Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


Murmushi yayi wanda ya bayyanar da hakoransa,

"To wannan auren namu menene sunanshi?"

"Auren taimako domin taimako na zakiyi mutukar da gasken kana kaunata"

Murmushin yasake yi,

"Gashi nikuma ban shirya aure kwana kusa ba"

"Karka damu zan baka dukkan abubuwan da za ayi amfani dashi, ni dakaina zan hada lefe inbaka akawo da komai da komai"

"Sai kace acikin shirin film ko littafin hausa? Gaskiya bazan iya wannan auren ba, da dai aure zamuyi halattacce kamar na kowa shine sai indage inyi iya bakin kokarina inga nasamo abinda zan aureki cikin watannin da kika fada amma wannan auren gaskiya ba daniba..."

Daga haka yamike yana kallon agogo,

"Ni zan wuce, nabarki lafiya"

Ya fita daga gate din gidan bata iya cemasa komai ba saboda tsananin mamaki ashe haka yake da baki da iya zance bata saniba? Ganin zaman babu amfanin da zai tsinana mata yasata tashi tashiga cikin gida, wurin ammah tawuce ta zauna anan ammah ke tambayarta waye yazo nan ta sanar da ita sabon saurayi tayi kuma dagaske yake yashirya aure, fatan alkhairi ammah tayi domin ita zabin bilkisu shine nata.

Koda ta shiga daki kasa zaune tayi ta kasa tsaye bata son damarta tawuce, ya kamata tayi amfani da wannan yaron wurin cikawa hamood burinsa,

Wayarta tajawo ta shiga kiransa, tana daf da tsinkewa yadaga,

"Hello, sorry hajjaju wanka na shigane"

"Babu komai dama na kiraka ne infada maka na amince ayi yadda kakeso din, ya kakeso ayi?"

Wata sanyayyar ajiyar zuciya ya ajiye sannan yayi magana cikin taushin murya,

"So nake muyi aure irin wanda kowa yake, sannan bana bukatar ko sisinki kibarni inyi komai kamar yadda kowanne ango keyi..."

"Na amince..." Tabashi amsa,

"Yawwa ko kefa to shikenan insha Allah babu matsala zan fara shiri daga yau dinnan, Allah yawuce mana gaba"

"Amin"

Daga haka sukayi sallama, kowannensu zama yayi yana tunanin abinda zai tunkara, ita dai bilkisu dawowar hamood take hararowa bayan tayi wannan auren na wucin gadi yayinda shikuma fahad anasa bangaren yanda zaije ya tunkari su Ayiyah da maganar aure yake tunani.....




*_Ummi Shatu_*

© _*HASKE WRITERS ASSO.*_


*KAMAR DA WASA...!*


_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*



*11*


*Littafin kamar da wasa na kudine dan Allah idan har kinada bukata to kibiya kudi kisiya sai ki karanta.*


***Da tunanin ta yadda zai jewa su ayiyah da maganar aurenshi yashirya, bakin jeans yasaka da jar t shirt mai dogon hannu kamar koda yaushe saida yasha turarenshi wadanda suka zauna ajikin kayanshi sannan yafito daga dakinnsu yana taje sumar kanshi da karamin cumb wanda keys dinshi ke makale jiki. Tsayawa cak yayi yana tunanin ina yadace yanufa ahalin yanzu,

Waje yayi domin baida bukatar shiga cikin gidan yanzu, zama yayi kan dakali yana cigaba da taje gashinsa daga karshe yasaka cumb din cikin aljihu yazaro wayarsa ya leka instagram daga nan yashiga facebook, sakon husna yagani hakan yasashi jan dan karamin tsaki,

"Wannan yarinyar ko mayya sai haka..."

