zata kunna, Khalil ya zaro ido tare da saurin ƙarisawa gabanta yana.
" Subahanallah!! Haba Mamma sigari kuma a cikin gidan nan, bazai yiwu ba, baki isa ba wallahi.!!!!"
" To fa ubana!!! Bazai yiwu ba kace, to danne ni ka ƙwace, kai ko ubanka fa bai Isa hanani shanta ba, bare kai, waima dakata, kalilu bala'i kake nema dani ne, sai famar shige min hanci kake, to wallahi zan facoka, ka fice daga idanuna na rufe yau naga tsiya, meye haɗin ka kaska da garahumi, nace na cireka cikin zuriata to meye ruwanka dani."
Tsuka Khalil yaja tare da saka hanunsa ya murɗe hanun Mamma ba tare da yayi magana ba, sigarin ya ƙwace da ƙarfi yana miƙewa tsaye yace.
" Na danne ki na ƙwace!!! Mamma sai kiyi abinda zakiyi, wallahi muddun zaki zauna a cikin gidan nan, to wallahi bazaki sha sigari ba, kuma na isa na dakatar dake, a ƙauyen ne zaki sha sigari ki zauna lafiya amma ba'a cikin gidan nan ba, ni ki daina zaro min idanu, ba tsoro zai bani ba!!!"
Yayi Maganar yana zarowa Mamma itama ido tare da ciro bindiga yace.
" Kuma kina magana zan ɗauke kanki da wannan bindigar kiyi kuma ki gani." Tsawa ya dakawa A'illo da Jummo yace " ku kuma bazaku nemi waje ku zauna bane kuka tsaya akan mutane kamar mashi."
Tura bakinta Jummo tayi tare da zama kusa da Mamma tace.
" Kiyi hkr Mamma Allah zai saka miki, wannan ai zalunci ne, wai kema Mamma dama kinsan wannan gidan na azzalumai ne shine kika taho dani, to wallahi ni bazan yadda da zalunci ba, kuma bazan yadda a zalunce ki ba, babu wani ƙato ko ƙatuwar da zai bani tsoro, har wani ciro bindiga ake, to wa yake tsoron mutuwa mtss............................"
😆😆😆😆😆 *GIDAN CAKWAKIYA KENAN, WACCE IRIN RAYUWA ZA'AYI NE A WANNAN GIDAN, KU BIYO NI DA GUDU DOMIN JIN INDA WANNAN CAKWAKIYA ZATA TSAYA*
*NAIRA 100 KACAL ZAKU TURO TA WANNAN ACCOUNT NUMBERN 0006064512 RASHIDA USMAN JAIZ BANK, KO HOTON MTN CARD NA 100 TA WANNAN NUMBERN 08147537180 SANNAN KIYI SCREEN SHORT KI TURO SHAIDAR BIYA*
*PLEASE DAN ALLAH MASU VTU KU DAINA, BANDA VTU BANA SO, PLEASE KU DAINA*
🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️🏃🏻♀️ *KUYI SAURI KU BIYA FREE PAGE YA KUSA ƘAREWA, ARAHA TAFI BASHI 100 NE KAWAI BABU YAWA INA ALFAHARI DAKU MASOYANA*
*UMMU NASMAH CE*
[4/15, 9:20 PM] UMMU NASMAH❤️: 🧺🧺🧺🧺
*GELLE ƁINGEL*
🏺🏺🏺🏺
*Story*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah)*
*Littattafan marubuciya*
Sauyin Rayuwa
Nasmah Ko Nasirah
Sara Da Sassaqa
Indo A Birni
So Bai San Jini Ba
Akan ƴar uwata.
Hatsabibiya Saude
Ruɗanin Zuciya Biyu.
Doctor Hassan.
Ƙauyenmu.
And now *GELLE ƁINGEL*
*SADAUKARWA*
Na sadaukar da wannan littafin daga farkonsa har ƙarshen sa ga ƙawata *ZARAH ABDUL MOMYN AHLAN* sonso nake fisabilillah.
*_________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_________________________________*
*FREE PAGE*
➰➰ *15 to 16*
Zaro idonsa Khalil yayi yana ƙarewa Jummo kallo, nuna ta da yatsa yayi yana zaro mata ido ciki tsawa yace.
