Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

za agabatar da misalin karfe daya nan tazauna tajirata harta gama daga nan sukaje suka dauki permission suka nufi babbar kasuwa.

Ko acikin keke napep bilkisu sunata waya itada hamood har saida suka shiga kasuwar sannan sukayi sallama tafito daga napep din tana yiwa khulsum kallon ta ina yadace mufara? Shagon sayar da kayan kitchen suka fara zuwa domin tanada sauran siyayya da yawa wadanda bata karasa ba, sun bata lokaci sosai awurin domin yau so take tagama da wannan bangaren awuce wurin. Sai da suka kammala siyan duk wani abu wanda ke rubuce jikin list din da tayi awata takarda sannan ta biya kudin suka shiga can tsakiyar kasuwar domin dubo kayan da amare zasu saka na fitar biki da wanda ita kanta zata saka itada kawarta khulsum.

***

Kamar koda yaushe yauma yatashi cikeda zumudin sake jin muryarta domin ayaune take gabatar da shirinta mai farin jini wanda yake sanyaya zukatan masoya da duk wani mai sauraron shirin,

Yana daga kwance saman dingimemiyar katifarsa ya dauki agogon hannunshi silver colour kirar kamfanin LX,karfe 11 saura yan mintuna, cikinsa yashafa sannan ya mike yana gyara gajeren wandon dake jikinsa, farar t shirt dinsa mai dogon hannu yaja ya mike yafita yanufi cikin gida yana mai saka rigar, baiyi mamakin jin gidan shiruba domin yasan su maryam sun tafi makaranta haka shima baba yafita kasuwa, sai dai ko motsin ayiyah da mamuh baiji ba, dakin ayiyah yadaga labule ya shiga, ga kayan karin kumallonsa nan ajiye agefe dan haka ya zauna ya lankwashe kafafu yajawo kwanikan, dan karamin food flask ne dauke da gurasa wacce tasha kuli kuli yaji sosai da man gyada hadida tumatur da albasa da koren tattasai sai zuba kamshi take sannan ga koko nan a dan madaidaicin kwanon sha na silver sai kosai shima awani kwanon na daban, bisimillah yayi ya soma karyawa yana tsice danyar albasar dake cikin gurasar domin shi baya cin danyar albasa da danyar tafarnuwa, yana daf da kammalawa yajiyo maganar mamuh wadda tafito daga bandaki tana rikeda bokiti da kwandon wanka,

"Wannan ja'irin yasamu yafito ne? Bacci sai kace mai baccin mutuwa"

Murmushi yayi yashafa kansa,

"Ina kwana mamuh, ina ayiyan ne?"

Saida ta amsa gaisuwarshi sannan tabashi amsa da,

"Taje nan makota gidan mai dan wake jajjabin yaronta murtala wanda aka sacewa babur shekaran jiya"

Mikewa yayi yana cewa,

"Allah yarufa asiri"

Daga haka daki yakoma yashiga wanka bayan yafito ya shirya cikin kananan kaya brown din riga da blue din wando, saida yagyara sumar kanshi sannan yafita yanata zabga kamshin turaren Amirul oud, cikin gida yafara shiga yayi musu sallama sannan yawuce shago.

***

Sosai bilkisu takashe kudi wurin siyawa amare kayan da zasu saka banda nata da na mama da ta siya material mai kyau light blue da manyan atamfofi guda biyu sannan ga ankon da zasuyi ita da khulsum na wani golden din leshi, tunanin wurinda yadace su kai dinki suka farayi domin bata son takai kayan gida batare da andinka ba, khulsum ce tace ta taba ganin shagon wasu teloli daga waje can a albarka plaza nan suka ciccibi kayan suka fita,babu wani nisa sosai amma agajiye suke jinsu lis, suna shiga plaza din suka wuce sama ahawa na uku suka ga shagon wanda ke dauke da zanen dinkunan mata kala kala ajiki anruba _Golden scissors and fashion design_ a mutukar gajiye suka kutsa kai ciki bakin khulsum yana dauke da sallama

*_Ummi Shatu_*

[11/28, 08:14] Hafsat Rano: © *HASKE WRITERS ASSO* _(Home of expert & perfect writers)_



