Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

wacce aka yimata takwara da bilkisu, dauka tayi cikeda farin ciki domin goggo bilki halinta daban yake tafi iyallo kula da faran faran,

Har yafito daga wankan waya takeyi, tagaisa da wancan ta gaisa da wancan, kayanshi ya dauka yakoma toilet zuwa can yafito yana rataye kayan da ya cire saman kofar toilet din, cumb yadauka yagyara sumarsa sannan yajuya yana kallonta lokacin da yake kokarin shafa turaren amirul hub, ido suka hada ta wani janye nata cikeda sigar harara yana jinta lokacin da tagama wayar,

Zama yazo yayi gefen katifar domin saka sabuwar bakar safar dake hannunshi,

"Hajjaju kin tashi lafiya?"

"Alhamdulillah..."

"Ya bakunta?"

"Lafiya"

Murmushi yayi ya kalleta,

"Bari naje nakarbo miki breakfast anjima sai na rakaki kishiga cikin gidan ku gaisa dasu"

Jijjiga kai kawai tayi amma bata yi magana ba hakan yabashi damar mikewa yafita, yana shiga cikin gidan masu tsokanarshi suka fara suna fadin,

"Ga ango ga ango..."

Su Mariya kuwa rugowa sukayi suka rirrike hannunshi,

"Ya fahad muje mugaida Anty yanzu?"

"A'a Mariya ba yanzu ba, yanzu hutawa take zan kai mata abinci taci idan tagama zata shigo ku ganta"

Dakin ayiyah ya furmutsa yashiga duk da dakin tafare yake da baki amma haka ya tsattsallakesu ya isa gareta, cikeda farin ciki ta amsa gaisuwarsa sannan tace yaje yasamu yaya asabe yakarbi abincin karin kumallon bilkisu, fita yayi bai tsaya jin dan bikin da abokan wasa keyi masa ba wadanda ke cikin dakin, wurinsu anty fauzy yaje suna zazzaune kofar kitchen suna dama kunun farar shinkafa can gefe daya kuma masu suyar fanke nayi ga kosai shima anata sakawa,

"Ah kaga shalelen ayiyah ango..."

Dariya yayi yaduka agabansu yana cewa,

"Kai yaya asabe bari kiran angon nan dan Allah"

"To ya kwanan amarya?"

"Tana nan lafiya, yanzu ma abincin ta nazo karba"

"Dakyau ango mijin amarya..."

Mikewa yayi tsaye yana kallon anty Fauzy wacce rufe bakinta kenan,

"Anty fauziyya kema haka zakice? Shikenan bani abincin natafi"

"Za abaka ai daina gaggauta, da alama gaba daya hankalinka na can..." Anty juwairiyya dake cikin kitchen itada anty kubra tafada tana dariya, shi sam baima gansu ba wallahi sai yanzu ashe suna ciki suna hadawa amarya breakfast,

"Ohh God....,ashe yan sa ido ana ciki..."

"Mudai ga abincin amaryarka sai ka sakar mana Mara muyi fitsari" Anty kubra tafada lokacin da take fiffito masa da abincin, kayan sunyi masa yawa dole sai su mariya yakira suka tayashi dauka domin bazai yuyu yadauka shi kadai ba, har cikin dakin suka kai masa abin mamaki sai yaga bilkisu ta sake dasu sosai harda cemusu su zauna suci abincin tare, harara ya zabga musu babu shiri suka fice simi simi, tabe baki tayi tagyara kishingidar da tayi, shi wallahi wannan mulkin nata dariya yake bashi, abubuwan da aka girka yafara dubawa, chips ne aka yimasa wani hadi na musamman da dan salad sai farfesun kayan cikin saniya sai bread da ruwan zafi,

"Ranki yadade ga abincin... Bismillah"

"Ok..."

A flate daya ya zuba musu komai yasa fork yafara ci, wayarshi ce ta katse masa hanzari, husnah ce bai san lokacin da ya girgiza kai ba yace,

"Allah sarki husnah bakiyi fushi ba?"

