Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

saita koreni ai gida yazama nata, ko kuma daga daki kasa akoroni falo"

Dariya sukayi gaba daya, har gida salim yakaishi sannan yatafi shikuma yashiga wurinsu ayiyah domin jin ba'asin kiran da ake yimasa, gyadar yatarar da mamuh na tacewa akwando ta dahu ligif kanfata yayi a cup yawuce falon ayiyah yana ci,

"Ayiyah wannan gyadar badai dadiba ta dahu wallahi"

"To santi kake kenan, yawwa dama maganar sati dayan da amarya zatayi ananne shine nace ai gara kafara tuntubarta tun yanzu dan tasani ko"

Dan jimm yayi, tabbas yasan kam haka al'adarsu ayiyah take yayinsu ma duk da sukayi aure saida matansu sukayi kwanaki bakwai bakwai agidan,

"Idan kuma kana ganin wani za atura babba to sai atura yaje yasanar dasu..."


"A'a ayiyah bari zanje anjima infada mata"

"Yawwa ka kokarta dama shine kiran da nake yimaka"

Saida ya cinye gyadar nan tsaf sannan yatashi yafita, yaci sa'a salim na gida dan haka Babur dinsa yaje yakarba yanufi gidansu bilkisu duk da baida tabbacin ko tana nan, dawowarsu kenan daga kasuwa sun siyo furnitures tana kokarin rage kayan jikinta yakirata yace yana waje, ita wallahi bataso wannan zuwan nashi ba haka dai ta daure ta zura doguwar riga da hijabi tafita....


*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO.*


*KAMAR DA WASA...!*


_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*



*16*


*Littafin kamar da wasa na kudi ne yar uwa idan kinada bukata kibiya ki karanta.*


***Ba dan tanasoba haka ta fito ta sameshi yana compound din gidan tsaye jikin wata bishiya,

"Baby..."

Batare da ta kalleshi tace,

"Yakake?"

"Lafiya lau ranki yadade, ya mutanen gida?"

Atakaice ta amsa da,

"Lafiya"

"Am dama namanta ne ban fada miki wani abuba shine yanzu nazo sanar dake, mu a family dinmu idan anyi aure sai ankai amarya gidansu ango acan za aware mata daki har sai tayi tsawon kwanki bakwai ko wani abu mai kamada haka..."

"Wannan al'adar wanne garine kenan?" Ta tambaya batare data kalleshi ba,

"Fulanin kura..."

"So yanzu dai kana nufin gidanku za akaini acan zan zauna har na tsawon 1 week?"

"Ba lallai yakai hakaba dama kawai al'adace amma yana yuyuwa ma bazaifi 3 days ba ko 2"

Jijjiga kai tayi ta jingina jikin bishiyar flower tana kallon gefe,

"Babu damuwa..., ya maganar dinkuna ne wai? Naji shiru kuma tun ranar fa nayi maka maganar"

"Bani intafi dasu adaren nan zan yanka, abubuwane suka yimin yawa wallahi baby ko bakiga har nayi baki ba na fada...?"

"Bafa na son sunan nan nafada maka, so kadaina"

Murmushi yayi shi wlhi drama din da zasuyi da bilkisu kawai yake hangowa,

"Am sorry bazan sakeba amma seriously na dan rame fa"

"To ya za ayi ai situation ne"

Daga haka tawuce ciki ta dauko masa kayan da zai dinka mata takoma wurinsa,yana tsaye a inda tabarshi yana yin waya ganin tana jiranshi yakatse wayar yamaida hankalinsa gareta,

"Gashi duk riga da skirt zaka yimin..."

"Banda doguwar riga?"

"To Kaduba dai kagani idan akwai wanda zaiyi kyau da doguwar rigar sai kayi min"

"Shikenan to, kigaida su ammah"

"Zasuji"

Fita yayi yatafi ita kuma takoma ciki wurin khulsum wacce ke jiranta tayi wanka su fita gidan da za ayi mata gyaran jiki saboda yau za afara.

