Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

raba dare yana yankawa amma ita ranar kwananta baya yin abu makamancin wannan. Ita kanta Bilkisu fa kawai tana zaune ne agidan bawai dan tana jin dadin zamanba musamman ma yanzu da taga husnah na neman hanyar da zata rainata tayi mata rashin kunya amma bata shiga shirginta, ranar da fahad zai dawo weekend wato ranar juma'a ranar ne yakama ranar sunan anty Fauziyya yayarsu wacce ta haifi yaronta namiji, su husnah tun safe aka shirya aka tafi sune yan aiki ita kam Bilkisu saida tadawo daga aiki sannan tashirya tatafi dama already tasiyo kayan barkarta. Lokacin da taje su husnah suna dakin mai jego an babbaje itada mutuniyar tata anty juwairiyya wacce ke kara hura mata kai tana zugata tana cewa sai yanzu fahad yayi aure ya auri daidai dashi amma da yawani tashi ya debo yayarsa, ai ko governor yazama itace first lady saboda itace yarinya wacce zasu tsufa tare, zama tayi gefen mai jego wacce keta lale marhabun da ita tare dasu anty asabe da nusaiba matar abba, tana rikeda jaririn anata cika mata gaba da kayan sanyi da abinci,batafi mintuna 20 da zuwaba taji husna na cewa,

"Ni alalen nan ce takasa isata anty juwaira..."

"Amarya ai ke wannan kwadayin mai daliline... Kinada cikakkiyar lafiya"

"Kai anty juwaira nifa ranar girkina ya fahad kwana yake yana yankan dinkuna..."

"Saboda tsabar rashin amfaninki..."

Dukansu da suke cikin dakin dariya sukayi banda Bilkisu wacce tasan da biyu husnah tafadi haka, wato habaici takeyi mata kenan, wai meyasa ita kishiya bata raina abin gori ne? Ta tambayi kanta gaba daya ji tayi gidan sunan ya isheta shiyasa ta yi musu sallama tayi tafiyarta gida, wannan karon bazata fadawa fahad ba amma wallahi takusa nunawa husnah true colour dinta, sai ta nuna mata ita ba sa'arta bace bawai ashekaru kawaiba har awurin mijin ai har gobe tana rikeda tutar soyayyar fahad duk da yayi watsi da ita bawai yana nufin yadaina sonta bane tunda duk lokacin da ranta yabaci agidan nakowa ma sai yabaci. Akule yadawo ya sameta ciki ciki sukayi magana yasake fita, bayan sallar ishah sai gasu tare husnah ya daukota daga gidan sunan dama adakinta yake ranar, bayan kwana biyu yakoma dakin Bilkisu dama akule take dashi saboda gorin da husnah tayi mata na wai kwana yake yi yana yankan dinki adakinta saboda batada amfani, ganin yashigo da atamfa a hannunshi yasata tashi zaune fuskarta adaure,

"Malam yaufa baza kayi min wannan yankan adakina ba... Idan yankan zakayi katafi falo Allah yabamu alkhairi"

Kallonta yayi da mamaki,

"Atamfa guda dayace fa..."

"Ita dinfa, wallahi bazaka yankata adakin nanba, sai dai kakoma can inda kafito kaje kayanka, ko acan din haka kakeyi? Wato saini da aka rainawa wayo ko? To wallahi bazai yuyuba..."

Shi gaba daya yanzu yakasa gane kan Bilkisu kullum awuya take jira kawai take ya tabata suyi rikici duk ta tada masa da hankali shikuma baya son tanka mata saboda husnah yasan tana iya ji ai kuwa kamar yasani dan husnah na labe tana saurarensu,

"Allah yabaki hakuri bari na ajiye"

"A ina? Wallahi kaji narantse atamfar nan bazata kwana cikin dakin nanba mayarta can inda ka dauko...."

