Join WhatsApp Group Join Telegram Download APK


Share this page
yake Bakaramin xafin shariyar datamasa yajiba ransa abace yakuma daka mata tsawa Badake nake magana ba fujj Cak ta tsaya tana juyowa tadawo gabansa ta tsaya shuru gurin yadauka bawanda yatankawa wani saidataga basarki sai Allah da kuma alama batamata lokaci kawai xaiyi shiyasa yatsaidata sbda shi yagama nasa uxirirrikan, Tadaga kai xatai magana tare da cilla masa harara saikuma suka hada ido Ganin baidaniyyar magana yasa ta fara kokarin fucewa abinta Karki sake kifita agidannan fujjilat kibiyo ni inason magana dake Yanafadan hakan yafice abinsa cike da takunsa nagirma daji daya isa Haushinsa ne yatsaya mata amakokota taja tsaki tana kallon hanyar dayabi domin shiga dakinsa bata falo yabi ba takofar dake wajen relan gidan yashiga tayadda cikin gida baxa asan yadawo ba Batagama tunanin taba wayar Shamsiyya ta shigo dagawa tayi tana cewa Wai kiji dan Allah wani abun takaici Shamsiyya wai mutanen nan me suke nufi dani kowa sai yadauko shirginsa yadoramin Shamsiyya tace Tsaya tsaya fujjilat menene kuma yafara nasan dai ba lfy ba yanxu kifuto kawai kixo dama ke nake jira komenene sai mutattauna shi agidan na mu Hawaye na kokarin xubo mata tace Yanxin kam xantaho domin ko baxan fasa futataba sbda wannan takurar tayi yawa kawai naxo futowa fa yah Muneeb yadakatar dani wai ba inda xani kinga Shamsiyya nifa ko magana bata taba hadani dashi ba tundaya dawo toh mekuma xaisa yashiga hurumina harda wani cewa insamesa dakinsa xai magana dani yaxanyi wai ni Shamsiyya ne ummm,? Gamama kinta saitaji Shamsiyya na dariya Humm karki damu bakomi kije kawai yanxu ni xanxo gobe gidan naku Kina ganin bakomi dai Eh wlh kije ai yayanki ne kuma Muneeb nayarda da hankalin sa kema ki kyautata masa xato Nagode sai anjima bari naje Kofar ta coge tana wasa da gefen hijabinta Fitowa yayi sanye da jallabiyya ash mai haske da alama yadan yi wanka sai kamshi ke tashi ajikinsa kujeru biyu ne akofar yatura mata daya yaja daya yaxauna Have a st Xama tayi tana kara jin xafinsa aranta bakidaya yagama raina mata wayo ma donme xairinka yimata abu isa isa Menene yake faruwa agidan nan Dasauri tadago kai tana kallonsa kafin taikasa dakanta Bangane ba kamar ya ya Kinsan me nake nufi kuma banason ki boye min komi tundana dawo banga mami ba kuma banji komaganarta anayi agidan ba toh sai shekaran jiya naje gidan dada muka gaisa dana tambayeta abindaya ke faruwa saitafara kuka batace min komi ba nasan agunki ne kadai xan iyasamun cikakken labarin abindake faruwa inasauraronki Kwalla fal idaninta tace Meyasa kaxabeni damafi cancantar wacce xakaji wannan bakin labarin abakinta Um um karki kuka banason hakan idan xantakura miki kitashi kawai kije amma karkixabi tafiyar sbda inaganin ko ba komi nacancanci afadamun damuwar gidan nan indai an daukeni dan gida Aa yaya Muneeb daga karshen komi da xakaji daga gareni xanfadamaka ne mami tabata sama da kasa anrasata bansan ina takeba ta mutu kotana raye bawanda yasani sai Allah abinkuma dakasani tun wanda kabari shi kadawo katarar dawanda yafisa Abba baxai chanja ba dada da bahba tun lokacin da aka nemi mami akarasa sika sami Abba akan yabasu ni yaki bayadda basu rokesa ba amma yaki yarda nakoma gurinsu dole suka hakura Hawaye suka sauko daga idanta Kasa yayi dakansa yana jinjinawa jin abubuwan dasukafaru bayanan kamar amafarki Allah yabayyana mami kidaina kukan nan haka yanxu miyasa bakya xuwa makaranta Abba yacireni