"A'a prince banyiba, angama biki lafiya? Allah sanya alkhairi yabada zaman lafiya agaida min da ita"

Jin abinda husna tace sai tausayinta yasake kamashi bai san da biyu ta kirashi ba dan saida kawayenta suka tirsasata sukace tayi masa kirsa irinta mata ta nuna bata dauki auren da yayi da zafiba karta nuna masa komai amma da zarar burinta yacika ta nuna musu tafisu iya wulakanci, wannan dalilinne yasata dannar zuciyarta ta kirashi amma fa can kasan ranta kishine fal dankare da tsanar bilkisu wadda bata ma san da ita ba,

"Amin husnah nagode sosai..."

"Babu komai Prince ai kafi haka agareni"

Ita dai bilkisu kallonshi ta tsaya tanayi yayinda shikuma keta yiwa husna godiya, cin abincin shi yaci gaba dayi zuwa can wayarshi tasake yin kara ya dauka yana dariya bayan yasaka a hands free,

"Kai gwauro ya akayi...?" Yafada yana dariyar shakiyanci, daga can bangaren salim yace,

"Malam wallahi yau kasan wanda zaiyi maka gadin gidanka nidai nagaji tahowa zanyi"

"Karka damu yau masu gidanne zasu kwana aciki, insha Allah yau anan zamu kwana kai kuma kaje ka karata da tsohuwar katifarka..."

"Ohh hakama zakace? To babu komai ai akwai gaba..."

"Wasa nake abokina... Yanzu kadan bada jimawa ba za akawo muku breakfast kaida babban yaya, dan Allah amika min gaisuwa"

Kit yakashe wayar yana yiwa salim dariyar shakiyanci, ita kallonshi ma kawai ta tsaya tana yi tana mamakin yanda yake da bakin tsiya,

"Hajjaju ya akayi ne? Nace kizo kici abinci kin ki ban saniba ko kina jin nauyina ne, amma ai ko za ayi fulako bai cancanta ayiwa mijiba domin shi sirrinka ne...."

Wani kallo tayi masa wanda ita kadai tasan ma'anarsa,

"Miji...? Miji kuma?"

Tsayawa yayi da cin abincin da yakeyi ya kalleta,

"Ina da wani sunanne da wuce wannan awurinki? Duniya da sauran jama'ar cikinta sun gama shaidawa ni fahad mijinki ne asalima harda sadaki na baki naira dubu talatin lakadan ba ajalan ba right....?"

"To ko in dawo maka da abinka?"

Girgiza kanshi yayi ya langabe kai yaci gaba da cin abincinshi,

"A'a, ni ai ban baki dan kisake dawo min dashi ba ranki yadade..."

Shiru tayi taci gaba da danne dannen wayar da takeyi tun dazu, zuwa can yasake kallonta yace,

"Kefa nake jira ki karya mu fita, dagaske yau zamu bar gidan nan mukoma namu..."

Tsam ta tsaya da abinda takeyi itama takai kallonta gareshi,

"To yanzu idan nashiga ciki me zanyi? Kasan dai ni ba sanin al'adarku nayi ba..."

"Karki damu zaki sani sannu ahankali"

"Dan rainin wayo...." Tafada acikin ranta sannan ta ajiye wayar hannunta ta janye flate din gabanshi zuwa gabanta ta dauki fork tasoma ci, kallonta yatsaya yi kafin ya nisa,

"Ranki yadade ai ba koshi nayiba..."

"Duk abincin da kaci daga daren jiya zuwa yanzu?"

"To ai na kwana biyu rabona da abinci fa"

Kafada ta daga,baiyi kasa agwiwa ba yasake mayar da nasa cokalin cikin flate din yaci gaba da ci atakaice dai shi yaci fiyeda rabin abincin, yarigata tashi dan haka yasake kintsawa sosai yasha hula sai kamshi yake, abokanshi sai kiranshi sukeyi awaya ana tayashi murna da fatan alkhairi, hannayensa duka biyu ya zuba cikin aljihun rigarshi yana zagaye dakin yana jiranta tagama, saida tagama jan ajinta da shan kamshinta sannan ta mike bayan tasake gyara fuskarta sosai,turare tasake fesawa jikinta sannan ta dauki babban mayafi tayafa tarufe fuskarta, dariya yafarayi ahankali wayarta kawai ta dauka amma yace mata,

"Da dai kin dauki handbag din naki da zaifi..."