Cikin kwana biyu yagama dinkunan bilkisu kala takwas ne shadda guda biyu leshi guda biyu sai material da atamfa suma duk kala bibbiyu amma abinda yabashi mamaki duk cikin kayan babu na cikin lefenshi wanda yasaka amma bai kawo komai aranshi ba tunda watakila wannan din agidansu aka yimata, bai samu damar Kai mata kayan da kansa ba sai salim ne yakai saboda shi ranar yana can gidanshi ana saka masa tile da sauran abubuwan da ba akarasa ba, washe gari aka karasa komai na gidan akayi fenti gida yafito rangadau dama unguwar shiru take babu gidaje da yawa ma domin sabuwar unguwace bata fara yawaba, agajiye yakoma gida bayan sallar ishah wanka kawai yayi ya kwanta ko abinci bai nema ba babu bata lokaci baccin gajiya yace muje zuwa, koda Abba yashigo yaganshi baje yana bacci dariya yayi yace,

"Dole kayi bacci ango, irin wannan commitment Haka?"

Dasafe garau yatashi sakamakon baccin da yasha sosai adaren jiya, miss called din bilkisu yagani har guda uku hakan yabashi tabbacin akwai dalili shiyasa yayi gaggawar calling dinta back,

"Fahad dakuna nawane agidan, kofofi nawane sannan windows nawane? Muna wurin masu dinka cuttens ne"

"To hajjaju bari naturo miki gaba daya pics din gidan ki ganshi"

"Yawwa dan Allah hanzarta"

Katse wayar tayi nan yashiga whatsapp yatura mata aranshi yana cewa,

"Akwai rikici nasani"

Bai kara jin duriyarta ba sai text tamishi akan yabasu keys din gidan saboda masu zuwa jeren kaya gobe nanma aiken yayi mata aka kai musu, sai ana igobe kamu ta kirashi tana yimishi maganar itafa baza suje wata dinner ba walima kadai zatayi da friends dinta dan haka shima ya hada reception da friends dinshi kawai ya isa, tayi hakane saboda kunyar yaje dinner mutane su ganshi take,bai musa ba yace to.

Tana zaune tayi uban tagumi bayan mai kunshi tagama yarfa mata jan lalle da baki, khulsum tashigo agajiye itama daga kunshin take, zama tayi kusa da bilkisu wacce ke kallon masu shigowa da masu fita tayi tagumi,

"Wallahi fahad dinnan yayi yaro da yawa, Allah mai yadda yaso..."

Dariya khulsum tayi,

"Baiwar Allah ki rungumi kaddara kiyi hakuri, haka Allah yashirya ko jinjirine dai shine mijinki uban yayanki..."

"Tab.... Allah ya kiyaye, nifa wallahi baki ma san wani abuba, kunyar nunashi nake a matsayin mijina"

"Sai kiyi kuma malama, wai inasu maama?"

"Suna can gidanshi karasa jere"

"Gidanki dai, kyace wani gidanshi"

"Kinga malama ni idan kina tashi kitashi mutafi kitson nan idan kuma baki zuwa ki sanar dani"

"Ahh kinga karki fada min bak'a, shirya muje amma wallahi da retouching kikayi zaifi kitson nan, kinga kanki yanzu fa kullum sai yaji ruwa"

"Kanki akeji, ni tashi mutafi dan bamuda lokaci"

Hijabinta tasaka har kasa suka tafi bayan tayiwa ammah sallama iyallo sai jaraba take wai yakamata ta daina fita hakanan amma tunda tazo gidannan bataga ta yini agida batare da ta fita ba, batace komai ba tabi khulsum suka tafi,

"Shagon ma da babu wani nisa nan bayane fa amma shine iyallo sai tayiwa mutane ihu aka, kai Allah yakyauta"

"Ai keda iyallon nan taku kuna sani nishadi wallahi, gaskiya i have been missing my grandma"

Dariya bilkisu tayi,

"Uhm ai iyallo bata haduba sam wallahi, hajjaye kakarmu ta wurin uwa tafi kirki"

"Kya hadu da Abba wallahi"

"Bawani nahadu da abba ai gaskiyace"

Har sukaje shagon hirar iyallo suke yi. Kitso hadadde aka yarfawa bilkisu dan har la'asar lis suna shagon ita kuma khulsum akayi mata retouching, tun suna hanya taga su meenah nata kiranta, koda tashigo gida suma suna gidan ana yimusu kunshi har angama musu yanzu hindu ake yiwa itama ankusa gamawa,