Miyasa? Shuru tayi tana junjina tayaya xata tunkaresa da maganar yadda umma taimata sharri tasa takara bakin jini a idaninsa Inajinki kinyi shuru fujjilat ke nake sauraro naga kubrah na xuwa kekuma islamiyya kawai kike xuwa itama dayamma meyasa? Bakomi bansan dalili ba Abba yadakatar dani daxuwa Tamike tana danne kukan dake taso mata daga can kasan ranta sbda tuna babban tabon da umma tayi mata wanda har ta mutu baxata taba wanke kanta ba mutkar ba umma ce ta wanke ta ba tahanyar shedawa Abba gaskiyar lamari, Tausayin ta yakamashi ganin yadda take kuka Dan Allah kiyi hakuri natabbata dawannan kukan naki nine sila na tilasta miki biyawa Aa bakomi bari nakarasa maka abinda bakasaniba sbda yakamata kasani tunda akwai tambayar acikin xuciyarka kuma nasan komi dade komu juma saika tanbaye ni tunda kaji yadda Abba yakira ni kaitsaye da sunan wanda duk wanda yaji furicin xaiso karin bayani Watarana dabaxan taba mantawa ba da asuba bayan nayi sallah toh nasaba bana komawa bacci musamman idan mamina ce da aiki xan tsaya nayi breakfast nashirya adani tukunna nakoma daki nadankara baccin ko kadanne kafin mutashi tohm ranar bayan nagama aikin saiga umma tashigo kitchen din hannunta rike da cop din madara freesh milik tamiko min Dan Allah fujjilat dan dan danamin madarar nankiji min ni nasha naji tana wani iri abakina kamar ta samu masala Tohm umma Na amsa nadan kurba nakara sha nabiyu saita amsa nace mata banji komi ba tace watakila bakin natane Tafuce nakoma dakina daniyyar nayi karatu sainaji bacci yakamani idanuna har wani dindintsewa yake Nan nafada katifana nafara sharar bacci banfarkaba saiwajen karfe goma nasafe nafarka atsorace jin yadda bulala ke sauka agadon bayana dadukkan jikina gashi jikina babu kaya fant da bara ne kawai ke tare dani mamaki yarufeni sbda nasan dakayana nakwanta cif harda dankwali amma menene yafaru kuka nake sosai ina ehun neman dauki amma anrasa me taimaka min gamamina atsaye sai hawaye take amma badamar tatanka masa umma nata kumbar baki dakirana karuwar gida ashe makarantar ma idan nafuta karwanci nake tafiya Lafawa yayi dadukan nawa ganin nakasa koda motsa hannu na amma ban suma ba sbda ina iya kallon kowa amma nikadai nasan irin masifar xafin da xugin dajikina yake min wani gardi naga yafito daga bayan labule daga shi sai gajeran wando rigarsa ahannu da dogon wandonsa da gudu yafita Abba ya bisa shima suka xuba dan danan nafahimci abindake faruwa watakara nasaki ina xubewa awurin sumammiya tundaga wannan lokacin nida mami muka kara shiga tsanani da bakincikin gidannan kasancewar Abba yajuya mana baya duka har xuwa lokaci da mami tabata. Wannan shine abindayafaru Naji Allah yakyauta umma batakyauta ba gaskiya abin yayi tsauri dayawa nima baxantaba yadda kin aikataba koda baki ban labarin gaskiyar lamarin ba naji Takallesa dasauri Hmm sbda me kake karfafa xatonka Ina dayakinine akan abindanake karewa karki tsawaita bincike akai kicigaba da hakuri dakomai Allah xaikawo miki sauki tahanyar dabaki yi xatoba kuma da gwaggwaban tukuicin mami bata tagayyara ba saikiga tafada hannu nagari wanda xai xamarmata masalaha Allah yasa hakan xan iya tafiya Ya lumshe ido tamkar mai sonyin bacci Ehh toh amma inkin koma inabukatar tea bayan sallan isha kafin kikwanta bacci Tohm shikenan amma yaya Muneeb dakayi hakuri kakira kubrah awaya saita kawoma Sbda me kikace haka Sbda umma tahanani kusantarka ko kadan tamin worninng akan karnasake wani magana yarinka hadamu kayi hakuri