Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

sai ka bani kudina sannan dolenka ka sakeni...."

"Banza yar gidan matsiyata ni zaki yiwa sharrin na karbar miki kudinki? Uban me uban naki yake dashi da har zan karba? Saki kuma bazan yiba ko kin zaci nima irin wannan sakaran yaronne da zan sakeki aduk lokacin da kikaso? Koda zan sake ki yazama dole inmore sadakina dan haka sai kishirya daukar kwayar cutar HIV...."

Tun kafin yakarasa bilkisu ta dadimeshi tana kuka,

"Ni ba yar matsiyata bace sai dai idan kaine dan matsiyata kuma wallahi daga yau nagama zama dakai...."

Wani marin yasake bata sannan yashiga dukanta babu ji ba gani har saida takai kasa lokacin ne yafara ball da ita yana nausa mata kafa aciki, kuka bilkisu takeyi tana ihun neman dauki ganin yana kokarin kasheta yasa wise zuwa tana kokarin hanashi amma yahaukace kwata kwata bayaji bare gani,

"Nashiga uku hamood ka kusa kasheta... Kar kayi kisan kai kaga yanda takeyi fa... Kabarta haka"

Shine abinda wise keta fada amma hamood yaki saurararta ganin haka yasata sulalewa daga gidan tagudu tun kafin hamood yakashe bilkisu azo tafiya dashi ahada harda ita.

Bilkisu kam tajima da fita daga cikin hayyacinta sakamakon na jakin da hamood ya lakada mata abu na karshe da zata iya tunawa shine taji hamood ya gwarata da kujera ta fadi akan hannunta na hagu wanda take awurin wani azababben zafi ya ziyarceta, cikin azababben ciwon kai take bude idanuwanta ahankali wadanda suka kumbura suntum sakamakon uban bugun da suka sha,

Ammah ce da meenah zaune acikin dakin wanda ko ba afada mata ba tasan asibitine domin ga alamu nan sun nuna hakan, ga ruwa nan ana kara mata a hannunta na dama sannan hannun hagun ta kuma an daddaureshi dasu bandeji alamun dori,

Wasu hawayen nadama ne suka zubo daga cikin idanuwanta, ganin ta dan motsa yasa ammah da meenah azamar tasowa dukkaninsu Wanda har bakinsu na haduwa wurin yimata sannu,

"Sannu mai gado..." Inji ammah,

Kai ta dan daga cikin azabar ciwo ta rinka binsu ammah daya bayan daya da kallo kamar yau tafara ganinsu. Bata iya cewa komai ba sai ciccije baki da takeyi sakamakon ciwon da dukkanin jikinta keyi mata musamman ma hannunta na hagu,

"Sannu adda labour.... Allah yatashi kafadunki"

Dagawa meenah kai tayi tana cije baki hawaye na kwaranya daga cikin idanuwanta ahaka su maama suka shigo itada Hindu,maama na dauke da sultan ita kuma Hindu tana goye da meenal abayanta sai hudah wadda hannunta ke rike da nata, cikin zuciyarta take wani irin kuka mai tsuma rai saboda ganinsu mama da 'yayayensu yasake fama mata raunin da take fama dashi, su gasu da yaransu agidan mazajensu cikin walwala da kwanciyar hankali amma ita tanata shiga cikin runtsin rayuwa,

"Allah ka gafarta min... Allah natuba... Astagfirullah..." Shine abinda taketa fada cikin zuciyarta, jinta take ta tsani hamood ta tsani duk wani namiji mai irin halinsa ahalin yanzu,

"Allah ya isa..." Shine abinda lebanta suka furta amma babu wanda yaji, cikin tausayawa da jimami maama da hindu suka karaso gaban gadon su dinma kamar zasuyi kuka,

"Sannu Adda.... Sannu... Sai Allah yasaka miki insha Allah" inji mamaa,

"Kuma inbanda zurfin ciki irin na Adda labour bata fa taba fadar irin zaman da sukeyi ba bare tafadi cewar yana dukanta..." Hindu tafada tana kokarin zama agefen gadon,

"Ni dama tun jimawa wallahi na fuskanci akwai matsala kugafa irin ramar da tayi har iyallo ke cewa ciki ne..." Meenah itama dake tsaye kusa da amma ta tofa nata,

