✨✨✨✨✨✨✨✨✨
" Wallahi wallahi na rantse da Allah Zee wallahi billahil'azim nice ƙalubalen Garkuwa a Wannan Duniyar wallahi muddun ina numfashi bazan taɓa barin wata mace ta kusance sa ba, sai yayi danasanin ɓatamin rayuwata, yau na dawo daga Egypt kuma a yau zan fara bibiyar rayuwarsa, da wannan yaron daya batawa suna yasa muka samesa ta hanyar banza, dashi zanyi amfani wajen ganin ƙarshen Garkuwa Zee koda komai na zai ƙare nayi yawo tsirara na rasa farcen susa muddun zanga bayan Garkuwa wallahi sai nabi Wannan Hanyar, a yanzu gani yake farmaƙin daya saka aka kawo mana duka mun mutu nida iyayena, na tsani Garkuwa duk sanda na tuno shine yayi sanadiyar mutuwar iyayena sai naji tamkar naje na kashe nasa ahalin Bayan ya rabani da mutunci na ya min ciki hakan bai isheshi ba sanda ya kawo ƙarshen iyayena Abbana Ummina Brother Saleem Aunty ummu lil Saleem duk ya saka an kashe su, da badan mahaifinki ba, da nima yanzu babu labarina, ni da abinda yake cikina wannan gidan yaron ne baya son na Haifa, kuma gashi yazo duniya dashi zan tozarta GARKUWA."
Numfashi Zee taja tana kallon *SAFREENA* da ke rungume da wani ƙaramin Yaro yana bacci hankalinsa kwance, tausayinta ya kama Zee TABBAS SAFREENA taga ƙalubalen Rayuwa, Soyayya ta zamo mata mungun dafi ta ajiye mata munguwar tarihi, da ana tariyo Rayuwar baya da yanzu SAFREENA cikakkiyar mai gata da iko ne lallai ne Maganar Hausawa *mutum mungun icce ne*
🤔🤔 Wacece SAFREENA menene alaƙar ta da Garkuwa waye mahaifinta duk zaku samu wannan cikakkiyar amsar sanƙame cikin wannan littafin mai matuƙar sarƙaƙiya da cakwakiyar soyayyah ku dai ku biyoni ta hanyar.
*Ki biya kuɗin ki Naira 100 ta wannan account numbern 0006064512 Rashida Usman jaiz Bank ko hoton Mtn card ta Wannan numbern 08147537180 sai kiyi screen short ki turo shaidar biya*
*ki biya tun yanzu kafin LITTAFIN ya koma 300 domin kuwa ya kusa komawa*
*Kuyi haƙuri yau na muku typing kaɗan hakan ya faru ne sakamakon uzuri da yayi min yawa sorry*
*UMMU NASMAH CE*
[4/15, 9:20 PM] UMMU NASMAH❤️: 🧺🧺🧺🧺
*GELLE ƁINGEL*
🏺🏺🏺🏺
*Story*
*Rasheedat Usman*
*(Ummu Nasmah)*
*Littattafan marubuciya*
Sauyin Rayuwa
Nasmah Ko Nasirah
Sara Da Sassaqa
Indo A Birni
So Bai San Jini Ba
Akan ƴar uwata.
Hatsabibiya Saude
Ruɗanin Zuciya Biyu.
Doctor Hassan.
Ƙauyenmu.
And now *GELLE ƁINGEL*
*SADAUKARWA*
Na sadaukar da wannan littafin daga farkonsa har ƙarshen sa ga ƙawata *ZARAH ABDUL MOMYN AHLAN* sonso nake fisabilillah.
*_________________________________*
*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*_________________________________*
*AFWAN AFWAN!!! AFWAN FAN'S JIYA BAN SAMU DAMAR TYPING BA GASHI KUMA BAN BAKU UZURI NA BA, INA NEMAN AFUWAR KU MUSSAMAN ƳAN PAID GROUP AMMA TABBAS UZURI NE MAI ƘARFI YA RIƘENI A JIYA*
*FREE PAGE*
➰➰ *21 to 22*
Nisawa Zee tayi tana gyara zamanta tare da saka hanu ta ɗauki Abdul ta dawo dashi jikinta, duban SAFREENA tayi ta fara magana cike da nutsuwa.