banaki bane Bata da hurimin hanani ko ta sani kuma haka bashine xaisa tahana Allah yin abundaya ga dama ba akanmu kinga ni nasaki don haka inajiranki anjima yatashi tare da shigewa cikin dakinsa Bayan ta idar tasallan isha i tayi addu ar ta kamar yadda tasaba rokon Allah yabayyana mata maminta sannan kuma yadai daita tsakaninta da abbanta tacika da salatin annabi tashafa tagama shirin kwanciya tsafa tabude data harta fara magana dawata kawarsu farra itada Shamsiyya saita tuna maganar Muneeb dasauri tatashi tasa hijabi tanufi kitchin tea tadafa tajuye afls tatafi kaimasa kiran Haisam ne yashigo wayarta kamar baxata dagaba saikuma tadaga Hello tace bayan taji shima yace Hello Inajinka ya dare? Normal amma kirkinki dayawa my fujji Murmushi tadanyi daidai lokacin data karasa kofar dakin Muneeb Haisam kenan me kuma nayi nasan laifi nayi duk lokacin danaji kakirani damai kirki Ehmana yanxu tun yaushe nake miki magana a whatsapp amma kinshare ni yakai sau goma maganar danamiki Hum bangani ba amma xanduba yanxu dai inaxuwa Ta datse wayar tana karasa wa cikin dakin da sallama abakinta kan doguwar kujera yake xaune yana daddana loptop ya amsa ciki ciki batare da yakalleta ba Ajewa tayi tana juyawa Dawa kike waya Haisam ne Harara ya cilla mata yana jan tsaki Jeki amma karki koma daki kiyi waya dare yayi kowaye ba Haisam ba dole ya hakuri dasafe yakira Tohm kawai tace tana fucewa dasauri Ture loptop din yayi daga gabansa afasace saura kadan tafadi kassan tayels din dake malale adakin sai daukar ido yake baisan meke shirin faruwa ba dashi bakidaya yadamu da ita dakuma dikkan abun dayashafeta ga wani dan uban kishinta dake danno masa kai cikin xuciya akan me sone ko duk dan 'yar uwarsa ce kai dasake Yamike yana fara xaxxaga dakin kamar mai neman wani abu 'YAR HANNU NA SHAMSIYYA ADAM YUMNAH Alhaji nafadamasa kamar yadda kace saidai bana tsammanin yaron nan xai je domin kuwa lokacin danake masa maganar baiwar Allahn nan saikaga yadda yadau abin don haka abindaxaifi yanxu kawai shine kafadawa Nu'uman shi nasan baida matsala Toh toh shikenan ai yakyauta bansan menene yake damun Aliyu ba shi yadauki duk wani bare ba mutum ba Allah yakyauta yanxu toh xansamu shi Nu'uman din kafin nafita abangarensu nasheda masa saiku shirya yakaiku Allah yasauketa lfy Amin Alhaji niyanxu babbar damuwata dabaiwar Allahn nan bata magana tunfa da dai muka dawo da ita cikin gidan nan batai magana ba balle musan a ina take amayar da ita Yayi murmushi Alhaji shafi U kenan Hakane dai kam da masala amma yaxa ayi xamujira ta haihu muga ko Allah xaitaimaka bakin yabude kinsan irin wannan fa laraba asirine ko jifa sabda son xuciya irin ta wasu mutanen sai su jefe dan uwansu don son xuciya irin nasu da neman duniya basu san kuma cewa itafa wannan duniyar dasuka samu itace xata ladabtar dasu asannu tadaukesu daf daf daf taisama sai takaisu kololuwar sama sungama shagala da jindadinta tukunna itakuma sai taxame su tiko wlh tallahi laraba ina baki labari irin wannan kayen da duniya takewa bawa irin sane baya moruwa yayi asarar dunuya da lahira kenan kinga kwa me gari ya waya Babu kam amma Alhaji kuwa wannan abu badadi kabata lahiranka akan ka cutar dawani bawa dan uwanka musulmi Allah yatsarkake mana xuciyoyinmu sannan ita ma Allah yabata lfy yarabata dawannan ciki kalau Amin amin toni bari nafita tunda naga ma shiri sainace kuma saikun dawo ko Tai dariya Alhaji kenan hakane mana Allah yabada sa ah yataimaka Amin rangida idan