Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yanzu me kake nufi? Nufinka kenan wannan ciwon da taji min taci bulus bazaka tsawatar mata ba?"

"Kinga bilkisu dan Allah kibarni naji da bakin cikin satar da akayi min, nidai nafada miki babu ruwanki da ita idan kuma bahaka ba to jiki magayi...."

Tsabar bakin ciki kasa cewa komai tayi har yafita daga dakin, tagumi ta rafka tama rasa wanne irin tunani yadace tayi. Tun daga wannan rana takoma rayuwar daki domin bata fitowa sai idan wani abu zatayi shiyasa zaman gaba daya ya dameta kuma ya gundireta wannan dalilinne yasata yanke shawarar tunkarar hamood da maganar komawarta aiki ko tasamu tarage kadaicin da take ciki tunda ko babu komai fitar zaiyi keeping dinta busy, aranar da daddare bayan yashigo ta sameshi da maganar wani kallo yayi mata irin na yan iska sannan yaci gaba da abinda yakeyi yana cewa,

"Mai gado kenan, wai ke wacce irin macece? Atunaninki zan amince dake har inbarki kifita aiki bayan alhalin nasan har yanzu wannan karamin yaron ba daina sonki yayiba? Ai sai kuhada kai kurinka ha'intata..."

Cikin bacin rai ta kalleshi bakinta har rawa yake yi,

"Hamood kallon da kake yimin kenan? Wannan itace sakayyar da zaka yimin? Idan har Zan iya hada baki da fahad inci amanarka to meya hana inzauna tare dashi tun farko?"

"Look mai gado dan Allah karki nemi yimin hayaniya yanzu saboda agajiye nake i have to rest so pls walk out....."

Bakinta abude da mutukar mamaki tajuya tafice zuwa dakinta rasa wanne irin fassara zata yiwa wadannan kalaman na hamood tayi, wato dai yanaso yace mata bai yarda da itaba? Kasa bacci tayi a wannan daren shiyasa tunda sassafe takira abbanta awaya ta sanar masa nan yace zai kira hamood din tabashi number dinsa, wurin 9 yashiga dakinta yace tatashi zasuje gidansu abbanta na nemansu duk wannan maganar yana yinta ne cikin daurewar fuska, haka suka je gidan babu wanda ke cewa ko uffan Abba yana zaune falonsa yagama karyawa amutukar ladabce hamood yagaida Abba da Ammah kowannensu ya amsa fuska asake sannan Abba yayiwa hamood maganar da yakirashi dominta wato na komawar bilkisu aiki,

"Hamood mai gado ta kirani tace tana son zata koma aiki amma da tayi maka maganar kanuna kamar baka aminceba domin ma tamkar har yanzu baka gama yarda da itaba hakane....?"

Sosa keya yasoma cikeda ladabin karya yace,

"Abba wallahi bahaka nake nufiba, nidai kawai banida ra'ayin matata tayi aikine nafiso tazama full hause wife"

"To shikenan ke mai gado kinji abinda yace, tunda baya bukata kiyi hakuri...
Kibari anjima zan turo miki kudi a account dinki sannan duk sanda kike da wata matsala ki sanar dani..."

"Shikenan Abba, nagode madalla"

Tafada tana share hawayenta, anan hamood yatafi yabarta zata wuni bayan yatafi su amma Nasiha suka yiyyi mata har tasaki ranta, tun kafin tabar gidan taga abba yatura mata dubu dari biyar cikin account dinta, bayan sallar magrib tana niyyar tafiya saiga Abba yadawo shida ya mudan wanda yakawoshi gida daga garko domin yau can abban yaje kuma cikin rashin sa'a motar da suka tafi da ita tasamu matsala ganin zata tafi Abba yace ya mudan yakaita gida, baya tashiga suka tafi lokacin da sukaje kofar gate din gidan anan ta sauka suna yin sallama da ya mudan hamood yadanno motarsa shida wise hakimce agaba kamar kullum tayi daurinta na ture kaga tsiya.........



*_Ummi Shatu_*

*Wannan littafin na siyarwa ne me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*



34 ***Tana shirin barin wurin hamood yakaraso shida wasila wani mugun kallo ya watsa musu ita da ya mudan sannan ya danna hancin motarsa zuwa cikin gida, bata kara ko mintuna ukuba tashiga itama tabar ya mudan zaune yana jimami tambayar zuciyarsa yake tayi,

"Wai dama wannan shine mijin da bilkisu ta aura?"