Chaten yaci gaba dayi har magrib yana zaune awannan wurin yana ganin masu wucewa daga can cikin gida yashiga yayi alwala yafito yawuce masallaci bayan an idar da salla yanufi gidan yaya Asabe babbar yayarsu wadda ke aure acan ladanai, tana tsakar gida itada yaranta guda biyar wasu nayin homework wasu kuma na game a wayarta ita kuma tana marking din test din yara domin malamar makarantace awata private school dake unguwar, ganinsa yasata ajiye abinda takeyi tana yimasa sannu da zuwa yaran kuma nayi masa oyoyo,

Kan babbar tabarmar da suke kai yahau ya zauna yana rikeda humaira wacce itace karama dan ko tafiya bata faraba,

"Autan ayiyah daga ina haka?"

"Anty wallahi yau takanas nazo miki dan wallahi akwai magana"

Dariya tayi takalli 'yarta mai sunan ayiyah yar kimanin shekaru 9 tace,

"Ilham jeki ki kawowa uncle fahad ruwa da lemo mai sanyi kinji sai kizo ki zubo masa abinci idan kin kawo"

Saida taga tashin ilham sannan ta maida hankalinta gareshi,

"Meyake faruwa?"

"Anty aure nasamo amma ban fada agidaba tukunna"

Dariya ita abinma yabata saboda jin abinda yace domin ai fahad yarone, nawama yake da har zaiyi maganar aure yanzu?

"Fahad aure kuma? Wai dagaske kake koda wasa?"

"Dagaske nake Allah"

Kafin takara magana ilham takaraso dauke da aiken da tayi mata nan ta karba ta mika masa gabanshi ta ajiye sannan ta kalleshi,

"Amma fahad aure yanzu anya baka ballowa kanka ruwa ba? Haba fahad inama laifin kakoma karatunka yar degree dinnan da kowa keyi kaima kaje kayi inyaso idan kagama sai kayi maganar Auren amma yanzu dududu nawa kake? Ai ko Abba bana jin zai jajibo aure yanzu bare kai, shiyasa tun jimawa nake cemaka kakoma karatu amma kaki...."

Murmushi yayi bayan ya kwankwadi lemon dake hannunshi,

"Anty inada burin komawa karatu amma gaskiya ba yanzuba..."

"Sai yaushe? Saika Tarawa kanka nauyi yayi maka yawa? Ai tun yanzu yadace kakoma da baka da nauyin kowa amma haka kawai kaki karatu?"

"Anty asabe nidai kawai kiyi min fatan alkhairi"

"To shikenan Allah ya tabbatar da alkhairi, ga abinci nan kaci"

Yajima agidan dan acanma yayi sallar isha'i sannan yatafi gida, akofar gida yaja burki yanemi wuri ya zauna yakira bilkisu,

Fitowarta kenan daga wanka tadauki wayar tana kokarin zama agefen gadonta,

"Ya akayi?" Shine abinda tace lokacin data daga wayar,

"Babu komai, ina wuni?"

Ajiyar zuciya tasauke aranta tana jin tafiyarsu zatazo daidai dashi domin da alama sai yanda tayi dashi,

"Lafiya lau dama nima ina son kiranka, gobe idan Allah yakaimu inaso kazo domin zaka gaisa da ammah sannan zakazo kagaida Abba ma"

"Babu matsala Allah yakaimu amma da kamar yaushe zanzo?"

"Koda yaushe kazo ma babu matsala koda yamma koda daddare"

"Tom zanzo da daddaren dan gaskiya kunyar zuwa da yamma nake"

Murmushi tayi amma bata bari yajiba tace,

"Shikenan Allah yakaimu"

"Amin kiyi bacci cikin aminci da farin ciki,saida safe"

"Allah yakaimu"

Daga haka takashe wayar ta ajiye gefe, koda tagama shirin bacci sai kuma tunani ya addabi ruhinta wato kamar da wasa karamar magana na shirin tabbata dakyar tasamu ta fidda tunanin aranta tayi bacci. Shima fahad da tunanin abin ya kwana aransa shi yanzu babban abinda ke fadar masa da gaba tayadda iyayenshi zasu amince yayi auren nan alhalin ga Abba nan agabanshi wanda shi yadade ma da budurwar amma har yau ba afara maganar aureba. Washe gari bilkisu bataje aikiba domin bata da aiki,tana dakin ammah tana gyarawa bayan tagama wanke toilet taji sallamar maama atsakar gida,