Batare da tace komai ba ta dauka tafita, rufe dakin yayi sannan suka nufi cikin gidan ai tana jiyo hayaniyar mutane tayi azamar sake lullube fuskarta saura kadan tayi karo da itacen da aka girke domin dafa sanwa, hannunta yayi saurin rikowa dama tun adaren jiya yake da wannan burin sakamakon tafiya da hankalinshi da kunshinta yayi, babu damar yin musu domin bata ganin gabanta sosai kanta akasa yake sannan mayafin mai duhune sosai, har dakin ayiyah ya shigar da ita ya zaunar da ita nan fa aka shiga zuba guda ana shewa, shidai ficewa yayi yabar dakin duk kuma sai taji wani iri wato wurima da wanda kasani dadi gareshi amma idan akace baka san kowaba to baka iya sakewa, tana jiyoshi atsakar gida suna yarawa da kakanninsa wato abokan wasanshi yana cemusu,

"Ni duk kunyi min tsufa, ga matata can duk tafiku kyau kuje ku ganta gyalenta kadai ya isa ya siyeku gaba daya...."

Daga haka yagudu bata sake juyo maganarshi ba, duk kuma sai tashiga kadaici danma anata zuwa gaisheta kamar wata sarauniya, tana zaune shiru shiru sa'arta daya Maryam da Mariya na kewaye da ita nan tayi masa text massage tana daga tukunkune cikin mayafi,

_Wai kana inane?_

Babu jimawa saiga reply yadawo mata dashi,

_Ina zuwa nan bada jimawa ba._

Zaman shiru taci gaba dayi sai dai idan ankirata awaya ta daga amma tana jiyo hirar mutane awaje group group. Wurin sha daya da wani abu tafara jiyo guda sosai da karfi aifa nan mata aka kifa kwarya ana kida mai dadi wasu kuma na rera wakar aure,

Wasa wasa gudar nan har cikin dakin da take ta cikin mayafin ta samu nasarar hangoshi sanye da babbar riga da hula, har inda take yatako yazo ya dagata, tsakar gida suka fita inda ake yin wannan kidan, daya bayan daya ake zuwa ana zuba musu kudi shi sai asaka masa acikin aljihunshi ita kuma cikin jakarta, sunfi minti talatin tsaye ana zuwa zuba musu kudin nan ita har tagama kosawa da wannan tsaiwar danma jingine take jikinsa amma babu wanda zai gane, saida kaf dangi na uwa da na uba suka gama zuba musu kudin sannan aka maida ita daki, shi kam ficewa yayi bata kara jin alamunshi ba har azahar lokacin ne kuma aka maida ita dakinshi dake can soro wai tayi salla taci abinci, kamar kuwa sun san tana da bukatar komawa dakin domin amatse take da ta canja pad din jikinta dan ita atabar pad tadade ajikinta to tayi awa uku,neat tasamu dakin anshare angyarashi an fitar da kwanukan abincin daren jiya ankunna turaren wuta na tsinke.

Bayan su anty juwairiyya da suka rakota sun fita wanka tashiga tayishi sauri sauri tafito dan kar wani yashigo ai kuwa tana fitowa tana kokarin manna pad jikin pant dinta yashigo, danma lullube take da mayafi, bai kalleta ba yawuce gaban akwatinshi sannan ya janyo kayanshi dake rataye jikin kofa yasaka cikin akwatin, kasa saka pant din tayi agabanshi sai bathroom tawuce tasaka sannan tafito lokacin yana rufe akwatin,

"Ranki yadade kiyi sauri ki shirya yanzu za akawo miki abinci...."

Bai karasa rufe bakinsa ba yaji knocking abakin kofa, tashi yayi daga gaban akwatin,

"Inajin ma gashi nan ankawo... Bari mugani"

Kofar yabude yafita ai kuwa su mariyane dauke da kwanukan abinci, karbowa yayi yashigo dashi lokacin tana saka bangles, ajiye mata yayi yajuya ya dauko wasu kayanshi dake kan drewar din dakin,

"To hajjaju nabarki lafiya, sai mun hadu a sabon gida..."

Zama tayi tana kallonshi,

"Ban ganeba, wai kana nufin ni kadai zan zauna adakin nan shiru har lokacin da za araka ni gidanka?"

