Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dasu. Washe gari takama ranar daurin auren husnah da fahad sai Abba da nusaiba kanwarsu salim amma shi fahad nashi auren a Kaduna za adauroshi gidan da ake rikon husnah, Bilkisu na can dakinta tana aikin da babu gaira babu dalili dan kawai ta debewa kanta kewa tarage damuwar dake ranta wacce bata san ko ta mecece ba fahad yashigo cikin shirinsa tsaf na tafiya daurin aure, farar shadda mai tsada yasaka sai jar hula da farin takalmi wato dai kwankwasiyya atakaice sai zuba kamshi yakeyi,

"Ranki yadade ni nafito, sai Allah yadawo dani... Insha Allah tare da amarya zamu taho..."

Banza tayi dashi saboda aganinta wannan ma ai rainin wayo ne wato saima yanzu zai sakaya sunanta da yake maganar aurenshi zai fada mata,

"Mai gado bakiji ni bane....?" Yafada yana tsuke fuska,

"Idan najika me zanyi maka? Ko daukarka zanyi akaina inkaika har wurin daurin auren?" Tafada cikin masifa,

"A'a nidai yau ba ranar fada bace ranar farin cikina ce ranar da bazan manta da ita ba, ki nemi abokin fadanki amma ba Muhammad fahad ba...."

Daga haka yajuya yafita hakanne yasake kular da ita har taji kwalla tafara zubo mata, wurin karfe 10:30 khulsum tazo lokacin tagama kukanta amma idanuwanta jajur suke,

"Labour kuka kikayi ko? Haba ke kuwa sai kace karamar yarinya?" Khulsum tafada tana kallonta,

"Hmm khulsum ba zaki gane bane yaron nan ya iya bakar magana kamar rainon gwauro..." Tafada acikin ranta amma afili sai tacewa khulsum,

"Nifa babu kukan da nayi uwar son jin tsurku.... Zaki fara sa idon naki da kika saba..."

"Allah ya shiryeki kawata, kina wahalar da zuciyarki wallahi.... Tab inama nice fahad"

"Da kece me zakiyi?" Bilkisu ta tambayeta tana harararta,

"Da Allah kadai yasani...."

"Kya dai ji dashi"

"Allah dai yabar kawata uwar gida agidan fahad wallahi ko amarya tazo kece star...." Khulsum ta fada tana rangada guda, tun Bilkisu bata biyeta har ta biye mata suka yita yarawa zuwa can saiga meenah da maama amma banda Hindu wai bata jin dadi kuma da yake cikinta ya tsufa haihuwa ko yau ko gobe, sune suka raya mata gidan har tasamu damar manta damuwarta. Har dare suna gidan dan acewarsu sai ankawo amarya akan idonsu hakan kuwa akayi bayan sallar magrib sai ga yan kawo amarya damma sun tsaya agidansu fahad anyi budar kai amma tun yamma suka iso, duk da su maama suna taya Bilkisu kishi amma hakan bai hanasu tarbar yan kawo amarya da fara'a ba, ita dai Bilkisu tana daki ita da meenah, tana ji yan kawo amaryar wasu daga cikinsu na cewa su dai baza suje dinner ba sun gaji, tabe baki tayi tabi lafiyar gado ta kwanta, fahad kuwa tun safe lokacin da yayi mata sallama yafita bata kara sakashi cikin idanuwanta ba, shikam yana can gidansu dakinsu na da shida ya abba tun bayan dawowarsu daga Kaduna yake cikin ruguntsumi bai samu kansa ba yanzu ma haka shirin tafiya dinner suke yi shida abokansa dan hatta su mukhtar duk sun zazzo suna dakin salim ansaukesu acan.