"Yar halak" tafada azuciyarta, babu jimawa sai gasu sun shigo itada huda wadda ke gudu dan tazo wurin bilkisu,

"Sannu Adda, kawo intayaki"

Sakar mata mooper din tayi ta dauki hudah dake rungume da ita,

"Ina kwana Adda labour?"

"Lafiya lau Maman hudah, wallahi yanzu nake tunaninki nake cewa to ko inje gidanki tunda ba fita aiki zanyi ba?"

"Wallahi nima daku na tashi shiyasa muna tashi nacewa abban hudah tare zamu fito idan zaije office yasauke mu"

"Ai kuwa kin kyauta, nasan daga nan har dare kuna nan kamar yadda aka saba"

Dariya maama tayi tace,

"Abinda kema kin sani adda labour"

Kinkimar hudah bilkisu tayi suka koma falo wurin ammah nan maama tafito ta samesu.

Da daddare misalin karfe 8 fahad yayi mata waya cewar yakaraso dama lokacin tana daki tanata faman caba ado kamar gaske, maama dai na kwance tana lallaba hudah tana kallonta, mayafi tadauka tafita tana zuba kamshi dama tun yamma ta fadawa ammah fahad zaizo gaishesu,

Kamar koda yaushe yana tsaye hannunsa daya cikin aljihu yana sanye da farar shadda sabuwa fil tasha bakin aiki wannan dalilinne yasashi sanya bakar hula da bakin takalmi,

"Yaron akwai daukar wanka babu laifi matsalarshi daya yayi yaro dayawa" tafada cikin zuciyarta,

"Barka da fitowa, ina yini?"

Yace da ita yana kallonta,

"Lafiya lau, muje ko?"

Jerawa sukayi zuwa cikin gidan, wurin ammah suka fara zuwa tana zaune afalo lullube cikin mayafi, akunyace yacire sau cikin kafarsa yashiga falon daga shi sai bakar safa akafar tashi, zama yayi kanshi akasa yana gaidata, itama ammahn kanta akasa ta amsa bata ko daga kaiba bare ta kalleshi, hakan da sukai sai yabawa maama da bilkisu dariya nan kowa yayi tasa aboye, duk jinsa yayi yatakura shiyasa ko ruwa yakasa sha daga karshe yamike yafita bayan ya ajiyewa ammah kudi, bin bayansa bilkisu tayi domin takaishi wurin Abba.

Afalon Abba sukaja birki ya kalleta fuskarsa cikeda annuri,

"Ban daiyi rashin kunya ba ai ko?"

"Da kayi me?"

"Dana zo mana"

"Uhmm zancen kakeso"

Murmushi yayi baice komaiba har Abba yashigo daga can wata kofa wadda da alama itace hanyar bedroom dinshi,mikewa tsaye fahad yayi Abba na zuwa ya durkusa kasa da niyyar gaisheshi amma sai Abban ya ruko kafadarshi yana bubbuga bayanshi ahaka suka gaisa, sannan Abba yajashi kan kujera mai zaman mutum uku, abin gwanin burgewa Abba sai janshi yakeyi da hira yana yimasa tambayoyi dangane da tushensu cikin barkwanci da dabara irinta manya daga karshe Abba yace yana son ganin mahaifinsa, duk da yaji dadin ganin Abba da hirar da sukeyi amma yakasa sakin jiki duk atakure yake jinsa dan haka cikeda girmamawa da alkunya yayiwa Abba sallama yafito dama bilkisu tuni ta dade da zamewa tafice, koda yafito tsaye ya sameta tana yin waya da kanwarta mina ganinsa yasata yiwa Mina sallama ta juyo tana kallonsa,

"Ya kukayi?"