kuma kundawo saiki kirani naji yaya kukayi da likita Tohm shikenan. Cikin shigar farar shadda yake kansama farar hula ce saurayine fari tas mai tsaho kuma ba silili bane yanada kumari fuskarsa xagaye ta ke da kasimba idanunsa fararene kal kal masu girma haka bakinsama da karamine hancinsa tsayayye mai tudu amma ba irin katon hancinnan bane mutum ne mai sanyin hali da rashin magana haka kuma baison surutu yagwamci ya kadai ce guri daya yana game ko kallon ball ko rage aikin office wanda yataho dashi gida shine dah na biyu agurin mahaifansa labara da Alhaji shafi U, Aliyu shine babba saishi Nu'uman da kannansu biyu mata khausar anmata aure danta daya sai muhsana dake makaranta sunada hadinkai sosai kasancewar suntaso acikin tarbiyya da kulawa dakuma soyayyar iyaye balaifi Alhaji shafi U na dakudi daidai shi yana harkar gwangwan yaransa biyu maxan duka sunyi karatu kuma sunsami kwali masu kyau Aliyu dr ne babba kwararre afannin tiyata Nu'uman kuma aiki yake awani compny dake aikin shinkafa kuma yanada matsayi agurin kasancewar sa md ne acompny Karasa sa agogon sa yake yashigo falon Mikewa tayi tare dakama hannun matar dake gefenta wacce itama kanta bata san sunanta ba mikewa itama tayi tana kallonsu kamar yadda kullum hakane ke faruwa Mama antshi lfya? Nu'uman yagaidata Lfy klau kafito toh ai saimu tafi naga bakidaya bajindadin jikin takeba kawai don ba bakin magana ne Ayya sannu Yace yanadaga mata hannu alamun gaisuwa Dagamasa kai tayi kawai tana sakin murmushi Tohm muje mama saina saukeku ahospital din nafice offoffice Tohm Allah dai yayi albarka Nu'uman kaji Yayi murmushi axuciyarsa yace amin amma afili baikuma cewa komi ba harsuka futa yadaukesu Bayan kwana goma sha biyu mami tahaifi danta santalele gwanin kyau murna agurin labara ba acewa komi muhsana kuwa saikiran kawayen ta take tanafada musu tayi kani bayan kwana bakwai akayi suna Alhaji yayanka ma jarari raguna biyu yaradamasa suna jaleel itadai mami binsu kawai take da ido sbda badamar magana kuma takasa tuna komai game da rayuwarta nabaya baya n suna saisuka koma kiranta da maman jaleel Nu'uman nason jaleel sosai tundaya fara wayo yake tare dashi kodayaushe daxarar yadawo gida wajen mami xaiwuce yagaidata ita kamar kullum dagamasa hannu xatai tana murmushi saita dauko jaleel tabasa yafuto yay tamasa wasa shikuma yana wangale baki dayake yanxu watansa shida bakaramin so Nu'uman yake yiwa jaleel ba ya shaku dashi sosai,. 'YAR HANNU NA SHAMSIYYA ADAM YUMNAh Aikina kawai nakeyi akitchin abincin dare nake kokarin ganin nakammala sbda nasamu lokacin xama nayi bitar karatuna na islamiyya sakamakon yadda masabaka ke dosoma kuma inafatan naxo ta daya in Allah ya yarda Karar wayanane yakatse min tunanin danake naduba Haisam nagani sunan yabayyana goge hannuna nayi da dosta ina daga wayan Kina ina ne nashigo gidan banganki falo ba Humm bana nan. nace kawai ina datse wayar sbda banason alakata da haisam tacigaba da wanxuwa tunda har yataba furta min soyayya da alama rayuwata yake son shiga duka kuma ba abune mai yuwuwa ba Inuwa datagani akanta yasa tadago kai haisam ne tsaye hannayensa harde asaman kirjinsa yana kallonta tunsanda yakira ta awayan yana bakin kitchen din baikarasa shugowa ba saiyanxu Sunkuyar dakai tayi kasa tana ture salad in datake yanka wa Me nayi miki wai dan Allah idan wani abun nake miki wanda bakya so kifadamin nagyara amma why not, kwana biyu duk kincanja min kuma sai wasan buya kike dani Idaninta cike