"Ai Dr yace babu wani ciki yanzu... Yace bata da komai, gara ma da Allah bai bata ba domin hada zuri'a da irinsu wannan hamood din hatsarine... Allah yabata masu albarka nan gaba" maama tafada tana kokarin mayar da kwallar da take kokarin cikowa idanunta, ammah dai har akayi aka gama bata tofa tata ba suna nan zaune sunata yimata sannu har Abba yazo yadubata yatafi hakama mazajensu duk sunzo sun dubata, khulsum amarya itama daren ranar sai gata, kowa yaga bilkisu sai yaji tausayinta sakamakon kumburar da fuskarta tayi tsabar duka. Lokacin da dare yayi meenah ce tace zata kwana da ita amma ammah tace a'a kowa yatafi gidansa inyaso Rabi mai aikinta sai tazauna su kwana tare hakan kuwa akayi, ita dai bilkisu kasa baccinma tayi sakamakon suyar da zuciyarta keyi motsi kadan zata furta,

"Allah ya isa..." Acikin zuciyarta kokuma afili. Saida tayi kwana uku agadon asibiti sannan tafara tashi har ta zauna kuma an danyi sa'a kumburin fuskar tata ya dan ragu, har ranar babu wanda yayi mata maganar hamood may be suna son abar asibitinne tukunna sai asanar mata abinda yafaru, aranar tana zaune maama na kusa da ita agefen gadon tana bare mata ayaba tana ci sai ga hajiya iyallo ita da yakumbo mai gado, tunda iyallo tashiga dakin take tsinewa hamood,

"Ni dama wallahi wannan yaron ban yarda dashiba... Yaro sai kace dan dambe wani murgujeje dashi... Wallahi tsohon mijinki shine miji mai gado... Yaro mai kunya ko gaisheka yakeyi idanuwansa akasa bazai taba yarda ya hada ido dakaiba amma shi wannan idonsa atsakar ka yake sai yasaka idonsa cikin naka sannan zaiyi maka magana....Allah yasawwake,Allah ya kwashe masa albarka macuci"

Tun abun na bawa su maama haushi har yadawo yana sakasu dariya, iyallo nata faman hamuki ya mudan yashigo wanda dama shine yakawo su,yana yiwa bilkisu yajiki iyallo tahau cewa,

"Ai shikenan yanzu sai acika min burina ayi hadin nan.. Ni dama tun farko mudansiru naso abawa aka ki..."

"Dan Allah iyallo mu ki kyalemu muji da abinda muke ji..." Maama tafada tana hararar gefe,

"To fitsararriya dadinta ma dai bake naceba balle kiyimin rashin arziki... Fitsararriya kawai.."

Shi dai ya mudan ficewa yayi daga dakin da alama shima baiji dadin maganar iyallo ba ko meye dalili? Bilkisu kuwa jin iyallo ta ambaci fahad har tana yabonsa yasata dulmiya kogin tunani.....


*Wannan littafin na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*



*_Ummi Shatu_*

*Wannan littafin na siyarwane me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*


_BILKISU_

37 ***Har iyallo ta karici bambaminta tagama bilkisu batace uffan ba kusanma gaba daya yanzu tadaina fahimtar abinda suke cewa domin tadade da yin nisa acikin kogin tunani tabbas maganar iyallo gaskiya ce fahad yarone mai kunya kuma nagartaccen namiji domin ita kanta ta shaida hakan duk da har yanzu bata jin zata iya zaman aure dashi domin yayi mata kankanta shekarunta sunfi nasa, to tayaya zatayi rayuwar aure dashi? Tayaya zai rabeta amatsayin matarsa? Haba ai da kunya,jikinta yanzu yafara bata cewar wannan abunda yafaru da ita harda hakkin fahad kila Allah ne yayi masa sakayyar cutarwar da tayi masa itada hamood shiyasa ya hanasu jin dadi da farin ciki a lokacin zaman aurensu, ita kanta sai yanzu take ganin wautarta da rashin wayon da ta aikata gaskiya hamood ya shammaceta ya cutar da ita, wasu hawaye masu zafi taci gaba da zubarwa ganin haka yasa iyallo sake dagewa wurin tsinewa hamood ita kuwa bilkisu ita kadai tasan dalilin kukanta gashi kukan zuci takeyi marar sauti sai dai kawai aga hawaye na zuba alhali likita yace irin wannan kukan yafi illa dan haka ta nisanceshi amma ita kanta tasan bazata taba iya hana wadannan hawayen zubaba domin direct suke tahowa daga can cikin zuciyarta.

