Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
kafadi ba kwari kuma wlh baxantaba sonkaba Tafuce da gudu Dakyar ya iya kaikansa daki yana sakin kuka maicike da tuna maraicin sa yaukam yatuna mamansa da babansa yanaji kamar yabisu duniyar duka ta ishe sa Game da Ubaid kuwa Allah ne kadai yasan irin abindaya gama kullawa adaren. BAYAN WATA HUDU Muneeb tunda akasa ranar fujjilat yabar kano yay maiduguri dangin mamansa yakwashe komi nasa dake gidan Abba yabar kano Yau saura sati daya bikin fujjilat idan kaganta ta rame sosai kullum cikin kuncin rai da kunar xuciya basa waya da Ubaid sbda baya daga wayarta daga karshe ya aje layin akasa yadaina amfani dashi har satar hanya tayi taje gidan su amma ummi bata sakar mata fuska ba haka tafuta jiki ba kwari shirye shiryen biki kuwa kowanne bangare yakam kama ranar laraba akakawo lefe kamu yaxama ranar juma ah kenan, hankalin umma baigama tashi ba saidataga uwar duniyar da aka xubo lefen fujjilat akwatu goma sha biyu da key na mota sarkunan gwal guda shida abin ba acewa komi umma kamar tai hauka haka taxama agidan. Kubrah ce takira umma awaya take sanar mata duk abindaya faru kamin kace me umma tayanke jiki tafadi tamkar gawa Shamsiyya takalli fujjilat Amarya bakya laifi Fujjilat taharareta Wlh kuwa wannan karon wannan amaryar xatai laifi don xata kashe ango kota kashe kanta Dawani lafiyayyen mari Shamsiyya takasheta tana mikewa Ke mahaukaciya ce yau natabbatar menene aibin Nu'uman me yayimiki wlh kinyi mummunar furuci kuma sainafadawa mami don nasan duk macen datai irin wannan furucin saita aikata dama abin damata suke yi kenan yanxu kashe maxa au dama kema kinacikinsu inna nillahi wa inna ilaihir raji un Saikuma tasa kuka Fujjilat kinxama abindakika xama yanxu miyasa xaki maidakanki haka Tamike Aa dan Allah Shamsiyya kiyi hakuri kawai nafadane amma ba iya aikatawa xan ba wlh Hummm bakisan xuciya bane fujjilat dakinsanta dakin amsa da eh xaki aikata amma yanxu taimako daya xanmiki naje natabbatar wa dasu mami sbda karkije ki hallaka mutum koki hallaka kanki tunda taurin kankin yahanki ki fahimci gaskiya. Dan Allah karki fadawa mami najanye xan yi hakuri nakoyawa kaina sonsa amma rabona da Nu'uman tunkafin asamana rana shima yadaina sona yadaina kauna ta haka xa ayi auren ba ango. Wannan mai sauki ne yakyaleki ne kihuce sbda kin nunamasa kiri kiri bakyasonsa wasu maxan kuma kinsansu da xuciya. Yaya shirye shiryen bikin Fujjilat ta karyar dakai gefe Humm tohm gashi nan mami natayi, Xandawo gobe saimuga abindaya kamata mu yi, Ok! Bayan tafiyar Shamsiyya daf daxata tsallaka titi Mota yasha gabanta Gamamakinta koda akasauke glass din Aisar ofisa tagani fuskarsa dauke da murmushi Angai da sayyadata Harara ta watsa masa tare da tattaro dik wani fadanta guri daya Kashiga hankalin ka dani gefen rijiya ba wajen wasan yaro bane kai dakanka kasan wannan karnin ba naka Bane Yasake sakin murmushi Daxaki mai da wukar ai, tunda ni bani nakar xoman ba rataya akabani shin koxan samu lokacin ki yau naxo gidanku anjima Aa nace aaa karka sake kaxo domin kuwa wlh mutkar kaxo komi nama kaikajawowa kanka dan iska kawai ko kunya bakaji ba Tabar gun ranta abace lallai Aisar naneman shiga rayuwar ta amma xatai maganinsa Shikuwa dakallo yabita sbda bakaramin birgesa take ba da alama kuma xaisha wahala kafin tasaurari ainihin munufar sa da aiki agabansa. Kafin kubrah takaraso gida mami harta kira likitan gidan yaduba umma banda kuka