" SAFREENA karki sake wani kuskuren na biyu, domin zai iya jawo miki tashin hankali da yafi na baya, sanin kanki ne ba imani bane da Garkuwa zai iya aikata komai akanki domin ganin ya kawo ƙarshen ki a wannan duniyar saboda ya fahimci baki da wani burin da ya wuce ki tozarta shi, ki daina kafa hujja da Abdul zai iya kasheki ya ɗauki wannan yaron ya fitar dashi daga Nigeria ya kaisa can wata ƙasar yayi Rayuwa ba tare da kowa yasan jinin sa bane, gudun kar asirinsa ya toni a gane shi fasiƙi ne, ubansa sanannan ɗan kasuwa ne kin sani babu wanda bai san Alhaji Buba Garko ba, kinga kuwa dole ya nemi duk hanyar da zai tseratar da mutuncin ubansa, kasheki a wajen Garkuwa ba komai bane, SAFREENA ina tausayinki yasa nake faɗa miki iya gaskiya ta, kina da tarin a hali sai dai ba su da amfani a gareki SABODA basu ƙaunar mahaifinki bare kuma ke, Daddy shi kaɗai ne gatanki a duniya kuma yanzu babu shi, ki riƙe maraicinki SAFREENA karki sake shiga safgar Garkuwa, a baya soyayya ta jefaki cikin mungun yanayi harta yi sanadiyar rasa farin cikin ki, a yanzu kuma na hango ƙiyayya tana shirin ƙara jefaki cikin masifa, dan Allah SAFREENA karki sake hasashena ya zamo gaskiya, ki barsa da Allah ki rungumi ɗanki ki basa tarbiyyar da ta dace, ki manta da Garkuwa a rayuwarki karki sake koda wasa yaga Abdul domin zai rabaki dashi."
Hawayene suka zubo daga ƙwayar idanun SAFREENA cikin sanyin jiki da rawar murya tace.
" Na sani Zee bani da gata yanzu na rasa gata na ta sanadiyyar Garkuwa Da son zuciyata, dalilin da yasa nake jin bazan taɓa samun sukuni ba, idan banga Garkuwa a ƙasƙance a wulaƙance ba, na rantse miki da Allah bazan bar Garkuwa yaji daɗi a rayuwarsa ba, sai na toshe duk wata hanyar da farin ciki zaizo masa, sai na ɗanɗana masa baƙin ciki fiye da wanda ya sani a cikin sa, dan haka ki adana kalamanki domin bazasu shiga kunnuwa na ba, saboda suna toshe babu abinda yake yawo a cikin su sai sautin ƙara da ihun iyayena, ina jin sautin su acikin kunnuwa na, suna ihu wuta na cinsu, Abba da ummi sun mutu ne da sunana a bakin su, sai ni kuma na kasa ɗaukar fansar su, muddun ban ɗauka musu fansa ba, rayuwata bazata taɓa samun nutsuwa ba, Zee na San a baya soyayya ce ta jefani mungun halin da nake ciki yanzu dalilin da yasa naji na tsani soyayya da duk wani mai yinta, na tsani maza bana son ganin su, wallahi Zee da wannan hanun nawa zan kashe Garkuwa nayi wannan alƙawarin kuma sai na cikasa koda nima zan mutu, menene a rayuwata ban yiwa GARKUWA ba, numfashi nane kawai ban basa ba, amma ki duba kiga a ƙarshe abinda ya saka min dashi, ko wannan yaron idan na kallesa na tuno jinin Garkuwa ne sai naji na tsanesa, ji nake tamkar na shaƙesa masa wuya ya mutu, bazan ɓoye miki ba Zee bana son ganin fuskar Abdul saboda babu inda yabar Garkuwa, Baba ne yafi ƙarfina wallahi da bazan shayar da shi ba."
" Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!!!! Me kike faɗa ne haka SAFREENA shin ƙiyayyar Garkuwa tasa kin haukace ne, sai abubuwa kike ta famar yi irin na mahaukatan da aka saka a turu, shi wannan yaron meye laifin sa, sanda zakuyi zina ku samu cikin sa ya sani ne, shima baiƙi ya fito ta hanyar halak ba, SAFREENA karki haɗawa kanki zunubi biyu akan Abdul, ga zunubin kawosa duniya ta hanyar zina ga kuma zunubin azabtar dashi, baisan komai ba tsakanin ku, dan Allah karki hukuntasa da laifin da ba nasa ba, tunda kince bazaki haƙura kibar Garkuwa ba, shikenan amma shi dai Abdul dan Allah karki cutar dashi ki jashi a jikinki a yanzu bashi da wani gata idan ba ke ba."
