An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya
Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,
Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490
A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,
Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu
Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC
Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku
This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng
You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services
Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us
Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it
Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng
For feedback and support
Facebook : https://facebook.com/taskarnovels
Twitter : https://twitter.com/taskarnovels
Telegram : https://t.me/taskarnovels
[10:48AM, 1/24/2017] βͺ+234 806 448 1931β¬: [15:41, 1/21/2016] nusnim: πππLABARIN NI'IMAHπππ1β£
sarautar uban dawaki, babbar sarautace a garinfanta gori can cikin jihar neja. Babban gari ne wanda al'ummar cikin sa sukabunkasa wajen noma dakiwo.Gidan uban dawaki, alhaji uwaisu malami ubandawaki, katafaren gida ne cike da zuri'a masu yawa, na kannen sa guda biyu, kuma shine babbab su kat!
Sassan sa yafi kowane sasa girma da tsari ginin zamani ne. matar sa daya Hajiya Halima da ya'ya maza uku a jere. Abdul-kadeer, Abdul-kareem da Abdul- rahman. sai autar su ya mace tilo a cikin su. Ni'ima sunan mahaifiyar uban dawaki gare ta, shi yasa suke kiranta (mama).
Sataleliyar yarinya wacce allah yayi wa sura tamkar ita tayikanta, kusan zuri'ar gidan haka suke da kyau na fulani . amma ita mama ta fita dabam wajen cikar sura , daka ganta , dole gaban ka ya fadi , saboda tsabar kyau.
Shiyasa tun shekarunta ba su kai ko'ina ba samari suka yanyame ta, kowa na so, musamman cikin gidan su, watau yan'uwanta, abin har yana so ya zama rigima a tsakaninsu.
Sai da uban dawaki da kansa ya tara su ya tsoke zancen soyayya da mama ya kuma ce kar wanda ya sake kiranta da sunan tadi. yayi haka ne don a sami maslaha da zaman lfy. Allah ya taimaka kowa ya gama bacin ransa ya hakura.
Baya ga haka yana ganin Ni'ima bata kai shekarun da za ta tsoma kanta kogin soyayya ba. Alhalin tana tsaka da karatun ta, mafarin kenan da za ta tafi babbar scondry. yayi kokari ya samar mata makarantar kwana ta yan mata da ke bakori watau (F.G.G.C BAKORI).
sannan hankalin sa ya kwanta, amma wannan hukunci nasa yayi wa wasu daga cikin iyaye mata ciwo har suna ganin saboda kyan da mama ks dashi ne, yasa iyayen ta suke wulakanta ya'ya'yen su. suka rika ganin kamar suna son su dauki dogon buri ne su dora mata.
Tabbas uban dawaki na da buri akan yar sa tilo, diyar sa mace , sai dai yasha bamban da irin burin da matan gida ke nufi cikin zukatan su. wanda bazai wuce ya aurar da ita ga hamshakin mai kudi ko basarake.
Shi buri sa yar sa tayi zurfin karatu kamar sauran yayyinta maza wadanda a halin yanxu Abdul-kadeer major ne na soja, Abdul-kareem accounter ne a babbar bankin Najeria da ke minna, watau CBN. sai Abdul-rahman dake bautar kasa a jalingo . ya kuwa lashi takobin ko bashi da rai yan-uwanta su cika masa wannan burin nasa.
TAKU UMMU RUMAN WATO (NUSNIM)πΊπ
[15:41, 1/21/2016] nusnim: πππLABARIN NI'IMAHπππ4β£
Bako? a ina? tace,, oho wai nan gidan alhaji lado ku ke cewa? Eh, wai nan ne gidan kakarsa. Ahmad yace min sunan sa. Bakinta har kunne ta jawo hannunta suka tafa, ban mukashe yar uwa bakar fata. kice kinyi gamo da katar. Likita bokan turai.
Ta ware ido kina nufin Doctor ne? kwarai kuwa, ko bai kammala ba kiris ya rage, don tuntuni naji ana fadin sabis yake yi. Ta kama baki, har kin kara min son shi, ina ma ace wannan abu ya tabbata, kusha bikin likitoci, au ke ma likita ce?
Tace zauna nan. ina gaya miki jiya jiya abba ya gaya min abinda zan karanta kenan, kuma gaskiya yayi min, matsalar kawai abba. A'a ina cewa ya soke maganar su yaya ali?