Yayiwa kansa tambayar nan tafi sau dari kawai tunani yake shin yafadawa bilkisu gaskiya ko kuma karya fada saboda ko babu komai ai yar uwarsa ce daga karshe dai yabi shawarar zuciyarsa na kawai yaja bakinsa yayi shiru domin gudun abinda zaije yazo jan motarsa yayi yabar wurin yanufi gida.

Bilkisu adarare tashiga cikin gidan saboda iya kallon da hamood kadai yayi musu ya isa sanar mata cewa there is something wrong, tana shiga falo suna tsaye shida wise juyowa gaba daya yayi yana harararta,

"Daga ina kike? Maigado bafa zan lamunci yawon ta zubar ba acikin gidan nan..."

Ita tsabar takaici ma sakin baki tayi tana kallonsa, har saida yadiga aya sannan tayi magana,

"Lallai hamood, ya mudan nefa dan uwana abba yasa yakawo ni tunda kai bakaje ka daukoni ba..."

"Ni bawanki ne da zanje na daukoki ko kuwa ni driver dinkine? Kishiga hankalinki kin gane ko..... Aikin banza kawai Malam haka kawai najawa kaina masifa naje na jajibo yar matsiyata...."

Zaro ido bilkisu tayi tana kallonsa,

"Hamood ni kake kira da yar mutsiyata? Wallahi karyar mutum yakira iyayena da wannan sunan, yayan matsiyatan dai suna inda suke..."

Daga haka tawuce sama tana shiga daki tazauna tana ta surutu ita daya cikin masifa,

"Haba wannan wacce irin rayuwace wai? Mutum kullum idan banda cin mutunci da jaraba bashida zance.... Ni wallahi zaman gidanka yafita akaina gaba daya nagaji da igiyar aurenka haba...."

Tun daga ranar tsakaninta da hamood babu daddadar magana abu kadan sai zagi ita dai ji take ankusa zuwa gabar da dole zata bar gidansa domin gudun kada cutar hawan jini ta kamata saboda kullum cikin bacin rai take da damuwa idan yau basu debota da hamood ba to sai sun haura da wise shiyasa duk tabi ta lalace ta fige, tana cikin wannan halin bikin khulsum yazo bilkisu nason taje ayi komai da ita kamar yadda khulsum din tayi mata amma fafur hamood ya hana sai bikin dai yabarta ranar da za afara bikin tun sassafe tabar gidan domin dama jinta take kamar akan kaya, gidan hamood ya zame mata tamkar kurkuku, duk ankon da aka fitar ta turawa khulsum kudi ansiya mata dama ko takan hamood bata bi ba domin wani wulakanci yake ji kwana biyun nan, zuwanta gidan bikin cikin mutane yasata mancewa da damuwarta domin ga kawayensu nan yan makarantarsu da abokan aikinsu, kwana uku aka dauka ana yin bikin sai da aka kai amarya gidanta sannan bilkisu tasamu zama. Lokacin da ta koma gida babu kowa agidan daga hamood har wise din asalima ita daya ta kwana agidan, washe gari ma haka kai saida tayi kwana uku ita daya ce kwal cikin gidan tana rayuwarta takira hamood yace mata yana abuja amma yau ko gobe zai shigo so take yadawo ayi wacce za ayi domin yakamata su nemi magani saboda tagaji da wannan zaman na cuta domin akwai cutarwa acikinsa. Tana zaune falo tana kallon tashar zee world mai gadi yayi mata knocking, hijab tasa ta leka cemata yayi sunyi bako wai hamood ne ya aiko shi, fita compound din gidan tayi, kamar a mafarki taga dr Abrar wato tsohun saurayin khulsum kawarta domin kamarma shi zai auri khulsum din Allah ne dai baiyiba kawai,

"Ahhhh likita... Yau kai nake gani?"

Murmushi yayi yafito daga cikin motarsa,

"Hajiya Bilkisu yan jarida..., ya aikinku? Ina kawarki ashe tayi aure ta kini ko?"