Juyawa yayi yafita, husnah najin alamun fitowarshi taruga zuwa dakinta ta kwanta, yana shiga ya jefa atamfar kan akwatunanta yajuya yafita. Zaman dai duk babu dadi gaba daya Bilkisu tasake ramewa duk ta kare atsaye ita wallahi da ace abbanta zai yarda haya zata kama tabar wannan gidan amma tasan ko tafada su Ammah bazasu yarda ba ga yanzu wani sabon iskanci da husnah ta tsira duk ranar girkinta sai ta rinka boye fahad ko Bilkisu nason ganinshi indai yana bacci bazata tasoshi ba sai tace wai dan tsabar rashin tausayi baza abar mutum yahuta ba yaje shago yadawo, shiyasa duk abun yafita ran Bilkisu ko zaman falo bata cika yiba dama kallo ke zaunar da ita da taga abin da rainin hankali sai tasa aka siyo mata babbar plasma sabuwa da receiver da komai aka kafa mata acikin bedroom dinta bayan ta falonta amma fa kallo daya zaka yimata kagane takasa da akiba. Sauki daya yanzu suka samu dukansu basa zama agida saboda husnah takoma makaranta ammafa kusan kullum sai sunzo da kawayenta su Fa'iza suna yadarwa Bilkisu magana sai dai bata fiya jinsuba saboda idan acikin bedroom take zaka isketa ta kunna tv shiyasa bata fiya jiyo hayaniyar da take gudana afalo ba kuma abinda ta lura duk ranar da fahad ke gari husnah bata wannan iskancin bata kawo kowa amma idan baya nan to kullum tare da friends dinta suke zuwa har magrib suna tare, yau ita Bilkisu tana gida bata fita aikiba saboda ciwon mara take yi kamar me kusan tun lokacin da ta fara period bata taba ciwon Mara mai azabar wannan ba shiyasa ko fita batayi ba, saida taji ya lafa mata sannan ta shiga kitchen zata dafa ruwan zafi tana sanye da doguwar riga marar nauyi da hula baka, tana kitchen su husnah suka shigo su uku tana ji husnah na cemusu wai su shiga kitchen su dafa musu abinda suke so, ganin Bilkisu na ciki sai suka fara rashin mutuncin nasu,

"Kawata ya babynmu? Meyake so ne?" Inji fa'iza,

"Ai wai dama kawarmu har mun samu karuwa?" Inji Ruky,

"Tun wanne zamani? Ai ni ba juya bace wallahi kuma sannan matar so ce shiyasa cikin kankanin lokaci aka dirka min ciki, yanzu inajin yayi 2 months da yan kwanaki...."

"Ai wasu ba juya bane kawai duniyancine ke hanasu haihuwa..." Ruky tafada tana dariya, Bilkisu na jinsu tana kokarin juye ruwan zafinta,

"Ehh mana ai dama wasu ba wucema shekarun haihuwar sukayiba kawai tsabar iskancin da suka shuka ne awaje suka yita shan pills suna abortion da haka suka kashe mahaifar...." Husnah tafada tana dariya harda shewa, kashe gas dinta tayi ta dauki tea flask dinta tafita, aganinta rashin class da rashin tunanine zai sata tanka musu saboda yaran da basufi meenah ba karamar kanwarta akanme zata tsaya tayi kace nace dasu? Tana shiga daki tazauna tarasa abinda keyi mata dadi kawai sai tafara kuka kukanne yasaukar mata da zazzabi mai zafi dama gashi bata jin dadin jikinta agaskiya tagaji da wannan rainin wayon dan haka barin gidan fahad zatayi inyaso yazauna da husnan, text ta tura masa cewar ita gida zata tafi, tunda yaga text dinta yasan ba lafiyaba duk da shima din tsakaninsu akwai rashin jituwa amma ai lafiya suka rabu yasan may be itada husnah ne, tun kafin tafada masa abinda yafaru yaji ransa yabaci, aranar yabaro kaduna yadawo gida bayan sallar magrib sai gashi, kowacce na dakinta,dakin Bilkisu yashiga ya sameta zaune tsaf cikin shirinta dama shi take jira tasan yana hanyar zuwa,idanuwanta kadai yakalla yasan tasha kuka,

"Bilkisu meya faru?"

"Kasan me? Nagaji da zama da matarka, kawai ni ka sawwake min inbar mata gidan, ni sa'arta ce da zata rinka kawo kawayenta suna haduwa su zageni? Ni nataba yimata haka? Yarinyar nan yau harda suce waini juyace,kuma wai....." Wani kukan tasake fashewa dashi cikin sauri yazauna kusa da ita ya kwantar da ita kan kirjinsa akaro nafarko,

"Am sorry.... Stop shading your tears... Fada min abinda yafaru wai me?"