"Adda labour dan Allah kiyi hakuri kidaina kukan nan haka.... Maganin me kukan zaiyi ne?" Mama tafada cikin rakwarkwabewar fuska,

"Mamaa yazama dole inyi kuka... Barni in koka ko zuciyata zatayi sanyi...."

"Kidai yi hakuri kuma ki daure dan Allah...."

"Maama..... Bazan.... Baz....."

Ai bata kai ga karasawa ba kirjinta ya sarke idanuwanta suka kakkafe, wata gigitacciyar kara maama tasaka yayinda su iyallo kuma suka hau zuba salati, karar da maama tafasa itace ta janyo hankalin ya mudan yashigo cikin dakin cikin tashin hankali ganin abinda ke faruwa yasa shi fita da sauri zuwa office din likita, maama na rike da ita tana gunjin kuka likita yashigo yafitar dasu ta hanyar basu umarnin su fice daga dakin, yajima akanta sannan yafita har lokacin jikin maama bai daina rawaba da nasu iyallo domin su duk atunaninsu mutuwa bilkisu tayi amma sai likita yace musu bahaka bane su kwantar da hankalinsu da ranta kuma insha Allah zata samu lafiya, ita dai bilkisu na can bata san abinda ke faruwa ba domin tadade da rabuwa da hankalinta, lokacin da su ammah sukazo ma baccinta take tasha sai ruwa da ake kara mata, tsaki meenah taja tasamu wuri ta zauna kusa da Hindu bayan tadawo daga leken bilkisu ta window din dakin da take ciki,

"Wai dan Allah sai yaushe za abar baiwar Allahn nan tahuta ne? Haba jama'a Karin ruwa yaki karewa...."

"To ya za ayi Ameenah... Allah dai yabata lafiya..." Inji ammah, zama sukayi jugum jugum har sai da likita yakira ammah nan suka rankaya gaba daya suka tafi, dan takaitaccen bayani yayi musu dangane da matsalar da bilkisu tasamu amma yace yanzu sun samu nasarar shawo kan matsalar sai dai yanada kyau ta guji tunani da shiga bacin rai domin maganar gaskiya zuciyarta na daf da bugawa saboda damuwa, duk cikinsu babu wanda bai kokaba sai Ammah kadai itace ke basu hakuri, zuwa dare bilkisu ta farfado hakan ya dan kwantar musu da hankali musamman ma da sukaga duk wuraren da yataru jini ajikinta ya barbaje, babu laifi taji sauki sosai sannan ta samu lafiya matsalar kawai dorin hannunta ba akunce ba likita yace sai nan da sati biyu haka suka yita faman kaiwa da komowa har zuwa lokacin da aka kunce dorin aka sallamesu, duk bilkisu tabi tasake kekashewa kamar wadda tayi shekara akwance. Lokacin da suka koma gida ba karamin mamaki tashiga ba domin ganin kayanta gaba daya nasawa andebosu da duk wani abu wanda yake mallakinta ne, ita dai har ta kwana ta yini tasake kwana babu wanda yayi mata maganar hamood ko wata magana mai kama da haka, shi kansa abba baiyi mata maganar ba iyakaci idan taje ta gaisheshi suka gaisa shikenan amma bai yimata maganar hamood ba haka itama ammah duk da suna zama suna yin hira, sai akwana na biyarne maama tasake dawowa gidan domin dubata itada hudah harda farfesun kaji da dambunshi wanda ta iyowa bilkisu, cikeda sha'awa bilkisu ke kallonta domin har cikinta ya dan fara turowa duk da dai tanada girman ciki amma kowa yaganta yaga mai juna biyu, saida suka sha hira afalon ammah ganin lokacin salla yayi yasa bilkisu tafiya dakinta tayi wanka tazura doguwar riga tayi salla tana idarwa maama tashigo tana rikeda hannun hudah, kwantar da ita tayi kan gadon bilkisu sannan ta yunkura zata tashi nan bilkisu tayi hanzarin dakatar da ita,

"Yawwa maama wai dan Allah waye yakaini asibiti ne? Sannan hamood kuwa yayi sakin?"