Bilkisu na kwance tana jin hayaniyar dake tashi ta yan kawo amarya ga kawayen amarya sai ihu da shewa sukeyi bata samu taji gariba har saida suka tafi dinner dinnan nan su khulsum suma sukayi mata sallama suka tafi da sauran yan uwan su fahad, bayan kowa yatafi amma tana jiyo yar hayaniya adakin husna ta shiga wanka tayi shirin bacci ta kwanta duk da tasan yaudarar kanta kawai takeyi dan ba yi zatayi awannan lokacin ba, 12 saura aka dawo daga dinner din nan sabuwar hayaniya ta tashi hakan yasake kona mata rai bayan kamar mintuna talatin taji karar tashin motoci zuwa can kuma taji tsitt alamun kowa ya tafi, ita dai tana kwance daga inda take bata ko motsa ba, 12 da wani abu taji motsin shigowar fahad, kai tsaye dakinta yafara shiga yana rike da leda a hannunshi na dama hannunshi na hagun kuma yana rike da wayarshi da babbar rigarshi, kai daga gani kasan a mutukar gajiye yake domin hakan ya bayyana akan fuskarshi karara, langabe kai yayi yana kallonta cikin shagwaba yace,

"Shine ko nemana ma ba ayi?...."

Wata harara ta dalla masa amma sai yayi murmushi, ya karasa gaban gadonta ya ajiye mata ledar, kallonshi tayi afakaice yana sanye da dark purple din shadda dinkin half jamfa da hula babbar rigar kuma na rike hannunshi,

"Ga kayan kwalam da makulashenki..."

"Bana so ka kaiwa amaryarka......"

"Karki damu tare na siyo muku nata yana falo, yanzu zanje na kai mata...."

Bata tanka ba ta dauke kanta taja duvet ta dan jiyo kadan ta kalleshi,

"Zanyi bacci dan kashe min hasken idan zaka fita..."

Murmushi yayi maimakon yafita saima ya zauna kan stool din dake gaban mirror,

"Basai fa kin koreni ba zan tafi, bari na dan huta..."

Bata kulashiba taja duvet ta rufe har kanta tana sauraron ajiyar zuciyar da yake saukewa ahankali zuwa can kamar bayan mintuna 15 taji yatashi yakashe mata wutar yafita, tofah kamar amafarki sai taji kuka ya subuce mata wanda bata san musabbabinsa ba,ni kaina Ummi A'isha so nake naji dalilin kukan Bilkisu........



_jiya yar dakina asked me wai sis ummy wacce irin kamace da yan Jami'a? I laugh over and over and over again then nace mata, yan gayu masu class kuma wayayyu saboda seriously duk wadda tayi jami'a zaki sameta komai nata is different tun daga mu'amalarta da mutane and so on, hatta a dressing dinta ma wallahi zaki fuskanci mai class ce babu baragada da yawan hayaniya shiyasa kukaji na siffanta husnah da haka, da nace kana ganinta zaka gane yar Jami'a ce what i mean is da zarar ka ganta kaga mace mai class kuma abar burgewa, and da nace tayi hudar kunne guda uku bawai fa ina nufin hakan baida kyau ba a'a kawai inaso innuna irin ta kure kwalliya da gayu mai yawa so dan Allah kar ayi min mummunar fahimta wallahi duk abinda nafada da kyakkyawar niyya nafada, tnx for ur love and support._



*_Ummi Shatu_*

*Littafina na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*

50***Kuka take yi harda shessheka gaba daya ta jike pillow din da take kai, ga wani matsanancin ciwon kai wanda yafara damunta har tsawon karfe daya da kusan rabi takai tana wannan kukan,
Dai dai wannan lokaci shi kuma fahad na can tare da husna, lokacin da yashiga kishingide ya isketa ta dan fara bacci, tashinta yayi ta hanyar kama yan kafarta wadanda sukasha jan lalle da baki yana jansu ahankali, bude ido tayi tana kallonshi cikeda gajiya da tarin bacci,

"Ya fahad... Sai yanzu kadawo?"

"Wai har kin fara bacci asma'u? Oya tashi kici abinci sai ki kwanta..."

Yafada yana janyo hannunta, kafada ta noke tamaida kanta ta kwantar saman pillow,

"Ni bana jin yunwa, kaci kayanka..."

Murmushi yayi ya matsa jikinta, ahankali yace,

"Ko kema kina jin tsorone?"

"Name?" Tafada tana bata rai,

"Kar kici min kazata kuma nace sai kin biyani......!"

Daga shi har ita dariya ce ta subuce musu ta harareshi sannan ta gyara kwanciyarta izuwa rigingine,

"U kid yourself sweetheart.... Good news da zan baka yanzu shine am off, soo allow me to sleep pls....."

