fahimta cikin sauri Jummo tace.
" Baki fahimce ni ba Aunty Zarah, meye laifina dan Momy tayi kuskure zan gyara mata.?"
" Karya kike Jummo babu gyara a cikin lamarin ki, sai tsantsar munafurci idan ba munafurci ba, meyasa zaki sanar da Mamma Momy taje wajen boka, haka ake gyara, idan gyara zakiyi, kamata yayi ki nunawa Momy kinsan abinda take, ki nuna mata ta gyara cikin masalaha, ba wai ki kwashi magana gulma da munafurci ki kaiwa Mamma ba, wannan haɗa faɗa ne da ƙara rura wutar ƙiyayya a tsakanin su."
" Aunty Zarah wallahi ba nuf................"
" Karki cemin komai na riga na gama fahimtar waye ke, rogo nake yiwa kallon kitse........................."
*Wannan littafin na kuɗi ne akan farashi mai sauƙi Naira 100 kacal zaki biya ta wannan account numbern 0006064512 Rashida Usman jaiz Bank ko ki turo hoton Mtn card na 100 ta wannan numbern 08147537180 sannan ki turo shaidar biya.*
*Kuyi haƙuri dan Allah yau kun sami readmore kadan abubuwa suka min yawa, amma dai hausawa sunce da babu gara ba daɗi, kuyi manage*
*UMMU NASMAH CE*
[4/15, 9:20 PM] UMMU NASMAH❤️: 🧺🧺🧺🧺
*GELLE ƁINGEL*
🏺🏺🏺🏺
*Story*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah)*
*Littattafan marubuciya*
Sauyin Rayuwa
Nasmah Ko Nasirah
Sara Da Sassaqa
Indo A Birni
So Bai San Jini Ba
Akan ƴar uwata.
Hatsabibiya Saude
Ruɗanin Zuciya Biyu.
Doctor Hassan.
Ƙauyenmu.
And now *GELLE ƁINGEL*
*SADAUKARWA*
Na sadaukar da wannan littafin daga farkonsa har ƙarshen sa ga ƙawata *ZARAH ABDUL MOMYN AHLAN* sonso nake fisabilillah.
*_________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_________________________________*
*FREE PAGE*
➰➰ *27 to 28*
" Hmmm!!! A iya sanina gyara bai taɓa zama munafurci ba, na sanar da Mamma gaskiya ne domin tasan yanda zata kare kanta daga sharrin Momy, wai ma na tambayeki Aunty Zarah, wani daɗi Momy ta miki da har zaki shiga gabanta ki kareta, ki tsaya a gaban karya domin karya gwiwwar mai gaskiya yin hakan kuskure ne, kuma wallahi Aunty Zarah bazan taɓa sauyawa daga ƙudiri na ba, muddun ina tare da Mamma bazan taɓa bari burin Momy ya cika a kanta ba."
" Ai dama bazaki bari ba, Saboda kina da mungun niyyar raba uwa da ƴaƴanta miji kuma da mata, to niyyar bazai taɓa cika akan Momy ba, muddun nima ina cikin gidan nan, domin kuwa baki fini iya wayo ba, daga ƙauye kika fito ni kuma a cikin birnin kika shigo kika sameni dan haka dole na fiki waye wa, zan kare Momy kota halin yaya mugun nufinki bazaiyi tasiri a kanta ba."
Murmushi mai sauti Jummo tayi tare da matsowa gaban Zarah tace.
" Ina ta baki mutuncin ki amma naga alamar bakya son mutuncin da nake baki, kin min hallaci bazan so ɓata miki ba, shiyasa bana son kisan waye Jummo, ki tambayi A'illo labari na a ƙauye ba'a taɓa Nasara a kaina duk abinda na saka a gabana sai na cimma nasara, amm Aunty Zarah tabbas daga ƙauye na fito, amma zan nuna miki wayon ɗan ƙauye yafi na ɗan Birni mu buga wasan ƙarshen wasan shi zai bayyana mai Nasara, fatan Nasara Aunty na."