Dariya bilkisu tayi,

"Likita ba kinka tayi ba kawai dai Allah ne baiyi zaku zama ma'aurata ba..."

"Adai yimin dadin baki irin na yan jarida..."

"Ba dadin baki bane gaskiya ce kawai Dr..."

"Wai dama kece wacce hamood yace inkawowa sakon nan?"

"Ehh nice..."

Tafada cikin murmushi,

"Ok to amma meyasa ban taba ganinki a asibitinba? Ai akwai tarurruka da ake shirya muku domin wayar muku dakai da kuma shawarwari da ake baku na musamman domin kula da lafiyarku... Idan har zakubi ka'ida to ko mai lafiya bazai fiku walwala da tsawon kwana ba...."

"A'a likita wai meke faruwa ne? Wanne ciwo kenan?"

Gyara tsayuwarsa yayi, cikin murmushi yace,

"Karki damu bilkisu u know am a Dr,wai dan nasanki ko kin sanni isn't something bad duba da yanayin aikinmu am always confidential soo feel free, wallahi da asibiti ma kikazo bazan taba nunawa cewar nasanki ba that's the rule.... Mu a ka'idar aikinmu koda ace kasan mutum when he comes to u with such case zaka nuna kamar ma baka taba ganinsa ba sai ranar unless shine yayi maka magana i hope u understand?"

Goge fuskarta tayi da gumin dake tsattsafowa tasake kallon Dr abrar dakyau,

"Likita dan Allah fada min in a simple way da zan fahimta saboda ni duk wadannan maganganun naka babu wanda na fahimta am confuse...."

"Bilkisu kenan.... Wai bake hamood yacewa zai aiko akawo muku magani ba? Last 3 days yaje hospital wurina karbar drugs dinsu wanda yakesha saboda lalurar da yake dauke da ita but unfortunately ranar babu maganin ba akawo ba kuma yace min tafiya zaiyi amma idan ankawo intaimaka inkawo masa gida zan samu matarsa sai nabata saboda itama tanada bukata u know he's my childhood friend...."

"Nidai to... Amma wallahi har yanzu ban ganeba da dai wasila na nanne may be ita yake nufi not me..."

"Wasila....?, wasila kuma? Har yanzu suna tare da wasila?"

"Likita kasanta ne...?"

"Ehhh ai itace ta jona masa HIV din... Can wurin yawon barikinsu suka hadu, dama suna tare?"

"Kana nufin ba matarsa bace?"

"Mata? Mata kuma? Tayaya wasila tazama matarsa? Sai dai ko farkarsa...."

Ai tun kafin ya karasa bilkisu take jin jiri yana daukarta abu biyune suka taru suka dagula mata lissafi awannan lokacin nafarko jin wai hamood yanada HIV na biyu kuma jin wai wasila karuwarsa ce, sama sama take jin bayanin likita amma tunda jimawa tadaina fuskantar komai maganin tasa hannu ta karba daga nan tawuce ciki jiri yana cigaba da daukarta ko sallamar da yake yimata bataji.


***

Cikin nasara admission dinsu fahad yafito kuma yasamu inda suka bashi BSC laboratory level 200 saboda result dinshi na diploma yayi masifar kyau dan da distinction yafita kuma SLT ya karanta shiyasa, shi anasa zabin ma pharmacy yaso subashi yadora amma suka bashi laboratory dole babu yadda ya iya hakan zai daure ya karanci lab din,babu bata lokaci yashirya yaje ya karbo admission letter dinshi, har makaranta ya kaiwa husnah tagani tayi congratulating dinshi, suna tare yaya Baffa yayan salim yayi masa waya wai yazo ya sameshi agida, sallama yayiwa husnah yahau Babur dinshi yatafi yana zuwa yaya baffa ke sanar dashi wai wasu turawa ne zasu karbi hayar gidansa idan har zai basu zasuyi aiki na shekara daya agarinne kuma a wannan area din suke son gidan, baba fahad yakira awaya ya sanar masa babu bata lokaci baba ya amince shima fahad baida zabin da yawuce ya amince din, cikin kwanaki biyu aka gama komai aka bawa turawa gida suka hau gyarashi,kudi mai yawan gaske suka biya aka sakawa fahad cikin account dinsa. Da wadannan kudin yadiba yaje yayi registration ya kama hayar dakin da zai zauna anan opposite din makarantar wanda ya kasance private hostel na manyan yara shi dinma a babban yaron yafito bayan yagama registration yakoma gida zaije yashiryo yadawo saboda nanda yan kwanaki za afara lectures.