"Cewa yayi inturo mahaifina zai gana dashi"

Ajiyar zuciya ta sauke batace komai ba tayi masa alama da hannu suje ta rakashi, shi dinma baice komai ba yawuce tana biye dashi a second gate sukayi kicibus dasu Hindu itada mai gidanta wanda yazo daukarta ganin su bilkisu sun fito yasata komawa domin yiwa Abba sallama dama su take jira sufito. Gaisawa sukayi da mijinta da fahad daga nan suka wuce waje,

"Yanzu menene next abu da kake ganin zamuyi?"

"Bari dai infara yiwa babanmu maganar tukunna inyaso sai sauran su biyo baya..."

Sallama yayi mata yahau roba roba din da yazo dashi na salim yatafi, ciki takoma ta iske Hindu na jiranta nan tafara yimata santin haduwar da fahad yayi tana cewa,

"Su iyallo masu fatan tsiya to zasuga mijinki yawuce tunaninsu"

Ita dai bilkisu dariya tayi daga nan sukayi sallama tashige gida sukuma suka tafi.

Adaren ranar bayan fahad yakoma gida yasamu baba da maganar a turakarshi, dafarko shi kansa kunya abin yabashi shiyasa yarasa ta inda zai fara sanar da baba, kawai sai yaji kunyar yacewa baba aure yakeso yaje ya nema masa dakyar dai yadaure yace,

"Baba dama.....dama akwai wata..... da nake zuwa wurinta..... to yau naje ingaida mahaifinta...... shine.....shine.... yace wai yana son ganinka...."

Shiru baba yayi ya zuba masa ido hakan yasashi kara yin kasa da kansa, mamuh kuwa dake tsaye bakin kofa wacce shigowarta kenan kuma da alama taji komai tafa hannu tafara yi tana rafka salati.....




*_Ummi Shatu_*


© *HASKE WRITERS ASSO*
_(Home of expert & perfect writers)_


*KAMAR DA WASA....!*



*_NA_*

*_UMMI A'ISHA_*



*12*


*Kamar da wasa na siyarwa ne yar uwa idan kinada bukata kisiya saiki karanta.*


***Ji yayi jikinsa yayi mutukar sanyi hakan yasashi yarda aransa cewar iyayen nashi ba lallai su amince da batun nasaba,

"Yanzu kai fahad har kafara maganar aure? Ahh lallai zamani yazo...." Inji mamuh, kasa yasake yi da kansa, dariyar baba yajiyo daga bisani yaji yana fadin,

"Ai ba auren akace za adaura ba kawai dai mahaifin yarinyar ne ke son ganawa dani, menene na saurin karaya kodai baki shirya aurar da d'an nakiba?"

Dariya itama tayi takarasa shigowa cikin dakin ta nemi wuri ta zauna,

"Bahaka bane baban asabe ko gobe akace mu fito muna iya fitowa tunda yarona ba zaman banza yakeba yana da sana'arsa"

"Gashi babarsa tana adashi..." Baba yafada cikin raha,

"Ni yaushe rabona da adashi baban fahad?"

Jin su baba sun mayar da abun raha yasashi zare jikinsa zai fice har yakai bakin kofa yaji baba yace masa,

"Gobe idan Allah yakaimu zanje sai ka sanar musu"

Daga kai kawai yayi yana shafa sumar kanshi batare da yace komai ba, ganin sun cigaba da maganar su yasashi karasa ficewa dasauri.