Kasa magana tayi sai sautin kukanta dake tashi cikin dakin har lokacin tana rungume ajikinsa yana shafar gadon bayanta, saida yabatar tagama kukan ta dan tsagaita sannan yayi magana,

"Me tace miki bayan haka?"

"Cewa fa sukayi wai saida nagama yawon iskancina nasha pills da abortion sannan na aureka shiyasa wai har yanzu ban haihuba..."

Ji yayi ranshi yabaci sosai kwata kwata bai taba zaton husnah zatayi masa hakaba, sakinta taji yayi ahankali sannan yamike yafita......



Yau banyi editing ba kuyi hakuri da spelling mistakes

*_Ummi Shatu_*


*Littafina na kudine me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*



51***Amutukar fusace yashiga dakin husnah, ransa idan yayi dubu to ya baci yau, tana kwance rub da ciki da waya a hannunta tana rubuta assignment, figota yayi ya finciko ta, atsorace tabishi yana rike da ita yana janta har dakin Bilkisu wacce ke zaune har lokacin bata daina kukaba, jin tahowarsu tareda husnah yasata saurin hadiye kukanta ta goge fuskarta, banko kofar fahad yayi yatura husnah yana huci,

"Husnah.... Maimaita abinda kuka fada mata keda kawayenki...."

Zaro ido husnah tayi kafin ta dora hannu aka,

"Nashiga uku ni asma'u...
Anty me mukace miki? Nida wa? Ni yau ma da babu inda naje shine zakiyi min karya ki hada min sharri....." Tun kafin ta rufe bakinta taji wani wawan mari wanda ko tantama batayi fahad ne ya dauketa dashi dan ransa yakai makura wurin baci gaba daya idanuwansa sun juye daga farare zuwa jajaye,

"Waye yake yimiki karyar? Sa'arkice ita? Kifada min abinda yafaru ko inyi ball dake....."

"Ni wallahi karya take yimin... Karya ne.... Bance mata komai ba amma dan tsabar munafurci shine zata hadani dakai saboda tana bakin cikin muna zama lafiya... Wallahi karya tak...."

"Idan kika kara cewa karya take yimiki wallahi sai na fasa miki baki... Dama bakida mutunci ban saniba? Matar tawa zaki saka agaba kirinka zagi? Sa'arki ce? Ni kin taba ganin na zageta? Zaki fada min abinda yafaru ko sai nayi wasan kura dake?...... Ki fada min inda kika ganta tana zubar da ciki ko tana shan pills kamar yadda kuka ce....."

Ganin yayi kan husnah gadan gadan yasa Bilkisu saurin mikewa ta tashi tasha gabanshi, kokarin tureta yayi yana cewa,

"Asma'u baza kiyi min bayanin abinda kukayi ba sai na hau ruwan cikinki?.... Bari na kamaki"

Rikeshi gamm Bilkisu tayi ta kalleshi da idanuwanta wadanda ke jajur, sannan ta kalli husnah,

"Zo ki fice.... Fitar min adaki..."

Sim sim husnah tawuce tana harare harare, duk fahad yana kallonta lallai yarinyar nan munafuka ce wato saima ta nuna ita sam batayi hakaba sharri akayi mata shifa yatsani zama da mutum munafiki wanda baya kaunar zaman lafiya, har husnah tafice Bilkisu na rike dashi, hannuwanshi duka biyu ta kama tasaka cikin nata,

"Kai kuma ai bahaka akeyi ba.... Meyasa zaka kawota gabana har karinka marinta kana neman dukanta akaina....., bazata ji dadiba, gara ka tambayeta kaida ita idanma fadan ne sai kayi mata daga kai sai ita amma idan ka kawota gabana kayi mata fada ai tamkar kayi mata cin fuska ne......"

Kallonta yayi da idanuwanshi wadanda ke cikeda bacin rai shi yasan ba abanza yake kaunar Bilkisu ba, tanada sanyin hali da farar zuciya sam bata da mummunan nufi akan kowa,

"Kiyi hakuri kinji....insha Allah zanyi maganin abun..."

"Na hakura amma gaskiya gida zan tafi.... Gidannan yayi mana kadan mu biyu, matarka bata san ganina haushina takeji, nima kuma haushinta nakeji kaga zama wuri daya bazai yuyu ba... Ni kawai duk ranar da kasamu damar canja min gida sai indawo amma yanzu gida zan tafi...."