*KAMAR DA WASA....!*



_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*



*3*



***Nazifi ne ya amsa musu sallamar yayinda sauran kowannensu yana duke yana aikinshi,

Khulsum ciki tawuce ta zauna kan kujerar roba dake kusa da keken nazifi yayinda ita kuma bilkisu tazauna daga bakin kofa kusa da keken fahad wanda kansa yake asunkuye yana hada wata skirt ta atamfa, kamshin da yajine tun lokacin da ta zauna ya janyo hankalinsa har ya daga ido ya kalleta domin wannan shine karo nafarko da ya taba jin wani turare wanda ya sanyawa zuciyasa wani al'amari, ganinta yayi tana latsa wayarta yar karama kirar baby Nokia, ahaka yake dinkin sannan kuma yana aikin kallonta wanda kusan ita bata ma san yanayiba jimm kadan wayar tata tayi kara nan tatashi tafita yabita da kallo,shigarta ita tafi komai jan ra'ayinsa agameda ita domin gaba daya jikinta a lullube yake babu abinda zaka iya gani sai tafin hannunta da fuskarta dan ko kafarta asakaye take, bata wani jimaba ta dawo ta zauna tana sauraron su khulsum wadanda ke maganar dunkunan da suka kawo,

"Kawata ya za ayi? Daga nan gida zamu wuce ne ko zamu koma office?" Khulsum tafada tana kokarin ciro kayan da suka kawo daga cikin leda,

Saida ta dan ja numfashi sannan ta kalli khulsum din,

"Gaskiya muyi tafiyarmu gida..., yanzu haka da kikaga nafita director programs ne ya kirani wai naje nayi program dina shine nace masa bana nan kawai amaimaita na baya"

Tunda tafara magana ya dakata daga dinkin da yakeyi yana kallonta kasa kasa, muryarta ce ke kai kawo acikin kunnuwansa tabbas ko shakka babu itace macen da yajima yana burin gani, itace wacce muryarta ke sanyaya cikin kunnuwansa dan tsananin sanyinta sannan take sashi nishadi cikin kowanne irin yanayi ya tsinci kansa.

"Yanzu waye zaiyi mana wannan dinkin na amaren acikinku?" Khulsum ta bukata,

"Gaskiya sai dai ko prince domin kamar yafi iya dinkasu" Nazifi yabata amsa,

"Ina shi prince din?" Khulsum tasake tambaya,

"Gashi can " yanuna fahad da hannunsa, daga bilkisu har khulsum juyawa sukayi gareshi suna kallonsa hakan yasashi dauke manyan idanuwanshi daga kallon da yake yi mata kamar wani tsohon maye,

"Dan Allah zamu samu dinki?" Bilkisu ta tambayeshi tana kallonshi, lumshe idanuwanshi yayi sannan yabude cikeda kasala,

"Kala nawane?"

"Ko iya na amaren ne ma kala biyu sai kayi mana"

Girgiza kanshi yayi yana juya skirt din hannunshi,

"Zanyi harda nakin ma"

"Nikuma fa?" Inji khulsum,

"A'a ke banda naki"

"Ai kuwa baka isaba wallahi, mu kawo dinkin tare ita kayi mata ni ka ki yimin?"

Murmushi yayi batare da yadaga kansa ya kalli kowaba,

"Kawo kayan nagani" yace da Bilkisu, mikewa tayi bayan ta dora wayarta akan kekenshi taje ta dauko ledar kayan ta soma fito masa dasu tana yi masa bayani, shagala yayi da sauraron muryarta harta gama, tasowa khulsum itama tayi tazo ta ajiye masa nata bai ki ba duk ya hada ya karba yana tambayar measurements dinsu, khulsum Bilkisu tafara gwadawa da tape din da yabasu sannan itama khulsum tafara gwadata sai dai tun kafin khulsum ta fada masa yake rubutawa wuri dayane aka samu sabani Boob's dinta ya rubuta 34 khulsum tace masa 38,jinjina kansa yayi ahankali ya furta,

"Manyan mata"

Saida komai ya kammala sannan Bilkisu ta tambayeshi kudin dinki, na amaren cewa yayi subada 10k sai na khulsum 6k sai na mamaa ita kuma 4k,handbag dinta ta dauka tana kokarin ciro kudin,

"Nikuma nawa fa?"