" Ni ba gatansa bane ki daina kirana a matsayin gatansa, Abdul bashi da laifi kike cewa, karki manta da cewa ƙaddarar haihuwar sa ta hanyar da bata dace ba, shiya jawo min duk wani tashin hankali da nake ciki,. Sannan kice bashi da laifi, HMMM!!!! Idan kika ambato min kalmar zina sai inji tamkar zagina kike, kinsani ni na mazinaciya bace ƙaddara ce ta faɗa min da duhun Soyayya, kin sani rashin kuɗi yake sa ayi zina, ni kuma ban rasa komai ba a rayuwata sanin kanki ubana ya ninka uban Garkuwa goma a kuɗi ki dinga saka lamarina cikin kaddara."
Tana gama faɗin haka ta miƙe ta fice tana kuka, hawayen daya ɗan taru a idanun Zee ta goge tana goya Abdul a bayanta ta hau jijjiga sa.
✨✨✨✨✨✨✨✨✨
" Asabe yanzu kina nufin goben dole sai da sassafe zamu tafi kin sani fa Alhaji bazai barni nayi fitan sammako ba."
" Haba dai Hajiya Zainab, ya kamata ki nemo duk wata hanyar da zai barki ki fice domin kuwa uban layi ake samu wajen bokan nan, idan ba sammako mukayi ba, ƙarshen ta musha wahalar banza ne bamu samu ganinsa ba, kiyi ƙoƙari kisan ƙaryar da zaki masa mu tafi 5:30am."
Shuru Momy tayi kafin tace.
" Shikenan zan gwada Allah yasa ya barni, wallahi haushin tsohuwar nan nake ji, ta tsaneni tun ina budurwa har kawo yanzu girma ya fara kamani amma bata barni na huta ba, ni a wannan karon so nake a raba tsakanin su da Alhaji Buba kowa yaji ya tsani ɗan uwansa, uwar ta tsani ɗan shima ɗan ya tsani Uwar, su rabu kawai na huta."
" Wannan fa ƙaramin aiki ne a wajen wannan bokan dan haka karki damu duk abinda kike so zai iya miki muddun zaki sake masa kuɗi."
" Kinsan kuɗi ni ba matsala ta bace, muddun za'a rabani da Mamma wallahi zan kashe ko nawa ne."
" Shikenan ni bari na koma duk yanda kikayi naji kota waya ce."
Da to Momy ta amsa tare da tashi ta rako Asabe har compaunt ɗin gidan sannan ta dawo, cike da masifa take kwalawa Zarah kira, Zarah dake zaune ita da Jummo a bedroom ɗin Mamma ne ta jiyo muryar Momy na kiranta wani irin tsinkewa zuciyarta tayi, da sauri ta miƙe tana amsa kiran ta fito da sauri, da kallo Jummo tabi Zarah yanda taga ta gigice, Mamma kuwa dama baccin ta take sha, a falo ta sami Momyn tsaye, ta risina tace.
" Gani Momy."
" Uban kikeyi a cikin bedroom ɗin Mamma, uban waye zai miki ayyukan cikin gidan nan, naga alamar yanzu kin fara koyon munafurci ko, kega annamimiya uwar iya kissa, Saboda a soki ko, tunda mutanen nan suka dawo cikin gidan nan naga kin nane musu sai shiga jikin su kike, to bari kiji bazan kamu ci munafurci ba, daga yau babu ke babu sake zama a ɗakin Mamma iyakarki da ita ki shiga ki gaisheta ki fito, munafukar Banza, ki shige gacan wanki na sun taru kije ki wanke min, sannan yau tuwo zakiyi mana miyar ganye a cikin gidan nan shasha."