"Wai wai wai... Gaskiya yakamata yaya fahad yaga wannan kitson da lallen" inji Hindu bayan bilkisu tacire hijab din kanta,

"To ke gaggawar me kike ko kin mantane nanda jibi suna jone ana..." Maama tafada cikin shakiyanci, tun kafin tarufe bakinta bilkisu takai mata duka ta gudu,

"Allah adda labour idan ya fahad yaga kunshin nan da kitson nan zaucewa kawaine bazai yiba" meenah itama ta karbi zancen,

"Wai dama haka kuke bakuda kunya?" Khulsum tafada tana rike haba,

"A'a wallahi Anty khulsum ai kin san Adda labour kakarmu ce fa dole mu rinka janta" inji meenah,

"Adda mai gado ki fada masa angama komai yatura wadanda zasu jire gidan saboda anjima suma su yafendon zasu taho"

Bata tanka ba takarasa shiga cikin daki wanda yanzu kayan ciki suka zama sai saura domin duk su maama sun shirge mata kayanta sunyi mata gaba dashi sai wanda zata nema kawai aka bari, zama tayi gefen gadonta tana kallon tv domin wani Indian film ake haskawa atashar MBC Bollywood mai suna a gentleman, wayar fahad takira ringing biyu yadauka,

"Ranki yadade..."

"Am yawwa kaga angama jeren nanne shine zan fada maka katura wasu sai su kwana agidan"

"Angama ranki yadade"

Katse wayar tayi tamike tafita waje wurinsu khulsum. Kamar yadda yafada da daddare su salim da Abba ya tura domin su kwana agidan,lokacin da zasu tafi jan salim yayi yace masa,

"Allah karku kwanta mana agado kasan dai babu kyau..."

Dariya salim yayi yakai masa duka,

"Allah ko fitsararre? To ai ya Abba yadace ka fadawa tunda shine babba amma baniba"

"Shi ai nasan bazaiyi hakaba sai kai...."

"To kuwa kwana bisa gadonku daram..."

"Wallahi karka kuskura..."

"Sai kayi kuma...."

Daga haka yayi gaba abinshi, fahad kam neman wuri yayi ya zauna nan kofar gida domin cikin gidan cike yake da mata yan uwa da abokan arziki, saida yakira bilkisu yasanar da ita yatura wadanda zasu yi gadin gidan sannan hankalinta ya kwanta.

Washe gari da shirye shirye aka tashi kasancewar ranar za ayi kamu, kuma anan compound din gidan za ayi kamun domin ita bata da ra'ayin zuwa hall, kowa kagani acikin hidima yake fuskarsa dauke da farin ciki ba ma kamar ya mahaifiyarta ammah wacce ke jin kamar ancire mata k'aya, yanzu kam tasan zasu huta da wadannan maganganun da habaice habaicen da ake yimusu acikin dangi, mutane sukan manta da cewa Allah shine gwani wurin iya tsara komai na rayuwar bayinsa kuma duk yanda ya tsara to hakance zata faru ko anaso ko ba aso, ko anshirya ko ba ashirya ba. Su meenah dai ana can wurin masu decoration ana nuna musu muhallin da yadace asaka kowacce kwalliya domin gudun kuskure, amarya fa? Ana can daki tareda bakinta wadanda suka zazzo daga sassa daban daban na jihar Kano musamman ma wadanda sukayi secondary school tare da wadanda sukayi Jami'a shiyasa itama yau tasamu nasarar warewa ta cika da farin ciki saboda ganin wadanda tajima bata ganiba amma da har masifa tayiwa khulsum lokacin da ta turawa class mates dinsu invitation card ta group chat dinsu dake Facebook da whatsapp tana cemusu ga labour prefect dinsu fa zatayi aure dan haka su daura damarar zuwa shan shagali, ai kuwa sunyi mata kara domin kusan duk wadanda ke zaune acikin kano sunzo,anyi bushasha babu laifi domin chicken pepe da lafiyayyar fried rice aka dafo aka kawowa friends din nasu wanda wannan yana daya daga cikin gudunmawar khulsum banda kayan sanyaya makoshi cikin manya manyan kuloli, ba karamin kyau amarya tayiba tun kafin tayi shirin zuwa wurin kamu, karfe uku tayi wanka da ruwan lalle da turare, tana yin sallar la'asar kuma mai kwalliya tafara aikinta, wanda suka dauki tsawon lokaci sunayi,