"Ke sai bayan nagama dinkawa"

"To shikenan ga wannan din"

Kudin ya karba yana ciro wayarshi daga aljihu sakamakon karar da yaji tanayi ganin husnah ce ke kiranshi yasashi saka wayar a silent ya ajiyeta gefe, sallama su khulsum sukayi masa suka fita nan yayi tagumi yabisu da kallo su nazifi binshi da kallo kawai sukeyi domin su dai asanin da suka yimasa baya karbar dinki kai tsaye haka musamman irin wannan na gaggawa. Yajima ahaka kafin ya hakura yasoma tattara kayan yana sakawa cikin leda kamar amafarki yaga wayarta kan kekensa bayan ya dauke atamfar dake wurin, jujjuya wayar ahannunshi yayi kafin ya bude yasaka number dinshi ya kira, goge number tashi yayi bayan yakira wayarshi ya ajiye wayar agefenshi. Bilkisu kam saida sukayi nisa da kasuwa sannan ta farga cewar ta manto wayarta ashagon dinki cikeda takaici ta sanarwa da mai keke napep din yajuya suka koma. Koda sukaje gaban plaza din ita kadai ce tafita domin zuwa karbo wayar tabar khulsum acikin keke napep din,

Tunda ya hangota tana tahowa ya kafeta da idanuwansa domin dama gaba daya hankalinsa awurin yake, cike da nutsuwa take takawa sannu sannu wadda kallo daya zaka yi mata ka fahimci cewar hayaniya bata rabeta ba sannan ba magananniya bace domin yanayinta kadai ya isa ya gamsar dakai hakan.

Yana nan zaune tayi sallama tashigo, shine ya amsa mata sallamar domin su nazifi basu ma kula da shigowarta ba dalilin hankalinsu yana can ga kallon kwallon da sukeyi a yar karamar television dinsu dake can saman wata kanta,

"Sorry kamar nabar wayata a nan ko?" Tafada tana dube dube,

"Ehh gashi, nayi niyyar inbiku inkai miki ma but har kun rigada kun tafi"

Hannu ta mika ta karba tana fadin,

"Babu komai nagode"

Hannun nata yabi da kallo wanda yatsunta sukasha dark maroon din lalle wanda yayi mutukar kawata hannun,

"Karki damu, Allah yakiyaye hanya"

"Amin, nagode"

Daga haka tajuya tafice daga cikin shagon, kamar dazu yanzunma binta yayi da kallo kamar zai cinyeta har yadaina hangota sai lokacin hankalinsa yakoma jikinsa domin gaba daya lokacin da tana nan baya tareda shi. Murmushi yayi yajingina da jikin bango yana bin number dinta da kallo wacce ta kasance special number, sumar kanshi yashafa yana murmushi,

"Wato komai nata special ne kenan kamar yadda itama take special...."

Haka yaci gaba da zama yana kallon number dinta har husna tashigo ta iskeshi ahaka, zama tayi akujerar dake gaban kekenshi,

"Ya fahad murmushin me kakeyi?"

Duk da yana son ya daure mata fuska kamar yadda yasaba yau yagaza yin hakan yasan hakan baya rasa nasaba da farin cikin da yake ciki, lumshe idanuwansa yayi yana sake tuno fuskarta mai dauke da beautiful points wadanda ke kara mata kyau,

"Ya fahad ina dinkin nawa?"

"Na saidashi"

Murmushi tayi dadi yana ratsata, yau wacce rana fahad ya sakar mata fuska harda tsokanarta,

"Idan kasiyar ai nasan zaka siya min wanine shiyasa"

Tallafe kumatunshi yayi da tafin hannunshi na hagu yana kallonsa, hannu takai zata warci wayarshi yayi saurin kaucewa yana harararta,

"Wai bana hanaki tabani ba?? Meyasa bakya jin magana ne?"