" Keeee!!!! Dan ubanki waye ƙaton ko ƙatuwar, dawa kike, kai!!! Momy kina jin abinda wannan ajabon yarinyar take faɗa mai kama da Aljana."
Yayi Maganar yana ɗauke Jummo da mari, saurin dafe kuncinta tayi ganin wasu taurari masu bala'in haske sun shige ta gabanta, bai sauƙe hanunsa ba, itama Jummo ta ɗaukesa da mari, daga Mamma Momy har su A'illo a razane suka miƙe suna kallon Jummo, duk da Jummo ba yau ta saba dakuwa da maza ba amma wannan marin da tayiwa Khalil sanda ya razana kowa a cikin falon cike da tsantsar mamaki , khalil yake kallon ta, ji yayi tamkar ya ɗauketa da bindigar da take hanunsa, sai kuma yaji hanunsa ya masa nauyi, idan harma yace zai daki wannan yarinyar mai zai samu a jikinta ai sai dai ya ɓallata, amma tabbas wannan babu hankali a jikinta, haka kuma ya tausaya wa rayuwarta domin kuwa duk mace mai ɗabi'ar Jummo abun tausayi ce, tabbas akwai ƙauyanci da jahilci yana yawo a jikinta shi kuwa jahili babu abinda bazai iya aikatawa ba lallai wannan yarinyar tana buƙatar tarbiyya shikaɗai yake zancen zucin yayin da ya juya cikin ɓacin rai, Momy kan Jummo ta hau da masifa tamkar zata daketa cike kuma da ƙyamar ta, Mamma ta dakatar da ita.
" Kul kul!!! Kika saka hanu jikinta Zainabu, shi wanda ta mara ɗin ganin mutunci manya yake ai gara itama marinsa kawai tayi, shifa yanzu yaso kasheni Allah ya tsererar dani, waini dama Zainabu haka ake rayuwa a cikin gidan ki babu tarbiyya da kwaɓa eh lallai dole na samu zama a cikin gidan nan duk na gyara muku zama."
Momy cike da takaici tana hararar Jummo ta haura sama Zarah ta kwaɗawa kira, da sauri Zarah ta fito tana amsawa a bakin kofa ta samu Momy tsaye tace.
" Gani Momy."
" Kije ƙasa ki kaiwa Mamma ruwa da abinci, tana can tana mita ni bazan iya zan shiga ɗaki na kwanta."
Da to Zarah ta amsa Momy ta shige bedroom ɗinta, Zarah bakinta ta taɓe tana cewa.
" Har kin fara jin haushi kenan, hmmm!! Abinda kike min kema shi ake miki, ba gara Mamma bama DUK tsiyar da zata shuka miki, bazata azabtar da mutum da bauta ba, mtss ai naji daɗin zuwan Mamma gidan nan."
Ta ƙarisa Maganar tana sauƙa ƙasa, fuskarta cike da murmushi, jikin Mamma ta faɗa tana dariya tare da cewa.
" Oyoyo Mamman mu, oh tsohuwar nan, sai yau kika ga damar kawo mana ziyara munyi kewarki har mun gaji."
Itama dariya tayi tana riƙo hanun Zarah tace.
" Ke dai zara'u bari, gajiya nayi da zaman ƙauyen nace bari na dawo binni na ɗan sha jar miyya, yauwa ƴar albarka zara'u ba ƴar soyayyiyar kaza ne, a kawo mana mu ɗan goge bakin tunda wannan shegen mijin naki mai baƙin ran tsiya ya ƙwace sigarin."
Dariya Zarah tasa tare da cewa.
" Kai Mamma gidan son da daɗi, ai kuwa ba'a taɓa rasa nono a ruga, bari naje na kawo kaza kici harta isheki."
Wangale baki Mamma tayi tace.
" Ke dai sannu ƴar albarka, ai duk rugar da aka rasa nono bata amsa sunan ta ruga ba."
Dariya Zarah tayi ta cewa A'illo.
" A'a harda Hajiya A'illo ne, lallai zuri'a ta haɗu, wannan fa waye ce Mamma ban Santa ba."