Bayan fitarshi baba yadubi mamuh cikin nutsuwa,

"Abinda nakeso daku idan har dagaske auren aka bashi to mu mara masa baya yayi tunda har yafurta, yin hakan yafi fiyeda mu bada gudun mawa wurin lalata tarbiyarsa da ruguza rayuwarsa, saboda yaran zamanin nan da kike ganinsu sai dai abarsu kawai shiyasa komai kankantar yaro ko yarinya idan suka nuna aure sukeso kawai yimusu ka huta domin idanfa baka yimusu ba to watan hanyar zasu bi ta daban,... Ai mu da muke fita waje mune muke kallon abubuwan dake faruwa Rahmatu"

Gyada kai mamuh tayi cikeda gamsuwa tace,

"Hakane Baban asabe ubangiji Allah ya shirya mana zuri'a da sauran al'ummar musulmi"

Daga nan sun jima suna tattauna maganar atsakaninsu.

Abangaren fahad kuwa ko zama baiyi adakin ayiyah ba yadauki abincin shi dake rufe yafice, dakinsu yabude yashiga sai lokacin yaji nutsuwa tazo masa domin da alama su baba bazasu hanashi wannan auren ba zama yayi bayan yarage kayan jikinsa ya zamana daga shi sai vest da gajeren wando, abincin yabude yafara ci nan kuma hankalinsa yakoma kan lissafin abubuwan da zaiyi tofa account dinshi yaduba yaga nawa yake dashi daga nan lissafe lissafe yatashi wanda ya daukeshi tsawon lokaci daga karshe abincin ma barinshi yayi. Sai da yasamu nutsuwa bayan yayi wanka sannan yakira bilkisu wacce tuni harta kwanta amma ba bacci takeyi ba,

"Kaje gida lafiya?"

Shagwabe fuska yayi kamar tana kallonshi,

"Ni wallahi bazan amsa ba tunda ai baki kirani kin tambayeni ba...."

"To ai sai kayi min uzuri dai ko"

"Nayi miki ranki yadade, dama mai gidane yace zaizo gidanku gobe wurin Abba"

"To Allah yakaimu, amma da yaushe zaizo?"

"Da safe naji yace,sai ki sanar dasu"

"Babu matsala Allah yakaimu"

"To saida safe? Ko zamuyi hira?" Yafada dan jan magana,

"A'a saida safen dai" tabashi amsa tana yatsina fuska,

"To kihuta lafiya baby...."

"Thanks" tafada cikeda bacin ran kiranta da baby da yayi,

Daga haka takatse wayar juyi tayi ta gyara kwanciyarta aranta tana cewa,

"Wannan shine Abu kamar da wasa yana shirin zama babba,hamood meyasa kayi min haka? Amma babu komai tunda ban san abinda ke faruwa ba sai dai nayiwa kaina alkawarin zama injiraka har lokacin da Allah zai sake hadani dakai..."

Sake muskutawa tayi cikeda damuwa,

"Lallai yaron nan ni yake kira da baby? Tab ai kuwa dolene ma na yanka masa serious warning wallahi...."

Da bacin rai tayi bacci wanda bata san ko na menene ba amma tafi alakantashi da rashin sanin takamaimai halin da hamood ke ciki da kuma kiranta da baby da fahad yayi.

Koda gari yawaye bayan tafito suna karyawa da ammah take sanar da ita batun zuwan babansu fahad wurin Abba, ai ammah farin cikine ya mamayeta harta kasa boyeshi saida ya fito fili bilkisu tagani,

Shiru tayi aranta tana jin tausayin ammah domin azahirin gaskiya bata jin zata iya zaman aure da wannan karamin yaron kawai dai aure ne na wucin gadi za ayishi da zarar abin sonta yadawo zata koma gareshi domin shine yadace da ita ba fahad ba.

A bangaren fahad kuwa tunda ya kwanta bayan yayi sallar asubah bai tashiba har 9 saida ayiyah tazo ta buga masa kofa tace baba na kiranshi sannan yataso da hanzarinsa yana kokarin zura doguwar rigar jallabiyarsa wadda yacire bayan ya idar da salla. Lokacin da yashiga dakin baba yasameshi yana karin kumallo da kakkauran koko da kosai nan ya durkusa yagaidashi baba ya amsa cikin fara'a kana yace,

"Nayiwa babanka Alhaji Nuhu magana mahaifin salim yanzu haka yashirya ni yake jira zamuje gidansu yarinyar, a ina gidan yake?"