Marairaicewa tayi tana kallonshi,

"Am very sorry my heart beat"

Baice komai ba yasoma laluben kayanta acikin tulin himilin kayan dake gefenshi, aranshi yana tunanin halayyar husna ta son tabashi shiyasa baya sakar mata fuska sosai saboda indai zatazo wurinshi to sai tayi yunkurin taba masa hannu ko wani abu mai kamada haka, ciro mata kayanta yayi ya ajiye mata agabanta sannan yatashi ya hado mata kan kwanukanta wadanda take kawo masa abinci duk da bawai ci yakeba dan su nazifine ke cinyewa, saida tagama janshi da magana da wasa sannan ta kwashi kayanta ta tafi, tashi yayi yafita salla ana idarwa yadawo yazo yasoma yanka kayansu Bilkisu.

***

Agajiye lilis takoma gida kamar koda yaushe yauma gidan acike yake da makota da kawayensu meenah amare domin anata shirye shirye,kanta yau har wani ciwo yakeyi sakamakon uban yawon da suka sha a kasuwa itada khulsum ga yunwa da take ji,

Sama sama take amsa kowa ta bude dakinta ta shiga itada hudah wacce ke makale da ita, tana zama Hindu tashigo rikeda lemon roba mai sanyi da ruwa,

"Yawwa yar albarka kamar kuwa kin san kishi nake ji sosai, gaskiya yau mun kwashi rana"

"Sannu anty mai gado, ai duk wanda yaganki yasan kin wahala"

"Kedai bari Hindu" tafada tana balle murfin robar lemun"

"Inkawo miki abincin?"

"Kawo min Dan sai nafara ci sannan zanyi salla" tabata amsa tana kokarin bawa hudah lemon abaki, fita Hindu tayi ita kuma taci gaba da karbar lemon tana bawa hudah.

Shinkafa da wake da ganye Hindu ta kawo mata da manja da yaji nan ta sauko taci sannan tashiga ta watsa ruwa tafito tayi salla, nan inda tayi sallar suka baje itada hudah suka hau bacci.

***

Fahad bai bar shago ba sai bayan sallar magrib domin saida yagama yanka kayansu Bilkisu kaf sannan yanufi gida duk da irin tarin yunwa da gajiyar dake baibaye dashi, lokacin da yaje gida bai shiga cikiba dakinsu yafara shiga yayi wanka sannan yashiga cikin gidan, dukkansu suna falon mamu suna kallon wasan kwaikwayo na aku mai labari wanda ake gabatarwa agidan television din ART, daga bakin kofa yatsaya yagaidasu sannan yawuce dakin ayiyah duk da yanajiyo tsokanar da mamuh keyi masa bai kula ba domin yunwa yakeji dan rabonshi da abinci tun safe.

Abincin dare yazuba yaci wato tuwon biskin masara miyar taushe yana ci yana santi har yagama yafito bai koma inda su ayiyah sukeba yafice ya nufi dakinsa, farar jallabiya yasaka yafita sallar isha'i domin daf ake da ashiga. Koda aka idar yadawo kwanciya yayi da niyyar runtsawa amma sam yakasa yin baccin sai juyi da yafara yi, fuskarta kawai yake gani wacce ke dauke da murmushi tana yimasa magana,bashida zabi illa na yabi shawarar zuciyarsa ko zai samu sassauci.



*_Ummi A'isha_*


11/28, 08:14] Hafsat Rano: © *HASKE WRITERS ASSO.* _(Home of expert & perfect writers)_


*KAMAR DA WASA...!*??



_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*



*4*



***Kasa nutsuwa yayi sakamakon dukan luguden da zuciyarsa keyi tamkar zata faso kirjinsa tafito waje dan tsananin zafin sonta, ahankali cikin sanyin jiki yatashi ya dauko wayarshi wacce ke ajiye tana charge saboda akwai wutar nepa agari,

Komawa yayi ya kwanta ya lalubo contact dinta, _soul mate_ shine sunan da yasaka mata nan yakurawa number tata ido kamar wanda ke son haddaceta har zuwa tsawon wani lokaci, yanke shawarar tura mata da sakon karta kwana zuciyarsa tayi nan ya rubuta mata ya tura mata cikeda shaukin kaunarta har saida yaga sakon ya tafi sannan yaji ya dan samu nutsuwa, ajiye wayar yayi akusa dashi kamar wadda ake jira nan tasoma tsuwwa amma bai kulaba domin jikinsa yabashi husnah ce wadda ba komai zata fada masaba illah ta kara masa damuwa dan haka yashare yaci gaba da tunanin abar kaunarsa.