Tayi Maganar tana murmushi tare da barin wajen ta nufi bedroom ɗinsu, Aunty Zarah dafe kanta tayi ta nemi waje ta zauna cike da tsantsar damuwa, bata taɓa zaton wayon Jummo ya kai haka ba, (duk da babu shiri tsakanina da Momy komai tsiya ai ta zamo uwata tunda ina Auren ɗanta ya zamo dole na kareta daga sharrin Mamma da Jummo, domin barin Momy cikin gidan nan yana nufin rugujewar farin cikin mijinta ita kuwa bazata jure ganin mijinta cikin damuwa ba, farin cikin sa shi take buƙata, zatayi wannan yaƙin ne domin farin cikin mijinta) numfashi ta sauƙe mai nauyi tare da miƙewa ta shige kitchen, itama Jummo bakin gado ta zauna tana ji a cikin ranta bata kyautawa Aunty Zarah ba da ta mayar mata Magana ko yayane Aunty Zarah ta nuna mata ƙauna da duk wata wayewa, "amma ya zamo dole ta kare mutuncin Mamma a da Soyayyar Garkuwa ne ya kawota gidan nan, sai dai a yanzu komai ya juye ta fuskanci matsalar Mamma da ciwo a raba uwa da ɗanta sai gashi Momy ta raba Mamma da ɗanta na tsawon shekaru, ta daɗe Mamma CIKIN ciwon rashin ɗanta a kusa da ita, sai yanzu ta samu damar zama kusa dashi ace za'a koreta sam bazan bari hakan ta faru ba, zan ajiye Soyayyar Garkuwa a gefe domin kare Mamma ta zauna da farin cikin ta Buba, ya zamo dole na zamo ƙalubalen Momy koda hakan yana nufin ƴaƴanta zasu tsaneni na rasa Soyayyar Garkuwa, na yadda na kare Mamma."
Bakinta ta cije tare da Kwanciya ta runtse idanunta, A'illo da kallo ta bita tare da saka hanunta cikin na Jummo tace.
" Mamma itace ta goyeni tun ƙaramar yarinya ta bani tarbiyya ta mantar dani maraicin iyayena komai tana min babu mugunta, ada ina jin zafin ki, sai kuma gashi a yanzu ina jin ƙaunar ki, kin san meyasa Saboda kin ɗauko hanyar dawowa Mamma na da farin cikin ta, sanda muke ƙauye a ko wani dare sai Mamma tayi kuka tana cewa, Buba ya gujeni baya zuwa wajena ɗansa kawai ki ziyartana sai dai ya min aike nakan fi shekara banga Buba, nafi buƙatar ganin Buba a kusa dani fiye da kuɗi da kayan abinci da yake aiko min A'illo matar Buba ta rabani dashi dama sunyi wannan alwashin ita da iyayenta cewa da zarar Buba ya tafi da Zainabu Birni bazan kuma ganinsa, kinga kuma maganar su ta tabbata tunda buba ya tafi binni bai kuma zuwa wajena ba sai aike kawai da yake min, sai yaushe zan zauna inuwa ɗaya da Buba sai yaushe A'illo" numfashi A'illo ta sauƙe tare da duban Jummo ta cigaba da cewa " Sai gashi ta sanadiyyar ki domin nemo miki Soyayyar ki Mamma tace mu taho Birni neman gidan Buban ta, ƙaddarar ki itace ta dawo da Mamma cikin gidan ɗanta, dan Allah Jummo karki bari Mamma ta koma ƙauye na tabbata idan Mamma ta koma ƙauye baƙin ciki ne zai kashe ta, shikenan ni kuma na rasa gatana na rasa me kula dani."
Miƙewa Jummo tayi ta zauna tare da ƙara danƙe hanun A'illo ta fara magana cike da rawar murya.
" Yanda ƙaddarata ta dawo da Mamma gidan ɗanta insha Allah haka ƙaddarata zata zaunar da Mamma gidan ɗanta har abada, insha Allah burika na zasu cika ina ji a jikina komai daren daɗewa zan mallaki yaya GARKUWA, sai dai nasan akwai tarin matsaloli a gabana, bani ƙarfi sai na Ubangiji ƙarfin hali kawai nake a wannan yaƙin, addu'a zaki tayani A'illo Allah ya bani Nasara a kansu, Allah yasa kar su suyi Nasara a kanmu, zanyi Magana da yaya khalil maybe shi zai fahimce ni."