Ta nuna Jummo, murmushi Mamma tayi tace.
" Au wannan Jummo kenan, jummon INNO da Mamma, tare muka zo jikar aminiyata ne, INNO, tare zamu zauna na aurar da abina a gidan nan."
Murmushi Zarah tayi bata fahimci Maganar Mamma na ta aurar da Jummo a gidan ba, ta matsa kusa da Jummo tare da cewa.
" Sannu da zuwa Jummo, kin min kyau."
Dariya Jummo tayi haka kawai taji Zarah ta shiga ranta, tana dariyar tace
" Nima kin min kyau, zaki koya min irin gayunki, ina son nima nake irin wannan kwalliyar taki.?"
Dariya Zarah tayi tace.
" Ai daga yau kin dawo ƙawata, zan koya miki, bari ma kiga naje na kawo muku abinci idan kunci sai na rakaki kiyi wanka na miki kwalliyar."
Dariya Jummo tasa tace.
" To meye sunanki?"
" Sunana Zarah amma ki kirani da AUNTY, tashi muje kitchen ɗin ki tayani kawo abincin."
Da to Jummo ta amsa tare da tashi suka shiga kitchen ɗin tare, murmushi Mamma tayi tare da jin Zarah ta ƙara kwanciya a ranta, cikin minti goma Zarah da Jummo suka fito da abinci tare da kazar da Mamma ke so, sosai suka gyara zama suka kwashi abincin, sai Jummo bata wani ci sosai ba, kasancewar ta wanda bata da yawan cin abinci bare kwaɗayi, bayan sun gama ne Zarah ta kama hanun Jummo suka haura bedroom ɗin da Sadiya ke sauƙa idan tazo, fallen zani Zarah ta bawa Jummo tace ta cire kayanta ta ɗaura babu musu kuwa Jummo ta cire tolet suka shiga, gashin kan Jummo dake naɗe timili guda, Zarah ta sunce take gashin ya zubo bayan, gashi ne mai tsayin gaske baƙiƙƙirin sai datti dake danƙare a cikin sa, shanfo ta ɗauka ta fara wankewa Jummo gashin sosai ta wanke gashin ya fita tas, sannan ta matsa mata makilin a sabon brush ta bata tace ta wanke bakin, tana tsaye take gwada mata yanda zata wanke, tsabar yalon da hakwaran Jummo sukayi sai da yayi jini wajen wankewa, alhamdulillah kuma haƙorin ya fara fita ba laifi, sannan ne fa Zarah ta fita tabar Jummo tayi wanka, bedroom ɗin ta ta koma da niyyar ɗaukowa Jummo kaya a cikin nata ta saka, a zaune ta samu khalil ya haɗa tagumi yayi shiru, kusa dashi ta zauna cike da nutsuwa tace.
" Ya khalil, meya sameka haka kayi tagumi cike da tunanin, madadin wannan tagumin ai gara ka dinga ambaton innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!!! Sai Allah ya sanyaya maka zuciyarka, ya yaye maka damuwarka, tunda kaga dai ba kyau tagumi waima tukunna meya faru haka wannan tagumi Bana son ganinka cikin tunani mijina Please tell me."?
( Haka ake son mace ta kasance mai yawan nuna damuwarta ga mijinta idan ta ganshi cikin wani hali, tambayesa damuwarsa cikin hikima da iya zance, ina tabbatar miki, zai sanar dake matsalarsa.)
Numfashi Khalil ya sauƙe tare da kwantar da kansa a kafaɗar Zarah.
" My dear!! Tarin matsala zasu ƙaru a cikin gidan nan sakamakon zuwan Mamma ina gudun faruwar abubuwa da yawa nan gaba, bata ƙaunar Momy na tabbatar zaman Mamma cikin gidan nan matsalace ga Momy ko nace tashin hankalin ta, Mamma fitinanniyar tsohuwa ce wacce sam bata da fahimta, bansan taya zan fara fitar da Mamma daga cikin gidan nan ba, ta koma ƙauye, gashi tazo da wata tantiriyar yarinya marar kunya, kinsan yarinyar nan har marina tayi, amma na mata uzuri da alamu akwai jahilci a jikinta, domin baƙauyen mutum zai iya aikata ko wani irin aikin rashin hankali, shiyasa idan kika cewa balaraben mutum ɗan ƙauye, to kin gama masa zagin duniya tana buƙatar mai bata tarbiyya yarinyar."