ba abinda umma take Tanaganin kubrah tarike hannunta suka fada daki mami ta tabe baki tana cigaba da aikace aikacenta. Kince me kubrah dagaske shagon mu na abuja ya kone shikenan fa yanxu muke dashi garin yaya Wlh umma domin kuwa lokacin da wutar takeci saida saif yadauko vidio yaturo min aiyanxu tashi xaki kawai muje magani Ina din kixo ke kije kawai amma ni Alhaji baxai barni ba don doka yasamin satin nan baxanfitaba amma akwai masala mutatrara dukiya min jibga aciki kinsan gidajen nan naki nasayar dasu aka shigo da manyan kayannan dasuka kusa bamu masala don dakyar akasakar mana Bakomi umma Allah yakyauta yanxu saimu amshi kudinmu na hannu Alhaji tasiu bakaku kawai kija jari dasu nikam aure xanyi don ranar alhamis xanje maiduguri nadawo da muneeb baxan iya rayuwa babu shiba Kut! Wlh baki isaba kubrah maganar aure tafuta daga bakinki au ke bama asarar damukeyi kike dubawaba aa aure ne aranki Eh sbda nagaji da sabon gaskiya xan tuba nayi aure kodakwa muneeb baxai aure ni ba Umma hannu tasa aka tana sakin wani karamin kuka Wlh baki isaba nidake naga wanda tahaifi wata dole saikin sake sabon shiri munsamu abin damuka rasa tukunna Haka tayini sokoko magana kwa ita kadai ma yitake daga karshe wayata daga takira Alhaji bakaku akan yaje abuja yaga abindake faruwa ya amsa da tundayaji lbari yanxuma yana hanya, 😘 INA SONKU MASOYAN LITTATTAFAINA GAISUWA MAITARIN YAWA Kinga naji amma fa baxai yuwu ayi kashi mu rababa saidai ko 'yar milion biyun nan nabaki kirage xafi sbda wlh idan kiga irin wahalar ma danasha saikin saramin Alhaji bakaku yakaimaganar yana sake cewa Acikin darenfa nasa wadanda suka sabamin aiki mukaje aka kwashe kayan dake shagon akabar kadan sannan muka sa wutar nakusa konewa sbda bakaramar wuta mukasaba Aikinku yayi kyau ammafa kasan ni nayi maka hanyar safara u harmuka samu wannan arxikin ajikinsu yanxu kuma da milion biyu xankare Hajia mamu ikon Allah makirar mace mai fuskar kura. Karki damu xamu game ai awani aikin yanxu idan nagama da wadannan naga ansamu kari akan nadah toh xakiga dori akan wanda nafadamiki Tayi dariya Kokaifa mutumina ainafisu aharkar nan tunda dai duk tamuce ace ba wani ware ko danniya yanxu sakaryar mai takira tace ma ka? Tambaya ta take nasan shagon su na abuja yakama da wuta nace eh anfadamin ina mahanyaar xuwa abujan Suka kyalkyale da dariya harda tafawa Hajia mamu tace Yayi yayi toh inafa sauraronka xankoma yanxu saina jika Shikenan. Tofa anawata gawata inji dan chacha meke faruwa muje dai mugani amsar nagaba MAI DUGURI. Tunda Muneeb yakoma can haka aikinsama yasamu trnsf gidan kanin babarsa yake sunji dadi sosai daya dawo cikin su kuma har yau yaki fadar me akayi masa har kawu isa yahakura da tambayar sa Kawu isa matarsa daya Aliya yaranta hudu babbar itace mohini sunan ta aysha sanda tana yarinya ne suna kallon india film suka ga wani film Mohini yarinyar cikin film din tayi jarumta sosai shikenan tace ita sunan ta aysha mohini tun anafada da wasa yaxo yaxama yabita sunan har amakaranta iyayenta ne kadai ke kiranta aysha Saikannenta uku ali abvas kamriyya shekarar ta goma sha tara tayi conday harta fara xuwa jami a, Aysha mohini nutsatstsiyar yarinya saidai akwai rawar kai ga iyayi surutu acikinta kamar yakasheta batajurar axauna ayi gumm shiyasa ma kullum tana tare da kawar ta hanifa inbasu da daukar darasi. Lokacin da Muneeb yaxo gidansu time din data fara ganinsa kenan yayi mugun shiga ranta taji sonsa yakewaya