Kanta A'illo ta girgiza tare da cewa.
"A'a Jummo karkiyi Magana da Yaya khalil domin kuwa baya son laifin Momy shi duk abinda tayi akan dai-dai take, gara ma yaya Garko shi mutum mai fidda gaskiya a duk sanda tazo koda akansa ko akan Momy ko Daddy baya tsoron ya faɗawa mutum gaskiya, gara shi kiyi Magana dashi akan yaya khalil."
" A'illo ni kuma bazan yi magana da Garkuwa ba, saboda a halin yanzu yana ɗaukata ne a matsayin jahila mahaukaciya wacce bata san abinda take yiba, a haka yake ɗaukata, dan haka bana buƙatar Magana dashi, shima KHALIL ɗin na barsa."
" Shikenan to Allah ya mana jagora."
Da ameen Jummo ta amsa tana maida kanta ta kwanta.
Momy kuwa tunda ta shiga bedroom ɗinta ƙirjinta ke suwa wani irin tsana da haushin Jummo take ji, tunda take a rayuwarta bata taɓa jin tsanar mutum bilhaƙƙi da gaske ba sai Jummo, wani irin mataki ya kamata ta ɗauka akan wannan agolar Yarinyar, ita wannan yarinyar take neman ta tonawa asiri, numfashi Momy ta sauƙe tare da furta.
" Hmmm!!! Lallai akwai Babban ƙalubale a gabana dole sai na fara kawo karshen Yarinyar a cikin gidan nan kafin na juyo kan Mamma wannan wani irin masifa ce, kai kaji yarinya da ƙwaƙkwafin tsiya wato ma turo ta Mamma take tamin laɓe, ai kuwa zanci ubanta zan nuna mata ruwa ba sa'an kwando bane, zan nuna mata na haife ta, bata isa nuna min wayo ba."
Zama tayi ta dafe kanta ta furta.
" Wannan wacce irin masifa ce take tunkaro Ni, dubu hamsin na bawa wannan malamin yamin wannan aikin sannan kuma ace nayi asaran kuɗina, ina Wallahi bazai yiwu ba!!! Dole ne sai Mamma taci wannan maganin" shuru tayi tana tunanin sai can zuciyarta ta ayyana mata mai zai hana tayi amfani da Zarah wajen kalallameta ta samu ta sakawa Mamma wannan maganin "taya zan fara" zuciyarta ce tace mata " ta hanyar nunawa Zarah kulawa da nuna mata cewa Mamma tana neman rayuwarta tun ba yau ba tabbas kika je mata cikin kuka dole zuciyarta zai karaya taji tausayinki ta baki haɗin kai, idan har kika samu nasarar jawo Zarah jikinki tabbas aikinki zaiyi kyau." Murmushi Momy ta saki tare da miƙewa tsaye tana cewa " tabbas haka zanyi" ta ƙarisa Maganar tana shigewa cikin tollet.
Jikinsa ta mirgino tana sakin murmushi tare da riƙo yatsar hanunsa ta saka a bakinta, lumshe idanunsa yayi yana jin wata nutsuwa na sauƙa masa a hankali ya furta.
" Sadiya kina da ni'ima tamkar Sweet haka kike zaƙinki yayi yawa, hmmm!!!"
Murmushi Sadiya tayi ta cire yatsar daga bakinta tace.
" Duk daɗi na ban kai kaba kai na musamman ne, shiyasa nake fatar na kasance mata a gareka, dan Allah ka aureni yaya Garkuwa, wallahi da kai kaɗai zan iya rayuwa kaine zabin zuciyata."
Gashin kanta ya shafa tare da cewa.
" Sadiya tun yaushe nake ce miki ki daina min zancen Aure, ban miki alƙawari ba Sadiya, amma shi Aure mukaddari ne, Allah shi kaɗai yasan matata, dan haka ki dage da addu'a idan Allah yasa kece fine."
