin ahmad ne, Eh abokinshi ne, tare suke aiki kuma tare sukayi hatsaren nan amma shidai rauni yasamu sosai,, nima kwanciyata asibiti lokacin da aka kaini daga makaranta nasanshi. ayya ashe shima likita ne, bayan sungama hira suka kira gida suka ce sun iyasa lfy kowa yaji dadin hakan,washegarin ranar monday suka shirya cikin kaya kanana amma suka daura after dress akai dai dai nan sunfito sai ga mutumin daya kawo su yaxo daukan su, suka gaisa har kunshir yane eh to muje, sun isa jami'an gaban Ni'ima yafadi sai taji wannan kamshin turaran ya buso hancinta alamu mutum ne yawuce ta bayanta, tajuya kuma bataga kowa ba, sundoshi inda zasu karbi komai nasu sannan yanuna musu depertment dinsu, yace anjima zan kawo muku motarku sai innu na muku hanya, yadda zaku iya zuwa da kanku, to mungode.
Sun shiga class dinsu sukayi introducing din kansu kuma sun samu karbowa, amma sai kallon mama suke kamar dama yar indian ce, dabadan tafada musu daga inda take ba da sai suce itama yar indian ne, sun sami waje suka zauna. sai sukaji an musu sallama, suka amsa wata kyakkyawan mace suka gani, tana musu murmushi, sai tafara magana da hausa ni sunana rumana, asalinmu yan nigeria ne aikine yakawo babana india, nagankune kun min shine nace inba damuwa inaso muzama friends, ba komai nice to meet u rumana, sukayi dariya amma ku yaya da kanwane ko baraka tace Eh nice yaya ita ce kanwa, sai rumana tace amma kuma tafiki kyauba, daba don nasan kasarmu daya ba da sai ince Ni'ima yar india ce, kai rumana har da zolaya haka, suna ta hirarsu. rumana tana matukar son Ni'ima haka kawai taji tashigar matarai.suna cikin hira sai ga lectura din su yashigo ya ijye pepper kowa tazo tasa sunanta da sing, mama tasa mrs Ahmad da wannan sunan zatayi amfani. bayan sun dau lecture sun fito don tafiya gida, ni'ima takara jin wannan kamshin kuma tarasa ta ina yake fitowa, sai gawanda yakawo su yazo tare da motar su, sukayiwa rumana sallama, tace ita zataje tasami yayanta a asibitin can suwuce ne ok badamuwa, suka daga mata hannu suka wuce. baraka tace kai wannan rumana akwai surutu kuma daga ganinta yar gidan masu kudine kuma yarinyace ma, nikam bata min ba wlh" mama tayi dariya ko, nikam tayi min.
TAKU UMMU RUMAN( NUSNIM) acce huwa koyi huwa ๐บ๐
[10:49AM, 1/24/2017] โช+234 806 448 1931โฌ: ๐๐๐LABARIN NI'IMAH๐๐๐1โฃ8โฃ
Ai sai tayi tamiki, suka shige mota abinsu yanuna musu wajaje da dama kuma harkasuwa sukaje, sukayi siyayya, sun fito daga kasuwar kenan dai dai wajan da suka ijye motar su, suka ga wata mota hadaddiya yayi musu kyau, baraka tacewa mama irin wannan mota haka ai sai wane da wane, kuma ma in anbibiya mai motar ha dadde ne, uhmm kyaji dashi, in hadaddene ina ruwanki kozaki ce kina son sane nikam dai baza ataba bawa yayana kishiya ba, atoh garama kiji inba haka ba infada mashi. eyye sannu mai yaya.
kika sani ko shima yana can da wata daban, ina yayana bazai tabayin hakaba sbd yana matukar sonki, allah ko suna ta surutu har mai motan yazo yaja motarshi tare da barmusu kamshin wannan dai turaren, da mama takeji sai da suka lumshe ido tare. tafiyar motan suka gani kawai, sun so suga waye acikin motan.
Kingani ai halama yaji maganar da muke gashi yawuce bamu ganshiba sai kamshi turaren dana ji adakin da muka kama farkon da zamu shiga. mama tace ashe kingane tunda nazo india nake jin wannan kamshin, har amakaranta ma, amma kuma abun mamaki ina tunanin nataba jin wannan kamshin acan gida nigeria amma narasa nawaye ne. kajiki da shirme mama dan allah muje nikam nagaji suka wuce gida bayan sun sauke wanda ya kawo su, yanxu dakan su zasu dinga zuwa, sbd sungane hanya.
Akwana atashi bawuya yau watan su mama biyu a india, kuma karatun su yana tafiya daidai yadda ya kamata har sunyi farkon test dinsu kuma suncinye, don sunfi kowa marks sbd suna da kokari sosai har ana mamaki. rumana tana yabawa da irin kokarinsu wanda ita bata kaisu ba, sai kara mannewa su Ni'ima take wanda hakan bayawa baraka dadi, wai ke baraka me rumana ta tsare miki ne wlh haka kawai bana sonta gashi tacika shegen shagwabar tsiya,, to ina ruwanki.
Yau sun shigo makaranta da wuri don sun riga rumana da ita take rigasu sbd yayanta inzaizo asibiti dawuri yake zuwa, suna tsaye jikin motar su sai ga wannan motar da suka gani akasuwa tazo tayi parking nisa dasu, baraka ta bude baki ta tabo mama kinga abunda nagani sosai ma kuwa wannan motar ne yau zamuga waye zai fito daga motan.
suna ko shikin magana sai suka ga kafar mace tazoro amma basu ga gangan jikin ba da alamu ba ita kadai bace amota, tana magana da wani ne, bayan tagama sai tafito ta rufe motar, tana daga mai hannu yaja motar ya karasa, sai tajuyo sukayi ido hudu dasu mama. tayi musu murmushi takarasa inda suke, suko duk suna cikin mamakine bare ma, mama taji wani abu ya tsoketa azuciya tashiga cikin wani tunani, sai da rumana ta tabata lfy mama tunanin me kikeyi haka.
Baraka da bakinta ba ya iya shuru, tace rumana da ma wancan motar kuce, tace Eh motar mijina nane tazaro ido dama kina da miji,