kaf ilahirin jikinta batajinxataci gabada kula musab sbda yanxu taga namiji wanda ya isa tasoshi takuma rayu dashi amma matsalar daya ce baida fara ah ko gaidashi tayi ransa abace yake amsawa baya sakarwa kowa fuska agidan inba kawu ko mamansu ba suma daya gama gaisawa dasu xaibar falon ko minti daya baxai karaba balle taga damarsa abin yadameta amma bayadda xatai kuma ita ma ajinta baxai xube ba akansa batajin xata iya furta masa so kodakwa yana da faran faran acikin mutane, Wannan kenan. Kuka take sosai bayan tafiyar malama kasancewar yau akayi kamu tasha lalle saidaukar ido take ga gyara da mami tasa akamata Fujjilat kukan me kikeyi ko har yanxu sokikeyi kitabbatar min bakya kaunar Nu'uman Tana shashsheka tadago kai Mami kigafarceni akan abindaxan fadamiki yanxu Banaki Nu'uman bane saidai nariga danagama son wanda nakeso mami Ubaid kadai nakeji acikin xuciyata duk yadda naso dana manta dashi abin yagagara yataimaka min lokacin danake bukatar taimakon yakuma soni yaban kyakkyawan kulawa tamkar kanwarsa umminsa tadaukeni tamkar 'yarta alhalin basu san kowacece ni ba, tayaya xan iya manta wadanda sukamin wannan alkhairi acikin dan kanin lokaci kamar wannan aa kitaimaka min dan Allah mami Saikuma tasake fashewa dakuka tanafadawa jikin mamin Baki chanja ba daga halnki tun nayarinta kafiyarki tana dayawa kuma abayama taban wahala amma baxanki daukar hakan kaddarar so ba tako wanne yanayi yana xuwa ma mutum don haka kiyi hakuri munriga damun gama magana jibi daurin aure ba fashi ita xuciyar taki kije kikara tirsasata xata amshi xabin namu idan har dagaske kinhaifu 'ya kuma daga cikina kika futo xuwa duniya, Mami takai maganar rai avace tabar dakin Kuka fujjilat tasa mai tsuma xuciya wanda yatada hankalin 'yan bikin sukayo kanta ana bata baki Umma kuwa taji dadi da fujjilat bataso kuma aranta addu ah kawai take Allah yasa afasa auren. Washegari walima akayi ankimtsa amarya cikin kayan ado masu tsada tadan saki rai sbda tafara gane illar taurinkai takuma fuskanchi mami tayi fushi mai tsanani da ita haka Abba ko maganar kirki baya yi da ita sbda tabata masa rai ranar juma ah aka daura aure karfe takwas bayan amarya tasha nasiha daga wurin inna habi da dahdah aka kaita gidanta mami kuwa cewa tayi baxata yimata fadaba sbda bajima takeba taurinkai yamata katutu duk yadda akabata baki ki tayi saicewa tayi kawai Nayafe miki duk abindakika min kibi mijinki umar nin Allah ne wannan tina miki nake nikawai Tana kuka tamkar ta mutu haka aka dauketa sai gidanta. Ko minti talatin bawanda yakara agidan bayan santi da yaba kyawun gidan da 'yan kawo amarya sukayi akadebesu akamaidasu Shamsiyya dama tun yamma kanta ke ciwo sbda kukan datasha narabuwa da aminiyarta shiyasa tabi motocin takoma nanma dakyar fujjilat tasaketa suka tafi akabarta daga ita sai halinta saikuma getman dake bakin get. Mutum biyu ne suka shigo kamar abokan ango getman yatare su me suka fadamasa oho yabasu hanya suka huce daya yashiga dayan yatsaya gurin motarsu dake waje Jin mutum yashigo yasa fujjilat kara kamewa jikin gado tanasakin sabon kuka yau itakam dawa Allah yahadata ko sallama bai iyaba Baby taji ankirata dasunan dashi kadai ke kiranta dashi Dasauri tayaye mayafin kanta Yaaa uu ubb Ta kasa hada sunan sai rawa jikinta da bakinta keyi meyakawosa gidan mijinta kuma ranar farko? Kinyi mamakin ganina ko Yafada yana murmushi Takasa magana sai murgina kai take Karki mamaki baby dama wannan ranar