Murmushi yayi,

"Ehh mana, kodai kinfi son nazauna mu zauna tare? Kibari zan turo miki su Mariya suzo su tayaki zama"

Daga haka yadauki kayanshi har katuwar akwatin yafice, bai jima da fita ba sai gasu mariya sunzo ai kuwa tasha hira domin yaran sunada surutu shiyasa taji dadin zama dasu inbanda labarin gidan da na makaranta ba abinda suke bata. Har la'asar tana tare da yaran amma mutane na dan shigowa musamman baki masu tafiya suna yimata sallama da fatan alkhairi shiyasa zuwa karfe biyar na yamma gidan tsit sai mutane kadan na kusa amma bakin nesa kam duk sun tafi, bayan sallar magrib su anty Fauzy suka zo suka shigar da ita cikin gida lokacin ma baba yadawo har turakarsa suka kaita ta gaidashi sannan aka maida ita dakin ayiyah, ayiyah kam sai nan nan take da suruka matar auta guda komai tagani ta tura mata gabanta da haka har motar daukarta tazo, anty Fauzy da anty Kubra ne zasu rakata, daki daki aka bi da ita tayiwa kowa sallama sannan aka fita da ita bayan anfitar da kayanta,Baffa ne yayan salim a motarshi shi yadaukesu yakaisu wanda tafiyar bata da wani tazara sosai can, koda sukaje su basu wani jimaba suka yimata sallama suka fita, hamdala tayi acikin zuciyarta ta bude fuskarta tana bin dakinta da kallo wanda yasha kayan alatu domin gadonta kadai abin kallone gashi dakin babu laifi da girmanshi saboda ya cinye komai dan iya mirror dinta kadai duniyane wurin da ya lashe ba dan kadan bane cire mayafin tayi ta fita falo wanda shima ba laifi ga dining area taciki ga kitchen nan ga store cikeda kayan abinci domin komai biyar biyar abba yayi mata kama tun daga kan shinkafa, taliya, macaroni, indomie, crate din kwai,semovita manja, man gyada komai biyar,

Ba karya gidan fahad yayi domin yarone mai zuciya shi dai barshi da kwalisa da iyayi amma yanada zuciyar neman na kanshi duk da baiyi karatu mai zurfi ba domin iyakacinshi diploma kawai sai sana'ar dinki da yasaka agaba kuma yayi sa'a sana'ar ta karbeshi, iyakar gata tasan iyayenta sun nuna mata domin komai mai kyau da tsada aka yimata ita kanta gidan ya burgeta dan dagwas dashi shi ba kato can ba kuma shi ba karami can ba abinta dai dai misali, tsakar gidan dan madaidaicine yasha interlocks harda flowers shuke sai pop shikenan sai kofar falo ma'ana dai safe content ne komai aciki, abu dayane yabata takaici bedroom guda daya zasuyi shearing tunda ga dayannan ba agama ba asalima data buda ko fulasta ba ayiba sai uban tarkacen kayan aikin gidan da aka zuba aciki aka rufe, alhalin gado guda biyu abba yasai mata kamar sauran yan uwanta gashi karshenta sai dai komawa akayi dashi gida......


*kamar da wasa na kudine idan har kin san baki biyaba dan girman Allah karki karanta.*



*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO*


*KAMAR DA WASA...!*


_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*


*19*



Cikin bedroom dinta takoma ta zage tashiga toilet tayi wanka tafito ta zauna tayi shirin bacci cikin wani night wear milk colour riga da wando,wandon iyakarshi cinya sai rigar da bata wuce cinyaba itama, handbag dinta ta janyo ta debo wayoyinta gaba daya ta kashe sannan ta rufe jakar da kamar ta zauna zaman kirga kudaden dake ciki wadanda aka zuzzuba mata tabari sai zuwa gobe ta kirga domin bacci kawai take ji, kashe wutar dakin tayi tai kwanciyarta bayan ta lulluba domin bata iya kwanciya da kaya ba ajikinta tasan babu mamaki cikin dare idan zafi ya dameta ta fige rigar ma gaba daya. Misalin karfe 10 saura fahad yashigo gidan tareda tawagar abokanshi wadanda suka iyo masa rakiya, key dinshi yadauko yabude gidan yashiga yana jin wani farin ciki na ratsashi, har falo suka shiga danma baiyi garajen kaisu dakiba kamar yasani yace kawai su tafi yasan yanzu tayi bacci amma sukace karyane kawai dai yana yimusu kora da haline, bedroom yawuce yana shiga ya kunna fitila awayarshi ya haska ya kunna wuta, bude ido daya tayi ta kalleshi jikinta lullube da duvet hular kanta ta cire saboda santsi,kitson ya zubawa ido kamar yasamu tv

"Yadai....?" Ta fada tana yamutsa fuska domin ba kadanba sosai tafara jin dadin baccin da ya katse mata ta hanyar kunna wuta itafa duk dadin barci da nisan da yayi matsawar zaka kunna wuta to sai ta tashi,

"Ah babu komai..."