Shuru Sadiya tayi tana duba agogo 6:30pm duban sa tayi tare da miƙewa daga jikinsa ta ma nufar tollet wankan tsarki tayi tare da fitowa ɗaure da towel kayanta ta mayar tana furta masa cewa.
" Lokacin komawa na gida yayi, ni zanje na hau adaidaita."
Da to ya amsa yana miƙewa shima, ya ciro 70k ya miƙa mata, hanu tasa ta karɓa tare da ɗaukar bag ɗin ta ta fice tana ce masa sai ya dawo, tollet ɗin shima ya shiga yayi wankan tsarkin tare da ɗauro alwala kayansa shima ya mayar tare da kwasar wayoyinsa da key ɗin motar sa, ko kaɗan bai lura da camera dake maƙale jikin window dake saitin su ba, ya fice, yana fita ma'aikacin ya shiga ya ɗauki camera tare da seving ɗin videon, ya fito yana sakin murmushi, Zee ya kira tare da faɗa mata aiki ya kammala zata iya shigowa ta karɓa, sannan ya katse wayar.
Wajen bakwai dai-dai Sadiya ta shigo gidan, babu kowa cikin falon zata haura sama taji muryar Aunty Zarah tana cewa.
" Sai yanzu kika ga damar dawowa, amma ba ce miki nayi 5 zaki dawo ba shine kika je kika kai har 7."
Juyowa Sadiya tayi tana murmushi tace.
" Oh Aunty na faɗa miki gidan su zarina naje, kasuwa na rakata shiyasa mukayi dare."
" Kyaji dashi dai" Aunty Zarah ta furta tana shigewa kitchen, murmushi Sadiya tayi ta shige bedroom ɗinsu Jummo ta samu zaune tana lazimi, baƙin ta Sadiya ta taɓe tare da furta.
" Wai dama su ƴan ƙauye har sun iya karatun Sallah ne."?
Murmushi Jummo tayi domin kuwa taji sarai abinda Sadiya ta faɗa kuma tasan da ita take, ta rasa meyasa Sadiya take jin zafin ta alhakin babu wani saɓanin daya shiga tsakaninsu, ko meyasa take mata haka, ita dai Jummo bata tanka mata ba.
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
" Lallai Rayuwarki tana daf da ƙarewa muddun wannan azzalumin shine wanda zaki iya rayuwa dashi."
Safreena tayi Maganar idanunta na kan videon da Sadiya da Garkuwa suke tsirara haihuwar uwarsu tana lalata, murmushi safreena tayi tare da ɗago Abdul dake calla kuka ta rungume sa tare da cewa Zee.
" Zee Wannan Yarinyar bata da hankali fa, kina ji darect yake sanar da ita bazai aureta ba, amma dake ƙaramar ƙwaƙwalwa ke gareta ta kasa fahimta, da ace Garkuwa ya furta min shigen kalaman gaskiya da yake nunawa wannan Yarinyar wallahi da ban sakankance dashi ba, yanzu meye abun yi."
Murmushi Zee tayi tare da amsar camerar ta cire memory ɗin, wata waya Android dake gefe ta ɗauka ta saka memory ɗin, tare da cewa.
" Ita wannan yarinya duk inda ta fito jaka ce marar basira dan haka rabu da ita kawai muyi abinda ke gaban mu, kinga wannan wayar na saka mata sabon layin da akayi registration ɗinsa ba hoto, address kuma ba nan garin na saka ba, Bauchi na saka, sannan sunan da nayi amfani dashi wajen registration ɗin shine *D N G* dashi zamuyi amfani wajen tsorata Garkuwa, yanzu zamu tura masa wannan video ɗin ta WhatsApp ɗinsa."
Murmushi safreena tayi tare da furta *D N G S* meaning *DANGEROUS* murmushi ta saki tare da karɓar wayar ta tura masa saƙon tana sakin murmushi.
Yana tafiya ta kashe datar tare da duban Zee tace.
" *Wasan ya fara daga yanzu* .........................."