nake jira shiyasa nayi shuru tamkar nahakura ba lokaci ban hanninki muje Make kafadatayi Aa aa yah Ubaid ni nahakura nahakura xanwa iyayena biyayya baxan bar gidan mijina ba kaima kaje Allah yahadaka da wacce tafi alkhairi Yasan haka xaifaru shiyasa yashirya sannan yataho Baki isaba kuma ai yaxama dole kitaso kibini Wlh baka isaba Kafin tarufe baki yawatsa mata hoda. Shine agaba sai abokinsa abdul dake rike da leda babba Ango ango Nu'uman yahade rai Har kasa naji kamar hakan ne Abdul yayi murmushi Hakane mana yaufa amarya nanan tana jiranka ba shakka yaukaima kaxama mu daxaran ankwana an hantse kuma komai yafaru yakare xaku gane annabi yafaku Nu'uman yadanyi murmushi Hala kamanta amarya batason angon nata, ko toh bari kaji nifa baxan saurareta ba harsai mun sai saita kanmu tadawo tana sona koda kwatan wanda nake mata ne toh saina neme hakkin auren nawa amma inba hakaba saita rainani taga ma kamar na auretane saboda jikinta. Hmm Allah yadai daitaku aboki Amin Duk inda Nu'uman yaduba babu ita kaf gidan donhaka daga shi har Abdul sunshiga rudani gun mai gadi yanufa Waye yashigo bayan wadanda suka kawo amarya Nu'uman yatambayi getman akagauce xuffa naketo masa Ranka shidade abokanka mana sune suka xo suka shiga ciki nikuma dama nashiga bandaki bansan sanda suka futaba wlh Wani wawan mari Nu'uman yasauke wa maigadi Kai banxane lusari wlh uban wa yafadamaka inada abokan dahar xan amince musu su shigo min har dakin amarya ta alhalin koni banshigo ba mahaukacine kai kome? Abdul shikenan ansace amarya Abdul yasaki salati suna karasawa da maigadi Ardo Nu'uman yacilla masa harara kafin Abdul ya yunkura Nu'uman yayanke jiki yafadi kira yake Abdul fujjilat waye yadauketa waye wannan xasu cuceni dan Allah kanomin ita Abdul dakyar ya iya lallashinsa suka tafi gidansu mama da Alhaji shafi U najin abindaya faru hankali yatashi kiran Abba Alhaji shafi U yayi awaya yasanar masa kafin goman dare tarufa Nu'uman yayi suma samada biyar sai hospital Aliyu yawuce dashi ga musahna tasa kuka bayadda abba ya iya haka yakira mami yasanar mata nanma gidan yakacame da hayaniyar 'yan biki wadanda basu komaba nagari mai nisa amarya tabata fujjilat wani yasaceta umma bakaramin dadi tajiba Allah yasa baxa aganta ba,. Kimanin sati guda kenan babu fujjilat ba labarin Haisam Abba yake xargi ansa 'yansanda suntsaresa ana tuhumarsa kullum yasha bakar wahala sosai amma kullum amsar daya ce bashi yadauketa ba baisan inda take ba gidan su Ubaid kuwa anje yafi sau goma amma ummi tace batasan ma indayake ba itakanta bayadda suka iya haka 'yan sanda suka mata wasu 'yan tambayoyi game da inda yake xuwa tabasu amsa amma banda guri daya shine garinsu rogo, Ubaid Tafiya maitsayi akayi kafin axo wani tangamemen gida dakansa yasabota akafadarsa yashigar da ita cikin dakin dake dauke da gado da sif harda toleit aciki Yafuta dasafe musalin karfe takwas yadawo lokacin farkawarta kenan tanasakin salati tare da mika ganin inda take ne yadawo da ita hayyacinta sosai tana bin ko ina nadakin da kallo karaf idaninta suka sauka akan Ubaid wanda yashigo yanxu, Barka da tashi. Tamike tana kara murxa idaninta sbda kamar amafarki take ganin abin ina ne nan waya kawota me Ubaid kenufi dani amatsayina na matar wani? Xuciyar ta ke ta jefo mata wannan tambaya amma batada amsar ta yanxu tunda itama batasan komi ba bayan lokacin da aka kaita gidan miji Ubaid yashigo sunacikin magana kuma shikenan taji bacci mai nauyi