Murmushi yayi yajata bakin gado ta zauna shikuma ya tsugunna agabanta yana kallonta,

"Kawai sai kitafi gida kije kice musu kin kasa kishi da yar karamar kanwarki akanta kika dawo gida?"

"Ni ba akanta bane, fitinace bana so.... Kana jin fa abinda suka fada min wai ni yar iskace...."

"Kibar maganar nan pls.... Nidai ai nine na aureki ko? To ban zargeki da hakaba dan haka duk wanda ma zaice kinyi haka kar abin ya dameki tunda ni mijinki ban zargi haka daga gareki ba.......ni nasan atsaftace kike soo don't worry about that...."

Shiru tayi batace komai ba har lokacin idonta bai bar fitar da kwalla ba saboda ba ataba jifanta da wata muguwar magana makamanciyar wannan ba,

"Ina zuwa...." Ganin yamike yasata rikoshi,

"Fahad karfa kace zaka daki yar mutane.... Babu kyau duka...."

"Ni ba dukanta zanyi ba, ina zuwa..."

Dakin husnah yakoma wacce itama sai yanzun takoma bayan tagama jin duk abubuwan da suka fada shida Bilkisu, zama yayi agefen gadonta ita kuma tana tsaye atakure duk atsorace take dashi dan bata taba sanin cewa yanada zuciya har hakaba,

"Husnah abinda kikayi kin kyauta kenan? Meyasa zaki fada mata haka? Kin san zunubin dake cikin wannan maganar kuwa? Ko court fa takaiki za a iya yimiki bulala saboda kazafi kika yimata......."

"Dama ai ita kafi so shiyasa kullum abayanta kake, baka son laifinta...."

"Husnah ba maganar ita nafi so bane... Maganace ta gaskiya.... Bilkisu ba sa'arki bace bai kamata kizo ki rinka fada mata magana irin hakaba..."

"Gaskiya ya fahad wallahi kaima tagama dakai inbanda haka ya daga fada maka magana zaka hau kai ka zauna batare da kayi bincike ba? Ni kasan abinda ta fada min?"

Mikewa yayi cikin fushi,

"Karya kikeyi babu abinda ta fada miki.... Kin san wani abu husnah? Wallahi zan yi mugun bata miki rai akan wannan maganar, matsawar kina son mu shirya to yazama wajibi ki iya bakinki bana son rashin kunya kuma bazan taba lamunta ki raina min mataba saboda ai ko bata girmeki ahaifeba ta rigaki zuwa gidan nan anan kika tarar da ita, ita bata takura miki ta hanaki kwanciyar hankali ba sai kece zaki takura mata? Da lokacin da zan auroki ta tada fitina tanuna bata yarda ba kina tunanin zan aureki ne?, wallahi tun wuri ki shiga hankalinki......"

"Amma dai ya fahad ai....."

"Will you shut up ko sai na bigeki.... Ban san bakida kunyaba ai sai yau... Mun kusa fara fada dake asma'u"

Mikewa yayi cikeda fushi sai kuma taga yakoma ya zauna hannunshi kan kirjinshi, babu shiri yazame ya kwanta kan gadon kafafuwanshi akasa hannunshi dafe da chest dinshi, lumshe idanuwa yayi yana jin bugun zuciyarshi yana fita ahankali ba normal ba, tsugunnawa husna tayi gabanshi ta dafa shi,

"Sannu ya fahad.... Dan Allah kayi hakuri.... Yau kasha maganinka?"

Kai ya daga mata hakan yasata sake matsawa kusa dashi,

"Ka kara wani pls..."

"Nabarshi a kaduna..."

"A'a akwai wani anan... In dauko maka?"

"Kar yazama over dose husnah kinga dazu nasha wani..."