Komawa maama tayi ta zauna tana kallon bilkisu,

"Adda labour wallahi ranar hudah muka kai asibiti nida abbanta, gaba daya sai najini ba anutse ba sannan hankalina duk yatafi gareki shine fa nace masa mubiya inganki dakyar ma yayarda wai yana gudun makara a office, ina shiga na iskeki cikin wannan halin hamood yanata kwallo dake.... Abban hudah ne ya daukeki yakai cikin mota bayan nakiraki shine muka wuce dake asibiti, sai bayan da akayi admitting dinki sannan nakira su ammah..."

Jijjiga kai bilkisu tayi cikin damuwa sannan ahankali tace,

"To ya maganar sakin? Ya sakeni?"

Kai maama ta daga mata cikeda damuwa,

"Ya sakeki bayan sun debota da Abba domin Abba waya yayiwa uncle dinsa yasanar dashi komai nan uncle din nasa ke cewa shi dama bashida wani hadi dashi inbanda almajiranta da yazo yi har Allah yahadasu yake wanke wanke agidansa dahaka yazama tamkar dan gida.... Ke intakaice miki zance ma shi kansa hamood din saida Abba yasa aka nemoshi sukayi babu dadi dan cewa yayi shi bazai sakeki ba har sai anbiyashi komai nasa tun daga kayan lefe har sadaki... Sai da Abba yabiyashi sannan ya sakeki saki biyu..."

Tagumi bilkisu ta rafka tana jin kirjinta nayi mata suya,

"Lallai hamood yacika marar mutunci.... Nimafa akwai kudina a hannunshi wanda Abba yabani yace wai in ranta masa wani mutum yasiyarwa da mota to kuma yanzu yadawo masa da ita shine zai cika yabashi kudinsa saboda already kudin hannunshi ya tura za a kawo musu sabbin cars...."

"Babu komai adda maigado kawai kiyi addu'a insha Allah bazaki tagayyara ba kuma sai Allah yasaka miki... Ni wallahi idanma son samune tsohon mijinki yadawo kusake dinkewa.... Allah sarki ya fahad bawan Allah komai nasa na mutunci...."

Shiru bilkisu tayi tana saurarenta har saida taji tayi shiru sannan tasauke nannauyar ajiyar zuciya tana kallonta,

"Maama kenan...."

"Wallahi dagaske adda labour fahad shine yafi dacewa dake saboda yanada yakana da alkunya..."

Rasa abin cewa tayi daga karshe taja bakinta tayi shiru tana jin maama sai faman kwarzanta fahad take tayi.

Sam abinda maama ta fada baiyi tasiri acikin zuciyarta ba sai dai yatsaya mata arai fiyeda tunanin mai tunani domin daren ranar kawai tunanin rayuwar da tayi agidansa tayita yi tana tuna dabi'unsa da kuma halayensa wadanda ko makiyinsa bazai kushe ba, tarasa a wanne aji yadace tasaka wannan al'amari, shin yanzu idan fahad yadawo zata iya aminta dashi? Wannan shine tambayar da tayiwa zuciyarta amma sai ta girgiza kanta,

"Dan mutunci kam bani da ja yanada mutunci da hankali amma zamana tareda shi a matsayin miji da mata.... Hmmm" sai kuma tayi shiru takasa karasawa, karshenta dai wannan dare sai bacci barawo shine yasamu nasarar saceta lokacin da take tsaka da tunani tana tambayar kanta wai meye dalilin da yasa kowa ke yimata fatan fahad yadawo gareta?.