yadauke ta, Karfa ki wahalar mn dakanki wurin tsauwala tunanin ya akayi kikaxo nan ninakawo ki domin nan yafi cancanta dake mu more rayuwar mu yadda yakamata bawanda yasani bawanda xaisan indakike xankokarin ganin nakwatar miki da hankali kinmanta dagida sbda nasan kinasona banda matsala da wannan fujjilat akwai rayuwar dana shirya mana dake xakiji dadinta Wani kallon mamaki tabisa dashi Abu mafi sauki agareka Ubaid kadaukeni kamaidani gidan mijina da aurena fa yanxu kuma kasani toh wacce irin rayuwa kakeso muyi kaga nifa nahakura kaima ka hakura mana Baxan iyaba wlh babu wanda ya isa yarabamu dake ketawace ni nakine dole murayu tare awata rayuwa mai cike da sanyi da farinciki Dawa? ni? Karya kake wallahi Kabata kabata kabar hanyar Allah dahar kake tunanin akwai wata rayuwa daxa ka iya ginata da matar wani. ya kyalkyale da dariya Hmmm bari nabarki kihuta kici abinchi ki sallah xuwa anjima xandawo. Taja tsaki tana rakasa da harara. Kullum abindake faruwa kenan duk yadda Ubaid yaso daya kusanceta abin yagagara taki yarda yayi lallashi yayi kalaman amma innaa saiyanxu tagane shidin ma maxinaci ne domin agabanta yake shigowa da karuwa sukwanta ko afalone ko adakin daya ajiyeta tarame sosai tarokesa yakaita yagida yaki gawasu kattai daya xuba suna kulada gidan xata futo falo amma banda cikin gida sbda ita tsoron kattan ma takeyi manyane masu jajayen idanu ga karnuka har biyar agidan dai dai da mai aikin gidan namijine shiyake dafamata abinchi da wanki duk da bata chanja kaya sai wata doguwar riga kadai take chanjawa da tarufe jikinta da mayafinta wanda tun wanda aka kaita dakin mijinta dashi. Yauma tare dawata karuwarsa suka shigo tana makale ajikinsa, Afalo suka xube tana tsotsar bakinsa shima shafata yake ta ko ina idaninsa arufe sbda yagama kamuwa anan falon suka cigaba da aikata masha arsu inda fujjilat tatashi dasauri tabar falon idaninta cike da hawaye tayi nadamar sanin Ubaid arayuwarta yau satinta biyu kenan ahannun sa itakanta tanajin yadda jikinta ke wuri sbda bata tayi wanka ba agidan ga kaikayin da jikinta ke mata Tunanin halin da mami xatashiga da Abba shiyafi damunta hala ma ace guduwa tayi tunda tanuna batason auren afili lallai ko tana ruwa Allah yasa sugane saceni akayi ba gudu nayiba babu waya ahannunta sbda randa xa akaitama agida tabar wayar Bakinciki ya ishi fujjilat kukan yau daban nagobe daban afalon kuwa bayan Ubaid yagama xinar sa da maleeka tsohuwar budurwar sa shine silar jefata karuwanci kuma suna tare har yanxu ko wandansa baisa ba yanufi dakin da fujjilat take yana rike da gabansa Kanta yatafi xaifada tamike tare da dumtse idaninta Inna nillahi wa inna ilaihir raji un Menene haka Ubaid bakada hankali xaka shigomin tsirara ko mummunar manufarkace tadawo dakai Kwarai kuma yau wannan kaxar sainasha manta yasin donhaka kikawo kanki tunkan nayi muki yadda saikinga likita Wlh baka isaba kana matsowa inda nake xan soka maka wuka saina yanke fasikar dake jikinka kamutu kowa yahuta mugun mutum mai mummunar dabi a, Kanta yayo dagudu kafin yakaraso tabude kofar ta arce kafin tafuta saidata tsaya ta kullesa acikin dakin saibugu yake amma fujjilat ta fuce kaitsaye waje tanufa tana lekawa tajuyo dasauri sakamakon ganin kattan nan arelan gidan yasa tadawo jikinta kawai rawa yake da kyarma addu ah take Allah yasa yau tabar gidan mugun nan maleeka dake kwance tasha giya tai mankas saisurutai take tana dariya fujjilat tanufota tana kokarin neman