Murmushi yayi yana shafar lallen hannunta,

"To kinga dadinma zagewa kici kaza kenan tunda ba biyana zakiyi ba, wake up pls"

Girgiza kai tayi tana lumshe idanuwanta,

"Na koshi wallahi, sai da safe zanci...."

"Ok, sleep tight my love, good night...."

Bata amsaba ta gyara kwanciyarta ta hanyar juyawa daya bangaren, shikam yunwa yakeji sosai saboda yau da yunwa yawuni throughout shiyasa ya zauna yaci rabin kaza yasha madara, tashi yayi yashiga bathroom yayi wanka yafito ita dai husnah ko kayan jikinta dakyar ta iya canjawa saboda tsabar bacci da gajiya,shiryawa yayi cikin kayan baccinsa maroon colour masu santsi sannan yatashi yafita, dakin Bilkisu yanufa saboda haka kawai yake jin zuciyarshi bata nutsu da yanayin da Bilkisu ke cikiba shiyasa yasake niyyar komawa dakinta yaganta,

Kamar amafarki taji bude kofa babu shiri ta hadiye kukanta ta toshe bakinta da hannunta guda daya, fitila ya kunna sannan cikin sassarfa yakarasa gaban gadon da take lullube ta wani tukunkune wuri daya,

"Billy....." Taji yafada cikin son jan magana amma sai tayi shiru kamar mai bacci,

"Billy tashi kiji.....kinji"

Nan dinma shiru tayi masa tana shasshekar kuka azuciyarta,

"Wai kina nufin kema kinyi bacci? Ok shikenan good night.....have a nice sweet dream"

Daga haka yajuya yaje ya kashe mata wutar yafita bayan yarufe mata kofa. Yana fita ta cigaba da shasshekar kukanta,kusan daren gaba daya bata samu runtsawa ba har saida asubah takawo jiki lokacinne bacci yasamu nasarar yin gaba da ita, su fahad kuwa tunda yabar dakin Bilkisu yana zuwa ya kwanta kusa da husnah babu jimawa yabi sahunta wurin yin bacci saboda tsabar gajiyar dake tattare dashi sallar asubah makara yayi dan sai wurin 6 sannan ya tashi, yana yin salla yasake kwanciya daidai lokacin ita kuma husnah ta tashi, wanka tayi ta caba ado ta sake kwanciya gefen fahad tana kallonsa yana ta sharar bacci hannunsa kan cikinsa, hamdala ta shiga yi ga ubangijin rahma dan ko yanzu ta mutu tasan Allah ya cika mata burinta, kasancewar jiya da yunwa ta kwana yasata jin cikinta yafara kiran ciroma babu shiri ta tashi tajanyo ledar da fahad yazo da ita adaren jiya, kaji guda biyune aciki amma yaci rabin guda daya sai fresh milk kwali biyu, fresh milk din tafara sha sannan taci rabin kazar da ya ajiye, rasa abinda zatayi tayi gashi takasa komawa bacci kuma lokacin karfe bakwai da wasu mintuna wadanda bazasu gaza biyar ba, tana nan kwance tana kallonsa har shima yafarka hada ido sukayi tayi masa gwalo, hannu ya mika mata amma sai ta gagara kama nashi saboda yau jinta take awani takure duk da ba yau tafara kama hannunshi ba amma dai na yau ya banbanta da na kullum, jikinsa ya matso da ita yana tsokanarta da idanuwanshi,

"Kin ci abinci?" Ya tambayeta ahankali, daga kai tayi sannan tace "ehh"

"Husnah kenan wai duk kinyi laushi why? Dan Allah kidaina tsorona,bari ma ki gani wanka zanyi infita..." Daga haka yatashi yawuce toilet kafin yafito ta dan gyaggyara dakin duk da babu wani datti da yayi sai dai dan abinda ba arasaba. Falo ta dan leka tana sa ran ko zata ga matar gidan amma shiru babu motsin kowa, kafin takoma daki fahad yashirya saima da ta daidaci cewar ya shirya sannan tashiga dakin, yana tsaye gaban mirror dinta yana karya hularshi da zai saka,

"Ya fahad ina kwana?" Tafada tana murmushi sannan tana kallonsa,

"Lafiya lau husnatah, ya bakunta?"