***

Jikinta sanye da yar guntuwar karamar riga kalar ruwan madara wacce take marar nauyi da kauri tana tattara wani report da zata gabatar acikin laptop dinta taji shigowar sako, duk da bata dubaba saida tayi murmushi domin tasan bazai wuce hamood dintaba wanda ko mintuna biyar kwarara basuyi da gama wayaba, saida ta shanye sanyayyen lemon dake gabanta sannan ta janyo wayar bayan ta rufe laptop din. Kwanciya tayi tabude sakon, abin mamaki yabata saboda ganin wata number wadda bata hamood ba, cikin mamaki ta soma karantawa kamar haka, _Salam yake kyakkyawa,hakika kinyiwa zuciyata wani tarko mai wuyar Ketarewa, ganinki sau daya tal yana barazanar kawar da tunanina daga gangar jikina, wallahi ban taba ganin wata halitta wacce tayi daidai da ra'ayina kamarki ba, kece mace tafarko da nafara so tun kafin nayi ido biyu da ita, dan Allah karki ki k'i amsar soyayyata domin idan baki amintaba zan iya rasa rayuwata akan sonki, wallahi ina mutukar sonki, ina sonki bilkisu._

Dora wayar tayi akan kirjinta gabanta yana faduwa sannu sannu, aranta tana tunanin to shikuma wannan waye shi? A ina yataba ganinta da har yaji yana sonta? Bata da amsa dan haka tayi watsi da tunanin batare da tabarshi yayi tasiri acikin zuciyarta ba. Addu'ar bacci tayi ta shafa tayi kwanciyarta bayan takashe wayarta, amma me koda gari yawaye tana kunna wayarta sakonshi ne yafara shigowa cikin wayarta inda yake yimata barka da safiya da wasu kalaman soyayya masu sanyaya zuciyar masoya, dan guntun tsaki taja ta ajiye wayar gefe ta kwanta batare da tabi takan mai turo sakon ba.

Aranar ko aiki bataje ba domin sunata soye soye da dafe dafe kasancewar ranar za akawo lefen meenah, itace akan komai gashi gidan ba laifi yayi albarka domin yan uwa na kusa da makota duk anshigo domin karbar kayan, sai misalin karfe uku na yamma aka kawo kayan nan aka shiga tarbar baki da abubuwan da aka tanadar musu basu bar gidanba sai bayan da sukayi sallar la'asar sannan suka tafi nan kuma makota aketa shigowa ganin kaya wadanda suka kasance akwatuna hudu manya sai dan karamin kit na biyar kalar ruwan kasa ita kuma Hindu sai nanda kwana biyu za akawo nata. Ita dai bilkisu yau tunda tatashi kanta adaure yake domin maiyi mata sakon nan ba dainawa yayi ba sau hudu kenan yau yana turo mata sakonni masu dauke da kalaman so da kauna tun tana sharewa har ta zauna tana son sanin waye.

***

Fahad yau tunda yafita shago baiyi aikin kowaba sai nasu bilkisu nata yawuni yana hadawa domin dinki na musamman yayi mata wanda babu irinshi ashagon kuma koda yagama hadawa bai barshi ashagon ba bare har aratayeshi a hangar wurin da suke rataye kayan da suka dinka, shi kansa ya yaba da dinkin da yayi mata shiyasa yake jin zuciyarshi wasai, Abu daya kawai yanzu yake bukata shine yaji muryarta amma yasan hakan ba mai yuyuwa bane. Wata numbershi wadda bai cika amfani da itaba yasa numberta yakirata amma harta tsinke ba adaga ba sai da yasake kira sannan yaji ta dauka cikin sanyayyiyar muryarta wadda kamar tana bacci, sallama tayi amma sai yasamu kansa da kasa amsa mata domin wani irin faduwa gabanshi yasoma yi wanda bai san daliliba,