Eh mana, to ai baki sani ba, tsoke wannan maganan ita zata jawo min tsiyar, kina zaton su kawu ba zasuji haushi ba, an ce karatu zanyi, amma wani yazo anbarshi, ai sai umma tayi bakin jini a cikin gida. Bansan yadda zanyi ba. shi kansa ya ban tausayi, duk ya damu. Tahowa ta kawai nayi na kyale shi, kinsanni da karfin hali.
Baraka ta bata rai, kai ya kamata anema mafita, Ahmad yayi kawata zanso ki dashi, don na hango kundace kawai, ta sata ta, ta zabga ta gumi ta zubo mata ido, Ina tsoron abba baraka,.ba zan iya dunfarar sa da wannan magana ba, bayan jiyannan ya jamin kunne, ya gaya min burin sa a kai na,, ina zansa raina, nima ina son Ahmad.
Ta dafe goshi, ga koshi ga kwanan yunwa, baraka tayi tunanin ta, ta rasa mafita, saboda tsoron hanyar da za'abi a donfara uban dawaki, don haka ta nunfasa, tace to ai shikenan , sai ku dauki hakuri, idan kuma zai iya jira, yana iya dakatawa bayan fage ya jiraki ko kuwa? tace kyale ni, haushi ya isheni. dauko wani topic din, ko na manta da wannan.
Tayi yar dariya to ya school? mu koma wancan fannin dame dame suka faru? ta gyara zama suka tsinke da hirar makaranta, daga abinci sai sallah har zuwa bayan la'asar, lokacin da mama ke niyyar tafiya, da zarar ta idar da sallah.
Ta sallamewa yaro ya shigo wai ana kiranta ta leko tace,, je ka ce ta tafi, Inna ta leko, tace uwaki, baki zuwa kiga kowa nene, kai kace gatanan zuwa,, yaro ya fice, yayin da inna taciga ba da fada,, babu kyau wulakanci ko baki son sa, ki saurare shi, kibashi hakuri sai a zauna lfy ta shiga daki, Inna kenan bazaki gane ba.
Ta maida ( after dress) dinta, tasa maya fi tace da baraka, zo ki rakani. don allah ki tafi ke kadai, kinsan sirrin da zakuyi? ta ja tsaki ta fito, yana tsaye kofar gdan, haba gimbiya kuma sai ki wuce ki barni da tension. ina kike so insa raina yau? wlh ko abinci nakasa ci saboda tunanin matsalar da kika ambato.
Tayi masa zuru, tausayin sane zalla yake bin jinin jikinta, yana kashe mata gabobin, ta numfasa ta ce, kasan allah nima ina tunani na ya kare na rasa me zance wa abba, ganin yan"uwana na ma jini ya dakatar dasu balle wani. kuma watakila kana bukatar auren ne da wuri, kaga abba ba zai amince ba.
TOFA YAU AKEYINTA TUN BA'A FARA SOYAYYA BAMA,,, WANNAN INA GA ANFARA,,, SHIN ABBA ZAI YARDA,, KO KUMA YAN UWANTA SU ALI TUNDA SUN RIGA SONTA,,, DA ALAMU AKWAI RIGIMA KUBIYONI AGABA DON MUJI
TAKU UMMU RUMAN (NUSNIM) mujse aphaki yadaati apti haiπΊπ
[15:41, 1/21/2016] nusnim: πππLABARIN NI'IMAHπππ2β£
Kwance tashi mama tashiga aji biyu na babbar secondry kuma yau suka yi hutun zango karatu na biyu, watau ( second term) tun safe uban dawaki ya tura direban sa ya je daukar ta.
Basu iso fantagori ba sai bayan sallar la'asar kowa na ta murna, musamman yara da suka fito suka yanyame ta tare da kwashe mata kaya zuwa sasan su. ta shigo da sallama. umman ta ta tarbe ta suka rungume juna. ta shiga sauran sasan ta gaishesu . salis da dan lami kadai ta samu a cikin samarin sasan.
Ta zauna suka taba hirar makaranta, sannan ta tashi ta koma sasan su. tana shiga umman ta tace, abban ki na nan ya dawo . ta wuce da sauri ta same shi a falon sa, bakin ta har kunne ta dan rankafa ta ce, Allah ya taimaki mai martaba!.