mafutar daxata bar gidan nan batare da kattan nan sun gane taba take wani dabara yaxo mata kayan maleeka data hango ayashe rigane doguwa da siket mai tsaga abaya sai mayafi guntu ko dan kwali babu sai wani bakin mayafi karami data daure gashi dasauri fujjilat ta tube kayanta taxira na maleeka wannan bakin dan kwalin tayi likaf dashi tadau mayafin maleekan tayafa tajuya dasauri tabar falon ganin yadda Ubaid yakusa balla kyauren kofar tafuto Allah yataimaketa ma tsakanin falon da farfajiyar gidan da nisa bamai juyo bugun dayake Dafarkon futowar ta mutum biyune akofar dake kallon cikin gidan har xaitare ta dayan yace Yarinyar oga ce fa baka kulada kayan data shigo dasu daxu bane Yayi wani juyi yakoma Ai kasan naxaga bayi lokacin bansanma sun shigo ba Toh ai yakamata ka kula domin akan anty maleeka oga xai iya komi kam Suka sheke da dariya Aikuwa fujjilat tarike mayafinta gam jikinta yasoma rawa dakyar ta iya dai daita kanta sbda tagama tsorata da lamarin Ubaid kam harta karasa bakin get sbda tsinin takalmin maleeka takusa faduwa sbda batasaba amfani da takalmi mai mugun tsayi hakaba plt shouse shine takalmin datake sawa, Get man dasauri yakarasa budemata yana fadin Hajia asauka lfy Daga masa hannu fujjilat tayi kawai tana karasa fucewa saura kadan ta xabga dagudu Aikuwa tanagama futa tasa gudu ko ina gudu take saidata futa titi tasamu nafef Inaxaki hajia Idaninta wuki wuki tace Inane nan ina ne malm Juyowa yayi yakalleta Rogo mana Xaro ido tayi rogo itavama tataba sanin sunan garin ba sai yanxu Kakaini tasha dan Allah OK Kodaya kawota bata da sisi sai hakuri tabasa dayake yaga afurgice take yahakura kawai yatafi abinsa motar dataji anacewa kano ita tahau saikuka take likaf din yajike sosai da hawaye da majina Matar dake kusa da ita tadubeta Yarinya lfy kuwa kike kuka Duban da fujjilat xatakai ga matar saitaga ashe Anna ce babar shamsiyya rike hannunta fujjilat tayi tana xare likaf din Anna nice fujjilat ce Anna taxabura tariketa gam saikace wacce xata gudu Allah da iko yake keko 'yar nan ina kika shiga ake ta nemanki yau sati biyu babuke ba labarinki haba fujjilat kinsan wanne hali xaki jefa maminki kuwa mijinki nacan kwance asibiti shamsiyya ma nacan akwance mami sumanta shida Abba yakusa xaucewa sbda gigitar abin keko kina ina Jin wannan labari yasa fujjilat kara tsinkewa da kuka tana fadin Wlh Anna sace ni Ubaid yayi yakaini gidansa dake nan rogo Anna maigidan gidan Nu'uman shine kadai shedata baguduwa nayiba, Lokacin da Ubaid yaballa kofar yafuto wando yaxira yayo waje yana masifa Tagudu tagudu duk baku da amfani kunxama aikin banxa wlh yanxu duk bugun kofar danakeyi babu wanda yaji don iskanchi kuma inban wulakanchi kuna kallon ta tabar gidan nan Oga hajia ce fa Inji uban wa? Haka maleekan take kamar bulalar kadan kanya, kayanta tasa tafuto tagudu donhaka abaxama anemota duk inda tashiga nafadamuku kufuce oya Yabuga musu tsawa Komawa ciki yayi yasamu maleeka saibacci take hankalin ta kwance bakinta duk yawon barci yadda yabarta tun daxu tsirara haka yanxu ma take wani haushinta ne ya lillibesa don duk ita tajamasa datasa kayanta fujjilat bata dawata dabarar daxatayi don barin gidan Donhaka yayi kwafa yashiga daki yadauko murdediyar waya ta lantarki yadawo kanta tunkarfinsa yafara kilarta saifarkawa tayi taga Ubaid ne kemata wannan dukan gaddin Ehu take tana basa hakuri amma bai saurara mata ba saidaya mata jina jina dakyar take futar da numfashi sannan