Dariya tayi tazauna agefen gadon tana kallonsa ta cikin mirror shima kallonta yayi yasakar mata murmushi sannan yajiyo,

"Bari induba hajjaju ko ta tashi..." Kai ta daga masa hakan yabashi damar wucewa yafita, dakin Bilkisu yabude yashiga da sallama akan labbansa, tana zaune gefen gado tana shafa mai da alama daga wanka tafito sai dai fuskarta duk a dan kumbure,

"Ashe kin tashi? Yakike?", dan tsuke fuskarta tayi saboda tasan rainin wayon nashi yazo yimata inbanda haka menene nashi na wani cemata yatake, jin bata tanka masa ba kuma taki kallonshi yasashi dan matsawa gab da ita,

"Billy yakika tashi...?"

Sam kin yarda ta kalleshi tayi saboda bata son yaga yanayin da idanuwanta ke ciki, har yagama neman maganarshi yafita bata tanka ba kuma bata kalleshi ba, wurin husnah yakoma yayi mata sallama yafita. Fitarshi babu jimawa su Anty Fauziyya sukazo da sauran yan uwan husnah wadanda suka kwana agidansu fahad, food flask din da aka zubowa kowa breakfast dinshi daban, anty asabe ce tashiga wurin Bilkisu takai mata nata, basu dade agidanba suka tafi sai lokacin da zasu tafi sannan Bilkisu tafito ta rakasu bakin kofa sannan takoma ciki tayi kwanciyarta, haka tawuni adaki a kwance dolece kawai take tadata ango kuwa bashi yadawo gidanba sai dare saboda anata baki yan uwa da abokan arziki duk wanda yaje gidan ya Abba to gidan fahad zai zarto shiyasa husnah yau tasha baki har ta godewa Allah amma fa Sam bata ga bilkisu ba hakan yasa mata tunani aranta na anya kuwa ko lafiya?.

Lokacin da yadawo dakin Bilkisu yashiga har lokacin tana kwance bakinta akekashe alamun bata ci komaiba, zama yayi saman bedside drewar yana kallonta,

"Kinci abinci ne?" Wani kallo tajuya tayi masa sannan takawar da kanta duk sai yaga tayi masa wani iri kamar marar lafiya,

"Dan Allah kici abinci rabin raina..." Yafada yana dariya shiru tayi masa, tashi yayi yafita yana fita taja dan siririn tsaki tagyara kwanciyarta, shi kam yana can suna zuba love da husnah dan yana kwance dare dare akan kafafunta tana bashi labarin irin bakin da tasha yau, daga nan bai sake fitaba sai dai idan salla zaije, ana yin sallar ishah kuwa yarufe gida yashiga gida yana tunanin ya kamata ya hada husnah da Bilkisu inyaso ko gaisawace suyi, yana shiga dakin husnah yaga tasha wata kwalliyar kamar bata kwanciya bacci ba, saida suka gama hira suka ci abinci yayi shirin bacci sannan yashiga dakin Bilkisu, itama tuni tayi shirin baccin tana zaune tsakiyar gadonta tana cin abincin da aka kawo musu daga gidansu fahad,

"Billy husnah zata zo ta gaisheki..."

"Ina ciwo ne?" Ta tambaya batare da ta kalleshi ba,

"A'a" yabata amsa,

"To bana bukata, ko zamana takeyi agidan?

"Allah yabaki hakuri, inzo muci abincin?"

Nan kuma bata tankaba saboda taga nema yake ya maidata wata bi ta nan, yana fita ta tashi tamayar da kofarta ta kulle, daren yau dai babu laifi ta dan samu damar yin bacci da wuri saboda jiya batayi ba yayinda ango da amarya ke can suna debewa junansu kewa danma dai har yanzu amaryar bata samu tsarki ba amma duk da haka an aikata abinda ba arasa ba, fahad baiyi bacci da wuriba yanata tunani wato dan adam yana nashi ne Allah na nasa, shi ko acikin mafarki bai taba zaton cewa zaiyi tarayya da wata mace koma bayan Bilkisu ba ashe husnah matarsa ce bai saniba sai yanzu. Washe garima haka Bilkisu tawuni curr adaki abinci kuma daga gidansu fahad ake kawowa, gaba daya zaman gidan ya isheta ya gundireta yakuma gama fita akanta, saida husnah tayi kwana uku gidan sannan suka hadu, ita Bilkisu tafito ita kuma husnah na zaune falo da waya a hannunta tana yin game, sama sama suka gaisa Bilkisu tawuce kitchen tayi abinda zatayi tafito, daren ranar fahad ya sameta da maganar girki domin yakamata husnah tafara girkinta adaina kawo musu daga gidansu fahad acewarta shine yake tambayar Bilkisu ya abin zai kasance,