" Hmmm!!! Ya khalil wace irin matsala kuma a tunanina babu wata matsala da Mamma tazo gidan ɗanta, ita dai Momy dole itace zatayi haƙuri da Mamma, Maganar ka maida Mamma ƙauye bai taso ba, Daddy ma ba yadda zaiyi ba, Ya khalil ka ɗauki komai da sauƙi sai yazo maka da sauƙi, yayin da kuma ka ɗauki abu da zafi, to da zafin zai tafi maka, ko yaushe kaine kake bani baki kana nuna min nayi haƙuri da Momy, to meyasa ita Momyn bazaka nuna mata tayi haƙuri da Mamma ba, haba ya khalil karka zamo mutum mai son kai mana, kaso mahaifiyarka fiye da mahaifiyar wani, wannan sam ba adalci bane, kayi tunani akan haka, ya khalil Maganar marin da Jummo ta maka kuma, dan Allah kayi hkr, bazance yarinta ke damunta ba, amma zance maka jahilci ke damunta kamar yadda ka faɗa, to ya khalil meyasa bazaka taimaka mata ba, wajen ganin ka inganta rayuwar ta, domin da alamu Jummo tana da basira idan Allah ya taimaka sai ta amfani al'umma da yawa, ka tallafa mata nima kuma ina da niyyar bata gudumowa."
" My dear, na sani nan gidan ɗan Mamma ne, ban miki musu akan haka ba, amma nina san abinda ke baki sani ba, wallahi ko rantsuwa nayi bazanyi kaffara ba, ba zuwan Allah da Annabi Mamma tayi ba, tazo ne kawai domin ta tadawa da Momy hankali akan wata hujjar ta marar ma'ana wanda dalilin rashin jituwar Momy da Mamma yasa bana shiri da Mamma, ko shaƙuwa ta tsakanin kaka da jika babu tsakanina da Mamma saboda bana taɓa bari Mamma ta ciwa Momy mutunci muddun ina kusa, bazan juri ganin Momy cikin tashin hankali ba, dole ne Mamma ta koma ƙauye, da kike Maganar na taimakawa wannan yarinyar, ta wacce hanyar kike tunanin zan taimaka mata, ni da nake neman yadda zanyi su koma inda suka fito."
Numfashi mai nauyi Zarah ta sauƙe tare da ɗaura hanunta a cinyar khalil tace.
" Kayi hkr insha Allah babu wata matsala da zata faru a cikin gidan nan, idan ma kuma akwai ta, to na ɗauki alƙawarin dakatar da ita, ina tabbatar maka babu abinda zai faru, idan kuma har abinda kake gudu ya faru, to ka ɗaura laifin komai a kaina, zan dakatar da gabar dake tsakanin Momy da Mamma, na sanya soyayya da shaƙuwa tsakanin su, na ɗauki wannan alƙawarin, Maganar Jummo kuwa, ma yita wata rana, amma dai yanzu kamin alfarma ka yafewa Jummo marin da ta maka, sannan kuma ka saki ranki naga farin ciki da annashuwa a gareka, domin farin cikin ka ya fimin komai daɗi a duniya."
Ta ƙarisa Maganar tana murmushi tare da ɗan jawo gemun khalil alamun rarrashi, murmushi Khalil yayi tare da kwanciya yana jawo Zarah ta faɗo jikinsa rungumota yayi yana dariya tare da cewa.
" Tabbas samun mace ta gari irinki a wannan zamanin yana matuƙar wahala, a duk sanda na shiga damuwa kinsan yanda zaki sanya ni farin ciki, ke ta dabance a cikin mata."