Daga haka yakashe wutar yafita,

"Ai nafada muku dama tayi bacci, yanzu gashinan haka kawai kunsa na tashi baiwar Allah..."

"Dakyau mijin yar gata... Wato ma idan tana bacci ba atashinta" inji hamza na shagonsu, shi dai alla alla yake su tafi domin shima yana son ya kwanta ya huta, ai kuwa sun wahalar dashi kafin su tafi daga karshe daya bayan daya yarinka turasu sannan yamaida kofar gidan yarufe yadawo ciki itama kofar falon yarufe yashiga dakin, wannan karon bai kunna wuta ba kawai da fitilar wayarshi yayi amfani yashiga bathroom bayan yadauki kayan baccinshi, wanka yayi,yana cikin wankan yalura da pad din data jefar cikin dustbin duk da haka bai hakuraba saida ya dauki dustbin din yayi masa kallon kurulla daga karshe dai yagane menene, baki yatabe yasaka rigar baccinshi armless da wandonta duk jajaye, yana rike da kayan da yacire, drewar yabude ya watsa kayan sannan yafita falo dan bazai iya bacciba sai yaci wani abu, balangun da yazo dashi yabude kulli daya yaci yakoshi sannan yasha yoghurt guda daya sauran yasa cikin fridge, dakin yakoma yaje kan gadon yana shirin kwanciya yaji tace,

"Malam yadai?"

"Kamar ya? Kwanciya zanyi mana"

"Bana skwatin, ban iya kwana mutum biyu agado daya ba..."

Da mamaki yake kallonta duk da ba ganinta yakeba tunda dakin akwai duhu,

"Amma dai ai kema kin san gadon nan yayi miki girma ke kadai...."

"Dagaske fa nakeyi, dan naga kamar kai kadauki abin dawasa..., ga spare mattress nan kadauka sannan kaduba cikin drewar akwai sabbin bedsheets da blankets idan kana da bukata...and lastly ka kashe wannan hasken domin bana bacci da haske akaina" Daga haka tamaida kanta ta gyara kwanciyarta, fasa kwanciyar yayi ya nufi drewar yabude yadauki duk abinda zai bukata yana kunkuni, pillow yazo yadauka guda daya yayi hanyar falo yana cigaba da kunkuninsa,

"Amma bar miki dakin gaba daya kije ki cinye..... Nima bana bacci aduhu.....haka kawai dan takura zaki wanice ke kadai zaki kwanta akan gado...."

Katifar yadawo yadauka yaje yayi shimfidarshi afalo sannan yasake dawowa dakin, wannan karon wuta ya kunna dan neman magana,

"Me kuma yafaru?"

Tafada tana bude ido dakyar dan bacci,

"Sucket nake nema zan saka charge"

"Acan inda zaka kwanta din babune? Pls malam kashe min wuta bacci zanyi..."

"Ehhh ai dai kin tashi...."

Yafada cikin kunkuni yanda bazata jiba, wutar yakashe yafita yana ja mata kofa dama babu wani charge da zai saka kawai son yatasheta ne yasashi kunna wuta, akusada doguwar kujera ya shimfida katifar tasa ya kwanta yadora kafarsa daya akan kujerar yakunna data awannan daren yashiga instagram daga can yafita yakoma Facebook, bashi ya hakura ba sai wurin daya da rabi a lokacin yaji bacci yaci karfinshi, ajiye wayar yayi bayan yakashe yayi addu'a babu jimawa sai bacci. Daf da asubah yatashi saboda fitsarin da ya takurashi kusan ma shine yatasheshi, bedroom yashiga mutuniyar tasa tana tukunkune sanyin asubah da na fanka na kadata duk ta takure wuri daya, fankar yarage mata sannan yashiga bathroom din yayi abinda zaiyi yafito yakoma falo yayi kwanciyarshi bai kara motsawa ba sai karfe bakwai saura, yana bude ido yakalli agogo gani yayi sun zabga makara gashi ko salla baiyi ba, bedroom din yanufa kansa tsaye yakama handle yabude tana zaune kan gadon ta ziro kafafunta kasa tana daure kitsonta da tacire ribom din cikin dare batare da ta saniba dan hatta rigarma sai yanzu ta mayar, babu zato taganshi yashigo cikin azama ta yayibi duvet tarufe jikinta tana kallonshi,

"Meye haka? Ya zaka shigo min daki batare da taking excuse ba....."