*_Ummi Shatu_*

*Wannan littafin na siyarwa ne,me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*


35***Babu bata lokaci fahad ya kammala shirye shiryensa na tafiya makaranta domin shi aburinsa idan yatafi bazai dawo gidaba sai semester ta kare, duk abubuwan da zai bukata ya tanadi kudinsu domin acewarsa baya so ya debi kaya daga nan kano har zuwa kaduna wai za arainashi yafi son sai yaje can sannan yasiyi komai, anan gida dai ayiyah da mamuh sunyi masa jar miya cikin plastic da dakakken jan yaji mai daukeda tafarnuwa wai dan adan saukaka masa yayinda su anty Fauziyya suka yimasa snacks. Ana igobe zai tafi yaje gidajen yan uwansa duk yayi musu sallama shida salim bayan sallar ishah suka dawo gida bai samu ganin husnah ba a wannan dare domin ka'idar makarantarsu karfe 6 ake rufewa, shiyasa yabari sai washe gari da safe zaije ganinta before yawuce.

Lamo yayi kwance bisa katifarsa yana sake sake acikin ransa wato gaba daya rayuwar nanma jarrabawace acikinta da gaibu saboda duk yadda kakai ga shiryawa kanka rayuwa baka taba sanin abinda zai faru gobe komai iya hasashenka shidai koda wasa bai taba kawowa zai yi soyayyar aure da husnah ba asalima kallon mai dan tabin hankali yake yimata ada amma yanzu duk da bajin sonta yakeyi acikin ransa ba tana da wani muhimmanci agareshi, bilkisu dai insha Allah yamanta da ita koda kuwa hakan zaisa ya dawwama acikin bakin ciki da damuwa. Washe gari kamar yadda ya tsara bayan yagama shiryawa cikin kananan kaya bakin jeans da t shirt din polo yellow, hatta takalmin da yasaka na kamfanin polo ne da p cap, gidansu salim yaje yayiwa mamansu sallama sannan suka wuce wurin husnah tare, kasancewar weekend ne bata da class shiyasa da personal tafito tasha yellow din atamfa mai zanen kwarya, tana karasowa salim yafara tsokanarsu,

"Kaga amarya da ango.... Wato tsabar ma zuciyoyinku anko suke da juna shine harda saka kaya kala daya...."

Murmushi fahad yayi itama haka amma batace komai ba sai fahad ne ya mayar masa da martani,

"Kasan aduk lokacin da masoya suka shaku da juna to komai nasu rikidewa yake yakoma iri daya shiyasa sai ka gansu tamkar wasu yan biyu... Ni bakaga har wani kama mukeyi da ita ba.... Ko husnah ta? Ai kamarmu daya ko?"

Dariya tayi tarufe fuska tana fadin,

"A'a ya fahad wallahi kafini kyau..."

Dariya yayi yana kallon wani wuri,

"To ai kinfini haske Asma'u kuma ma dai kamar tamu daya..."

"Kana dai kawai tsokana tane fa..." Tafada cikin shagwaba,

"To kuma meye abun turo min bakin? Ko kina son inbaki goodbye kiss ne...."

Dariya tayi ta juya masa baya,

"Nidai bana so..."

"Nima bance kina so ba kawai tambayace yan matanah...."

Shidai salim ashe yajima da sulalewa yabasu wuri yana can zaune gaban wata bishiya mai dauke da benci a karkashinta,

"Ya fahad dan Allah idan katafi karka manta dani.... Karka maye gurbina da wata... Wallahi idan kayi min haka zan iya rasa raina..."

Saida ya matsa kusa da ita sannan yafara yimata magana kasa kasa cikin alamun rarrashi da tarairaya,

"Haba husnah ai ko amafarki bazan taba mantawa dake ba.... Kina da wani babban bangare acikin zuciyata, kisa aranki akoda yaushe kina cikin zuciyata kuma insha Allah bazan taba zama sanadiyyar rasa rayuwarki ba domin zan baki kulawa zan sadaukar miki da lokutana aduk lokacin da kika bukaci hakan.... Amma kin san me? Karfa nima ina tafiya kiyi min kishiya...."