"Masha Allah...masha Allah" shine abinda kowa ke fadi lokacin da amarya tafito domin ba karamin kyau tayi ba, tayi kyau na bugawa ajarida, komai na jikinta golden colour ne kama tun daga material din jikinta wanda akayi kyakkyawar doguwar riga irinta amare zuwa head din dake nade akanta da takalminta,pose da komai da amarya ke sakawa har sarka da dan kunne, kidanta daban aka saka mata lokacin da ta karasa wurin khulsum na rike da hannunta, fuskarta abude take amma da akwai wani net me kyau akanta, kujerar da aka tanada musamman dominta taje ta zauna babu bata lokaci aka fara gudanar da abinda yadace daidai lokacin dangin ango suka karaso nan aka tarbesu aka basu wurin zama suka zazzauna. Babu karya kamun yayi kyau domin babu tarkacen shirme aciki kawai dan abinda ba arasa ba aka gudanar daga nan su iyallo suka zo suka sakawa amarya lalle lokacin magriba takusa, dangin ango basu tafiba saida aka gama komai, suka daddauki pics da amarya da danginta sannan suka tafi bayan anware musu manyan jakunkunan da aka rarraba awurin. Ango kuwa yana can gidansu salim adakinsu amma yana ganin duk abinda yake faruwa awurin kamun domin yatura mutane biyu daya zaiyi video coverage dayan kuma zai rinka turo masa ta whatsapp, hakance kuwa tafaru domin komai kamar akan idonsa akeyi....


*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO.*


*KAMAR DA WASA....!*


_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*



*17*


*Kamar da wasa na saidawa ne yar uwa idan kinada bukata kisiya sai ki karanta.*

***Ba karamin kyau tayi masa ba, yau sai yaga tafi koyaushe kyau kamar zaka saceta ka gudu ko kuma ko dan bai taba ganinta cikin kwalliya kamar haka bane shiyasa yau yaga kamar canjata akayi? Kunshin dake hannunta yaketa zooming yana kallo sannan yakoma kan fuskarta itama yarinka zooming dinta yana gani,dariyar shakiyanci yayi lokacin da ya kurawa kirjinta ido bayan yayi zooming,

"Aita boye abu ayita boye abu to yau dai gashi ina kallo..."

Saida yagama ganin komai sannan yatashi yafita sallar magrib bayan ya kullewa salim dakinshi, daga can gidansu yawuce alla alla yake yi gobe tayi adaura aurensu da bilkisu shiyasa a wannan daren baccinshi rabi da rabine yayinda ita kuma amaryar ma gaba daya daren ranar kasa bacci tayi kwata kwata bare gashi bata salla balle tatashi tayi sallar nafila ko tarage damuwa shiyasa abun yayi mata yawa, juyi kawai tai tayi danma da alama agidan ba ita kadaici bata yi baccin ba domin tana jiyo kannen ammah sunata shan hira da yan garko awannan tsohon daren, sai daf da asubah tasamu bacci ya dauketa,wurin 6 da wani abu tatashi tayi wanka tashirya cikin daya daga cikin dinkin da fahad yayi mata,yake kawai takeyi amma zuciyarta cike take da damuwa da bacin rai, gashi ta kasa cin komai sai ruwan lipton kadai da tasha. Fahad kuwa tun asussubah yatashi dama bacci sama sama yayi shi, karfe tara zasu tafi garin garko inda acanne za adaura auren, kamar bilkisu shima kasa cin komai yayi dakyar ayiyah ta tirsasashi yasha ruwan koko daga nan wanka yayi, tun yana cikin toilet din yasoma jiyo hayaniyar mutane yan zuwa daurin aure domin kofar gidansu ne m point din, yana fitowa babu bata lokaci yazuba sabuwar farar shaddarsa harda babbar riga yasha turare, kai wannan ango yasha kyau gaskiya domin ba karamin fitowa yayiba fess, koda yafito kansa har wani sara masa yayi saboda al'ummar da yagani, abokanshi ne, yan shagonsu, abokan yayyenshi, yan uwa da yan unguwa ga uban tarin motoci jere reras, salim ne yakama hannunshi sukaje har gaban motar da zai shiga suka shiga nan kowa yashiga dama su baba sunyi gaba nan suma suka dauki hanya, haka kawai garin yayiwa fahad kyau bama shi kadai ba kusan kowa da wannan shine zuwansa nafarko garin ya burgeshi, babban masallacin garin acanne za adaura auren bayan an idar da sallar juma'a,