*Wannan littafin na kuɗi ne akan farashi Naira 100 kacal ki daure ki biya sai ki cigaba da karatu cikin nutsuwa Free page daga 30 ya ƙare zaki cigaba da samun wannan littafin ne idan kin biya ɗarin ki.*
*Ki biya ta wannan hanyar 0006064512 Rashida Usman jaiz Bank ko mtn card wannan numbern 08147537180 sannan kiyi screenshot ki turo shaidar biya 100 ce kaɗai babu yawa.*
*UMMU NASMAH CE*
[4/15, 9:20 PM] UMMU NASMAH❤️: 🧺🧺🧺🧺
*GELLE ƁINGEL*
🏺🏺🏺🏺
*Story*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah)*
*Littattafan marubuciya*
Sauyin Rayuwa
Nasmah Ko Nasirah
Sara Da Sassaqa
Indo A Birni
So Bai San Jini Ba
Akan ƴar uwata.
Hatsabibiya Saude
Ruɗanin Zuciya Biyu.
Doctor Hassan.
Ƙauyenmu.
And now *GELLE ƁINGEL*
*SADAUKARWA*
Na sadaukar da wannan littafin daga farkonsa har ƙarshen sa ga ƙawata *ZARAH ABDUL MOMYN AHLAN* sonso nake fisabilillah.
*_________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_________________________________*
*LAST FREE PAGE WANDA YA BIYA KUƊIN SA NE KAWAI ZAI CIGABA DA GANIN WANNAN BOOK ƊIN, IDAN KINA RA'AYI ƳAR UWA MAZA HANZARTA KIZO KI BIYA KUƊIN KI NAIRA 100 NE KACAL BABU YAWA BATA FI ƘARFINKI BA, DOMIN KEMA A DAMA DAKE CIKIN WANNAN CAKWAKIYA MAI RIKITARWA 08147537180*
*Masu tambayar daga Farko idan kinji kina ra'ayin book ɗin biya ɗarin ki kawai sai ki samu daga farkon🥰🥰*
*LAST FREE PAGE*
➰➰ *29 to 30*
Murmushi Zee ta saki tana faɗawa saman kujera tace.
" Ƙawata aiki ya fara daga yau, na kuma san wasan zai fara armashi ne da zarar Garkuwa yaci karo da wannan saƙon ke dai kwantar da hankalin ki ki naɗe ƙafafunki ki bawa Garkuwa nan da awa ɗaya, zai fara cin karo da ruɗani."
Murmushi mai sauti Safreena tayi tare da cewa.
" Zee ai a yau kam na fara jin nutsuwa amma fa hankalina bazai taɓa kwanciya ba har sai naga Garkuwa a ƙasƙance."
" Hmmm!!! Saurin me kike Safreena, ai Garkuwa kam ya shiga tarkon mu, a yanzu mune zamu ke juya rayuwarsa muna wasa da ita ta yanda ƙwaƙwalwar sa zata gaza jurewa wannan wasan."
" Hmmm!!! Na yadda dake ƙawata kuma nasan duk abinda kika faɗa tabbas zaki iya, muje muyi dener dan yunwa nake ji sosai."
Dariya Zee tayi tare da cewa.
" Da kuma duk bakiji yunwar ba, sai yanzu sorry na manta ban sanar dake ba, Baba da Mama suna hanya gobe zasu shigo Nigeria."
Tsalle Safreena tasa tana dariya tace.
" Alhamdulillah wallahi naji daɗi dama na tsani zaman mu mu biyun nan, Allah ya kawo mana su lafiya."
Da ameen Zee ta amsa suna tashi suka nufi daining table.
Khalil shigowar sa cikin gidan babu kowa cikin falo, bedroom ɗin Mamma ya shiga tana zaune ta kunna sigari sai zuƙa take idanunta sunyi jajur dasu gefen ta Jummo ce da A'illo, saurin toshe hancinsa khalil yayi a rayuwar sa ya tsani warin sigari, ransa ne ya ɓaci cike da jin haushin Mamma yaƙi kulata Jummo ya kalla tare da cewa.
" Jummo zo falo ki sameni."
Tsaki Mamma tayi tare da cewa.
" Idan ma ka kulani ka raina Uwar da ta haifeka shege mai baƙin halin tsiya."