"Ni zan dafawa matarka abincin da zata ci? Tabdijam to wallahi bazai yuyu ba, kowa yayi girkinsa final.... "

Shifa yagama lura da Bilkisu yanzu akusa take abu kadan ke bata mata rai tayita surfa masifa, baice komai ba yabar maganar sai da yakai 12 adakinta suna zaman kurame sannan yatashi yakoma dakin husnah,washe gari tunda sassafe Bilkisu ta tashi ta shirya saboda ankirata awaya wai Hindu ta haihu ansamu mace amma suna asibiti saboda yarinyar ba lafiya ansakata cikin kwalba, ganin shiru ango bai fitoba yasata kiranshi awaya amma wayar akashe, tsaki taja ta dauki handbag dinta tafita falo daidai lokacin shikuma yafito daga dakin husnah,

"Ya naganki haka? Lafiya?"

Batare da ta kalleshi ba tace,

"Asibiti zanje Hindu ce ta haihu"

"Masha Allah, Allah yaraya.... Zan kaiki ne?"

"A'a kayi zamanka zan hau napep" tafada ciki ciki saboda harga Allah haushin fahad takeji irin karshen nan,

Adawo lafiya yayi mata bata kulaba tafice bayan ta rufe dakinta,husnah dake tsaye bakin kofa duk abinda yafaru tana ji, komawa dakin husnah yayi nan suka bude babin soyayya wato ansamu dama tunda Bilkisu bata nan shine yau ake baja kolin soyayya. Tunda Bilkisu tabar gidan bata dawo ba sai dare saboda a asibitin suka wuni gaba dayansu,lokacin da tashigo gidan suna falo zaune suna kallo yayi pillow da cinyar husnah amma ganin Bilkisu sai yatashi zaune suna yimata sannu da zuwa ciki ciki ta amsa daga haka tawuce bedroom nan yatashi yabita ciki, bata kalleshi ba ta shiga rage kayan jikinta tana amsa masa tambayar da yake yimata wai ya tabaro masu jiki? Toilet tawuce taje tayi wanka tazo ta kwanta kasancewar tayi zirga zirga yau babu bata lokaci bacci ya dauketa bata ma san lokacin da fahad yazo yimata saida safe ba. Tun daga ranar bata wuni agida acan asibiti take wuni tun safe idan tatafi sai dare,ranar da kwanakin da zaiyi adakin husnah suka kare zai koma dakin bilkisu yaga ikon Allah kasancewar yajima adakin husnah bai fito ba lokacin da yashiga dakin Bilkisu wata uwar harara tarinka zuga masa shi dai baice komai ba katifa ma ya shinfida akasa bai nemi hawa gadonba duk da yasan idan yayi niyya bata isa hanashi ba, bedsheet yaciro sabo daga cikin kayanta nan ta harareshi,

"Malam ajiye min kayana.... Ita matar taka bata baka nataba?"

Ajiye mata yayi yafita zuwa dakin husnah mintuna kadan sai gashi yadawo dauke da Sabon bedsheet harda bargo hakanne yasake kular da ita shiyasa bacci sai sama sama tayi abinda bata saniba shine shi har lokacin ma babu abinda yashiga tsakaninsa da husnah saboda tun ranar da aka kawota acikin period take kuma irin matannan ne masu yawan kwanaki gashi dadin dadawa baya son mai afkuwa ta afku Bilkisu tana nan yafi son sai bata nan sai ya sha angoncinsa hankali kwance, wannan dalilinne yasa lokacin da tace masa agidan Hindu zata kwana ana igobe suna bai hanaba saboda daren ranar ango yake,Bilkisu kam ana can gidan mai jego anata shirye shiryen suna tama manta da rayuwar wata aba wai ita husnah amma abinda yake daure mata kai shine tana yawaita tunanin fahad haka kawai sai taji yafado mata arai. Kamar yadda ya tsara adaren ranar yasamu kasancewa da husna, duk da ta nuna jarumta da daurewa amma hakan bai hanata jigatuwa shiyasa kwana tayi tana yimasa raki abangarensa shikam ya godewa Allah sannan yasake bawa husnah wani gurbi mai girma acikin zuciyarsa saboda yasameta cikskkiyar budurwa wacce kowanne da namiji ke fatan samu. Da safe suna kwance tayi pillow da kirjinsa sai faman rarrashinta yaketa yi yana lallabata yaji kiran Bilkisu yasan maganar dinkice wadda yayi mata wannan dinma da fada da masifa tayarda zaiyi mata amma da wai shagon wasu zata kai ayi mata tareda su maama shikuma yace bai san maganarba idan bazata bari ya dinka mata ba sai dai ta hakura da dinkin gaba daya, ganin yakafe yasata bashi atamfa guda daya daga cikin lefenta shine ya dinka, daga wayar yayi idanuwanshi alumshe,