"Yi hakuri..." Daga haka yawuce zai shiga bathroom,kunkunin nasa yasoma yi shi kadai,

"Haka kawai kin saka mutane sun makara sallar asubah dan kawai kin san ke bayi zakiyi ba....."

"Magana kakeyi ne?"

"A'a..." Daga haka yafada toilet yayi alwala yafito bayan yayi brush, tana sanye da hijab har kasa da towel daure ajikinta tana gyara kan gadon, dan tabe baki yayi ya dauki rug din salla ya shimfida yatada salla, ita kuwa saida tagyare kan gadon tsaf sannan tawuce toilet domin yin wanka da kallo yabita sannan yamaida kallonshi saman gadon cikin kunkuni yace,

"Gashi dai mun dawo daya dake da kika kwana wajen kwanan mutum biyar da ni da na kwana awurin kwanan mutum biyu..."

Yana kan abin sallar azaune har tafito, handbag dinta ta dauka tanufi drewar tana cemasa,

"Dan bani wuri zan shirya..."

Mikewa yayi baice komai ba yanade prayer rug din ya ajiye saman bedside drewar yafita azuciyarshi yana cewa,

"Oho dai tunda nasan me za ayi har ake wani korata..."

Kwanciyarshi yayi saman doguwar kujera bai san lokacin da wani baccin yasake daukeshi ba. Ita kuwa bayan ta shirya wani material ta saka peach tasa sarka da dan kunne golden sannan tasaka abun hannu da agogonta na gold wanda ammah ta siyo mata last year da taje umarah, turarenta na garari na fitina tabi ta bazawa jikinta sannan tafito domin yanzune zata yiwa gidan kallon tsaf kasancewar safiya tayi dan harma rana tafito, fahad tagani kwance yana bacci nan kuma ga shimfidarsa ta daren jiya, tattara komai tayi ta dauke mattress din takai daki tazo ta kwashe sauran suma takai daki sannan tasake fitowa, ta kofar kitchen ta fita baya ta dudduba gidan wanda yake dan cicif sannan tadawo ciki sai lokacin ta lura da buhun Irish potatoes dake jingine acikin kitchen din, dayake anrigada anhada mata cylinder din gas dinta tukwane kawai tafara lalubowa dama cooker gas dinta babu ruwanta da neman ashana wurin kunnashi nan ta kunna ta dora ruwan zafi.

Dankali ta fere wanda zai ishesu su biyu ta soya bayan ta juye ruwan zafin acikin tea flask, da kwai ta hada tayi masa kyakkyawar suya yabada kala mai kyau dama bata da matsalar kayan kamshi da kayan dandano komai gashi nan a ajiye sai dai kawai ta dauka, hatta dakakken yaji gashi nan cikin karamin plastic haka su kuka,daddawa, kubewa etc duk su maama saida suka harhada mata aka dako sannan aka kawo mata, fridge din dake cikin kitchen din taduba kamar tasan yayi ajiya nan taga balangu da yoghurt da kayan marmari danginsu tufa, kankana da ayaba, balangun taciro tasaka acikin oven ta dumama bayan takara masa kayan hadi, saida ta kammala hada abin karyawarta tsaf sannan ta dauko ta kawosu kan dinning mai dauke da kujeru kwaya hudu,kayan tea dinma da alama babu dan haka tafasa shan ruwan zafin taci iya balangunta da chips din data soya. Tana daf da gamawa taga andawo da wuta mikewa tayi tanufi daki domin jona wayarta a charge da alama shima fahad yatashi domin bata ganshi awurin da tabarshi yana bacciba,akan gadonta taganshi yana cigaba da baccinshi,

"Wannan ko yasha wani abune? Bacci yaki karewa? Uhmm"