"No bazai zamaba, dan Allah kasha magani"

Tashi tayi ta dauko masa harda ruwa yasha yasake kwanciya babu jimawa bacci yayi gaba dashi, ita wallahi tana son fahad har cikin ranta amma ta tsani bilkisun nan bata kaunarta ko kadan gashi shikuma taga kamar yafi sonta. Bilkisu na dakinta bata sanma abinda ke faruwa ba tadai ga shiru bai dawoba, tunani tayi abinda fahad fa yafada gaskiyane idan taje gida me zata cewa su ammah? Tunda ita dai bada fahad sukayi fada ba tasan su abba bazasu barta ta zauna ba ai jarabar iyallo ma kadai ta isheta tunda kullum tana hanyar zuwa gidan dan bata cikakken sati biyu bata zoba, tashi tayi ta maida kayanta ta ajiye ta hada tea din da tun rana tayi niyyar sha amma yaran nan suka bata mata budget, yau kwata kwata babu abinda tasaka acikinta tun safe, zama tayi tasha tea din sannan tashiga wanka. Abangaren fahad kam yana can yanata bacci dan ko sallar ishah baiyiba har yanzu yanata bacci har 11 sannan yatashi husnah na zaune kasa ta kifa kanta saman gado itama anan baccin yayi gaba da ita, tashi yayi duk jikinsa babu kwari,tashin husnah yayi tana tashi ta tsaya tana kallonsa,

"Tashi ki hau kan gado ki kwanta..."

Tashi tayi tahau kan gadon shikuma yamike saboda baiyi sallar ishah ba gashi ma yunwa yakeji,

"Kinyi sallah?"

Daga masa kai tayi hakan yasashi fita daga cikin dakin yana zaro wayarshi daga aljihunsa, dakin Bilkisu yashiga ga mamakinsa idonta biyu tadai yi shirin bacci da laptop kusa da ita tana rikeda cup din tea,kunnenta ta makala earpiece tana sauraron kundin tarihi na Malam Aminu Ibrahim daurawa, daga kai tayi ta kalleshi dama dogoyen kayane jikinsa riga da wando na wa gambari kalar ruwan toka,zama yayi gefenta ya zare earpiece din guda daya yasa a kunnenshi,

"Me kikeji?.... Kekuma kina son wannan malamin naga alama...."

"Yana fadar abubuwa masu amfanine sosai shiyasa...."

"Hakane.... Bacci fa nayi sai yanzu natashi saboda dazun nan bana jin dadine"

"Sorry..."

"Gashi yunwa nakeji.... Kinada abinci?"

"Ni banyi girkiba.... Zakasha tea?"

"Sai insha din ya na iya...."

Tashi tayi tasauka daga kan gadon tatafi zuwa wurin wani dan karamin show glass wanda kayan tea dinta ke ciki tun lokacin da suka hada kitchen da falo da husna ta kwashe kayan tea dinta tadawo dasu cikin daki,shikam fahad tunda tace masa yau batayi girkiba yasan abin yazo domin har yaganeta idan tana period wuni zatayi shan tea, tea ta hado masa lafiyayye harda bread ta kawo masa yana zaune yana kallonta, rigar baccinta bamai nauyi bace kuma ba mai shara shara bace iyakarta gwiwarta da hular bacci akanta, karbar tea din yayi yace,

"Thanks..."

Daga haka yafara sha ita kuma ta koma saman gado taci gaba da aikinta har yagama yawuce bathroom dinta yayi alwala yafito, rug din sallarta ya dauka ya dan kalleta,

"Zo muyi sallar ishah naga kema kamar bakiyi ba...."

Tasan halin nasa zai fara shiyasa tace masa,

"Ni ai tawa tariga taka zuwa..."

"Seriously?" Yafada yana murmushi, batayi magana ba tadai jijjiga kai hakan yasashi shimfida abin sallar yayi, kafin ya idar har ta kashe system din da wayarta ta kwanta, sallama yayi mata yafita bayan ya idar saboda adakin husnah yake kasancewar wancan zuwan adakin bilkisu yabar gari. Washe gari da safe husnah agaba tasashi tana bashi hakuri amma yace shi bashi zata bawa hakuri ba Bilkisu yake so taje tabawa hakuri, tashi tayi tafita nan yayi hanzarin bin bayanta saboda gudun samun matsala, Bilkisu na gaban drewar tana fito da kayan da zata saka daga ita sai daurin kirji dayake daga wanka tafito,bude kofa husnah tayi tashiga,

"Anty kiyi hakuri akan abinda yafaru..."

Juyowa Bilkisu tayi tai mata wani kallo sannan tace,

"Pls walk out from my room... I said get out..." Daidai lokacin fahad yashigo,

"Kiyi hakuri..." Inji husnah,

"Yawuce but kifitar min adaki pls..."

Juyawa husnah tayi tafita shikuma fahad yamaida kofar yakaraso ciki, karasa fitar da kayan da zatayi tajuyo ta kalleshi,

"Kai kuma fa? Me kake bukata?"