Sau uku tana fadin "hello.... Hello....., hello"

Jin bai amsaba takatse wayarta, wata nannauyar ajiyar zuciya ya sauke sai lokacin yaji yasamu kwarin gwiwar yin abinda yake gabansa, tashi yayi ya tattara inasa inasa ya nufi gida lokacin misalin karfe biyar da wurin mintuna ishirin, yana zuwa gida kayan ball dinsa yasaka yafita batare da yashiga koda cikin gidanba acan yasamu ya ragewa kansa damuwa domin sai karfe 6 da wani abu yadawo. Wanka yayi yasha turare kamar wanda zaije zance yafita masallaci can yayi zamansa shida saleem har saida sukayi sallar isha'i sannan suka fito, wani sabon zaman suka sake dasawa akan dakalin simintin dake kofar gidansu saleem wanda wurin yake fuskar mutane ga hasken farin wata wanda ya hadu da hasken lantarkin dake kafe atsakiyar layin wanda ya ratsa ta cikin unguwar tun daga farkon layi har zuwa babban titi can gefe daya kuma yarane dankam masu soya awara nayi wasu kuma gyada suke saidawa da dafaffen kwai da sauransu.

Daga kansa sama yayi yana kallon taurari wadanda suka karawa sararin samaniya ado da kawa, cikin sanyin murya yafurta,

"Abokina am in love....."

Juyawa saleem yayi ya kalleshi yana murmushi sannan ga alamun mamaki nan bayyane akan fuskarshi,

"Yaushe? Kuma wacece?"

Lumshe idanuwa fahad yayi yana jin wata sabuwar soyayyarta tana shigarshi,

"Wata classic beb ce, kuma wallahi najima dauke da sonta"

"Kodai husnah ce?"

Harararsa fahad yayi kasancewar akwai yalwataccen haske yasanya saleem ganin hararar hakan yasashi yin murmushi sannan yadafa kafadarshi,

"Bani labarinta abokinah..."

Saida yayi murmushin da shi kadai yasan dalilin yinsa sannan yafara fada masa,

"Nafara sonta ne tun ban gantaba, tun ranar da nafara jin muryarta a radio tana gabatar da wani shiri naji tashiga raina, kullum da ita nake kwana nake tashi, cikin ikon Allah sai gata jiya a shagonmu ta kawo min dinkunanta..... Amma bana jin zata soni" Yakare maganar yana cizar lips dinsa cikeda damuwa,

"Saboda me kake ganin bazata soka ba? Kanada wani mummunan haline wanda ban saniba?" Saleem yafada yana fuskantarshi,

"Sam bahaka bane, saleem ta girmeni fa, jikina yana bani bazata yi accepting dinaba saboda zatace nayi mata yaro dayawa may be ma zata ji kunyar nunani awurin friends dinta da relatives dinta"

Dariya saleem yayi yana dafashi,

"To kai da waye ya aikeka son wacce ba sa'arka ba?"

"Saleem kenan, shi so ba ruwansa da cancanta,shekaru ko duba matsayi, kawai yakan shigane aduk sa'ilin da yaso koda kuwa ba ashiryawa hakanba, saleem wallahi dagaske ina sonta, ni girmemin din da tayi ba damuwa bace zan iya rayuwa da ita mutukar zata yarda ta aureni"

Shiru saleem yayi yana kallonsa, ganin yanda yanayin idonshi ya sauya zuwa ja yasashi gasgata aminin nashi,

"Abokina ka kwantar da hankalinka, ina kyautata zaton koma wacece zata soka itama domin baka da makusa kuma bakada wani hali ko dabi'a wadda bata kirkiba, kana da zuciyar neman na kanka sannan kana da kyakkyawar mu'amula da kowa, kayi addu'a abokina insha Allah zaka dace"

Kalaman saleem sune suka sanyayar mishi da zuciya sannan yasashi jin nutsuwa ta saukar masa, cigaba da kwantar masa da hankali saleem yayi har saida yaji acikin ransa zai samu bilkisu, cikeda farin ciki suka rabu da saleem yana tsokanarsa,

"To kai ka isa aurenne?"