Sunkuyar dakai fahad yayi sannan yasanar dashi, dayake sanannen mutum ne mahaifinsu bilkisun shiyasa baba bai wani wahala wurin gano inda gidan yakeba daga karshe yace fahad din yatashi yatafi. Yana kwance adaki yajiyo fitar baba hakan yasashi jin faduwar gaba babu kakkautawa dakyar yasamu yaji yakoma daidai amma baccin da bai komaba kenan hakane ma yasashi fadawa toilet yayi wanka yafito yashirya sannan yasaka kananan kaya yanufi cikin gida, yana shiga su mamuh na waje suna gyaran waken suya wanda zasuyi awara dashi da rana, ji yayi kamar yakoma dan kunya gashi yau sai yaji duk ya tsargu dasu saboda yanda daga ayiyah har mamuhn suka zubo masa ido gefe daya ga mariya tsugunne arakabe,

"Yaya fahad tattabarunka sunyi sabuwar kinkisa Allah leka kagani"

Dama mafaka yake nema dan haka yanufi dakin barun batare da yakarasa wurinsu ba yana cewa Mariya,

"Haba? Ashe zan baki biyu tunda kece kika fara yimin albishir"

Zuwa yayi ya lelleka nan yahangosu sun doshi goma koma fiye da haka, ma'ajiyar abincinsu yanufa yaje ya ciko musu kwano da hatsi yazo ya watsa musu sannan yakoma wurinsu ayiyah yana hararar Mariya,

"Ke meyasa bakije makaranta ba? Kema gardamar karatu zakiyi ko?"

Kafin Mariya tayi magana ayiyah ta amsa,

"Ka ganta nan da zazzabi tatashi da asibiti ma zan rakata babanku yace inbari anjima inkaita wurin murja nurse makotanmu ta dubata tunda can asibitinma idan anje layine kuma ba lallaima aga likitan ba watakil nurse din za agani"

"To Allah ya sawwake, ina kwananku?" Yafada bayan ya durkusa,

"Lafiya lau ango" inji mamuh, ai baice komaiba yamike yana murmushi yafada dakin ayiyah domin karyawa yanaji mamuh nacewa ayiyah,

"Sai mufara asusu tunda danmu ya lakato aure"

Dariya ayiyah tayi sannan tace,

"Atoh bikin auta guda ai dole anuna bajinta"

Agurguje ya karya yafito yabar gidan yanufi shago saboda yanada ragowar dinkunan da bai karasa ba kuma yaga har masu dinkin sun turo masa kudin dazu da asubah. Acike yasamu shagon kowa yafito harda yan karbar dinki da masu zuwa zaman hira shagon, hamza ya iske asaman kekenshi dan haka yanemi wuri yazauna yana jiran yagama yabashi wuri,

"Yau mutuniyarka zuwanta biyu nemanka ta dubaka taga ko ka fito amma shiru"

Duk da Tj bai fadi sunaba amma yasan husna yake nufi,

"Yar naci kenan, ni garama da ka tuna min bari inyanka atamfar can tata kafin inhau keke"

Atamfar yadauka da almakashi da sauran abunda zai bukata yafita domin yankawa.

Kamar yadda baba yafada shida mahaifin salim sukaje gidansu bilkisu a motar yayansu salim din baffa wanda shine yakaisu, lokacin da sukaje bilkisu tafita wurin aiki sun samu kyakkyawar tarba awurin Abba wanda ya karbesu hannu bibbiyu cikeda girmamawa da mutuntawa, kasancewa abune na manya masu ganin mutuncin juna anan aka kulla magana inda Abba yace yabaiwa fahad bilkisu sannan shi baya son wadannan bidi'o'in masu hana aure yayi karko dan haka nanda watanni biyu sai adaura musu aure yafi ayita dogon zancen nan suna sake shakuwa da juna daga karshe kuma ba asan me zai faruba, duk da baba yana ganin kamar hakan bamai yuyuwa bane duba da su ba karfine dasu kamar gidansu bilkisun ba amma haka yakarbi maganar Abba hannu bibbiyu aranshi yana cewa idan da yuyuwar su daga lokacin bikin sa sake dawowa su nemi alfarma, cikeda mutunta juna sukayi masa sallama suka fito inda yayi musu rakiya har gaban motarsu,wannan fa shi ake kira da babu zato babu tsammani daga zuwa tambaya ansaka ranar aure alhalin shi angon bai tanadi komai ba na biki.