_FAHAD_


Tuni fahad yafara zuwa shagon oga Abdul, lokacin da yafara zuwa Abdul din bai wani daukeshi serious ba domin bai zaci cewa ya iya dinki ba sai da yaje wurin sau uku sannan yace yazo yazauna ga keke nan yafara, wata atamfa yabashi da measurement da komai yace ya dinka, ai tunda fahad ya dinka atamfar nan sai Abdul yasoma bashi wani girma na musamman domin koshi fahad yafishi kwarewa afannin dinki expert ne awannan fannin tun daga ranar kasuwar fahad ta bude babu bata lokaci sunanshi ya yadu acikin makarantarsu domin duk wata budurwa mai ji da kanta ta fahad take bawa dinki, bama yan makarantar ba hatta daga cikin garin abuja ana kawo masa dinki, wasu bawai dinkinne damuwarsu ba a'a kawai so suke su kulla alaka dashi sosai oga Abdul yayi farin ciki da zuwan fahad shagon domin zuwansa yakawo masa alkhairi masu dinbin yawa ga fahad babu mugunta aduk lokacin da zaiyi yankan sabon style zaiyi agaban sauran yan shagon ya koya musu gobe ma wani zai sake kirkira. Sosai yamayar da kanshi mr busy domin har majalissin dare yake zuwa inda magidanta ke daukar karatu shima yadauka dan wayo kam yayiwa su mukhtar wayo,kullum yanada abinyi baya zaman banza shiyasa baida matsalar komai ahalin yanzu kudi suna shigo masa ko ta ina dan idan yayiwa yayan manya dinki sai an nunka masa kudin dinkin nasa sannan abashi koda kuwa yafadi abinda za abashin, husnanshi kuwa kullum suna tare awaya domin tunda yazo kaduna baije kano ba, kullum idan zaiyi girki sai yakirata ta koya masa yauma daga lecture yafito awahale domin tea kadai yasha da safe kuma sai 2 yadawo dakinshi wani tea din yasake sha saida yaji dan dama dama sannan yakira husnah domin ta koya masa yadda zai dafa dan wake dariya yajiyota tanayi tareda fadin,

"Ya fahad dan wake kuma? Tabdijam lallai yau dan wake zaisha jifa..."

Jin dariyar da takeyi yasashi sakin murmushi,

"Kinga idan bazaki koya min ba ni kawai ki fada min kin barni yunwa nata faman damuna..."

"Am sorry sweet prince..... Yanzu fara jika kanwa saboda da ita zaka kwaba fulawa din..."

Yamutse fuska yayi kamar tana kallonshi,

"Gaskiya husnah dan waken nan ba yau ba, bari kawai indafa indomie tunda naji shi nasa hadin yawa gareshi"

Kafin tabashi amsa aka bude kofa, bashir ne yashigo mukhtar na biye dashi,

"Malam tashi muje gidansu bash.... Wallahi kuma ko baka so sai kaje..."

Batare da yayiwa husnah sallama ba yakashe wayar yatashi zaune yana kanne ido daya saboda yunwa,

"Wallahi yunwa nakeji mukhtar kubari muci indomie mana..."

"Dallah kazo muje, akwai abinci acan fa..."

Baiyi musu ba yakama hannun mukhtar din yamike suka fita, lokacin da sukaje gidansu bashir kanwar bashir din mai suna suwaiba itace keta hidima dasu amma kuma sai kallon fahad take tayi kamar zata cinyeshi shiyasa duk ya takura, suna kokarin barin gidan babansu bashir yadawo Alh Usman mai fitila shahararren attajirin dan kasuwa,afalonsa duk yatara su yana yimusu fada da Nasiha kan su zauna suyi karatu banda wasa sannan su nemi sana'ar yi komai kankantarta ai nan su bash sukayi farat sukace fahad sana'ar dinki yakeyi hakan ba karamin burge Alhaji Usman yayiba nan yarinka saka masa albarka yana cewa yataimaka ya koyawa abokanshi ma domin ko karatun mutum yagama ba lallai yasamu aikin yi akan lokaci ba daga karshe yabaiwa fahad kyautar wani hadadden yadi na maza irin mai tsadar nan sky blue da turaren oud wanda shima kudinsa akalla zai kai dubu ishirin, bayan sun fito suwaiba ta biyosu tana ta yiwa fahad kwarkwasa da shagwaba shi dai baya iya cewa komai. Tun daga wannan rana suwaiba ta manne masa domin har number dinshi tasamo take damunsa shikuma harga Allah yanzu tsoron mata yake kuma ma banda haka ga husnah agefe, harsu mukhtar saida sukayi masa maganarta amma yace shi baya soyayya dakyar yasamu ya yageta daga jikinsa, ba ita kadai ba duk macen dayaga take takenta na sonshi take fita harkarta yakeyi. A daddafe dai yagama semester dinnan yakoma gida dauke da dunbin nasarori sau biyu kacal yaje ganin gida a wannan semester din.