Itama Zarah dariya tayi tare da haɗe bakin ta da nasa, a hankali ta lalumo harshen sa wani irin tsotsa take masa mai fitar da tunani, lumshe idanunsa khalil yayi yana jin wani munguwar feeling yana tsarga masa daga tafin ƙafarsa har tsakiyar kansa, a hankali ya saka hanunsa ya tallafo kanta tare da aika mata nasa salon, tuni Zarah ta manta da Jummo na jiranta, ta Lula duniyar ma'aurata.
Jummo tafi awa ɗaya tana jiran Aunty Zarah shuru babu alamunta, tun tana zaune a ƙasan tayels ɗin sanyin ac na kaɗata, har bacci ya fara kwasarta tun tana gyangyaɗi harta silale ta kwanta, bacci ne mai nauyi ya dauketa sakamakon ac dake kaɗata dama kuwa Jummo gwanar son sanyi ne.
Mamma kuwa tana hakince cikin falon zaune tace bazata bar wajen ba har sai Daddy ya dawo ta kurawa tv idanu, tana kallon wasan kwaikwayo na Arewa24 Daɗin kowa, sai dariya take ita ɗaya tana Magana.
Garko dake zaune bakin bed ɗinsa yana buga game a wayarsa ne yaji wayar tayi ringin " *SADIYA* " haka ya gani rubuce, numfashi yaja yana yamutsa fuska ya ɗaga kiran tare da yin shuru daga can Sadiya ta fara magana cike da muryar kuka.
" Ya Garkuwa, wai kana nufin kace baka ga text ɗina bane, kayi shuru baka kiran ba, baka kuma min refly ba, ya kamata kazo mu san mafita."
" Idan naga text ɗin ki To ya kike so na miki, so kike naje na rufeta da duka ne, taya kike tunanin zansan dalilin da yasa take son raba tsakanin mu, kinga Sadiya nifa wannan ba damuwa ta bace, dan haka ya rage tsakanin ki da ƴar uwarki."
" Ya Garkuwa!!! Ba damuwar ka ba kace, ƙoƙarin raba mu fa ake amma kake kiran bai dameka ba, ko ka manta da soyayyar dake tsakanin mune, ko kuma dama yaudarata kake jikina kawai kake so, me kake nufi..................?"
*Ki biya Nairar ki 100 kacal ƴar uwa, sannan ki cigaba da karanta wannan labarin cike da nutsuwa, biya ta wannan hanyar*
*0006064512 Rashida Usman jaiz Bank ko mtn card ta wannan numbern 08147537180 sannan ku turo shaidar biya, karku manta Naira 100 ne kacal Araha tafi bashi🥰*
*UMMU NASMAH CE*
[4/15, 9:20 PM] UMMU NASMAH❤️: 🧺🧺🧺🧺
*GELLE ƁINGEL*
🏺🏺🏺🏺
*Story*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah)*
*Littattafan marubuciya*
Sauyin Rayuwa
Nasmah Ko Nasirah
Sara Da Sassaqa
Indo A Birni
So Bai San Jini Ba
Akan ƴar uwata.
Hatsabibiya Saude
Ruɗanin Zuciya Biyu.
Doctor Hassan.
Ƙauyenmu.
And now *GELLE ƁINGEL*
*SADAUKARWA*
Na sadaukar da wannan littafin daga farkonsa har ƙarshen sa ga ƙawata *ZARAH ABDUL MOMYN AHLAN* sonso nake fisabilillah.
*_________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_________________________________*
*FREE PAGE*
➰➰ *19 to 20*
" Khalil har kana da zarrar ɗaurawa mahaifiyata bindiga a cikin gida na, Oh kai gaka jami'in soja bari ka taka kowa to kayi ƙarya wallahi zan iya rabuwa da kai akan Mamma, baka isa ka ci mata mutunci ba, muddun kana neman albarkata a rayuwarka dole kabi Mamma, wai ma na tambayeka wannan gidan naka ne ko nawa."?
Khalil kansa na ƙasa cike da ɓacin rai, dama ya sani zuwan Mamma cikin gidan nan babu alkairi tazo ne kawai ta tarwatsa musu farin cikin gida, girgizawa Daddy kai yayi alamun a'a.