Sunkuyar da kanta ƙasa Zarah tayi duk masifar da Momy take babu wanda Zarah ta mayar mata harta bar wajen, numfashi Zarah ta sauƙe tare da nufar bayan momyn ta ɗauko wankin nata zuwa yanzu wahalar da take sha a gidan na aiki yabi jikinta sai dai cin mutunci da zagin da Momy ke mata shi kaɗai ne yake ci mata zuciyarta, a bayan gidan tayi wankin tas ta shanya su, bisa mamakin kafin ta gama wankin ta fito ta samu, Jummo ta gyara mata falon tas har wanke wanke sai da ta mata, dubanta ta kai da gas dake kunne, wajen ta nufa tare da dafa kafaɗar Jummo, targen semonvita ta samu jummo nayi, numfashi ta sauƙe tare da cewa.
" Jummo duk ke kikayi wannan aikin wa yace miki tuwo zanyi yau."
Murmushi Jummo tayi tana zuba semon ɗin cikin tukunyar tace.
" Aunty ina jin duk masifar da Momy take miki, hmmm!!! Aunty Momy bata da kirki wallahi dani take yiwa zagin da ta miki Allah saina rama, naga alamun Momy ta tsaneki, Aunty me kika mata kin taɓa mata wani laifi ne."
Numfashi zarah ta sauƙe tare da cewa.
" Jummo ban mata laifin komai ba, aikine na makara, kuma kinga dole tamin faɗa a matsayin ta na uwata, kinga mubar zancen nan, tunda kin kusa gama tuwon ni bari na tsinke ganyen."
Shuru Jummo tayi bata kuma cewa komai ba, har suka gama aikin Jummo ganin ta gama nata yasa ta fito falo Garkuwa ta gani zaune ya maida hankalin sa ga tv yana kallon BBC news, zama a kujera Jummo tayi tare da cewa.
" Ya Garkuwa, kai kullum kana gida, baka zuwa aikine sai zaman banza."
Zaro idonsa Garkuwa yayi yana juyo da kansa ya kalleta wani irin bugawa zuciyarsa tayi, take yawunsa ya tsinke, ganin Jummo cikin ƙananan kaya riga da wando wanda ta ɗan kama mata jiki, ga dukiyar fulaninta sun cika rigar tam, shi kansa wandon ya ɗan kamata, gashi tayi fresh tayi kyau, ( wai dama haka take da kyau, hmmm!!! Lallai wannan akwai kayan daɗi a jikinta, Allah ya kai damo ga harawa ko bai ci ba yayi ɓarna) leɓensa ya cije tare da fasa yin masifar da yayi niyyar mata kau da kansa yayi tamkar baiji ta ba, Aunty Zarah dake tsaye bakin kitchen tana jin maganar da Jummo ta faɗawa Garkuwa ya sata yin dariya tace.
" Waya faɗa miki Garkuwa baya aiki, yana aiki a babban Companyn *A,A ASAD INTERNATIONAL AIRPORT* matuƙin jirgin sama ne, hutu ya ɗauka shiyasa kike ganinsa kullum a gida."
Taɓe bakinta Jummo tayi tare da miƙewa tsaye tace.
" Ummm!!!! Aunty wai fa sonsa Nak..................."
" Assalamualaikum."
Sallamar Sadiya cikin gidan shiya hana Jummo ƙarisa Maganar da tayi niyya, da kallon waye wannan Jummo tabi Sadiya, Sadiya ranta a matuƙar haɗe tana jefawa Garkuwa wani irin kallo mai wuyar fassarawa Garkuwa ɗago kansa yayi ya zubawa Sadiya ido tare da kau da kansa gefe, sai kuma ya saki murmushin gefen baki, wanda shi kaɗai yasan me yake nufi miƙewa yayi ya shige bedroom ɗin Mamma, numfashi ta sauke Sadiya tare da ƙarisowa ta zauna tana kallon Aunty Zarah.
" Sadiya lafiyar ki kuwa kika shigo ranki a haɗe, meya sameki."?
" Umhmmm!!! Ba komai Aunty yanayin nature ne, amm Aunty ina ya khalil ashe ya dawo.?"
" Eh ya dawo ya fita, sai anjuma zai dawo, zamu kwana ne ko zaki koma gida yau."
Kanta ta ɗaga ta kalli Jummo tare da cewa.
" Na dawo bani da Ranar tafiya akwati na yana wajen mai gadi yanzu zai shigo min dashi, wacece wannan Aunty."?