Murmushi tayi kwalla tana ciko idanuwanta,

"Ya fahad only u, kasa wannan aranka nice dai nake tsoron yanmatan Jami'a kar inje ina nan wata ta kwace min kai...."

"Husnah no need to worry about that....saboda ni wallahi tsoron mata nakeyi yanzu.... Karki dauka da wasafa... Seriously tsoron mata nake ayanzu dai...."

Kallonta yayi yanda take hawaye dagaske tana gogewa,

"To menene wai na kukanne?? Idan bakya son natafi shikenan sai infasa karatun husnah indai hakan zai saki farin ciki..."

Girgiza kai tayi tana share hawaye,

"A'a ya fahad kaje, Allah yabasa sa'a.... Sai munyi waya"

Daga haka tajuya tatafi yasan wani kukan takeyi wanda bata son yagani duk kuma sai yaji wani irin tausayinta yana shigarshi, shida yazo suyi sallama amma gashi tatafi da kuka ko sallamar ma bata bari sunyi ba.

"Allah sarki husnah Allah yabani ikon faranta miki...."

"Amin" salim ya amsa wanda karasowarsa wurin kenan, dafa kafadar fahad yayi yahau bayan Babur din yana cewa,

"Rabuwar masoya tana zafi gashi ku baku sababa....."

"Dallah can... Meye hakan"

"Ahh waka ce mana nake yimuku... Allah sarki husnah..."

Buga Babur din fahad yayi suka fita sai da suka bar kofar makarantar sannan yace da salim,

"Salim wallahi husnah tausayi take bani... Ina tsoron kar zuciyarta tashiga wani hali saboda soyayyata kamar yadda tawa zuciyar ta tsinci kanta sakamakon halin da bilk....."

Sai kuma yayi shiru domin baya son tunata baya kaunar tunawa da ko sunan bilkisu arayuwarsa domin abinda yafaru tsakaninsu shine abu mafi muni da ya taba faruwa dashi wanda baya jin zai iya mantawa,

"To ai indai zaka danne zuciyarka kanuna mata soyayya ka riketa da gaskiya bazata taba shiga halin da kake tsoron shigarta ba...."

"Zan kokarta insha Allah i will try my best to makes her happy,lovely and even special... I will for eva care for her"

Dariya salim yayi,

"Ai nasan zaka iya... Lover boy"

Da hirar husnah a bakunansu sukaje gidansu fahad yayi sallama dasu ayiyah har baba ma yana nan yana jiran tafiyarsa bai fitaba sai lokacin yake jin kamar zaiyi kuka, su maryam kam kukan suke tayi kamar anyi musu mutuwa shiyasa shima saida yaji kwalla na shirin zubo masa da koke koke dai yadau kayanshi yatafi shida salim wanda zaiyi masa rakiya har inda zai hau motar Kaduna.


Bayan sallar azahar yashiga kaduna, dakinsa wanda yakama yaje ya shirya kayansa yaci snacks ya kwanta domin hutawa duk da yana son shiga kasuwa yasiyo abubuwan da yake bukata na amfainin yau da kullum da kayan abinci. Zuwa dare ya kammala komai yagyare dakinsa tsaf ya siyo duk abubuwan da yake bukata, kwanciya yayi kan katuwar katifarsa ya bararraje ya kira gida saida suka gaisa da kowa na gidan sannan yakira ya abba shima suka dan taba hira sannan yakira husnah daga karshe ita kam hira suka sha sosai domin har 10 da wani abun domin shagwabar da yasaba yaketa zuba mata,

"Ko inje infadawa baba adaura mana aure akawoki nan mu zauna.... Ni kin san bana son harkar yunwa gashi bana son yin girki da kaina...."

"Ka rinka zuwa captaria kana ci mana..."

"Yanmatanah abincin saidawa farin maggi suke sakawa nikuma bana so idan naci sai nayi amai...." Yakarashe maganar cikin shagwaba, dariya husnah tayi,

"Ya fahad kaifa dadina dakai shagwaba...."

"Kin manta ni dan auta ne? Komai ayiyah tasamu ni take baiwa fa...."