Khalil bai kulata ba ya fice abinsa
Da to Jummo ta amsa ƙirjinta na bugawa domin kuwa tayi zaton Momy ko Aunty Zarah ne suka sanar dashi abinda ya faru, tashi tayi tabi bayan sa a zaune ta gansa, itama zama tayi tare da cewa.
" Sannu da dawowa yaya khalil."
" Yauwa sannu Jummo"
waya ya ciro daga cikin wata ƙaramar leda ya ɓareta da kansa infinix hot9 plus mai shegen kyau ya miƙa mata tare da cewa.
" Ki riƙe wannan naki ne, ni na sai miki, zata ɗebe miki kewa, sannan gobe ne malamar da zata fara koya miki lesson zata fara zuwa takwas na dare, wayar ki sakata a chaji idan ta cika ki min magana zan koya miki yanda zakiyi Amfani da ita, sannan akwai alfarmar da nake nema wajenki nasan kuma zaki iya."
Cike da murna Jummo ta amshi wayar tana dariya tace.
" Yaya khalil Allah wannan wayata ne da gaske ni ka sayawa."
Dariya khalil yayi tare da ɗaga mata kai alamun eh naki ne.
Dariya tayi tace.
" Kai amma na gode sosai yaya khalil, ya khalil faɗa min alfarmar da kake so na maka ni kuma insha Allah zan maka shi."
Murmushi khalil yayi tare da gyara zaman sa ya fuskanci Jummo yace.
" Jummo So nake ki taimakeni ki taimaki kanki ki taimaki Daddy, ki dakatar da Hajjo daga shan sigari, Jummo kin san illar shan sigari kuwa."
Girgiza kanta Jummo tayi alamun a'a, khalil cewa yayi.
" Sigari tana haifar da hujewar huhu ta lalata kayan ciki, a ƙarshe Mutum ya mutu a wulaƙance, ƙarin illar sigari, da zarar mutum ya mutu, duk sigarin da yasha sai ya fita daga jikinsa haka zai lalata masa likkafani, Jummo idan muka bar Mamma ta cigaba da shan sigari dole ne zai illata rayuwarta ga shi ta tsufa shekarunta sunja, zai yi saurin illatata, Jummo idan har da gaske kina ƙaunar Mamma mu haɗa ƙarfi ni da ke mu cirewa Mamma ƙaunar sigari a zuciyarta."
Shuru Jummo tayi jikinta yayi sanyi, ba Mamma take tunani ba INNO take tunani da bata da wanda zai hanata lallai lafiyar INNO tana cikin hatsari, numfashi ta sauƙe tare da duban khalil tace.
" Yaya khalil ba sai mun haɗa ƙarfi ba, ni kaɗai zan iya hana Mamma shan sigari insha Allah amma bazai yiwu ta daina lokaci guda ba dole sai a hankali."
" Ba damuwa Jummo, Allah ya bamu Nasara, Jummo dan Allah ki dage kiyi ƙoƙari ki maida hankalin ki ga karatu, karki bani kunya dan Allah, nima monday zan koma Abuja wajen aikina."
" Insha Allah Ya khalil bazan baka kunya ba, zanyi ƙoƙari sosai, Ya khalil dama a Abuja kake aiki to aikin me kake a can."
" Ni jami'in soja ne, Jummo."
Zaro idanunta Jummo tayi tace.
" Cap hmmm!!! Soja mugaye ne fa yaya khalil"
Dariya Khalil yayi tare da cewa.
" Oh mu ɗin mugaye ne, to yanzu kinga nima na miki kama da mungu."
" A'a kaikam kana da kir.............."
" Khalil!!! Khalil!!! Kai Khalil!!!"
Muryar Momy dake tsaye sama ne ya doki kunnen su, tana kiran sunan Khalil a fusace.
Ɗago kansa khalil yayi ya kalli Momy tare da amsawa tsawa Momy ta daka masa tare da cewa.
" Zancen uban me ka zauna kana yi da wannan tambaɗaɗiyar marar albarka!!!! Har dariya kake da ita?"
Cike da mamaki khalil yake kallon Momy tambaɗaɗɗiya kuma, wai meyasa duk macen da yake so Momy bata sonta.