" Okay shine kuma bari ka takurawa Uwata, to ta fika iko da gidan nan kai ko nima ta fini iko da wannan gidan bare kuma kai, wallahi khalil ka shiga hankalinka idan ba haka ba, zaka barmin gidana, kaje ka sunkuya ka bata haƙuri shasha, shima mai gadin zai haɗu dani ne, wannan ai rashin hankali ne, Kai Garko haura ka kira min uwarku naji idan tane ta ɗaure muku gindi ku ci mutuncin mahaifiyata."
Shi dai Garkuwa bai ce komai ba kasancewar sa mutum da bai shiga cikin hayaniya, aiken Daddy ya haura, shi kuwa khalil tamkar zai danna ihu tsabar takaici da haushin Mamma, bai cewa Daddy komai ba yaje gabanta ya tsugunna tare da cewa.
" Kiyi haƙuri Mamma Allah ya huci zuciyarki."
Taɓe baki Mamma tayi tare da kaiwa khalil ranƙwashi a kai tace.
" A yanzu dai na haƙura amma wallahi a kiyaye gaba a daina shiga gona ta idan ba haka ba, wallahi na fika iskanci, kai ga ɗan iska har wani zare min idanu kake kana nuna min bindiga, to wallahi duk wanda yaci tuwo dani miya yasha."
Cije bakinsa khalil yayi cike da jin haushin ta, ya miƙe tsaye ya bar gidan gaba ɗaya, Momy tare suka sauƙo da khalil ya nemi waje gefe ya zauna yana cigaba da danna wayarsa, Momy gefe da Daddy ta zauna tace.
" Sannu da dawowa Alhaji."
" Bana buƙatar sannun ki ki riƙe kayanki, yanzu ke Zainab kece zaki wulaƙanta min mahaifiyata, ki watsar da ita a falo ki shige kiyi tafiyar ki, saboda baki san daraja da girman uwa ba, idan ke baki tashi a gaban mahaifiyarki ba, shiyasa baki san girman ta ba, to ni na tashi a gaban tawa kuma nasan daraja da kimarta, muddun za ki cigaba da nuna rashin kulawa akan Mamma zamu samu babbar matsala dake, ba fuska zaki haɗa ba ko mutuwa zakiyi Mamma ta dawo cikin gidan nan kenan da zama idan hakan bai miki ba, kina iya tafiya, amma dai ki sani bazan yadda da cin mutuncin mahaifiyata ba."
Momy shuru tayi tana sauraron Daddy, harya gama cikin sanyin murya tace.
" Cin mutunci kuma Alhaji ta yaya zanci mutuncin Mamma, nima fa.........."
Dakatar da Momy Daddy yayi ta hanyar ɗaga mata hanu yace.
" Excuse me Malama, ƙarya Mamman zata miki, baki da bakin kare kanki a wajena, ki tashi ki tafi ki bamu waje."
Bata kuma cewa komai ba Momy ta miƙe tare da furta.
" Allah ya baku haƙuri."
Tayi Maganar tana barin wajen, Daddy Sosai ya dinga bawa Mamma haƙuri har ya samu ta sauƙo da kansa ya nuna mata bedroom ɗin da zata zauna, a ƙasan, sannan ya haura nasa bedroom ɗin domin ya watsa ruwa, A'illo ma haurawa tayi bedroom dinsu ita da Zarah ya rage daga Jummo sai Garkuwa a falon da hankalinsa ke kan wayarsa, Jummo tashi tayi daga inda take zaune ta dawo kusa da Garko ta zauna, muryar ta yaji ta daki kunnen sa.
" Ya Garkuwa na, shine bazaka ce nayi kyau ba, kai fa na yiwa kwalliyar nan."
Shuru ya mata tamkar bai jita ba, ƙara ce masa tayi.
" Ya Garkuwa ka kalleni fa wallahi nayi kyau."
Cike da tsawa Garkuwa ya ɗago kansa yana daka mata tsawa cikin sauti mai amo sanda Jummo ta razana.
" Ke dalla!!! Mahaukaciya jaka!!! Ni ina ruwana da kwalliyar ki, kin bi kin cika min kunne da zancen banza zancen hauka ke a hakan gani kike kinyi kyau, da kinsan yanda wannan kwalliyar ta mayar dake kamar jaka da baki zo kince min kinyi kyau ba, dubeki dalla wata mummuna dake ko tsari baki dashi tashi a gabana kona hanɓareki!!!"