da hawaye tadago takallesa Ba abindaka min haisam kawai xanjanye halakan dake tsakanina dakai ne. What! kanme? menene hujjarki ko wayasaki don wannan ba tunaninki bane Bakomi kuma bawanda yasani nikadai naxauna natauna da xuciyata nayanke wannan hukuncin sakamakon kuma shine wannan kayi hakuri haisam dole karabu dani kodakwa bakaso Dakata! Na fahimci inda kika dosa kuma nasan mexanyi akai domin kuwa baki isa kishiga xuciyata kuma kifuta ba donhaka kisan mafita akan abinda xanyi din Yafuce afasace tamkar yatashi sama sbda bacin rai Kaitsaye gida yanufa Mama yasamu itakadai afalon tana kallon tashar arewa Aa haisam lafiyanka kuwa xaka shigo ba sallama ranka abace haka Dai dai kafarta yaje yaxube tamkar maishirin kuka Sorry mama wlh kainane kemin ciwo kuma namayi sallamar saidai ko bakiji ba Ahooo Aidanace ko kanasani donkai halinka saikai ga wata zuciya dakake da ita kwata kwata baka iya bacin rai ba toh fadamin tun muna sheda juna nidakai meyake damunka domin kuwa nasan ba ciwon kai kedamunka ba, Mama Allah sh....... Ya isa tunda baxaka kafadamun gaskiya ba shikennan mike jeka kawai Yanasosa kai yafara magana Mama xanfadamiki saidai bansan yadda xakidauki maganar bane shiyasa nake tsoron sanar miki, Kaga haisam kafadamun koma menene sbda ni mahaifiyar kace idan bakafadamun damuwarka ba waxakafadawa Babu dama mama akan fujjilat ne inasonta sosai kuma naga kamar idan nace xanjinkiri wani xai min shigar sauri sainaga tunda mun fahimci juna yakamata manyana suje atsaida magana Shuru tayi nadan wani lokaci kafin tace Tohm banace aa ba domin kuwa dama nasan dawannan maganar taka da fujjilat sbda umman kubra taxo min damaganar cewa taga sai shishshige maka fujjilat take kodayaushe kaje gidan karkaxo kafada tarkon 'YAR HANNU da mutimcinka taso nakira ka naja maka kunne agabanta amma nace aa tabari basai tagani ba idan tatafi xankira ka nayimaka magana nidakai tohm Haisam nikaina ban tabbatar daxargin da akeyiwa fujjilat ba domin kuwa banga xahiri ba donhaka ma ni dakaina baxan dauketa 'YAR HANNU ba amma kasan cewa xai wahala umman kubrah tabar auren nan yayuwu dakai sabda tadauki tsanar duniya ta dorawa fujjilat nima narasa kishi irin nata amma bakomi kasami abbanku kafadamasa muga abin da Allah xaiyi Hakane mama xuciyar tace ahaka nikullum fatana karta dulmiyar dake ga dabi unta sbda basu dakyau tsantsar hassada ce da xalunci ne abun datake Haba dai ai komai lalacewar goma tafi biyar Haisam ashema bakagama sanin wacece mamanka ba Yayi dariya Ahhh aa mama na fuskanci yadda kike son kanwarta ki ne komai tafadamiki jikike Tohm naji sarkin surutu Allah yaxabamana abindayafi alkhairi Amin mama 💛💛💛 Gaban abba take axaune sai wasa take da yatsun hannunta Ahankali tana kallon abba datake ganin kamar yau yadansaki mata fuska gamamakin ta ma saiji tayi yakirata dasunanta wanda tunkafin mahaifiyar tabata rabon dayakira sunan fujjilat. Dasauri ta amsa Na am abba Kinason Haisam? Shuruuu tayi nawani lokaci har sai dayasake magana rufe fuskarta tayi domin kuwa batada amsar bawa Abba Haisam ba sa an rayuwar ta bane tayaya xaikawo maganarsu gaban Abba bayan bata tabacewa tanasonshi ba Fujjilat ko bakya sonshi kinfiso kita yawon banxa kinxabarwa kanki rayuwar bin maxako tohm shikenan ai Wani kukane maikarfi yakwace mata dasauri takara xubewa kasa tana sakinsa Dan Allah Abba kadaina fadan haka na amince wlh na amince Tatashi dagudu tanufi dakinta tana shan kuka mai cike da takaici datashin hankali yanxu