" Jummo ƴar uwar su................"
Dakatar da Aunty Zarah tayi ta furta.
" Jummo Jummo Jummo!!! (A zuciyarta tace Oh ko dai itace wacce Garkuwa yake bani labarin ta wacce take sonsa a ƙauyensu, to amma ya akayi har ta waye haka, bura'uba heee lallai banga ta zama ba, domin kuwa wannan nayi wasa wallahi sai ƙwace Garko daga hanuna.) Numfashi ta sauƙe tace.
*Wannan littafin na kuɗi ne akan farashi Naira 100 kacal zaki biya kuɗin ki ta wannan account numbern 0006064512 Rashida Usman jaiz Bank ko hoton mtn card ta wannan numbern 08147537180 sannan ku turo shaidar biya.*
*Ku HANZARTA ku biya Free page yazo ƙarshe Naira ɗari ce ba yawa da zarar Free page ya kare BOOK ɗin ya tashi daga Naira 100 ya koma 300 ku HANZARTA maza kar wannan damar ta shige ku.*
*Sorry for typing error banyi editing ba.*
*UMMU NASMAH CE*
[4/15, 9:20 PM] UMMU NASMAH❤️: 🏺 *GELLE ƁINGEL* 🧺
*(Garinsu yarinyar)*
*Na marubuciyar*
Sauyin Rayuwa
Nasmah Ko Nasirah
Sara Da Sassaqa
Akan ƴar Uwata
Indo A Birni
So Bai San Jini Ba
Hatsabibiya Saude
Ruɗanin Zuciya Biyu
Doctor Hassan
Ƙauyemu
And Now *GELLE ƁINGEL*
Sadaukarwa ga ƙawata Zarah Abdul Momyn Ahlan.
*Dan Allah ina roƙon namiji karya shiga group ɗin nan dan Allah*
*Wannan littafin na kuɗine idan kin san ba saya zakiyi ba kema dan Allah karki shiga, haka idan kinsan baza kiyi comments ba nan ma karki shiga Naira 100 ne kaɗai kuɗin littafin ban tsawalla ba in dai kina da niyyar saya, iya Free page kawai zaki samu a cikin gidan nan*
https://chat.whatsapp.com/LTWeFGmoKqTDbMbsU37088
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
*FREE PAGE*
➰➰ *17 to 18*
" Dakata dan Allah Sadiya!!! Wannan maganar taki ta fara toshe min kunne ta fara wuce gona da iri, dama akwai alkawarin Aure tsakanina dake ne yanzu koko nace miki zanyi Aure nan kusa, da zaki sawa zuciyarki nutsuwa ki kwantar da hankalinki idan Aure kike buƙata ki nemi wanda yake da niyyar yi kiyi Auren ki zai fiki alkairi, domin kuwa babu Aure a gabana ke ni aure nan da shekara biyar ma albarka, amma idan har na taɓa miki alƙawarin Aure sai ki tuna min, dan haka kiyi hkr kawai Sadiya Allah ya haɗa kowa da rabonsa."
Tamkar sauƙar aradu Sadiya taji Maganar tasa wani gumin azaba ne ya keto mata, take taji ɗakin na juya mata dafe kanta dake sara mata tayi, cikin nauyin baki tace.
" Please Ya Garkuwa ka daina min irin wannan wasan bana so yana tsinka min zuciyata, dan Allah ka daina."
" Wasa kuma Sadiya na taɓa irin wannan wasan dake, ba wasa nake miki ba Sadiya, wallahi babu Maganar soyayya yanzu tsakanina dake Saboda baki dace da ki zamo Uwar ƴaƴana ba Sadiya idan har namiji kike buƙata, ai naga ina ɗauke miki sha'awar ki idan kuɗi kike buƙata ina baki, meye a cikin Auren ina dai shine to wannene bana miki, idan har zaki iya mu'amala dani a haka babu zancen Aure ƙofata a buɗe take, Aure kam nida shi ba yanzu ba."