*_Ummi Shatu_*

*Wannan littafin na siyarwane me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*



BAYAN SHEKARA D'AYA


38***Yau garin kano antashi da muku mukun sanyi da tarin hazo wanda ya lullube ko ina shiyasa duk inda ka duba mutane tsilla tsilla kake gani kowa yana yin al'amuransa cikin rashin sakin jiki da takurewa saboda sanyi, a titina kuwa duk motocin dake wucewa da sauran ababan hawa kowa ya kunna fitila saboda nagabansa ko mai tunkaroshi yahangoshi tun daga nesa, fahad yabi sahun mutanen da sanyin yau ke takurawa, dawowarsa kenan daga asibitin koyarwa na malam aminu kano wato (Aminu kano teaching hospital) inda yake gabatar da practical dinsa tun sati uku da suka gabata yafara zuwa, yana dawowa yasa maryam ta dafa masa ruwan zafi yadaure yayi wanka yafito duk sai kakkarwar sanyi yakeyi, agogon wayarshi ya kalla nan yaga karfe biyar da rabi,

"Ohh Allah... Ji yanda lokaci yaja amma kai sai kazaci ba afi karfe uku bama...."

A gaggauce ya shirya cikin riga mai dogon hannu baka sannan yasake dora wata t shirt din mai gajeren hannu ita kuma ja yasaka bakin jeans, sannan yadora rigar sanyi akan rigunan da yasaka wadda takusa kai masa zuwa gwiwarsa, bakar hula yasaka kirar sakar inji ta kamfanin Nike domin ga sunan nan rangadadau agaban hular, har kunnuwansa yarufe da hular sannan yasaka bakar safa mai kauri akafarsa, dan guntun turarenshi da yayi saura shi yadauka yakarar dashi ajikinsa sannan yawuce gaban katifarsa yajawo system dinshi wacce ke kunne muryar sheikh abdurrahman sudais natashi cikin suratul kahfi, kashewa yayi ya ajiyeta kan pillow dinshi sannan yadauki wallet dinshi da bakin glass yafita, cikin gida yashiga gaba daya suma su ayiyah suna falon mamuh suna shan dumi cikin wani katon kasko wanda suka zuba garwashi aciki, su maryama na zagaye da kaskon suna jin wuta,

"Wai... Gaskiya dakin nan akwai dumi... Mamuh yau anan zan kwana..."

"Kai meyasa baka raboda sakarcine? To kazo ka kwana din ai sai mu kaika inda ranka ko taska muce ga gandamemen saurayi nan amma har gobe bai daina kwana dakin babarshi ba..." Mamuh tabashi amsa tana gyara lullubin dake kanta,

"Ayiyah kina ji fa... Kice wani abu"

"Kyaleta autana, yau wannan kaskon wutar adakinka zai kwana"

"A'a ai sai dai ku nemo naku ko kibada naki..."

Dariya sukayi gaba daya yamike daga tsugunnen dayake gaban kaskon wutar kusada su Mariya har yana dungure mata kai cikin fada yace,

"Ke dalla kirinka kula gashi nan zaki jefa gefen hijabinki cikin wuta... Karki jawa mutane gobara....."

Mikewa tsaye yayi ya kalli iyayen nashi,

"Sweet mamuh zan tafi store.."

Sake juyawa yayi ga ayiyah,

"Loving momy naje store..."

"Kai dai kasani ja'iri, adawo lafiya..." Inji mamuh, ita kuwa ayiyah dariya tayi tace,

"Allah yabada sa'a autanah.."

Saka kai yayi yafita yana jin su Mariya na hada baki wurin cewa,

"Ya fahad kasiyo mana chocolate..."

Yana kokarin fita kawai yakoma dakinsu mask yadauko domin yazama dole yatoshe kofofin hancinsa saboda hazo dan yasan muddin yafita ahaka akwai matsala domin bayan wani bangare na zuciyarsa da ya tabu sakamakon matsanancin hawan jinin dake damunsa harda wata lalurar mai kamada asthma amma kuma ance ba ita bace. Roba roba dinshi yahau yafita daga layin kafin yakarasa gidansu salim yazaro wayarshi daga aljihunshi yasoma kiran salim din, yana dagawa yace,

"Kai gwauro.... Dan Allah zo ka rakani store insai turare mana..."

Ai salim najin haka yasake tukunkunewa cikin bargo,

"Wallahi babu inda zan iya fita a wannan sanyin, kabari gobe da safe ko yamma sai muje mana,

"Tab kasan kuwa yanda na matsu da turaren nan? Ni bazan iya rayuwa babu turare ba malam..."

"To sai kadawo, nidai babu inda zanje..."