Abba akulli yaumin amatsayin 'YAR HANNU yake kallona niko mai xance wa umma amatsayin ta na wacce taimin wannan gaggarumin sharrin Allah kasaka min Allah kafahimtar da Abba na gaskiyar lamarin nan. Bayan kwana hudu aka kawo kudin Haisam da fujjilat tare datsayarda ranar aure wata uku ranar juma ah Farinciki ne afuskar Abba sosai yakarasa shigowa falon umma tamike tana kara kallonsa Nifa Alhaji bangane ba tundaxu kake farinciki harbakinka sukaxo yanxu suntafi naga kadawo cikin gida kana farinciki haka na musamman anya bawani abun alkhairin ne yasamuba ake mana nuni Yasaki dariya tare daxaro bandir biyu na dubu dubu yana ajewa agabanta Kinga kalli nan kudin neman auren fujjilat ne tare da sa ranar aure wata uku yau din nan karkice banfadamiki ba wlh nima abin baxata yaxomin sbda bantaba xaton wannan yarinyar fujjilat xata auruba amatsayin ta na 'YAR HANNU saigashi Allah yarufa min asiri kuma tasamu shiga Umma wacce tunda tafuskanci dagaske yake tai kicin kicin da fuska ranta aturbune takalli Abba Wannan kuma xance ne Alhaji kace wai fujjilat xatai aure aibari kaji adai eriyarnan wlh baxata samu miji ba sbda kowa yasan wacece ita da abunda take aikatawa don haka ka kori maganar nan da Allah kayi taji Humm safara u kenan tohm inaga ko dai ita yayar taki bata fadamiki va amma da mamaki Tsaye tamike tanakiran Wai mekake son cewa ne Alhaji? Kikara hajia lami awaya kimata Allah sanya alkhairi sbda kwa nan xaki samu karin bayani Yamike yafuce dakinsa yana kara danna kudinsa a aljihu Wata dunkuleliyar ashariya ta lailayo ta danna tare da rarimo wayarta saikuma tacillar tana jan hijabin ta dake kan kujera tai waje tana sakin wani xagin mai xafi, Hajia lami dake sallama da kawayenta su biyu dasuka xo mata murna taga shigowar umma afasace dasauri tagama maganar dasu tajuya cikin falon sbda sarai tasan meke tafe da umman kuma xata iya fadin komai agaban mutanen dasuka xo Anty lami menake jine haka me ke shirin faruwa damu ne? Da bangasgataba amma naji kamshin gaskiya afuskar ki dakuma wadancan munafukan matan dasuka futa yanxu shin dagaske ne fujjilat kuka kaiwa kudin aure da Haisam? Hajia lami tatsuke fuska tana kallon umma Eh hakane kuma karki korafin ba agayamiki ba mijinki ne yace abari sai ankawo kinsani Kut Aikuwa kunyi kuskure wlh toh bari kiji nixanfadamiki wannan wlh xaku gane kuskuren dakukayi nan da lokaci kdan haba Anty lami har wanine xaixo yashiga tsakanin mu dake karfa kimanta nikanwarki ce sha kikayi kikabani bamu da wani tsaiko daxaimana shamaki da kayanki danawa ni anawa tinanin duk dayane ashe bahaka bane anxo anmiki dadin baki kinyarda toh niba xanga abindaxai cutar da Haisam inbarshi ba ina gani don haka dole saina yanke duk wata alaka dakuke kokarin kullata atsakanin su sbda baxai auri karuwar gida 'YAR HANNU ba Hajia lami tamike tana karasowa kusa da umma ganin tana xub da hawaye Kiyi hakuri kanwata dan Allah kifuskanci al amarin nan da idon basira kamar yadda na fuskanta inaso intuna miki cewa wannan abin alkhairi ne akeso agina duk wani xargi kinga dole akaudashi sbda gudun raunin da xuciya xata fuskanta banhaka sbda na wafantar da matsayin ki aguna bane aa sai dai inaso kisa aranki haka Allah yatsara kinji karki damu Allah yashirye ta ta daina halinta Wata harara umma ta cillawa umma takasan ido tana xare hannunta daga nata Shikenan Anty lami nasan kunyi nisa sakamakon asirin da tayimuku amma baxan fasa nawa kokarin akaiba harsai na kubutar da Haisam daga tarkonta