" Tambaɗaɗɗiya kuma Momy ban gane ba."?
Cike da masifa Momy tace.
" Eh tambaɗaɗɗiya zaka gane idan na sauƙo na ci ubanka, ina ruwanka da ita meye haɗinka da ita da har zaka zauna da ita, to kul ka sake koda kallon tane ban yarda ba wallahi.!!"
Garkuwa daya fito daga bedroom ɗinsa ne ya zo gaban Momy ya tsaya tare da harɗe hanunsa a ƙirjinsa yana sauraron abinda Khalil zaice.
" Momy wai me kike faɗa hakane me jummon ta miki kike mata wannan munanan zagin."
Jummo bakin ta taɓe tare da miƙewa tsaye ta ɗaga idanunta suka haɗa ido da Garkuwa, murmushi ya sakar mata tare da ɗaga mata gira ɗaya yana kanne mata ido, wani irin zubawa tsikar jikin Jummo yayi tare tare da jin sonsa ya taso mata murmushi ta saki tare da shigewa daga wajen tayi bedroom ɗin Mamma, murmushi Garkuwa yayi cikin ransa yana zayyano zumar da Jummo zatayi, duban Momy yayi tare da ƙara maida kallonsa ga khalil yace.
" Ɗan uwa dan Allah rabu da zancen Momy, da alama dai yau Daddy ya kunnata ne shiyasa zata huce akan budurwar ka."
Yayi Maganar yana dariya tare da kallon Momy, tsinkewa zuciyar Momy tayi tare da furta.
" Budurwa kuma!!! Kai budurwar fa kace kana nufin Khalil ke son Jummo.?"
Shima khalil murmushi yayi tare da kaɗa kansa, shi kuwa Garkuwa ya faɗi maganar ce kawai cikin wasa amma madadin ya cewa Momy wasa yake sai ma ce mata yayi.
" Eh mana budurwar sa, ba kece kike so ya ƙara Aure ba, gashi dai ya samu budurwar ƴar cas da ita ƴar rugar su Daddy da Momy."
Yayi Maganar yana dariya cike da masifa Momy zata fara zagin khalil kamar walƙiya taga baya wajen harya tashi, gira Garkuwa ya dagawa Momy yana shigewa nasa bedroom ɗin.
Cike da masifa Momy take hargowa tana khalil ɗin zaizo ne ya sameta.
Shi kuwa Garkuwa datar sa ya kunna yana dariyar Momy kasancewar sa mutum mai barkwanciya, facebook ya shiga ya gama abubuwan da zaiyi har zai kashe datar sai kuma ya shiga WhatsApp saƙonnin mutane ya fara dubawa wani yayi dariya wani kuma yayi tsaki MUSSAMAN na abokan aikinsa, saƙo na karshe daya saura wata baƙuwar Number ya gani wanda bai santa ba, shiga cikin saƙon yayi, video yaga an turo a hankali ya danna video ɗin, ya hau Reading ɗin buɗewa, harya buɗe, danna videan yayi, shigar su bedroom ɗin hotel ɗin ya fara gani shi da Sadiya zaro idonsa yayi yana cigaba da kallon, a matuƙar razane ya miƙe tsaye gumi na keto masa wani irin tashin hankali ne ya ziyarce sa, shine fa tsirara da Sadiya suna zina.
" Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!!!! Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!!! Hmmm!!! Na shiga Uku waye wannan waye ne yamin wannan ɗaukar!!!?"
Hanunsa na rawa yake kallon wayar tare da runtse idanunsa yana jin zuciyarsa na tsinkewa, idanunsa ya kai kan profile ɗin ta, online ya gani alamun wanda ya turo saƙon yana online, da sauri hanunsa na rawa ya rubuta saƙo ya tura.
" Please waye kai?"
Safreena dake riƙe da wayar ce ta dubi Zee tana dariya ta tura masa.
" Meye damuwarka da sanin ko ni waye.?"
Runtse idanunsa Garkuwa yayi tare da tura mata.
" Damuwata itace wannan video da ka turo min, dan Allah waye kai meye ribarka idan ka tozarta Ni, kuɗi kake buƙata to faɗi