Bilkisu tana can gabanta sai faduwa yake wanda bata san dalili ba sai dai tana danganta hakan da wannan auren da za adaura mata shi yau gashi kuma ayau din za akaita gidansu fahad domin yau ammah ke gudanar da yininta shiyasa su maama sun kammala kintsa mata kayanta gaba daya hatta wanda zata tafi dasu gidansu fahad an shirya mata cikin daya daga akwatinta na lefe. Ana idar da sallar juma'a aka daura auren fahad da bilkisu akan sadaki naira dubu talatin,bayan an gama daurin auren sun daddauki hotuna suka dawo, direct gidansu bilkisu suka wuce lokacin tasake wanka tashirya cikin leshi riga da skirt,tun kafin tafito su meenah suka rigata sukaje sunata hotuna da ango da abokansa,ita kam adole tafita itada khulsum bayan angama yimata kwalliya,

Kasa kasa take kallonshi tana son taga koda gaskene yayi kyau din kamar yadda taji su hindu nata zuzutawa, babu laifi kam yafito sosai,shima anasa bangaren tunda ya hangota hankalinsa yayi kaura daga gareshi yakoma kanta saboda ta hadu iya haduwa shiyasa har dana sanin kwaso abokansa suzo ganinta yayi, wani kishine ke lullube zuciyarsa sama sama duk abinda yakeyi idonshi na kanta, saida suka gama yin hotuna da mutane sannan yamatso wurinta nan fa kowa yarude da daukarsu awaya, ita haushima abin yake bata,

"Barka da yau Hajjaju...,ya fama da jama'a?"

"Alhamdulillah"

Shine abinda tafada kawai suka cigaba da hotuna, ana gamawa bilkisu takoma gida, angwaye dai daga can wurin walima suka wuce wadda zasu gabatar afilin makaranta. Bayan su Abba sun dawo kiran bilkisu yayi domin abata sadakinta sannan yakara yimata Nasiha shida waliyyinta, duk saida tabi ta bata kwalliyar fuskarta da hawaye da kuka shiyasa tun daga lokacin ba akara samun kanta ba har dare lokacin da za arakata domin fada ne na iyaye daga wannan yagama sai wannan yazo yayi nasa, ya mudan shima harda zuwa yayi mata nasihar azauna lafiya sannan yabawa maama dubu goma yace abata Allah yasanya alkhairi, tun bayan magriba su khulsum ke binta tatashi tashirya amma taki tashi saida aka fadowa ammah ai iyallo naji tazo tahau fada babu shiri tatashi tashiga bathroom tayi wanka tafito, abinci kam rabonta dashi tun jiya da rana, kayan da zata saka sai faman jikeshi da turare su meenah keyi kamshin har hawa mata kai taji yanayi, hatta pant din da zata saka gani tayi maama na shafeshi da almiski, tabe baki tayi tazauna gefen gado ta bude drewar din gadonta ta dauko pad ta warce pant din a hannun maama azuciyarta tana cewa,

"Yara kwayi kwa gama"

Bra din da zata saka ma itama saida suka tsuma ta da turare daga nan kuma suka dawo kanta itama zasu shafeta da madarar turare, tana ki tana komai saida suka shafa mata sannan tasaka kayanta tanemi wuri ta zauna duk da tanaji ana cewa tafito amma taki koda motsi saida su hajjaye suka zo suka fito da ita, saida aka kaita wurin ammah da abba tayi musu sallama sannan aka fita da ita inda motoci ke jira, kawarta khulsum ce agaba sai su iyallo da suka sakata atsakiya ba awuce dasu ko inaba sai gidansu fahad inda dangi sukayi dafifi suna jiran zuwansu, dakin ayiyah aka kaita tana lullube cikin babban mayafi, saida aka gama yan gaishe gaishe da taya juna murna sannan aka damka amanarta a hannun su ayiyah daga nan yan kawo amarya suka tafi bayan su maama sun shigo mata da akwatinta.