Jikin Jummo sanyi yayi tayi shuru tana duban jikinta wai batayi kyau ba, wai kuma jaka, hawaye ne ya zubo mata, ta tashi da gudu ta haura sama tana kuka, runtse idanunsa Garkuwa yayi harga Allah idan yace batayi kyau ba, ya faɗa ne kawai saboda son ranshi, domin kuwa sosai ta masa kyau, sanin rashin mutuncin Jummo da rainin ta yasa yace mata batayi kyau ba, domin shi mutum ne wanda baya son raini, haka kawai yaji zuciyarsa bataji daɗin abunda ya mata ba, ji yayi zaman falon ma ya isheshi tashi yayi ya fice compaunt ɗin gidan.
Bedroom ɗin Aunty Zarah ta faɗa tana kuka, Aunty Zarah zaro idanunta tayi tare da cewa.
" Subahanallah Jummo lafiya."
Cikin kuka tace.
"Aunty wai banyi kyau ba, wai kamar jaka na koma, wai mummuna ce ni?"
Murmushi Aunty Zarah tayi tana girgiza kanta tace.
" Ikon Allah waye yace miki haka.?"
" Aunty Ya Garkuwa ne.?"
" Garkuwa kuma!! Hmmm ya faɗa miki son ranshi ne kawai amma shima yasan kinyi kyau, wama ya isa ya kiraki mummuna, ai a cikin kyawawan ma ke ta daban ce, rabu dashi zolayarki yake dan kawai ya saki kuka."
Sai yanzu Jummo tayi dariya tace.
" Allah Aunty zolayata yake, da har naji haushi."
" Ki daina jin haushi haka shi yake ya fiye tsokana."
Dariya kawai Jummo tayi tace.
" Aunty bari na tayaki aikin."
Tare suka ci-gaba da gyaran bedroom ɗin da Jummo, kafin suka koma kitchen.
✨✨✨✨✨✨✨✨✨
*Bayan sati biyu*
Sosai zaman gidan yake yiwa Jummo daɗi domin kuwa Aunty Zarah ta zamo mata tamkar ƙawa komai tana mata, haka komai tare suke yi, har ya zamanto Jummo ta fara iya girki da kanta, wannan yalon hakwaran nata duk ya goge, kwalliya kuwa sosai take yinsa Aunty Zarah da kanta ta saya mata sutura, yayin da zaman su da A'illo suke zaman doya da manja babu mai shiga sabgar wani, Mamma ma Sosai take jin daɗin zaman gidan Aunty Zarah na kula da ita yanda ya dace tamkar ƴar da ta haifa a cikin ta, Momy kuwa tana takure da zaman Mamma domin kuwa bata isa tayi koda motsi bane sai Mamma ta saka mata ido kullum cikin mita take yiwa Momy, hakanne yasa ta fara neman hanyar da zata kori Mamma daga cikin gidan cikin sauƙi ta tafi da kanta ba tare da Daddy ya zargeta ba, ta kira ƙawarta Asabe suka shawara, yayin da suka shirya zuwa wajen boka domin ya kora musu Mamma daga cikin gidan koda Momy zata samu sauƙi a cikin gidan, Zarah sosai taji daɗin zuwan su Mamma domin kuwa a cikin kashi ɗari na wahalar da Momy take bata babu kashi hamsin duk Mamma ta tare mata shi, shi kuwa khalil baima shiga sabgar Mamma iyakarsa da ita ya gaishe ta, da safe sai kuma idan yaga dama ya zauna da ita suyi hira sa'i da lokaci amma duk abinda zatayi ido yake zuba mata, haka take shiga cikin bedroom ɗin ta tasha tabarta ta ƙoshi babu wanda ya isa ya hanata, ganin da khalil yayi Mamma na son Jummo Sosai kuma tana jin maganarta, hakan ya sashi ya ƙudiri niyyar jawo Jummo jikinsa yayi amfani da ita wajen haramtawa Mamma shan sigari.