Fara'arsa ta karu, allah ya barmin mama ba, nashigo aka ce kina cikin sasa. Ta zube gaban sa tace ,Eh naje gaishe su ne, ina yini Abba? Lafiya lau, ya karatu? "To mun gode allah. ya ce ina ( Report sheet) a kawo in gani. tamike taje ta kwaso masa har da takardun jarabawa, yayi ta dubawa yana fadin da kyau.
Bayan ya kammala, ya dube ta, kin yi kokari sosai mama na, na yaba miki amma har yanxu kina da yar matsala kadan a Biology, sai kin kara bada himma. kin san dalili? Ta kada kai yace kara matsowa kiji. ta matso shi sosai kafin.
yace, Buri na kizama Likita mamana, saboda a rayuwa ta ina sha'awar in ga ya mace Likita, abin yana burge ni kwarai da gaske. shiyasa tun ranar da Allah ya bani ke, nake ta addu'ar allah ya raya min ke in samu in cika burina. ko kuwa ke ba kya sha'awar?
Tace, sosai nake son zama Likita Abba, kuma insha allahu zankara himma don ganin na gama da Biology. ya dafa kan ta cike da farin ciki yace, yauwa ni'imatah, to allah yayi miki albarka. Amin abba, Daga nan suka ci gaba da hirar su sai da akayi sallama da shi, ya tashi ya fita babban zaure inda majalisar sa ke taruwa.
Mama ta koma wajen umman ta a kicin suna aikin abinci, tana bata labarin abinda abbanta yace. umma tace yallabai kenan allah dai ya cika masa wannan buri na sa. Tace Insha allahu umma sai nazama. Tace allah ya yarda, wai wa ya gane min mama da fararen kayan nan? tana dariya tace na dan ratayo abin nan da suke sawa a kunne ina takawa ana ga Doctor Ni'ima nan zuwa.
suka fashe da dariya. washe gari misalin goma dai dai, mama ta fesa ado da koriyar atamfa, sannan ta dora( after dress) ta yafa maya finta ta sami ummu a daki, sai ina? tace zani gaida inna mairo ne, A'a, kice dai zaki gun Baraka .
Tayi dan murmushi, umma ai duk daya ne, idan na gaida innata, sai muyi hira da kawa ta. Tace" Uhm.... To ko dai lauya xaki zam ne, afasa likitan nan ? Tayi dariya " wai kina so ki hada ni da Abba kenan Lallai kam. To kice ina gaida mairon , idan ta gama dinku nan tabaki, kizo min da su. shikenan Amma ina fatan da akwai nawa aciki?
Tace babu naki, duk nawa ne. ta dan kime fuska, kai umma! ai kuwa zan xabi daya aciki, duk zannuwan ciki da alakun ne, rigunan kuma masu hannu. na canxa style, ni ina so haka nan. to ban bayar ba, ki amso min kaya na kawai, idan ta gama. ta jinjina kai , shi kenan umma ni na tafi tace, A dawo lfy, kar ki dai ki dade. ta saba jakarta tana fadin to.
salis na zaune kofar gida tana fitowa ya kare mata kallo sama da kasa kafin yace, sai ina kuma ? gidan inna mairo zani , Ok na kuwa ga baraka jiya itama ta dawo. ya mike, muje in rakaki, ko baki so? muje mana. ta wuce ya biyo ta suka jera.
Wai mama meyasa abba yake takuraki dayawa? kamar yaya ? baya son kina samari. kin kuwa san har yanxu yaya ali na sonki? ta dube shi, Farin sani kuwa, tunda yana gaya min asace. amma fitinar duk waya fara dauko ta?
ya ce A;' a, ba don wai muna uwa daya uba daya da shi ba, abinda yaya umar yayi ai bai kyauta ba. tunda ya san shi yana sonki, menene nashi na shigowa neman ki ? yafa san halin yaya ali, ba hakuri bane dashi ba, yan zunnan sai ya nuna maka hauka. ta dan tabe baki.
Tace Hmm... kai ni fa karatu ma zanyi, damasun sa ran su a inuwa. Babu wanda zan aura cikin su . koda abba bai dakatar da su ba . ya zura mata ido kina kina wulakanci mama, kice dama ke ma ba son su ki keyi ba?
Ba ka gane ba , me ki keso ki fadi ? karatu zai hana ki aure? ta kada kai, natsuwa nafi bukata, saboda karatuna mai son natsuwa ne, mezaki karanta? aikin Likita. ya ware ido, Uhm... Doctor Ni'ima kenan!