Duk dauriyarta saida tayi hawaye lokacin da taga kowa yatafi anbarta acikin mutanen da bata saniba,mutane sai zuwa ganinta akeyi amma babu Wanda yasamu nasarar ganin fuskarta saboda a lullube take. Har wurin karfe goma saura mutane basu daina shigowa ba sai gajiya su anty Fauziyya sukayi sukace arakata masaukinta ta kwanta ta huta, yaya asabe ce takama hannunta suka fita tarakata dakin dake soro wato dakinsu fahad su maryama kuma suka biyosu da akwatin kayanta da food flasks din abinci guda biyu, zame mayafin kanta tayi bayan sun gaggama ficewa tafara bin dakin da kallo, babu wani tarkace dayawa aciki sannan dakin baida girma caan dan madaidaicine mai dauke da babbar katifa anshifideta da sabod bed sheet sai akwati babba guda daya amma dakin fes yake yasha sabon fenti da jan carpet malale aciki ga kofar toilet nan komai dai neat, bata ko taba Food flasks din da aka kawoba taci gaba da zamanta shiru har goma da wani abu sai lokacin taji gidan ya danyi shiru alamar mutane sun ragu, sha daya saura yan mintuna taji alamun bude kofa gyara mayafinta tayi ta lullube jikinta,fahad ne yashigo rikeda leda,yana sanye da danyen boyel kalar ruwan siminti kanshi babu hula, sallamar da yayi kawai ta amsa daga nan ta guntse bakinta, agefen katifar ya zauna yana zaro wayarshi daga aljihu,

"Hajjaju yagajiya?"

"Alhamdulillah"

Bai kara magana ba yamaida hankalinsa kan wayar hannunshi, ita dai tana zaune ta jingina da pillow sai karkada kafa take kamar wata sarauniya, sunfi minti biyar ahaka babu wanda yasake cewa uffan sai karar fanka da ta cika dakin, ledar da yashigo da ita yamika mata gabanta ya ajiye,

"Ki ci abinci gashi nan..."

Batayi magana ba ta dauke kai,

"Kinji...."

"Naji..."

Tabaya ya kwanta rigingine yana kallon sama yana danna wayarshi zuwa can yadago ya kalleta,

"Bazaki ci abincin ba ne? To kitashi kiyi wanka ki kwanta"

Shiru tayi batayi magana ba yayinda shikuma yatashi zaune ya buda ledar dake ajiye agabanta yadauko malt guda daya ya balle ya dan sha sannan ya ajiye, Flaks din da ke ajiye ya bubbude, sakwara ce da miyar ganye tasha kaji gashi ta soyu, dama yunwa yakeji dan shima rabonshi da abinci tun yaushe mikewa yayi yashiga bathroom ya daurayo hannunshi yadawo yaja abincin gabanshi yafara ci tana zaune tana kallonshi dama guda ukuce sakwarar babu bata lokaci yatashi da guda biyu, kallonshi tayi adage,

"Malam jimana...."

Dagowa yayi ya kalleta,

"Ai abincin nawane ba naka ba so zaifi kyau idan kabar min kayana haka"

Tsame hannunshi yayi daga cikin miyar yamayar da murfin ya rurrufe sannan yajanyo ledar gabanta yabude, gasasshiyar kaza ce mai romo sai kayan sanyaya makoshi malt guda biyu da fresh milk zindimemiyar roba, kazar yabude yasoma yaga yana ci yana korawa da malt,

Harararshi tayi ta janyo flask din gabanshi tana turo baki budewa tayi itama tafara ci tana kallonshi yanata cin kazarshi,

"Gaskiya wannan yaron akwai mugun ci....tab"

Sai da yaci rabin kazar sannan yamike yashiga bathroom, wanka yazarce dayi shiyasa yajima aciki, tana cin abincin tana sake jinjina kuruciyarsa to inbanda kuruciya menene na zama yacinye kazar da ita yasiyowa?