Katse wayar fahad yayi yajefe cikin aljihunsa yaci gaba da tukinsa sakamakon yahau babban titi danma daga hancinsa har idonshi duk a rufe suke. Ihsan store yashiga cikin sa'a yasamu dukka turarukan da yake amfani dasu wadanda suka kasance ba masu matsanancin karfiba saboda shi yanzu al'amuransa sai ahankali,suma su ayiyah saida yadauka musu sabulun wanka sinki biyu domin duk wanda zai siya musu abu agidan to guda biyu yake siya, daga karshe yadaukawa su Maryam gidan chocolate yanufi wurinda ake biyan kudi, yana shawo kwana yayi kicibus da maama rikeda jaririn yaronta ahannunta, sam ita bata ganeshi ba domin fuskarshi arufe take,

"Hajiya maama...."

Taso ta dauki muryar amma saita kasa gane ko tawaye, ganin bata ganeshi ba yasashi cire glass din fuskarshi da mask din da yarufe hancinsa, cikeda mamaki maama taware idanuwanta tace,

"Ya fahad idonka kenan.... Yaushe akasa?"

Dariya yayi yamika hannu yakarbi awwab dake hannunta wanda tuni har yafara wayo,

"Wallahi hajiya maama ina nan, ina babynki hudah yanzu tagirma ko?"

Dariya maama tayi,

"Tagirma tana can gida wurin adda labour..."

Jin ta ambaci labour yasashi dan runtse idonshi,

"Allah sarki... Tana lafiya ko? Yanzu nasan ta haihu ma may be...koda yake bari nayi shiru kar mijinta yasa akamani"

"A'a wai baku taba haduwa ba? Ai tana gida, yanzu batada aure..."

"Ya salam.... Sun rabu da mijinne ko kuma rasuwa yayi?"

"Wallahi rabuwa sukayi, ai kwata kwata aurenta bai wuce 3 months ba suka rabu...."

"Ikon Allah... Allah yarufa asiri,wallahi ban saniba nima da yake yanzu nakoma Kaduna da zama can nake karatu, practical yanzuma nazo yi wallahi..."

"To Allah yataimaka amma dai yakamata kaida adda labour ku tuna baya, yanada kyau akoma gidan jiya"

Dariya fahad yayi ya rausayar da kai yana kallon fuskar awwab ganinshi yake kamar bilkisu ce ta haifeshi dan tsananin kamarsu kasancewar kamarta daya da maama,

"Ai yayar takice miskila ce maama... Tanada wuyar sha'ani...."

Dariya itama mamaa din tayi sannan tace,

"To ai zaku daidaita tunda kai kanada saurin fahimta da saukin kai..."

"Haka dai kikace, Allah yazabi abinda yafi alkhairi..."

Bata kai ga amsawa ba abban hudah yakaraso domin har yagaji da jiranta acikin mota,

"Haba nidai nasan tsayawa gaisawa da wata ko wani kikayi saboda naji shirun yayi yawa..." Yafada yana mikawa fahad hannu domin yin musabaha,

"Ehh wallahi mijin adda labour nagani shine natsaya muke gaisawa..." Tafada tana dariya, murmushi fahad yayi,

"Ahh kice yayanmu ne, babban yaya yakake?"

Dariya abin yabawa fahad jin mijin mamaa na kiransa da wai Yaya bayan kuma yagirme masa ahaife sosai, karbar pampers din dake hannunta fahad yayi bayan yamikawa abban huda awwab, dama pampers kadai tazo siyawa awwab irin babban nan, wurin biyan kudi fahad yaje yahada yabiya har da nasu duk da sunata cewa yabarshi, har zai tafi maama ta dakatar dashi ta karbi number dinshi domin ita dai haka kawai take kaunar fahad shiyasa ba ason ranta aurensu ya mutuba dan dai kawai kaddara tashiga cikine.Lokacin da yakoma gida magrib tayi shiyasa saida yatsaya yayi salla sannan yashiga cikin gida yakaiwa su ayiyah abunda yasiyo musu, sunata saka masa albarka yadauko abincinsa shida Abba yafito domin abban ma yana gari tun watanni biyu da suka wuce yagama service yanzu haka yana zuwa bureau of statistics acan yake dan taba kwadago,

Yana zama gefen katifa kamar da tunanin bilkisu yazauna domin gaba daya hirar da sukayi da maama ce tafara dawowa cikin tunaninsa, sama

Please Login or Register in order to submit comment