"Bilkisu... Ya akayi?"

Tun daga yanayin da taji yayi magana tagane akwai abinda suke yi, tsaki taja acikin zuciyarta tana cewa "kwa karaci iskancinku dama ai ba yau aka faraba"

"Ranki yadade ke nake sauraro....."

"Baka yimin dinkin bane?"

"Nayi mana, inkawo miki?"

"Idan baka kawo minba to da waye zai kawo?"

"Yi hakuri bari inkawo miki yanzu" yafada cikin sanyin murya sakamakon jin husna tana tsokanoshi, katse wayar Bilkisu tayi tana tsaki, kallon husnah fahad yayi sannan yashafa kanta,

"Bari naje na kaiwa antynki dinkinta da nayi mata..."

Makale kafada tayi,

"Ni kadai kuma zaka bari?"

Mikewa tsaye yayi yana cewa,

"To ko zaki rakani mu tafi tare?"

Daga masa kai tayi tana bata fuska,

"Sorry yanzu zan dawo.....ai bazaki iya fitaba... Keda naga kina tafiya irin ta yan kaciya..." Yafada cikin sigar tsokana, turo masa baki tayi tahau tirje tirjen kafafu akan gadon, kayan jikinsa yasauya daga na shan iska zuwa jeans da t shirt ta polo yadauki p cap yaje gabanta yayi mata kiss sannan yafita, tashi tayi tabi bayansa har zuwa tsakar gida yadauki machine dinsa yafita, saida taga tafiyarsa sannan takoma gida. Lokacin da yaje kofar gidan Hindu Bilkisu nacan suna aikin abincin suna sunata kukkulla alale da dafe dafen abinci,daga ita sai t shirt da bakar skirt ta fita ta yafa mayafi, yana zaune saman roba roba dinsa yabasar, daga nesa lokacin da take fitowa yake kallonta duk sai yaga tadawo masa wata yar yarinya da ita tayi karama, koda ta karaso kasa kallonta yayi saboda gani yake kamar zata fahimci abinda yafaru acikin idanuwanshi, kasa yarinka yi da idanuwanshi har yabata sakon yatafi bai yarda sun hada idoba,sai bayan da yatafi ma sannan yatuna bai tambayi Bilkisu sunan jaririyar ba, nan yakirata awaya amma har tayi tagama bata daukaba yasan tana can tana cikin aiki sai dai fa sosai yau dinnan tayi masa kyau kawai bai furta mata bane, lokacin da yakoma gida cigaba sukayi daga inda suka tsaya shida husnah sunsha amarcinsu sosai kafin Bilkisu tadawo dan sai washe gari tadawo bayan sun gama komai na soye soye da gyare gyaren gida, tunda ta dawo kuma sai fahad ya daukewa husnah diff sam baya yarda suyi wani abu na wasa ko raha afalo sai dai idan acikin dakine, haka suketa rabon kwana kowa kwana biyu girki kuma kowa nasa yakeyi sam basu ma cika haduwa ba saboda kafin husnah tatashi dasafe Bilkisu tabar gidan ta tafi aiki idan kuma tadawo husnah bata fitowa tana daki a kunshe indai kaganta tafito to tare da fahad ne. Haka kwanaki suka cigaba da tafiya dan yanzu wasa wasa su husnah zasu kai sati shida da aure, dan fahad har yakoma makaranta amma satinsa daya yadawo gida weekend, ranar asabar da hantsi saiga nusaiba matar ya Abba yakawota dama bata taba zuwa gidanba,Bilkisu na falo tasha riga da wando masu taushi blue colour tana aiki a system dinta gefe daya kuma tana sauraren malam Aminu daurawa cikin shirinsa na tambaya mabudin ilmi, ranar fahad zai bar dakin husnah yakoma nata amma baya nan tun safe yafita shago saboda yataho da dinkuna sosai daga kd, tarba sosai Bilkisu tayiwa nusaiba har husnah tafito suna dan taba hira ita dai bilkisu jine nata saboda bata fiya hayaniya ba ita saima ka zauna da ita awa guda baifi tayi magana sau ukuba zuwa hudu sai dai dasu Hindu da khulsum kawarta tana sakewa sosai tayi hira dasu,wanka ta tashi taje tayi tashirya cikin doguwar gown ta atamfa tafito,tambayar nusaiba tayi me zata dafa mata tace komai ma, kitchen tashiga ta dora girki doya da vegetables sos bayan tagama ta zubo mata takawo mata, zance ta iskesu sunayi wanda ya dangancin kishi sai taji husnah daga ganinta tana cewa,