Itama da kazar ta dora bayan ta cinye sakwarar amma bata ci da yawaba domin cinya kadai taci da dan abinda ba arasa ba saboda tarihi ko nan gaba zata tuna da taci kazar aurenta. Tana kammalawa yana fitowa daga wankan da kayanshi ajikinshi gaban akwatin kayanshi yatsaya yabude yaciro riga da wando roba kamar sport wear yakoma bathroom din yasaka sannan yafito tana zaune inda take yazo ya kwanta saitin kafafunta bayan yaja pillow daya, babu jimawa yayi baccinshi,saida taga yayi bacci sannan ta mike tashiga bathroom ita a ka'idarta idan tana period indai zatayi fitsari to saita canja pad, shiyasa saida ta dauki pad acikin handbag dinta sannan tashiga toilet, jikinta kawai tagyara amma batayi wanka ba ta canja pad tafito, akwatin kayanta tabude wai kozata samu kayan da zata saka tayi bacci dasu amma abin haushi duk night wears din bazata iya sakawa ba domin duk marassa nauyine kuma asha shagarai tasan da biyu su meenah suka yimata haka gashi ita bata iya kwana da kaya ajikinta ba, daga karshe dai sai hakura tayi tamaida akwatin tarufe, juyawa tayi ta kalleshi yawani baje yana baccinsa cikin kwanciyar hankali ga sanyin fanka yana fifitashi, bra din jikinta ta cire tabar kayan dake jikinta taje gefen katifar ta zauna ta kishingida, wayarta taciro ta duba misalin karfe daya nadare agogon wayar ya nuna mata, kashe wayar tayi tai addu'a ta shafa sannan tamaida kanta kan pillow dayake itama amutukar gajiye take bata wani jimaba bacci yace muje zuwa......



*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO*


*KAMAR DA WASA...!*


*_NA_*

_*UMMI A'ISHA*_



*18*



***Tunda fahad yakwanta bacci bai ko juya ba sai da asubah, tashi yayi yaje yayi alwala yafito yafita masallaci tareda baba suka shigo gidan lokacin harsu mamuh sun fito suna kokarin hada wuta, dakin yakoma bayan sun gaggaisa dasu,har lokacin bilkisu na kwance ta tukunkune acikin mayafi tanata sharar bacci, tashinta yafara yi tatashi tayi salla amma taki tashi dole sai kyaleta yayi ya janyo wayarshi wadda ke jikin sucket tana charge yasoma matsata. Sai karfe shida saura sannan ta farka, akwatinta ta janyo ta bude taciro soson wanka da sabulu sai brush da toothpaste tajiyo ta kalleshi yayi saurin dauke idonshi yamayar kan wayarshi,

"Malam dan bani wuri zanyi wanka..."

Kamar bazai tashiba zuwa can dai yamike da wayarshi ahannu yayi waje, saida ta tabbatar da ficewar yayi sannan ta kwashi duk abubuwan da zata bukata tashiga bathroom, harta fito tashirya tsaf tasaka wata pink din shadda riga da skirt bai shigoba, turarukanta na alfarma da sanyaya zuciya ta dauka ta shafe jikinta dashi sannan taciro mayafi ta zauna mayan ta maida akwatinta mazauninshi, handbag dinta ta bude ta ciro chingum ta saka abakinta ta dauko wayarta ta kunna. Bata dade da kunnawa ba kiran maama yashigo suka gaisa daga nan su Hindu suma suka kakkarba suka gaggaisa, bayan sun gama wayar dasu meenah saiga kiran khulsum,

"Amarya bakya laifi... Amarya kinsha kamshi"

Murmushi bilkisu tayi,

"Zan ramane wallahi, Allah yakaimu lokacin"

"Au danma na kiraki naji ya kika kwana?"

Kafin tabata amsa fahad yashigo direct bathroom yawuce tabishi da kallo,

"Ni lafiya lau natashi malama"

"Shikenan haka akeso ya angon namu?"

"Lallai kam, yana nan lafiya"

"To agaidashi ace sako injini nace ya kular min da kawata"

"Wannan sakon yafi karfina sai dai idan kun hadu ki fada masa da bakinki"

Khulsum nata tsokanarta tana ramawa daga karshe dai sukayi sallama takashe wayar, haka kawai sai kuma tunanin gida yafado mata nan taji kamar tafashe da kuka, Allah sarki rayuwa yanzu idan banda aure me zai rabata da gidansu, dakinta ne yafado mata arai da gadon da take kwanciya da komai nata dake cikin dakin, kiran da yashigo wayar tatane yakatse mata tunanin da takeyi, goggo maigado ce kanwar mahaifiyar Abba

Please Login or Register in order to submit comment