Runtse idanunta Sadiya tayi hawaye ne mai zafin gaske ya siraro daga idanunta, tabbas namiji ba ɗan goyo da zani ba ne, ta bawa Garkuwa rayuwarta harda mutuncin ta, amma yaci amanar ta koda a cikin mafarki bata taɓa tunanin garkuwa zai juya mata baya ba, ashe burinsa kenan akanta ya ta lalata da ita ƙarshe ya gujeta " innalillahi wa'inna ilaihirraji'un!!! Tabbas soyayyar Ya Garkuwa ta zamo min masifa" hawayen ta goge tare da cewa.
" Dan Allah ya Garkuwa ka rufa min asiri karka juyawa soyayyata baya, kai kaɗai zuciyata take so, bata da wani farin ciki idan ba naka ba ya Garkuwa, wallahi ina sonka, rasa ka gareni tamkar barazana ce ga rayuwata, karka yaudareni ya Garkuwa dan Allah ka Aure ni Wallahi kai kaɗai nake so meye aibuna da bazaka soni ba?."
Shuru Garkuwa yayi yana sauraron ta, sanda ta gama maganar ta cikin sannan Garkuwa ya sauƙe numfashi tare da cewa.
" Duk wani Maganar da zan miki ki fahimta, Sadiya nayi amma naga alamar kina da taurin kan tsiya, bazaki fahimta ba, dan haka ina mai gargaɗinki Sadiya karki kuma kiran wayata, idan kuma zaki kira wayata to ki tabbatar cewa kin amince ne mu cigaba da alaƙar mu kamar da, amma karki kuma min Maganar Aure this is the last warning."
Yana ƙarisa Maganar ya kashe wayar gabaki ɗaya, yana jan tsuka tare da jin haushin Zarah me take nufi da ƙoƙarin rabasa da Sadiya yasan bata san alaƙar saduwa dake tsakanin sa da Sadiya ba, to meye dalilin ta, na cewa Sadiya ta rabu dashi, harga Allah shi da zuciya ɗaya yake zaune da ita, sai gashi tana cin dunduniyar sa, tsuka yaja tare da ɗaga kafaɗarsa yana Kwanciya ya furta.
" Wannan damuwarki ne, dama can ni ba Auren ƴar uwarki zanyi ba, asali ma itace ta liƙemin tamkar cungam domin kuwa babu ta yadda zan yarda na auri mazinaciya,. Uwa ta gari ya dace na samawa yarana ba mace Irin Sadiya ba."
Numfashi ya sauƙe tare da lumshe idanunsa yana kallon slim.
Ita kuwa Aunty Zarah tuni ta manta da Jummo dake jiranta ta Lula rayuwar Auren ta, bacci ne mai nauyin gaske ya ɗauketa a ƙirjin Khalil, itace bata farka ba sai da taji ana kiran sallar magaruba a hankali ta buɗe idanunta akan fuskar khalil dake baccin sa hankali kwance.
" Bismillahil lazi ahayana ba'ada ma amatana wa ilaihinnushur!!! Subahanallah subahanallah subahanallah!!!! Wala hamdulillah Wala hamdulillah Wala hamdulillah!!! Wala ilaha'illallah wallahu akbar."
Wannan shine ya zamewa Aunty Zarah ɗabia a rayuwarta duk sanda ta farka daga bacci sai ta yi wannan addu'ar da ake so ko wanni musulmi ya jimance sa yayin tashi daga bacci, a hankali ta saka yatsanta a kunnen Khalil na sosa masa, domin ya farka, cike kuwa da nutsuwa ya buɗe idon yana kallon ta lumshe su yayi ya kuma sake buɗewa murmushi ya sakar mata tare da furta.
" Oh My dear wani irin bacci haka mukayi ba tsarki a jikin mu, kamar sallah ma naji ana kira ko.?"
" Sallah ake kira ya kamata ka tashi ka HANZARTA kayi wanka Kafin a shiga Masallaci."
Miƙewa tayi daga jikin sa tana jawo bargon ta ƙara rufe jikinta hanunta ta saka ta jawo towel dake jikin gadon ta miƙawa Khalil karɓa yayi ya miƙe tare da ɗorawa a ƙugunsa ya shige tolet, ita kuwa Zarah jingina tayi jikin gadon tana lumshe idanunta, Jummo ce ta faɗo mata a rai, saurin ware idanunta tayi tare da furta.
" Subahanallah!!! Oh My god, tana can sai zaman jirana take."