*_Ummi Shatu_*

© *HASKE WRITERS ASSO.*



*KAMAR DA WASA....!*


_*NA*_

*_UMMI A'ISHA_*


*13*



***Daga fahad har bilkisu babu wanda yakeda masaniyar abinda yake faruwa, shi fahad baima koma gidaba sai bayan sallar la'asar wannan dinma yunwa ce ta addabeshi shiyasa yana zuwa gidan ta kan abinci ya fara saida yaji ya koshi sannan yawuce dakinsu yayi wanka daga ayiyah har mamuh babu wanda yayi masa maganar kowa acikinsu kama bakinsa yayi yai shiru, bayan yagama shiryawa yafito yana kokarin rufe daki baba yashigo, kayan hannunsa yakarba sannan yashiga cikin gida baba yana biye dashi, bai san wa zai kaiwa kayanba kasancewar bai san wacce keda girki ba domin su al'adar gidan nan baka gane wacece ke girki saboda komai tare sukeyi wannan dalilinne yasashi ajiye kayan a kofar dakin baba yajuya yana kallon maryam da mariya wadanda ke ta faman kallonsa suna yar dariya kasa kasa,

"Ke Mariya kin warke zaki fara munafurci ko? Bari nazo nakama yarinya sai nayi ball da..."

"Ya akayi kuma? Dawa za ayi kwallo?" Baba yafada bayan yashigo,

"Ahh babu komai baba" fahad ya amsa yana shafa kai,

"To zo ina son ganinka..."

Bin bayan Baba yayi cikin turakarsa, sai da yajira Baban yazauna sannan shima yazauna bayan ya dora habarsa kan gwiwarsa,

"Muhammadu tofa karamar magana tazama babba, naje wurin mahaifin yarinyar nan kamar yadda ya bukata kuma mun tattauna dashi, ya yabeka iya yabo haka kuma ya kaunaceka domin duk mutumin da yaso hada zuri'a dakai to mai kaunarka ne, kuma naji dadi domin gidan da kaje gidane na mutunci da karamci saboda bana tunanin duk nahiyar nan bama cikin kano ba babu wanda bai san mahaifin yarinyar nanba..."

Shigowarsu ayiyah da mamuh ne ya katsewa baba maganar da yakeyi sukayi masa sannu da zuwa sannan suka nemi wuri suka zauna suna saurarensa,

"Yanzu dai zancen da nake maka fahad mutumin nan yabaka yarsa yace baya bukatar komai daga gareka domin har yama sanya ranar aurenku watanni uku, duk da nasan kanada sana'ar yi amma sai nake ganin kamar zaka shiga wani hali saboda aure abune mai wahalar gaske musamman ma a wannan lokacin..."

Shiru fahad yayi yana jin abun kamar amafarki wai shine zai auri bilkisu matar da yake mutukar kauna, maganar babace tadawo dashi cikin hayyacinshi,

"Yanzu menene abinyi? Kaga dai nafarko bakada muhalli domin baka gama ginin da kakeyi ba, na biyu rikon gida dole sai anshirya duk da nasan Allah shine da kowa amma mu ta bangarenmu zamu taimaka maka da abinda zamu iya sannan zan tattaro yayunka ma duk in sanar dasu"

"Baba nida tunanin da nayi ko insaida dayan filina dake digar maharba sai inkarasa ginin?"