"Su Mariya fa? Basune auta ba?"

"Ke wadannan fa "yayana ne, yaran sister nane..."

"Badai 'yayanka ba,'yayan Anty dai.... Kai ai tukunnah..."

Dariya yayi ya lumshe idanuwanshi,

"To me kike ci na baka na zuba..., nima din kwana nawane muna yin aure zaki haifo yan biyu kafin shekara ta zagayo...."

"Wai wai... Lallai ya fahad, yauwa dama inaso in tambayeka wai dan Allah...."

Jin tayi shiru yasashi bude idanuwansa,

"Menene? Go on ina jinki..."

"Wai meya rabaku da matarka"

"Husnah dan Allah kar muyi wannan maganar saboda ciwona zai iya tashi kinga nasamu kwana biyun nan yasauka...."

"Shikenan ya fahad insha Allah bazan sake yimaka magana kwatankwacin irin wannan ba,Allah yakara maka lafiya..."

"Thank you husnah"

Sun jima suna hira daga bisani sukayi sallama kowa zuciyarsa fari tass saboda dadadan kalaman da suka fadawa juna.

Washe gari yafara fita lectures tun aranar yayi friends guda uku dama su ukune tun level one suke tare haidar da Bashir sai mukhtar shi dai fahad baya son hada kai da kowa a makarantar nan kamar yadda su ayiyah sukayi masa fada akan ya tsaya yayi abinda yakaishi sannan banda kula abokai barkatai domin hakan babu fa'ida acikinsa amma saboda yanda suka manne masa dole saida ya kulasu dukda yana jin tsoro domin yaga kamarsu yaran manyane shikuwa ba dan kowan kowa bane sai dai sam ko kadan su basu nuna masa hakanba domin aranar ma dakinsa suka bishi bayan sun fito daga lecture harda kokawa akan guntun snacks din dake cikin jarida a nannade wanda yarage shiyasa shima ba adauki wani lokaci mai tsawoba yasaki jikinsa dasu saboda yaga basuda wani mummunan hali basa shaye shaye basa iskanci basa komai shi dama dan shaye shaye ya tsana bazai taba iya abota dashiba.Kullum suna tare su hudunnan kamar wasu yan hudu shi mukhtar gidansu a abuja yake sukuma su bashir duk yan cikin Kaduna ne, duk lokacin da suka fito daga lecture sai dai su zauna suyita bacci adakin fahad ko kuma wani lokacin suyita buga games a wayoyinsu ko game din kati shiyasa fahad yafara kokarin nemarwa kansa mafita domin baya son zaman nan na asara shiyasa ya yanke shawarar fara zuwa shagon dinkin da yagani tsallaken gidan da yake zaune su mukhtar nata tsokanarshi suna cewa yana babban yaro amma shine zai je yana dinki? Shi dai cewa yayi ehh babu komai ai Sana'a ce saboda yasan basuda masaniyar irin kudin da yake samu ta hanyar dinkin nan shiyasa kwana biyu da baiyiba duk jinsa yake sai shankali hatta kafarshi kumbura takeyi ita kadai tana sabewa.

***

Tunda bilkisu tazauna acikin falonta bayan tafiyar Dr abrar takasa samun nutsuwa gaba daya jinta take kamar acikin mafarki, takasa zaune takasa tsaye sai kaiwa da komowa takeyi burinta kawai taga dawowar hamood cikin gidan ta zazzage masa abinda ke cikinta,

"Wannan ai cin amanane da mugunta, ni hamood zai yiwa wannan butulcin...? Ohh my God.... What a heartless..... Wannan wacce irin mugunta ce..."

Wasu hawayene ke kwaranya daga cikin idanuwanta mikewa tayi tawuce bedroom dinta tasoma hada kayanta gashi abin haushi akwatunanta ansace balle tazuba kayan aciki duk da hamood yayi mata dadin bakin wai zai siya mata wasu, haka dai taci gaba da zama amma babu hamood babu labarinsa tana ta kiran wayarshi kuma akashe har dare bai dawo gidanba sai wise ce tadawo gidan da misalin karfe 10 nadare ko kallonta bilkisu batayi ba amma itama yau kallo daya zaka yimata kagane ashirye take da ko wanne irin bala'i wanda mutum keji dashi, babu wanda ya tankawa wani wise tawuce bedroom dinta wanda ke falon kasa sam hakan bai damu bilkisu ba ayau domin yanzu ita ba ta wasila takeba ta hamood takeyi so take yazo gidan ta kare masa tanadi amma abin takaici da bacin rai bai dawo gidanba har 12 nadare har lokacin bilkisu bata runtsa ba tana jiran taga ta inda hamood zai bullo anan falon ta kwana har asubah dama tunda tazauna bata tashi sai dai idan salla zatayi.