Tajuya dasauri tana sharar kwalla kamar gaske axahiri kuwa kwallar rashin nasara ce take ganin yadda hajia lami taki aminta da dukkan shirin ta lallai akwai sabon lale agabanta domin kuwa ba a isa anyi auren nan ba indai daranta Tunda abin yafaru nashiga wani hali nakuka da kunchin rayuwa badan komiba saidan yadda rayuwata takara kuntata umma kullum saita mareni akalla ta mare ni arana sau uku ko biyar ga aiki kala kala na wahala wataran har wankin bango take sakani idan taso na galabaita narame nakara tsayi idanuna duk sunfada inka kalleni tamkar wacce natashi ajinya wayanane yashiga kuka inaduba wa naga sunan yaya Muneeb nadaga Kina ina fujji Ina falon farko Ok ina xuwa Yakashe wayar nikuwa cigaba nayi da goge gogena danakeyi daga dakinsa yafuto hsnnunsa dauke da flas in tea Bakya rabo da aiki fujji hala kokina samun nishadi dashine ko Na rausayar da kai gefen sa Hmm yaya Muneeb waye xaice yana samun nishadi da aiki tab saidai kawai yayi sbda yakasance masa dole Yayi dariya kyawawan hakwaransa suka bayyana nayi kasa dakai na ganin xaidago kansa Dole aka miki kenan in nafahimta dai dai tohm nima kuma ganawa aikin tea nake so adafo min pls kikawo min daki xanfita ne yanxu kuma sai wajen tara xan dawo na dare Amsan flas in nayi daga hannunsa ina kallonsa kamar xammagana kuma sainafasa yasha kyau sosai kamar xance xashi nace araina yamin kwarjini Har yatafi yadawo Ummmmm fujji kihada min da lemon tsani guda biyu Tohm nace kawai ina binsa dakallo nayi tsammanin ya tafi ashe yana tsaye daura agogo yake har yagama yaganni ina kallonsa Aaa fujji ko akwai damuwa ne kintsaya Dasauri nadawo dakallona kan kujera ina cewa Aa kawai ina duba labule naga kamar yay dettiy ne anjima sai asake wani Yayi murmushi ganin yadda take abu kamar bataso asani humm lallai abindake damuna ke damun ta Shikenan bari naje Yafice dasauri yana murmushi Xaune muke da Haisam kujeru farare da yamma muna hira sbda yanxu soyayya muke sha sosai duk da banajin sonsa kamar yadda yakamata acikin xuciyata saidai nagama hakurkurtar wa xuciya ta akan sa takuma aminta dashi kadai xai iya xama dani duk da tabban dake jikina Fujjilat kinga yau saura wata biyu fa bikin mu har anci wata daya gaskiya lokaci namun yadda nake so yakamata ace nafara wani kokari naganin nagyara amaryar tawa yadda yakamata Ta sunkui dakai Hm nifa bawani abu daya rage min daya wuce lokacin sbda banida wani shiri bayan wanda kayimana tanadi Yana kallon ta yace Haba amaryar ango kardai kice baki dawani guxiri dakikayi na musamman domin kawowa angonki Humm Haisam ai tunda kaji toh fa haka nace katinafa bani dawani ishashshen gata abikin nan bani dakowa sai Abba shima baya tare dani asahihiyar hanya mahaifiya tamin nisan kewo kakanni anhanani mu amalantarsu, Shamsiyya kawata anyimana iyaka mai tsaho yaya kake ganin jikin da aka daddaure haka xaibada nishadi hummm Haisam gabadaya narasa nau farincikin saura naka kadai yarage mana kuma dirfafarsa rai biyu xai galabaitar dashi ya rusa sa sbda mai sa ah da marar ta basa tarayya wuri daya kaji kagani kuma ahakan ina tausaya maka ranar nadama akan hakan d................. Ya isa fujjilat Yadaga mata hannu tare da tsare ta da idanunsa kamar su fado ransa yayi mugun baci nadama! Nadama akan me? ke? Ko soyayyar danake miki? Ya Allah! Kin kuskurewa xato baxakuma yataba zama haka ba nifa nafi mahaukaci hauka akan sonki baxaki gane haka ba sai wani abu yaxo domin girgixa min soyayyata xakisha

Chapter 2 of 12