Girgiza kai yayi, "nothing"

"Ok bani wuri inshirya to..."

Kada kai yayi yafita, shifa yagane Bilkisu son girmanta ajininta yake wallahi, afalo yazauna ya kwanta yana danna wayarshi dan yaji motsin husnah acikin kitchen tana aiki, yana nan kwance Bilkisu tafito cikin shirinta na fita aiki, yau komai nata brown tasaka, kallonta yayi cikeda sha'awa,

"Kinyi kyau..."

Jin motsin husnah a kitchen yasata cewa,

"Thank u my dear..."

"Adawo lafiya but kamar bakiyi breakfast ba..."

"Bana jin yunwa karka damu, idan naje office zan karasa gida"

"Adawo lafiya" yafada yana kara kwanciya, duk abinda sukeyi husnah na labe tana jinsu akofar kitchen, kwafa tayi da karfi amma shi fahad bai jiyoba Bilkisu ita kuma tafita, husnah ita kadai tasan abinda zata shirya musu saboda taga fahad yama rainata akan matarsa harda marinta? Wallahi saita rama ta wata hanyar. Kamar yadda ta fadawa fahad yau gidansu takarasa wuni sai da magriba takoma gida,daren ranar ma adakin husnah ya kwana washe gari kuma zai dawo dakinta, ranar da yadawo dakinta tunda safe garin kano yake daure da wani matsanancin zafi kowa kagani rike yake da abin fifita masu kankara da ruwan sanyi kuwa kasuwarsu ce tabude ranar saboda kowa abu mai sanyi yake bukata, karfe 3 tadawo daga office saboda yunwa gashi ita har gobe takasa sabawa da cin abinci a office sam bata iyawa, tuwon shinkafa ta tuka miyar busasshiyar kubewa da kifi, sannan ta tafasa magarya wannan dabi'artane tun tana gida abubuwan nan guda biyu duk lokacin da tagama period tana amfani dasu almiski da magarya saboda tasan yau zata samu tsarki, dama bata wuce kwana biyar ata dade tayi shida. Bayan magrib tasamu tsarki tana yin sallar magriba fahad yadawo daga filin kwallo wanka yayi ya dauki mattress yafita tsakar gida yayi shimfida saboda zafi, Bilkisu na daki bata fitoba tana dai jiyo yar hirar da sukeyi shida husnah tana cemasa ita karatun nan yafi wanda tayi da wahala saboda tulin sunayen magungunan da suke haddacewa sannan sai sun haddace class din da yake da group dinshi da dossage dinshi na manya da na yara, dariya taji yana yi yanace mata ai dama kowanne karatu akwai irin tashi wahalar domin shima hakan take yanzu wata wahala karatunsu ke zubawa saboda yakusa zuwa karshe, ita dai bilkisu tana jinsu ne kawai batada niyyar shiga shirginsu koda akusa dasu ma take bare tana nesa, tunani itama tafara yi da tunifa itama tazama nurse ko Dr dan har tasamu admission a school of nursing amma taki yi tace mass com takeso saboda shi take sha'awa tun tana karama.

K'arfe 9 saura taji su husna shiru da alama sun bar waje sun dawo ciki amma kuma ai yau fahad adakinta yake, bata kai ga gama tunaninta ba taji yar kara daga waje kuma da alama fahad ne ta zaci abin wasane sai tajiyoshi yana ta salati, atamanin ta sauka tafita daidai lokacin itama husnah tafito rikeda wayarta wadda ta kunna light,

"Kuyi ahankali kar ta harbeku.... Kunama ce..."

Husnah na haskawa kuwa sai ga kunama katuwa irin rikakkiyar nan baka kirin da ita, wata zabura husnah tayi saboda tsoro sai Bilkisu ce ta kashe kunamar cikin rawar jiki, fahad kam na kwance yadafe gefen kanshi inda kunamar ta harbeshi,

"Kira min ya Abba... Yazo muje asibiti"

"Wanne yazo ku tafi asibiti kawai ya siyo maka magani saboda kar abata lokaci...." Bilkisu tafada tana dangwala masa dan yatsanshi ajikin wayar, husnah ta mikawa bayan tayi dialling number din ya Abba, yana dagawa husnah tace zata turo sunayen magani yayi sauri yakawo yanzu kunama ce ta harbi fahad,