Girarshi guda daya ya dage masa yana kallonsa cikeda mamaki,

"Nine ban isa aureba? Kabari abani matar a lokacin zaka fahimci na isa ko ban isaba"

Daga haka yamike yakama hanyar gida yana jin saleem har lokacin yana tsokanarsa amma bai tsayaba.....

© _*HASKE WRITERS ASSO.*_ _(Home of expert & perfect writers)_



*KAMAR DA WASA.....!*



***Hannayensa gaba daya ya aza cikin aljihun wandon bakin jeans din dake jikinsa, jar rigace ajikinsa mai rubutu kamar haka, _All the best_,yana tafe yana kallon dukkan jama'ar da kowa hada hadarsa yakeyi, wayarshi ya zaro daga cikin aljihun wandonshi domin duba ko waye ke kiransa sunan Nazifi yagani abokin aikinshi domin shagonsu daya, yana dagawa yaji yace,

"Prince ga wasu sun kawo dinki wai nanda next week suke so"

"Gaskiya bazasu samuba dunkuna sunyi min yawa"

"Hakane but amma naga ka karbi na wasu jiya ai"

"Ehh hakane amma ai kadai fi kowa sanin yawan dinkunan dake zaman jirana ko"

"Babu damuwa bari nakira hamza naji"

Katse wayar fahad yayi aransa yana cewa "yadai fi domin ita wadda kaga jiyan na karbi nata daban take bazan iya bari wani yayi mata ba shiyasa"

Ahaka yakarasa gida direct cikin gidan yawuce domin cin tuwo baba yahango kofar dakin mamuh yana magana dasu maryam wanda baya iya jiyo mai yake fada,durkusawa yayi kasa yagaida shi sannan yawuce dakin ayiyah yana dallawa Mariya harara saboda laifin da tayi masa da sassafe tun kafin tatafi makaranta, zaune ya iske ayiyah tana damawa baba fura acikin kwanon sha na silver da ludai ga sukari agefe cikin wani kofi madaidaici, zama yayi gefenta yana fadin,

"Ayiyah kamar kuwa kin san yunwa nake ji"

"To ai ga tuwon tsari nan miyar kubewa da mamanku tayi sai ka saka kaci idan kaci sai kasha fura"

"Ai kibar tuwon nan kawai ayiyah iya furar kadai zansha"

Kafin tayi magana baba yayi sallama yashigo, matsawa fahad yayi yabashi wuri ya zauna kan lallausar dardumar dake shimfide awurin,

"Muhammadu wai yaushe dan uwanka zai bullo ne?"

Murmushi fahad yayi domin yagane Abba yayansa baba yake nufi, gyara zamansa yayi yana daukar cup din furar da ayiyah ta zuba masa,

"Dazu munyi video call dashi baba yace insha Allah cikin karshen satin nan zaizo gida"

"To Allah yakawo shi lafiya muna zuba ido, ai saika yanke masa wadancan barun naka ko ko kaji ayi masa sauka"

Murmushi yayi bayan yazare cup din dake bakinsa ya hadiye furar da ya kurba.

"A'a baba,zan dai siyo masa akasuwa sai ayiya ta dafe masa su amma wadancan na kiwone bana ci ba"

Ayiyah tana mikawa baba furar da ta dama masa ta daga kai ta kalli fahad,

"Ni ban taba ganin irin wannan kiwon ba sai awurinka ayita kiwata abubuwa amma baza aciba..."

"A'a ai kedai babu ruwanki, barni dashi" Inji baba,

Murmushi fahad yayi yakarasa shanye furar da yake sha,

"Baba ayi min hakuri dai har sai sun kara yawa"

"Ni ai bance komaiba muhammadu, Allah yasa albarka"

"Amin babanmu"

Daga haka yatashi yafita,sai da ya leka dakin mamuh ya rarrankwashi mariya sannan yafito yana kunkunin idan tasake zuwa sassafe ta buga

Please Login or Register in order to submit comment