Ita kadai take maganarta tana kokarin saka wayarta a charge, handbag dinta ta dauko ta zazzage kudin data samu tafara shiryasu domin wasu yan dari darine sabbi fil wasu yan dari bibbiyu wasu kuma yan dari biyar biyar harda yan hamsin hamsin ma, hakura tayi da shiryawar tasake gwamutsasu ta maida cikin handbag din taje ta ajiye tafita falo, daga can tayi waje, flowers din da aka shuka sunyi masifar kyau ga kuma wasu kananan shukoki nan da suka dan fara fitowa kamar bishiya duk da dai bata gane menene ba,abakin slave din pop din kofar falon nasu ta zauna,

Gajiya tayi da zaman wajen tasake diba takoma cikin falon ta zauna, tana nan zaune yafito sanye da blue din shadda yana balle links din hannun rigar,

"Hajjaju barka da safiya?"

"Yawwa, katashi lafiya?"

"Lafiya lau, ya kwanan kadaici?"

Banza tayi dashi tamaida hankalinta kan agogon dake manne jikin bangon falon wanda yake tafkeken gaske mai dauke da hoton abbansu ajiki,

"Babu kayan tea ko? Bari naje nasiyo yanzu"

"Babu amma ai ga breakfast can na hada"

"Haba ranki yadade daga zuwa sai girki? Shikenan godiya nake"

Bai jira cewarta ba yayi dinning area din yazauna yaci abincin yayi dam dan babu abinda yarage yana gamawa yayi mata sallama yafice, wani takaicine kuma yafara ziyartarta shi yayi ficewarsa yanzu hakama gidansu yatafi amma ita gashi nan yabarta agida ita kadai gashi kuma tamanta ta tambayeshi taji ko anhada mata kayan kallonta, daki ta koma ta zare wayarta daga sucket ta kunna data ta fada yanar gizo wai ko zata rage zaman kadaici......


*Book dina na kudine dan Allah idan har baki biyaba karki karanta.*



*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO*


*KAMAR DA WASA...!*


_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*


*20*


***Fahad lokacin da yafita saida yafara zuwa gidansu yagaida su ayiyah yayi musu ban gajiyar biki sannan yawuce kasuwa duk abinda suke bukata na amfanin gida saida yasiyo daga karshe ya iyo cefanenshi na abincin rana ya hado kayan tea sannan yanufi gida, lokacin har bilkisu tagaji da chaten dinma ta kashe data tana kwance tarasa abinda yake yimata dadi, kitchen yakai kayan gaba daya ya ajiye mata sannan yanufi bedroom, akwance yaganta kamar marar lafiya tayi shiru,

"Hajjaju yadai?"

"Yawwa dan Allah wai ba ahada kayan kallon can bane?"

"Anhada mana.... Zo kigani"

Tashi tayi tabishi zuwa falo nan yajona komai saiga tashar mbc Bollywood takawo darr, ajiyar zuciya tasauke harta dan ji dadi ai kalloma ba karamin rage kadaici yakeba, yana debewa mutum kewa sosai sai yau tayarda,

"Ga kaya can a kitchen ni Zan fita.."

"Ina zaka fita? Ni kadai zan zauna agidan? Wallahi a'a kaima neman wuri zakayi mu zauna tare..."

Kujerar dake makotaka da tata yaje ya zauna, yana zama wayarshi na yin kara, cirota yayi yaduba nan yayi dariya ya daga,

"Allah yabar babban yaya, har ka tafi ne?"

Bata jin me ake cewa amma dai taji yace,

"Ehh to shikenan sai kazo"

Saida yakatse wayar sannan yajuya ya kalleta,

"Ya Abba ne wai zai koma school amma zai fara biyowa tanan kugaisa tukunna"

"To babu damuwa Allah yakawoshi lafiya"

Tashi tayi zuwa kitchen tana ware kayan da yakawo wanda zata barsu a kitchen din tabarsu anan wanda zata kai toilet ta kwasa takai sannan kayan tea din kuma takai dining area ta zuba cikin wani glass da aka tanada musammsn domin ajiya,

Saboda taji zaiyi bako shiyasa ta dora girkin da wuri sannan takoma falo ta iskeshi yana kallon spider man atashar mbc max, tana zama sukaji knocking, shine yaje yabude, khulsum ce kawarta bata hanya

Please Login or Register in order to submit comment