"A'a kabar filinka bari dai zamuga abinda za ayi, tashi kaje, zamu shawarta da iyayenka"

Tunda yafito sai yarasa me zaiyi yasan dai yau yana cikeda wani farin ciki wanda bai taba jin irinsa ba, tafe yake ahankali domin zuwa yasanarwa da salim saboda magana awaya bazata yuyu ba, idonshi ne yakai kan yaran dake tsugunne gaban wata yarinya wacce ke soya awara agefen titi, wurin yakarasa yazaro dari biyar ya mikawa yarinyar,

"Ki rabawa yaran nan sadakar ta dari biyar..."

Daga haka yawuce yanajin yaran sunata murna da yimasa godiya. A shagonsu salim ya sameshi yana kwance shi kadai bayan wasu mata sun gama siyayya sun tafi. Shiga yayi ya zauna agefenshi yana fadin,

"Washh..."

Kallonsa salim yayi, "yadai abokina?"

"Katashi kaji wani labari, ansa min ranar aure yau?"

Ai kuwa tun kafin yarufe bakinsa salim yatashin yana kallonsa,

"Dawa?"

"Da hajjaju mai gado"

Dariya sunan yabaiwa salim shiyasa saida ya dan dara sannan yace,

"Lallai mutumin nan kadage sai kayiwa Abba overtaking..."

Dariya fahad yayi,

"To ya za ayi lokaci nane kawai yazo"

Dariya salim yayi,

"Allah yasanya albarka tareda alkhairinsa, ya kuma zakayi da maganar husna?"

Canja fuska fahad yayi,

"Ya kuwa zanyi, ko na taba cemaka ina sonta ne?"

Jijjiga kai salim yayi,

"Tab akwai rikici, Allah dai ya kiyaye"

"Babu wani rikici malam"

Har dare suna tare da salim, saida salim yarufe shago sannan suka tafi gida gaba daya.

Tunda bilkisu tabar gida bata dawoba sai yamma tana dakinta bayan tafito daga wanka taji wayarta na kara, su elmustapha ne dan haka ta daga tana tsaki tasan maganar dai bata wuce ta kudi,

"Elmustapha ya akai?"

Daga can tajiyo muryar el'ameen yana cewa,

"Adda labour amarya, nine shi yashiga school"

"Amarya kuma?"

Dariya taji yayi mata sannan yace,

"To Allah yasanya alkhairi mudai aturo mana picx din babban yaya"

Daga haka yakatse wayar, ita dai kanta daurewa yayi jin abinda el'ameen yace, to meyake nufi, da haka ta kammala shiryawa ta sanya yar doguwar riga marar nauyi mai hannun shimi kalar ruwan hoda sannan tasa hijab tafita, farar shinkafa da miya tasa Rabi ta zuba mata tashiga dakin ammah wacce ke kwance tana kallon shirin dadin kowa,

"Ke, yaushe kika shigo kuwa"

Zama tayi saman rug dake gaban gadon ammah tana kallon tv din itama,

"Ammah na dan jimafa ai na leko kina bayi"

"Ehh ruwa na dan watsa saboda naji garin adaure yake"

"Gaskiya ana sheka zafi"

Har suka gama hirarsu tatashi tafita ammah bata yimata maganar ansaka ranar bikinta ba har saida Abba yadawo da daddare sannan yakirata yake fada mata, rasa wanne yanayi ta tsinci kanta tayi farin ciki ko bakin ciki? Share fahad din tayi bata nemeshi ba haka shima bai kirata ba. Har akayi kwana biyu basu magantu ba ita gaba daya haushinsa takeji kamar ba itace ta kawoshi ba shikuma barinta yayi ta sarara gashi hidindimu sun fara yimasa yawa saboda tun washe garin ranar da aka sanya ranar auren nan baba yakira yayun fahad din kamar yadda yafada suka tattauna dangane da yadda za ayi akan

Please Login or Register in order to submit comment