ya tsallaketa yafuce yana sake sakin kwafa Kuma wlh bani bake kinwa kanki kinjamin mummunar asara kuma kema gashinan kinji ajikinki jaka kawai dabba. Shima gidan yabari afasace yaja motar saura kadan yataka mai gadi badan ya kauce da gudu ba. Tasha suka shiga nema amma babu ita Rumgume mami take da ita tana kuka Abba sai murna yake yana tanbayar ta basu mata komi ba Tace baimata komi ba Duk wani bayani fujjilat tabama 'yan sanda game da Ubaid kuma xasuje sukamasa yau ba sai gobeba Haka shamsiyya murna harda kuka Nu'uman kuwa kodaya kalleta saudaya baikaraba saiya futa mami tadubeta Tashi kije Tamike jiki ba kwari tabisa Yakalleta sama dakasa saiyaji wani ciwo aransa yanxu wannan matar sace nan kuma satinta biyu ahannun saurayinta wanda take so tab kuma tace ba abindaya faru Hmmm dasake Tunanin da Xuciyarsa take kenan idaninsa akanta har yanxu Ganin yana binta dawani. Kallon tuhuma yasa taji duk ta tsargu kunya takamata kasa tayi dakanta nadamar abubuwa datayi masa abaya taxo mata. Shuru yagif ta nawani lokaci kimanin minti 30 kannan batare dayace mata uffan ba yafara tafiya alamun gun motarsa xaija yatafi tadago kai dasauri takallesa kamar xatai magana saikuma hawayen dake cike a idaninta suka shiga xirarowa tanakallo yashige motarsa yana jifanta dawani mugun kallo mai cike da xargi Jan motar yayi yafuce rai abace wani katutun bakin ciki ne yatarar masa acikin xuciya sam yakasa yadda dacewa Ubaid baimata komi ba yadda take nuna soyaayyar Ubaid ma komi yanema agunta xata iyabasa balle tsawon sati biyu suna tare tab wasu hawayen bakinciki ne suka xuba a fuskarsa yadaukesu da babban yatsansa nadama yasunan aurensu kenan badan mami ba xai hakura da ita ne kawai Dakyar yaje gida yana tunani kala kala daga wannan sai wannan Mama da dawowarta kenan itama daga gidan su mamin tadubesa Kaduba dai Nu'uman Allah yayi mana gyadar dogo anga yarinyar nan Allah dai yakyauta Amin kawai yace yanadauke fuskarsa daga barin maman Aa ya kuma naga yanayinka kamar bakajin dadine? Kai dayakamata kayi farin ciki anga matar ka Yagirgixa kai yana dafe fuskar sa Hakane mama Toh me yake kuma damunka ne ehhyee don jikinka naga duk bakwari kaxama kamar maiyin wani tunani karka boyen komi Nu'uman fadamin inji Allah mama bakomi To yayi Allah yamaka albarka gobe munyi dasu xa amarya maka da matarka insha Allahu daki. Mikewa yayi Ok Allah yakaimu Yasakai waje binsa tayi da kallo da mamakin yadda bai nuna farincikin ganin fujjilat ba bayan halin daya shiga lokacin da aka rasata Allah ya dai daita ku Tafada afili. MAI DUGURI. Mohini Jakanta bisa kafada tafuto cikin shirinta namakaranta Na am iya gayyar baki yaufa kekika biyon dole nai hakuri da wannan jawwababben kiran naki Hanifa tayi dariya Yo kece Allah indai xanbiyo miki saikin xaunar dani shiyasa ma kikaga ko ciki naki shigowa inda nashigo Allah ne kadai yasan yaushe xamu mufuto halama kija muyi misn din darasin mu. Mohini takama haba Wooo banda da wannan kinmanta text xamu fara next mon Inakwa xanmanta ke ma sarkin wasa baki manta ba Suka kyalkyale da dariya Mama tanajinsu amma batasa musu baki ba saida sika ce Mam muntafi Adawo lfy Allah yataimaka Amin mam Suka fuce Time din shigowar Muneeb kenan yadawo xaidau wasu takardu daya manta agida Hanifa Yah Muneeb antashi lfy? Can kasan makoshi dakyar maganar ta futo kamar anmasa dolen amsawa Lfy klau saikun dawo Yafada ahade yana saurin shigewa falon, Mohini taja tsaki

Chapter 9 of 12