Sauƙowa tayi daga bed ɗin tare da jawo zani ta ɗaura a ƙirjinta, ta buɗe wadrop ɗin ta ta ɗaukowa Jummo baƙar doguwar riga mai ratsin golden a jiki, hijab ta saka ta fita da sauri bedroom ta shiga, a yashe ta samu jummo a ƙasan tayels sai bacci take murmushi Aunty Zarah tayi tare da furta.
" Allah Sarki ta gaji da jirana har bacci ya ɗauketa" sunkuyawa Aunty Zarah tayi a hankali ta dinga tashin Jummo harta buɗe idanunta.
" Haba Jummo ganan gado me zai kwantar dake a ƙasan tayels wannan sanyin ai sai ya cutar dake, karki kuma Kwanciya a wajen baki ga A'illo tazo ta ajiye kayanta a gadon ba, nan shine ɗakin ku keda ita akwai ƙanwata da take zuwa ita ma a nan take sauƙa, Kiyi na barki kina ta jirana ko, Ya khalil ya sani aiki, yanzu kin san me za'ayi jekiyi alwala tunda kinji ana kiran sallah idan kinyi alwalar sai na miki kwalliyar sai kiyi sallar ki hankalinki kwance."
Ta ƙarisa Maganar tana zama bakin bed ɗin, Jummo da to ta amsa tana shigewa tolet ɗin, alwala ta ɗauro sannan ta fito, Aunty Zarah ta tsara mata kwalliya sosai Jummo tayi kyau bana wasa ba, doguwar rigar ta zauna a jikinta kasancewar Jummo ba dai dukiyar fulani ba, dariya Zarah tayi tare da cewa.
" Wow hajiya Jummo kinga kuwa yanda kikayi kyau anya kuwa bazan yiwa mijina kamu ba, kalli madubi kiga."
Madubin Jummo ta kalla tana dariya tace.
" Aradu nayi kyau Aunty, to Aunty zaki dinga min kwalliyar kullum."
Dariya Aunty Zarah tayi tare jan kumatun Jummo tace.
" Me zai hana, miki kai insha Allah ma tunda kina son kwalliya zan kaiki shagon makeup ki koya yanda zaki dinga yi da kanki ba sai na miki ba, yanzu dai je kiyi Sallah an shiga Masallaci, nima bari naje nayi sai na fito na shiga kitchen ko"
Da to Jummo ta amsa tana dariya ta ɗauki darduma ta hau Sallah, ita kuma Aunty Zarah ta fice nata bedroom ɗin.
✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Can kuwa masallaci khalil tare sukayi Sallah da Daddy kasancewar ya dawo ana kiran sallah parking kawai yayi ya shiga Masallaci, bayan an idar da Sallah ne khalil ya yiwa Daddy sannu da dawowa, fuskar Daddy cike da murmushi ya amsa yana kallon Garko dake tsaye ya zuba hanu a aljihunsa, murmushi Daddy yayi yace.
" Kai Garko ina sakon dana aikeka wajen Alhaji Isma'il?"
" Daddy naje ban samesa ba, still na dawo kasuwa wajenka Sadiq yace min ka fita."
" Okay mu ƙarisa cikin gidan."
Tare suka shiga cikin gidan da Daddy, da sallama suka shiga falon, muryar Mamma itace ta fara amsawa Daddy, sallama, shi kuwa khalil idanunsa ne suka sauƙa akan Jummo da tayi bala'in kyau tamkar ba wannan ƴar ƙauyen da suka zo da Mamma ba, wani bugawa zuciyarsa tayi, yayi saurin dafe ƙirjinsa tare da runtse idanunsa, shikam Garko baima lura da Jummo sam hankalinsa baizo wajen ba, waya ma yake da abokinsa Hashim, daddy waro ido yayi cike da farin cikin ganin Mamma ya ƙariso gabanta ya zauna a ƙasa gefen kujerar da take zaune.
" Mamma kece yau a gidan nan, sannu da zuwa, sannu da hanya, wa ya kawo ki Mamma."
Fashewa Mamma tayi da kuka tare da kaikaicewa ta fara masifa tana kuka.
" Buba ɗazu Tasiu ya kawoni nace ya dawo dani gidan ka na ƙarisa rayuwata anan nida jikokina, amma tsabar walaƙanci