Dukansu arikice suke saboda wani irin nishi fahad yakeyi mai wahalar gaske duk yabi yahada gumi sai sannu suke yimasa amma baya iya amsawa. Lokacin da Abba yakawo maganin duk yagama jigata, cikin azama husnah ta karbi maganin dama harda allura tayi gaggawar yimasa sannan suka bashi maganin yasha, alama yayiwa Bilkisu da ta kaishi daki nan ta kamashi akan kafadarta suka shiga ciki kayan shimfidar tashi ma da yayi sai ya abbane yashigar musu dashi falo yatafi ita kuma husnah tabishi tarufe gidan. Sosai Bilkisu tayi nadamar kamo fahad bata bari ya Abba yakamashi ba saboda nauyin da taji yayi mata sosai dakyar ta iya kaishi dakinta suna zuwa bakin gado saboda layin da yaketa yi hajijiya na daukarsa akokarinta na kwantar dashi suka fada saman gadon tare yabita ya rufe, iya yinta tayi amma tagagara tureshi saboda nauyinshi har lokacin garin adaure yake sai dai akwai kamshin ruwa alamun anyi akusa da garin, jin gumin dake fita daga jikinsa tasan yana shan azaba cikin ikon Allah nefa suka kawo wuta nan sanyin iskar fanka tasoma ratsashi yadaina gumin, hannunta ta mika ta warware net din dake jikin gadonta pink colour nan hasken yaragu akansu, ita gaba daya mamaki ya rufeta saboda jin nauyin fahad gaba daya yasakar mata nauyi dakyar take numfashi. Baccine itama ya saceta ahaka, husna daketa kaiwa da kawowa tana dan labewa ko zataji motsinsu tun lokacin da suka shiga daki amma sai taji shiru har 12 takai tana zirga zirgar laben nan idan taji shiru sai taje ta kwanta da anjima sai tasake komawa daga karshe sai gajiya tayi ta kwanta tai bacci. Misalin karfe biyu nadare fahad yafarka, daidai lokacin ansau iska agarin sannan yayyafi yafara sauka amma bamai karfiba, juyawa yayi niyyar yi amma sai yajishi ajikin Bilkisu dafarko yazaci ma husnah ce amma yanayin kamshinsu da ya banbanta yasashi gane Bilkisu ce yana kwance dumu dumu akanta ta zagayeshi da hannuwanta ta rungumeshi tsantsan, yayi pillow da kirjinta, ahankali ya bude idonshi ya kalleta har lokacin kanshi yana dan ciwo kadan kadan,

"Ohh Allah inama yau akwana ana lafta ruwa...." Yafada ahankali kafin yarufe bakinsa ruwan ya dan fara karfi daidai lokacin kuma difff nepa suka dauke wuta, ahankali ya dan raba jikinsa da nata yana sinsinarta daidai lokacin ruwa yasake karfi kamar da bakin kwarya......



*_Ummi Shatu_*

*Littafina na kudine me buqatar siya ya nemi wannan lambar 07084161619 kokuma 08030811300*


52****Cikin bacci yaci gaba da sinsinarta saboda kamshinta is special & different da duk kamshin da yataba ji abaya, duk dauriyarsa na wai yau yabarta kasawa yayi, baima san lokacin da yarabata da rigar baccinta ba, rawar sanyi yaga tafara sakamakon ruwan da ake shekawa bargo yajanyo ya lullubesu sannan yamaida hankali wurin ruda mata jiki da soyayyarsa mai zafi, duk kyankyaminshi amma yau haka yadage yana lasar ko ina na jikinta kamar wani tsohon maye, duk yabi ya rude yarasa ma ta ina zai fara,

Bilkisu kam cikin bacci taji abinda fahad keyi mata harga Allah tazaci cikin mafarki take, sosai itama take mayar masa da martanin abinda yake yimata, tun tana yi cikin bacci har tafarka saboda lamarin ya zarce tunaninta, koda tafara fahimtar abinda ke faruwa taso tayi gardama amma sai ya hanata ta hanyar rufe mata baki ruf da nashi, cikin lokaci kankani ya fitar da ita daga hayyacinta nan yarinka juyata son ranshi, abin yayi mutukar bashi mamaki saboda yanda take rawar jiki kamar yaune

Please Login or Register in order to submit comment