"Ai kuwa wallahi idan baka rike mijiba wata ce zata shigo ta rikeshi dakyau... Wasu matan akwai sakaci dan watama hatta abin shinfidar miji bata san ta adana ta alkinta ba sai dai idan yanada wata matar tabashi..."

"Ai mata sha'aninmu sai hakuri kishi yayi mana yawa..." Inji nusaiba, ita Bilkisu sarai tasan da ita husnah take sai dai bata da ajin da zata zauna tayi kace nace da ita, ita da wanda ya ajiyeta zatayi, akule tawuni har nusaiba tatafi amma bata tankawa husnah ba, la'asar liss fahad yadawo bata kulashi ba yayi shirinsa yafita ball, da daddare tana shirin bacci sai gashi yashigo tashi tayi tsaye cikin masifa tace,

"Malam bana bukatar wannan bargon da wannan bedsheet din acikin room dina ka fitar min dashi and you better warn your stupid wife wallahi idan tasake attempting yimin bakar magana ko gugar zana sai ranta yabaci saboda ni ba sa'arta bace..."

Tunda yaji haka yasan akwai abinda yafaru ko kuma husnah tafada mata wani abu, fita yayi yamayar dasu blanket din dakin husnah lokacin ma ita tajima da yin bacci, sake komawa yayi dakin Bilkisu yatarar tafito masa da bedsheet da blanket. Zama yayi saman katifar da scissors a hannunshi wanda zai yanka wasu dinkuna,

"Me husnah tayi miki?" Ya tambayeta yana auna atamfar da yaware,

"Meya hana ita baka tambayeta ba?" Tabashi amsa tana kokarin kwanciya,

"Tayi baccine ai..."

"To sai ka bari sai ranar da tatashi saika tambayeta..."

"Allah yabaki hakuri dai zanyi mata magana insha Allah"

Bata cemasa komaiba tayi kwanciyarta tabarshi yana aikin yanka dunkuna, washe gari saida yayiwa husna fada sosai akan koma me tayiwa Bilkisu to kar ta kara aikita irinsa saboda ba mate dinta bace, sannan yace tabata hakuri badan tasoba tabi umarninsa sukaje tabawa Bilkisu hakuri tun daga ranar zamansu yaki dadi saboda husnah gani take kamar fahad yafi son Bilkisu kai kamarma tsoranta yakeyi saboda duk dadin da sukeyi daga Bilkisu tashigo zai daina yauma suna falo suna soyayyarsu yanata goyata amma bilkisu na dawowa daga aiki yadaina da tayi magana sai cewa yayi bata ganin antynta ta dawo ai idan sukayi agabanta gani zatayi kamar sun cimata fuska wannan abu shine yakona mata rai har takasa jurewa saboda ko rikeshi tayi idan Bilkisu na wurin sai ya bata rai ita kuma bayan tadade da fara zargin kamar zamansu akwai wani abu saboda taga duk ranar kwanan Bilkisu da dinkunan da zaiyi yake tafiya dakinta acan zai

Please Login or Register in order to submit comment