Tayi murmushi, har kasa naji gingirin! yayi dariya daidai lokacin da suke tsayawa gefen titi. to Doctor Ni'ima, ni anan zan juya, na gode, ai kaga har nayi sauri da yake ana hira. yace dadin abokin rayuwa kenan , don ma ba yays ali bane. tayi dan tsaki, Get lost don allah, ka rabani da wannan zancen, yana dariya, ta tsallaka titi ta mike hanya, shi kuma ya juya ya koma gida.
mota yake kakkabewa, ya cire shimfidar kasa inda ake ajye kafafuwa lokacin da mama taxo wucewa yayi tsaye yana kallon wata surar da bai taba gamo da irinta ba. kai ya kasa daurewa, sai da yayi mata sallama.
TO KUBIYONI AGABA MUJI SHIN WANENE WANNAN YA YIWA NI'IMAH ( MAMA) MAGANA
taku ummu ruman (nusnim)πΊπ
[15:41, 1/21/2016] nusnim: πππLABARIN NI'IMAπππ3β£
Ta dago ido ta kalleshi tare da amsawa , sautin muryarta yaka rikitashi. ya bita da sauri, dan allah ko za kiban minti biyu kacal in tambayeki ? ta tsaya cak, tana duban sa, dogone sosai Allah yasa nasani.
Yace don allah agarinnan kike ? tambayar tasa ta mamaki tace eh mana. amma bantaba ganin ki ba, sai yau. tace kasan daurowa takeyi. gaskiya ne, ah sunana Ahmad , ina minna amma nan gidan kaka ta ne. na kawo mamana ne ma yanxu, sau dayawa ina zuwa nan, shi yasaki kaji natambaye ki.
Hakane yau ne Allah ya nufa zamu hadu. ya sauke numfashi, gsky ne. Allah ya hada mu, kuma take nan kin kwanta min arai, ko zan san sunanki? ta dan kauda kai, yana ji jim yan mata, sai da gabansa ya fadi, tsoro ya kama shi kar ya sha kaya.
Ya marairai ce, dan daure ki gaya min, ba don halina ba." Hali? Nasan halinka ne? Yace na mita da bakin naci. tayi murmushi, sunana Ni'imah. kai! sunan nan ya dace da wannan kyakkyawar sura. anan unguwan kike? ta dan kada kai, can gidan zani wajan kanwar umma na. Ok, ti gidanku fa.
Ta yatsuna fuska, alamun ta kosa ta wuce, har tafara takawa, ya biyota na dame ki ko? yi hakuri, so ne ya kama ni, ki taimake ni. Ta tsaya ta dubeshi da fararan idanuwanta kal!, Da su tace , kasan uban dawaki? yace can tsallaken titi kena. ni yar sa ce, idan kasan gidan, nan gidan mu. sai.dai akwai matsala.
Ya hadiye murmushin sa matsala? na shiga uku, A ina matsalar take? tace abba na baya bari ana zuwa waje na, yace sai na gama karatu. Hasalima bording na keyi, daga hutu sai sai hutu ake ganina. ya danyi shiru jim, kafin yace, To ya za ayi yanxu Ni'ima?
Gaskiya bada wasa nakeyi ba yaya za ayi? Tace Ban sani ba, amma ina ganin hakuri zaifi kyau, mu saurari lokacin kammala karatuna. ba kai kadai bane, akwai, wadanda suka rigaka magana kuma sun hakura.
Ya ce sun ga zasu iya ne,nikam bazan iyaba Ni'ima, ina sonki sosai. babu abinda nake rayawa cikin raina. face na aure ki. Ta dan kara duban sa, sosai yafara zama cikin ranta. Matsalar kawai bata san yadda zatayi da shi bane, har tace yaje gidansu.
Don haka tace dashi kayi hakuri ahmad. ta wuce da sauri ta barshi yana kira, Ni'ima! dan tsaya mana kiji, Gidaje biyu ta wuce na ukun shine na inna mairo. ta sa kai cikitare da sallama. Baraka dake tsaye sakar gidan tana gyara zaman mayafinta, ta juya da sauri baki sake.
Suka nufu juna suka rungume, gidan ku zantafi yanxu, ah haba? wallahi yanzun nan nake wa inna sallama har ta ban din kin umma, kin gansu. tace nayarda,, don nima ta aikoni zancen dinkin, ina innar? tana ciki suka shige tare. innar na uwar daka har can suka bita. au mama ce? kin rigata kenan. tana dariya ta zauna kusa da ita, sannu inna ina kwana?