Safiyar ranar da misalin karfe goma tana zaune tana zaman jiran tsammani domin bata son tatafi gida tasake dawowa tafiso tatafi gaba daya da takardar sakinta ko wani abu mai kamada haka, ga kayanta nan agefe wadanda ta shirya domin tafiya dasu, akan idonta wise tafito tashiga kitchen ta dafo indomie tazo takoma daki, har takosa da zaman tana shirin tafiya inyaso sayita su kare awaya taji dirin shigowar motarsa, mikewa tsaye tayi ta rike kugu tayi tsayuwar ashirye nake da duk abinda mutum yazo dashi tana jijjiga kamar ansaka mata wayar wuta masiface rubuce kan fuskarta ahaka hamood yabude kofa yashigo ya isketa.....



*_Ummi Shatu_*

36***Tunda hamood yashigo ta dauke kai tamayar dashi gefe daya ganin haka yasashi shima hade rai yadaure fuska kamar bai taba dariya ba,

"Macuci.... Azzalumi..... Mugu to Allah ya toni asirinka....yanzu dama hamood kasan kana dauke da kwayar cutar HIV amma shine ka aureni ahaka har kake burin hada shimfida dani?"

Wani mugun kallo ya watsa mata sannan yazare farin tabaran dake sanye cikin idonsa, zama yayi kan kujera ya dora daya kan daya yana watsa mata kallon dake kara tafarfasa ranta,

"To sai me dan na aureki ina dauke da HIV? Bake kika manne min kika like min akan dole sai na aureki ba? Karfa ki manta har aurenki kika kashe dan kawai in aureki in zauna dake...."

"Ya isa haka malam.... Ai duk wadannan abhbuwan dakake ikararin cewar na aikata na aikatane acikin rashin sani... Kuma ina nadamar hakan ahalin yanzu, wallahi hamood kaci amanata kuma ka zalunceni wanda bazan taba yafe maka ba har abada.... Sannan ka gaggauta sallamata domin gidan ubana zan tafi insha Allah nagama zama dakai...."

Wata shakiyiyar dariya yasaki irin wacce ke dauke da mugunta tsantsa aciki sannan yayi mata kallon uku ahu,

"U are such an idiot mai gado, sai yanzu nasan bakida tunani sam.... Hmmmm to idan ke shashasha ce ni mai hankaline... Bazan taba sakinki ba koda kuwa za amaimaita yakin duniya akaro na uku.... And lastly abinda zan fada miki shine u should mind ur tongue kisan irin maganar da zaki rinka fada min idan bahaka ba jikinki zai rinka gaya miki....."

Yana kokarin mikewa taje tasha gabansa cikeda masifa da tashin hankali,

"Wallahi hamood koda baka sakeni ta dadin rai ba to yazama wajibi ka sakeni ta dolen dole koda kuwa agaban kotu ne domin nagama zama da macuci,mayaudari, mashayi kuma mazinaci... Ko kana tsammanin har yanzu ban san irin kazamar rayuwar da kuke yi kaida waccan karuwar ba? To Allah yagama tonar asirinku dan haka kasakeni kuma kabani kudina naira dubu dari biyar wanda abbana yabani kai kuma ka lallabani ka kwace....."

Tafa hannaye wasila tashiga yi wacce fitowarta kenan daga cikin daki,

"My dear yanzu kana tsaye kanajin abinda wannan mahaukaciyar take fada maka amma shine bazaka dauki mataki ba?"

Tun kafin wise tarufe baki hamood ya dauke bilkisu da wani gigitaccen mari wanda yayi barazanar makantar da ita, zafin marin yasa bilkisu sake daga murya tana furta,

"Allah ya isana macuci azzalumi kuma wlhi

Please Login or Register in order to submit comment