Ta amsa lafya lau. andawo lfy? wallahi kalau inna. kinga dinkinta dama za'aje kai mata, ashe kina tafe, ta kuwa ce in tambayeki inkingama. Tace gasu nan na gama, na huta, ta fiddo su a ledar ta daddaga, kai atamfofin masu kyau. umma tasa anbata su Inna tace anbata?
Duba fa Inna wai wani ciki da alakun.tace uwar take yarinyace? suka fashe da dariya, zu mugudu kawa ta. Inna kibar su anan, idan zan wuce na dauka, tace sunanan suna jiranki. Baraka ta kamo ta suka wuce dakinta, kowacce ta yada mayafi da jaka.mama har da (after dress )din ta cire.
Tafada bisa katifa tace, tun da zu ya kamata in shigo gidan nan, bakon unguwar ku ya tare ni.
TAKU UMMU RUMAN( NUSNIM)PHYAR HAI ZINDAGI HAIπΊπ
[15:41, 1/21/2016] nusnim: πππLABARIN NI'IMAπππ6β£
Yace allah yasa goggo. suka baro zauran, hajiya nafadin kaifa nake jira kar ka shanya ni. ga ninan mama. mama tace allah ta kiyaye hanya ta amsa da ameen.
Ya gyara tsayuwa yace kin gani? kin gani bani kadai ke sonki ba Ni'im. saboda haka ki saurare ni. tace ina nan ina sauraron ka. alkah ya tabbatar mana da alkhairi. ameen gimbiyata, to bari mu lallaba. allah ya tsare, amma zakayi min alkhawari? me zai hana? fadeshi in dai bazaki cemin nadaina zuwa gunki bane.
Tayi yar dariya, bashi bane. kayimin alkhawarin zakaci abinci, idon son samune ma mama ta dan jiraka kaci ko yayane, kai likita ne ka san matsalar rashin cin abinci. Ya ware ido sosai yace waya gaya miki ni likita ne? tayu nuni cikin gida, yar'uwata dake nan gidan.
Yayi jim murmushi kawai yake fiddawa kafin yace is true, watanni shida dasuka wuce aka damka min takardar daukar aiku a ( A.B.U.T.H Zaria) ina fatan kina son likita? Da gefen ido ta dube shi, shi yasa shima ya tsira mata idonsa. domin kallon yayi masa ba jadan ba, ko shi kasai ya isa amsar tambayar sa, in banda son jin baki ba, bata gama dalilin wannan tambayar ba, don haka ra juya zata shige gida, Ni'ima.
Ya kirata a sanyaye. ta waigo dauke da murmushi tace a sauka lfy, Allah ya tsare. ta karasa cikin gida, domin ta lura idan ba hakan tayi ba. Ahmad ba zai tafi ba alhalin jiran sa akeyi, gabaki daya kasala ta saukar masa, ya sauke numfashi , yana ta damuwansa , bisa kofar zauran yake, ya jima tsaye, sannan yafito ya tafu mota inda mahaifiyar sa ke zaman jira.
A hakikanin gasky Ahmad ya kamu da wata sabuwar cuta wacce shi kansa a matsayin sa na likita bai taba cin karo da maganinta ba duk iya karatunsa da yayu, sosai yake ji acikin ransa idan bai auri mama ba. babu nakawa zai fuskanci matsala. shi yasa tunda ya damki hanya, baya iya magana illa addu'a allha yasa Ni'ima matarsa ce.
Haka kazalika wajen mama, tas! Ahmad ke neman rusa shirinta nason zurfin karatu, kamar yadda tayi wa abban ta alkgawari. a halin yanzu kam shirun da tayi bisa shimfidar, tun shigowan ta gidan, tunani auran Ahmad takeyi kuma da son samu ne, kar aja lokaci mai tsawo, anya abbanta zai yarda?
A dakin Inna ta sameta suna sallam, hannu ta daya rike da ledar kayan dinkin umman ta, ki gaida min ita sosai, sai nazo m. tace zataji inasha allahu, ta juya suka fito tarevda baraka.
Sawun tayoyin motar sa ta tsaya tana kallo, tsawon lokaci kafin ta dubi baraka,Ahmad ya wuce, ban jin